Showing 78001 words to 81000 words out of 176868 words
Chapter 27 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel
duk da ya gane halin da ya ke ciki na kasantuwar wata sabuwar nakasa wani irin suya da maƙaƙi da ɗaci zuciyarshi ke mushi to amman ya yarda da wannan sabuwar ƙaddara tasa yasan tun ran gini tun ran zane.
Su kuwa likitovin hakan ya sasu karsashi domin alamace ta nuna cutarsa batayi tsauri ba, alamace ta nuna bai samu damage sosai a jikin ba.
Bayan ya gama yin fitsarin Dr Ayman ya gyara mishi jikinshi ne,
sannan suka fara shirin yi mishi aikin taimakon gaggawa, kafin asan matakin da za'a d'auka, yayinda Dr Aliyu ya fara mishi nasiha cikin taushin lafazi yace.
"Saifuddeen kayi addu'a da fatan Allah ya bamu sa'an aiki, kana kasa a ranka nakasa ba kasawa bace, ka jajircewa zuciyarka, kasa a ranka wannan jarrabawace da ubangiji kan iya jarabtan dukkan bawanshi,
kaga misali a kaina gani bana iya mik'ewa tsaye kuma rana tsaka larurar ta sameni sakamakon had'arin mota,
wanda lokacin ina ganiyar k'uruciya ta, na gama karatu na kenan na fara aiki da mako biyu nayi hatsarin, wanda saida akayi tsawon shekaru biyu ana jinyata kafin na fara tashi zaune da kaina, kumani a lokacinma nakasata ta shafi lafiyata a matsayina na d'a namiji, koda na yarda da k'addara, nasan cewa jarrabawace bayan shekara 8 da faruwar abun lfyar mazan takana ya fara dawowa cikin ikon Allah kafin na cika 10 years da yin had'ari har nayi aure
sai da muka shekara 7 da ita kafin Allah ya bamu ciki a lokacin har na cire tsamnani,
Allah da ikonshi ciki nada wata 5 ya bare.
Nayi matuk'ar shiga damuwa a lokacin ashe abinda bamu saniba, cikin tagwaye ne d'ayan nan bai bareba,
bayan wata hud'u aka haifa min d'iya mace, daga kanta kuma Allah bai bamu waniba,
to nima kenan da nakasata tafi taka in sha Allah kai muna sa ran zaka samu lfy kuma Alhamdulillahi kaga kai matsalar bata shafi mazantakan kaba.
kasa a ranka kana nan da lfyarka."
kai ya rausayar tare da lumshe ido kana ya gyad'a kanshi kai alamar.
"To, ngd."
daga nan suka fara aikinsu ba kama hannun yaro, babu mgna sai nuneneniya, tuk'uru suka duk'ufa kanshi.
A can waje kuwa Ummi aje carbin hannunta tayi kana ta jawo wayarta ta fara karatun qura'an tanayi tana nemawa gudan jinin ta lfy a wurin mai rayawa mai kashewa mai badawa mai hanawa, Allahu wahidun k'ahharar.
Ya Rabi'u kuwa ya d'auki Aunty Mami sun tafi ya maidata gida, dan tayiwa bak'in nasu abinci, kana shi kuwa ya wuce ma'aikatansu.
Ishaq kuwa da Ahmad suna nan zaune suna dakon fitowan doctors dan suji menene matsalar Saifuddeen d'in.
Kana Hayatunddeen kuwa ya tafi Airport dan tarbo Dr Adnan.
Bayan kamar awa biyu suka fito a jere, Dr Ayman yana turawa weelchair d'in da Dr Aliyu ke zaune, yayinda, Dr Batulu ke biye dasu a baya.
Suna fitowa Dr Adnan da suka ise bada jimawa ba, ya mik'e da sauri, ya nufi inda suke hakama Ahmad da Ishaq wanda kunnuwanshi ke mishi jagora duk inda sautin muryarsu da sautin takun Ahmad yake bi, kai baka tab'a cewa makaho bane, domin mutunne mai cikar zarrah da zati kekyawane mai tarin tsabta da yawa sukance suna ɗan kama da Saifuddeen.
cikin girmamawa Dr Adnan ya d'an rusuno ya bawa Dr Aliyu hannu tare da cewa.
"Barka da hantsi sir."
cikin kula da dottaku Dr Aliyu yayi murmushi irin nasu na manyan doctors kana yace.
"Barka dai Adnan ashe har ka iso, ya hanya."
