Showing 102001 words to 105000 words out of 176868 words

Chapter 35 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

d'an kontar mata hankalin.
Sosai ya kontar mata da hankalin, sannan yayi bacci.

Washe gari bayan sun karya suka sayawa su Ahmad abinda zasuci sannan suka nufi asibitin.
Suna isa doctor na isowa, a tare suka d'anci abincin.
Tuni Dr Adnan kuwa ya kira Dr Acash prasat ya shaida musu suna kusa.

Suna gama woyar ya hangi Divia ta amsa kira sai kuma yaga ta nufi inda yake tare da ce mishi su shiga,
yana shiga suka tattauna da doctorn,
suna gamawa ya fita.

Yana dawowa wurinsu Ahmad yace.
"Har ka fito?."
"Eh na fito ya nuna min sakamakon gwajin da akayi ne,
ya kuma cemin gobe ne zasuyi aiki."

"To Allah ya kaimu." Ahmad ya fad'i yana gyara wuyan rigarshi,
Hayatuddeen kuwa Amin Amin yace tare da ajiye wayarshi kusa da kan Saifuddeen.

Washe gari kuwa k'arfe tara dai-dai na k'asar tasu.
Aka gama shirya Saifuddeen cikin shigar da akewa wad'anda za'ayiwa aiki,
tuni suma Doctors an gama shirya musu komai kayan aiki.

K'arfe goma dai-dai nurses suka shigo suka tura gadon Saifuddeen suka nufi wani corridor mai fad'i, a hankali Hayatuddeen ya bisu da ido da alamun karaya a idanunshi,
ganin haka yasa Ahmad ya jawoshi suka zauna kana ya d'an kontar mishi da hankalin.
Ganin ya d'an nitsune ya kira Ummi yace mishi tofa an shiga aiki ta tayasu da addu'a yana katsewa ya kira bappa Ali ya gaya mishi hakama su Salisu da Warisu duk ya gaya musu.

Shi kuwa Dr Adnan yana tare dasu Dr Acash dan shi a wurinshi kamar samun k'arin ilimi ne ace a gabanshi akayi aikin.

Suna isa d'akin da za'ayi aikin Saifuddeen yayi murmushi ganin Ya Adnan da irin shigar doctors d'insu,
shima Dr Adnan murmushi yayi dan yana jin k'arfin guiwa da karsashi daga ganin lafiyayyun kayayyakin aikinsu,
bugu da k'ari ga Dr Malik Khan shima dashi za'ayi aikin dashi.

Allurar bacci ko ince cire haiyaci sukayiwa Saifuddeen,
bayan sunga yayi lib alamun alluran sunyi aikinsu.

Nanfa suka fara aikinsu baji ba gani,
shiru kakeji ba magana ko tari basayi sai sautin AC da kuma d'an sautin injuna da d'an k'aran ajiye ababen aiki da sukeyi.

Surgery ba sauk'i kusan tsawon awa hud'u sukayi a kanshi,
sannan suka kammala komai,
canza mishi kayan jikinshi sukayi sannan suka canza mushi gado, kana aka turoshi tamkar gawa aka fito dashi,
ta gabansu Ahmad akazo aka wuce dashi,
mik'ewa sukayi suka fita daga wurin baki d'aya,
yayinda tuni su Ahmad suna biye dasu a d'aya,

Wani side dake can gefe suka shiga,
suna shiga wurin suka shiga wani babban parlour dake cike da kekunana da kuma d'an ma dai-daicin pharmacy kuma ga ma'aikata a cike da wurin.
Suna shaga wasu suka taso suka karb'eshi a hannun wad'an nan d'in,
wani d'aki suka shiga dashi dashi,
kuma basu hana su Ahmad shigaba sai dai suna shiga sukaga sun zuge wani k'ofa na glass sun shiga cikin d'an keb'an taccen wurin dake cike da,
na'urori.
Kontar dashi sukayi bisa gadon dake ciki sannan suka k'ara gudun AC tare da gyara mishi konciyarshi,
suna mgna amman su Ahmad bazasu jisuba.
suna gama kimtsashi sukayi d'aura mishi ruwa tare dasa ruwan allurai a ciki,
daga nan suka fito suka zo inda su Ahmad suke,
a nitse suka d'an musu bayanin cewar kada su yawaita hayaniya, kada kuma suce zasu shiga inda yake shida farkawa sai gobe iwar haka,
kada kuma su damu, su zauna na.
kai kawai suka gyad'a cikin gamsuwa da nitsuwa,
kana suka zauna a kujerun dake jere a wurin,
gaba d'aya Hayatuddeen ya kasa nitsuwa sai hawaye yaketa zubdawa da kyar dai Ahmad ke tausasa mishi zuciya.