"Alhamdulillahi ya aiki?." Adnan yace yana bin bayansu shida Ishaq da Ahmad suka shiga tamfatsetsen office d'in Dr Aliyun.
Ummi kuwa addu'a tayi kana ta kife wayar bisa cinyarta,
ido ta zuwaba Hayatuddeen dake tsaye gaban Dr Batulu yana neman a barshi ya shiga yaga d'an uwan nashi.
cikin kula tace.
"Kayi hak'uri bayan mun gama aikin bashi taimakon gaggawa an mishi allurar bacci so ana buk'atar ya huta."
sai ta kuma matso gaban Ummi da idanunta suka cika da hawaye,
ganin tazo gabanta Ummi tace.
"Dan Allah Dr ki gaya min halin da yake ciki? koda baya rayene kada ki boye min, tunda abinnnan ya farufa bangashi ba sai dai in haggoshi daga nesa, ke uwace kinsan abinda uwa kanji in makamancin wannan ya faru da d'anta please me ya sameshi?."
a hankali Dr Batulu ta zauna gefenta kana ta dafa kafad'arta tare da cewa.
"Abinda ma muke zaton zaiyi tsanani sai muka sameshi da sauk'i,
Saifuddeen bai mutuba yana raye kuma insha Allah da yamma ni da kaina zan shigar dake inda yake, kafin nan ya farka zaki ganshi ya ganki kuyi mgna dashi, yanzu dai da ku koma gida domin nan akwai masu kula dashi.
wadanda Dr Aliyu ya tanatar su zasu mishi komai,
sannan batun abinci ma karku damu akwai d'iyar Dr d'in duk abinda za'a bashi damar ci ita zata shirya mishi komai.
Yanzu kuje gida da yamma Ku dawo,zaku ganshi kuma Dr Aliyu zai gaya muku duk abinda ke damushi da matakin daya kamata ku dauka dama yadda zaku kula dashi."
sosai Ummi ta gamsu da bayananta kana taji sanyi a ranta, haka yasa tace.
"To ba matsala ngd matuk'a Dr in sha zanyita addu'a zamu koma biyar na yamma zamu juyo."
cikin fara samun nitsuwa Hayatuddeen yace,
"Dr zai gane mu ko? numfashi sa ya dai ta ko?."
kai ta gyad'a mishi tare da cewa.
"Sosai ma har magna fa yanayi mana da body language alamun yana gane duk abinda muke cewa."
a tare sukace Alhamdulillahi.
sannan Dr Batulu ta bawa Ummi number ta kan in sun dawo da yamma su nemata.
Su Abban Farida kuwa, da Dr Adnan da Ishaq bayasu shiga sun so Dr Aliyu yayi musu bayanin matsalar Saifuddeen, so amman sai ya basu hak'uri sabida ya gaji yana buk'atan hutu ya dai ce suje da yamma su dawo dukansu yana son ganinsu dan zai musu cikekken bayanin matsalar Saifuddeen d'in da basu shawara da da gaya musu dabarun kula dashi.
dole suka hak'ura kan saida yamman in sun dawo.
Kai tsaye gidan Ya Rabi'u suka wuce dan Ishaq ya k'i su Ahmad da Adnan suje su kama hotel.
A motar da Ya Rabi'u ya bari a hannun Hayatuddeen suka tafi,
amman Ahmad ya karb'i tukin a cewarshi Hayatuddeen d'an koyone bazai yarda ya jasuba,
Ummi na gaba kusa da Ahmad kana Ishaq da Adnan da Hauatudeen suna baya a haka suka tafi.
Aunty Mami kuwa tuni ta shirya musu abinci tasa an gyara BQ ensu.
*A garin Gombawa d'iban fari*
Yau tunda sanyin safiya Zaleeha ta shirya domin zata je kaltingo don zantawa da nakasassun wannan yankin.
Amman har zuwa ƙarfe taƙwas na safiyar ta gaza yin komai, ji takeyi tamkar tayi ta kurma ihu ta faɗi abinda folisawannan suka haneta faɗi tare dayi mata barazana da ranshi,
kukan da takeyi ya sanya ida nunta kumbura sukayi jazir ga wani fitinennen ciwon kai, ya zatayi a duniya ko wacw ƴa in tanada matsala uwarta take fara tinkara ,amman sam Mama itama bayan folisawan tabi.
tafin hannunta tasa ta share hawayenta a karo na barkatai, a hankali ta miƙe kana ta zari car key ɗinta, a falo ta samu Mama a hankali ta gaiseda da muryarta dake disashe, cikin haɗe fuska tace.
"Wato dai bazaki bar koke-koken nan ba ko, so kike sai an gane wani abu ya faru da ke ko?."
Kai ta jinjina cikin sanyi tace.
"Mama ai wani abu kam yama faru, sanadi nane fa akayi mishi komai, ban saniba yana raye ko ya mutu wani hali yake? tun randa abin ya faru da dare washegari naje asibitoci sunfi bakwai babushi ba dalilinshi, ni badan raina da sukayi min barazana da shiba, a a shida yake hannunsu nakeji kar su ƙara cutarmin dashi." ta ƙarishe maganar wasu zafafan hawaye na kwaranyo mata,
ita kuwa Mama kasake tayi tare da cewa.
"eyeh sannu uwarshi harda su wani kada su ƙara cutar miki dashi kamar kece uwarsa ko ƙanwarsa ko matarsa lallai Zaleeha kifa kiyayeni tam!."
tana faɗin haka tayi cikin kitchen, ita kuwa Zaleeha rumtse ido tayi hawayen dake ciki suka silalo kana ta fita ta nufi falon Baba Malam ,bayan sun gaisane ta ɗan gyara zama ciin disashewar murya tace.
"Baba Malam bari in fita zanje gidan Adda Maryam daga nan zanje asibiti dubo wani mara lfy, Baba Malam a sashi a addu'a Allah ya bashi lfy ya kareshi da sharrin masu sharri."
murmushi dottijon yayi tare da cewa,
"To Mamana in sha Allah zan sashi a addu'a Allah ya bashi lfy, kuma in kinje asibitin bashi kaɗai zaki duba ki ɗan zazzagaya ki tuba wasuma dan ki samu ladan dake cikin hakan." kai ta gyaɗa kana tamiƙe tare da sallamanshi ta
tafi.
Tana isa gidan Maryam kaitsaye bedrrom ɗinta ta wuce,
Maryam dake zaune gaban mirror tana kwaliyya ganin Zaleehan ne ya sata juyowa da sauri sai kuma tayi shiru ganin ta zauna ta kife kanta bisa cinya tana kuka mai sanyin sauti,
da sauri ta dawo kusa da ita cikin kaɗuwa tace.
"Meya faru ? Meya saki kuka gaya min dan Allah hankalina ya tashi ,Baba malam ne ba lfy ko ya Ahmad."
kanta ta ɗan nago ta kalli yayar tata cikin kuka tace.
"Ya Aminu yana nanne?."
kai ta jujjuya mata tare da cewa.
"A a ya fita ya kai su Abdul makaranta, amman zai dawo yanzu."
jin haka ta miƙe ta koma bakin ƙofa, rufe ƙofar tayi tare da gyara labulen sannan ta dawo ta zauna cikin kuka ta bawa Maryam labarin tun daga shagala da kallon Saifuddeen da tayi har ta kai ga buge motar Dalla da binsu da sukayi da dukansu da Saiddeen yayi da kuma dukan da suma sukayi mishi.
Gaba ɗaya jikin Maryam rawa da tsuma yakeyi tuni itama hawayen take zubdawa murya na rawa tace.
"Shike nan mun shiga uku Zaleeha Dalla kuma, shike nan sun kashe yaron nan, to ke me kikayi a kai?."
wasu sabbin hawaye ne suka kwaranyo mata kana taci gaba cewa.
"Daga wurin ban dawo gidaba police station name wuce, naje na shigar da ƙara na faɗa musu komai, amman da yake basu da imani ƙasar nan ba'a bin gsky sai suka zagayeni a wurin babban cikin su yace min wai,
na kiyayi kai na na haɗiye wannan maganar kada na kuskura na bari wani yaji koda da wasane,
yace min wai yanzu dai yana ƙarƙashin kulawarsu in banbi umarninsu wallahi zasu kasheshi, kuma nima zasu bawa Dalla adireshina, kuma wai duk wanda yayi yunƙurin ɗaga zancen zasu kasheshi."
kuka sosai taci gaba dayi tare da cewa.
"Kuma sai da suka haɗoni da police ɗinsu guda ɗaya ya kawoni har ƙofar gidanmu, yace min.
Duk abinda zanyi suna bibiyata kada na yarda na kuskura na bar koda alama ɗaya da a gida za'a gane akwai wata matsalar har a kai ga tambayata, muddin nayi yunƙurin zuwa wani police station zasu sanarwa Dalla komai ya tura yaranshi su kasheshi." ɗan zagaitawa tayi tare da cigaba da cewa.