A can kuwa ana fitar da Saifuddeen aka shigo da wani bature,
shima awa hud'u sukayi suna aiki a kanshi daga nan kuma,
suka firfito sai kuma gobe kasan cewar mutun biyu sukewa aiki kullum.

Suna fitowa Dr Malik da Dr Acash suka nufi can inda aka kontar da Saifuddeen
yayinda Dr Adnan ya bisu a baya,
suna shiga suka k'ara duddubasu da kyau sannan suka fito,
Nan Dr Acash ya kalli Dr Adnan cikin hausa yace.
"Kuje masauk'inku kada ku damu akwai masu kula dashi.
Dan koda kunza baza'a barku ku ganshiba ma'aikatanmu ne zasuyi mishi komai,
sai bayan sati d'aya zaku ganshi."

"To ba matsala Dr."
cewar Adnan kenan,
dole tasa suka koma masauk'insu.

Sai dai kullum zasu zo safe da yamma su ganshi ta cikin glass d'in.

Sosai ma'aikatan wurin suke kula da majinyatansu cikin iyawa da sanin makamar aikinsu,
tunda sun san irin mahaukatan kud'ad'en da suk'e karb'a a hannun 'yan uwan marasa lfy."

Yau kwana uku da yiwa Saifuddeen aiki Dr Acash ya nemi Dr Adnan ya bashi takardar daya rubuta wasu sabbin magunguna kala uku wanda zai shashu tsawon sati ɗaya rak.
Yana fita ya wuce pharmacy koda yaje ya basu takardar suka gaya mishi kud'in maganin kai ya kad'a dan daya lissafa da kud'in Nigeria dubu d'ari huɗu da sattin da biyar ne harda d'ari uku.

Bayan ya saya ne ya bawa masu kula da shi d'in.
Ba b'ata lokaci suka fara bashi mgnin.

Tun randa aka fara bashi magungunan ya fara jin sauk'in nauyin da jikinshi ke mishi.

Randa aka cika sati da mishi aiki kuwa a ranar jirginsu bappa Ali ya iso India daga k'asar saudia.
kasan cewar da asuba suka iso,
kai tsaye masauk'insu Ahmad ya nufa,
saida sukayi breakfast sannan suka nufi asibitin.


Suna shiga Dr Adnan ya kira Dr Acash ya nema musu izinin shiga wurin Saifuddeen,
jin haka yace su jirashi yazo.

Bayan awa biyu ya iso kana shida kanshi ya musu jagora har cikin d'an d'akin glass d'in nan.

Suna shiga duk sukayi...!




By
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:53 PM - Ummi Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

*NAKASA BA KASAWA BACE*


*PAGE 21*


NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇



_09097853276 ta nan zaku turo katin mtn na300 kacal, ko kuma ku turo ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo shaidar biyanki ta wannan no 09097853276_