"Wallahi ni ba don raina ba sai dan tseratar da ranshi yasa naketa boye abun a cikin raina har kwana biyu, ina tsiron kada su kasheshi, gashi naje asibitoci da dama na bincika babushi babu dalilinshi, na koma bakin sitadiyon ɗin ya kai sau biyar to wa zan tambaya ,jiya wuni nayi ina yawo, kuma ko yau da safe sun kirani sun gargaɗeni wai bani yar jaridaba in na kuskura maganar nan ta fito to wallahi kasheshk zasuyima suga ta zancen sunce min motata ince ƴan kalarene suka fasamin amman kada in kira sunan Dalla.
Adda Maryam ya zanyi ina zan shiga in ganoshi ina zan saka raina da nasa mu tsira daga sharrin Dalla da yan sandda ya zanyi in bashi kariya koda rabin yadda ya bani kariya ne! bani da konciyar hankali da nitsuwa bana iya bacci bana iya cin abinci, duk da sun gargaɗeni kada fa na sake damuta ta baiyana."
wannan al'amarifa ya firgita tunanin Maryam ya girgizata itama tuni hawayen takeyi sabida rauninta yama fi na Zaleeha cikin tausayawa tace.
"Kin gayawa Baba Malam ne?."
kai ta jijjiga tare da cewa.
"A a ban gaya mishiba kin san Baba Malam muddin na gaya mishi zai tada zancen zai sa Ya Aminu cikin mgnar su kuma zasu iya kasheshi, ni kuma bana son su cutar dashi ina son rayuwarsa fiye da tawa sabida shi Garkuwane magarcine ya ahlinshi zasuji tunda ni da bai sani bama ya zamemin Garkuwa inaga ahlinshi." sai hawaye shar-shar na bin fuskarta a hankali taci gaba da mgna wai dan kar Ya Aminu ya dawo ya jisu.
"Amman dai na gayawa Baba Malam ɗin cewa akwai wani mara lfiya yana buƙatar addu'a,
yace kuma in sha Allah zai sashi a addu'a, Mama kuma dana gaya mata wai ita ni take jiyewa cewa tayi muddin na gayawa wani bata yafe ba,
ni kuma in ban gaya mikibs na damuwar zata iya fasa min zuciya."
cikin sanyi Maryam tace.
"Kinyi dai-dai karki gayawa kowa,
sabida bisa dukkan alamu yana asubiti kuma duk inda yake zasu sani, kinga muddin kika ɗaga mganar suna iya kasheshin,
gatan da zamuyi mishi itace addu'a domin annabi yace addu'a'u saiful muminin mu zama garkuwarshi da addu'o'i in sha Allah bazai basu damar cutar dashi ba, ki dena kuka ki yawaita mishi addu'a kuma kici gaba da zuwa asibitoci, ki kuma koma police station ɗin ki ce su gaya miki asubitin da suka kaishi."
sosai taji daɗin shawarwarin ƴar uwar tata haka anan tayi wonka ta shirya, ta fita daga nan fa tayi ta bin asibitoci duk da anata kiranta wurin aiki,
sai da tayi sallan azahar kafin ta tafi kaltingo domin yin hira da Nakasassun wannan yankin.
Tun k'arfe biyu na rana take cikin garin kaltingo, sai k'arfe hud'u na yamma ta gama tattara rahotanninta,
kana ta kamo hanyar gombe, tana gab da shiga cikin garin taji wayarta na suwa,
ido ta d'an lumshe kana ta bud'e su tare da meda hankalinta kan draving d'in da takeyi,
wanda sanyi A,C da k'amshi ya cika motar kana sautim wak'arnan ta. Soyayyar dake raina bazan sauya ra'ayiba, wacce akewa taken
*Da ƙauna ta biki jiki an komawa wada ƙanwa*
hannu tasa ta k'ara volume d'in gaba d'aya Kasan cewar a gidan radio ensu na vision FM Gombe aka saki wak'ar wanda nanne ma'aikatan da take aiki inda take gabatar da program d'in ta mai taken *Mushsƙata da kuma Babu nakasasshe sai rago* wanda take hira da nakassu dan jin yanayin da suke rayuwa.
Kamar yadda yanzuma aikin ne ya kaita kaltingo wata k'aramar hukumar jihar Gomben.
kai take d'an rausayawa tana bin sautin wak'ar,
tamkar itace ta raira wak'ar, still kuma idanunta zubda zazzafan hawayen da duk sanda ta tuno Saifuddeen sai ta zubdasu, wanda kusan hakan yabi jikinta a cikin kwana biyun nan tayi kukan da itama da kanta batams san adadinshi ba,
taje sitadiyon yafi k'afa takwas hakama taje asibitoci da dama dan ko zata samu lbrinshi,
ganin ba lbri yasa yau da safe taje police station d'in nan amman sai suka nuna basuma san da wannan zancen da take musuba,
kuma abun mmki da tsoro bata ga police officers d'in da ta samu a wannan ranarba ko guda ɗaya, shiyasa gaba ɗaya ta rasa tudun dafawa.
Gudu take tsulawa kamar mai tashi sama, a hankali take bin sautin wak'ar still kuma hawaye na kwaranya a fuskarta har yana d'iga bisa tudun brest d'inta,
fuskarta d'auke da murmushi daya tunzura hawayenta tace.
"Ina kake wanne hali kake ciki me sunanka?."
sai kuma tace.
"Allah ya isanmin bazan yafe musuba, Allah zai saka maka zai taimaka maka fiye da yadda ka taimaka min."
wayarta keta ringing tanaji tana gani bata kula kiranba,
sai yanzu da taji an cire waqar daga can vision d'in ta d'an ja tsaki tare da d'ago woyarta ganin Abdussalam ke kiranta d'an minister, wanda yaketa nacin binta tun last week da suka had'u , Duwa plaza
taje sayan burger,
tsaki ta kuma ja tare da cewa.
"Wannan wanne irin maye ne da baida zuciya, ko uwar me yakeso in mishi da bak'ar fuskarshi kamar an k'ona taya."
aje woyar tayi dai dai lokacin data isa, bakin gate din (Jonopwd) d'in.
tafiyar mai d'an tsawoce kafin ta isa gab da ofishin nasu, dan sai ka wuce farfajiyar court d'in, dake wurin,
ido ta d'an lumshe kana tace kai.
"Ya Habu ka cika naci dan kawai ka bani motarka kaketa nacin kirana kamar bazan dawo ba."
haka nan har yanzu hawayenta sunƙi tsayuwa
sai kuma ta amsa kiran tare da yin kasa da murya tace. "Ya Habu sai yanzu na dawo, kuma yanzu ma haka ina, jonapwd ne."
sai ta kuma bud'e marfin motar kana ta zuro kyawawan k'afafunta woje,
sannan ta kuma yi muryar shogoban da yanzu mai tushe takeyi dan cikin kwana biyun nan ta zama uwa wata lalatacciyar jiniya abi kaɗan tasa kukan da taketa son ɓoye,
to yanzunma hawayen takeyi tare da cewa.
"Kuma sai naje Vision dan gabatar da program na."
A can gefen Ahmad ne ya amshi wayar Habu kana ya kara a kunne tare da gyara zamanshi kana ya rusunar da kai ya kalli mahaifin nasu kana yace.
"Baba malam ke nemanki, yace maza in kiraki ki taho gida."
fitowa tayi daga cikin motar, idanu ta lumshe still hawaye na tsiyaya jin wani sassanyan iska dake ratsa dukkan abin halitta dake wurin, a hankali ta bud'e idanun nata kana ta zuwaba jerin bishiyoyi da tsirran da sukayiwa harabar wurin k'awanya,
a hankali ta fara taku ih zuwa cikin asalin harabar ofishin,
kana cikin fargaba tace.
"Dan Allah Ya Ahmad kace wayata bata shiga, nasan abinda Baba malam ke nemana dashi."
cikin nitsuwa da kamala Ahmad yace.
"Yana ma jinki dan ina gabanshi."
ido ta zazzaro tare da dafe k'irjinta cikin kad'uwa tace.
"Gani nan zuwa."
tana fad'in haka ta katse kiran kana ta k'arisa bakin k'ofar ta shiga danna door bell.
minti d'aya tsakani wani matashi yazo ya bud'e mata k'ofar,
kana ta kusa kai ta shiga wani corridor tafiya kad'an ta bulla cikin wani tamfatsetsen office wanda aka k'awatashi da ababen buk'atar dan adam,
wasu kujerenu ne masu kama da mazaunin lilo ke zagaye da wani babban table na bak'in gilashi wanda yaketa shek'i
kana sai fankoki kusan guda biyar da sukabi layin tsawon table d'in, sai wani babbab firij dake can gefe kana, sai wani d'imemen TV sannan sai na'urar AC gudu biyu da suke fuskantar juna,
sai kuma