~Hmmm Daga gobene free page ya ƙare kun cinye alakoronku~


Sukayi saurin k'arasawa gaban gadon da Saifuddeen ke kwance,
gaba d'aya fuskokinsu k'unshe da murmushi ganin yana musu murmushin.
Bappa Ali kuwa hannunshi yasa bisa kanshi yana shafawa tare da fara jero mishi tambayoyi cikin kula yake cewa.
"Saifuddeen ya jikin? Da sauk'i ko? ina ke maka ciwo?."
ido ya lumshe mishi alamun da sauk'i,
Ahmad da Hayatuddeen kuwa ido suka zura mishi ganin gaba d'aya ya rame sai wani fari mai d'aukar hankali da ya k'ara.
Dr Adnan kuwa ido ya zubawa na'urar dake gefen kan Saifuddeen d'in wanda Dr Acash prasat ke kimtsawa,
Dr Malik kuwa hannunshi yasa yana jan yatsun k'afar Saifuddeen sannan ya juyo ya kalli Bappa Ali da ke cikin kid'ima cikin harshen larabci yacewa bappa Ali.
"Ba komai fa da yardar Allah zai samu lfy,
adai tayamu da addu'a in sha Allah zai samu waraka,
kuyi hak'uri komai zaiyi dai-dai amman sai mun hak'ura domin sauk'i a hankali yake samuwa."
kai bappa Ali ya jinjina alamun gamsuwa kana ya juyo da ganinshi kan Dr Adnan dake cewa.
"Yauwa Bappa Ali yanzu mu fita,
dan ba'a son yawanta surutu a kanshi."
Ahmad ne ya motso jikin gadon hannunshi yasa ya shafa fuskar Saifuddeen cikin sanyin lafazi yace.
"In sha Allah zaka samu lfy in Allah ya yarda zamu jure ko wanne wuya zamu kuma dage da addu'a in sha Allah zaka samu lfy."
sai kuma yayi sauri ya juya ya fita dan jin hawayenshi na zubowa.
Da sauri Bappa Ali yabi bayanshi, a wannan wurin suka zauna, shi kuwa
Hayatuddeen a hankali ya bud'e baki cikin sanyi ya kamo hannun Hamman nashi murya can k'asa yace.
"Ummi tace in gaidaka da jiki, Adda Raihana ma tace in gaidaka."
sam baya iya motsa komai na jikinshi shiyasa sai da ido yake musu mgn,
yana son ya d'ago tafin hannunshi ya sharewa Hayatuddeen hawayenshi dake kwaranyowa amman bazai iyaba, hakan ne ya sashi rumtse ido yana mai jin ciwo a duk wani sashi na jikinshi,
ganin haka yasa Dr Adnan yaja Hayatuddeen suka fira.

Bayan fitarsu da kamar 23 minutes su Dr Acash suka fito suma.
Dr Malik yace yana son ganin su da yamma.
to sukace sannan duk suka nufi masauk'insu.

Zaune suke a parlour kowa da abinda ke ranshi,
Dr Adnan ne yayi gyaran murya cikin sanyin sauti yace.
"Bappa Ali munyi yawa anan dole wasunmu su hanzarta komawa gida Nigeria dan zamanmu zai k'ara tada hankalin Ummi,
amman in wasu sun koma sun gaya mata jikin da sauk'i zatafi samun nitsuwa."
gyara zama Bappa Alin yayi tare da cewa.
"Hankali na ya tashi da yanayin jikin Saifuddeen, bana son inyi nesa dashi."
sai dai ko in Ahmad da Hayatuddeen ne zasu koma."
cikin sauri fuska cike da rauni Hayatuddeen yace.
"Bappa Ali in tafi in bar Hamma na kenan?."
shi kuwa Ahmad kai ya jujjuya tare da cewa.
"Kayi hak'uri kawu Ali, komarka nada mahimmanci dan Ummi zatafi gamsuwa da kalamanka, sannan kasuwancinmu yafi buk'atarka akan ni,
kuma kaga shima Ya Adnan ya kusa komawa, in mun tafi yazo shima ya tafi sauran kai d'aya,
bazaka iya d'awainiyar ba,
amman yanzu in kaje ka kwantar musu da hankalin bazai jimaba shima ya Adnan zai komo ya kuma kontar musu hankali ni da Hayatuddeen kuwa zamu kula da komai in munga sauk'in jiki sai nima in koma sai su Ummin suzo su dubashi."
shiru sukayi baki d'aya dan jin ta bakin bappa Ali.
Cikin gamsuwa yace to ba matsala in sha Allah cikin satin nan zan wuce.
sosai Dr Adnan yaji dad'in hakan.

Da yamma Dr Adnan da Bappa Ali suka shirya suka koma cikin asibitin kai tsaye office d'in Dr Malik Khan suka wuce.
Nan suka samu Dr Acash ma a nan bayan sun gaisane Dr Acash ya gyara zamanshi tare da fuskantarsu da kyau cikin nitsuwa yace.
"Jikin Saifuddeen dai da sauk'i sosai, amman akwai buk'atar k'arin kula da jinyarshi,
in da hali nanda wata biyu zuwa uku akwai buk'atar canji asibiti daga nan New Delhi za'a maidaku Mumbai zuwa babban asibitin.
Orthopedic hospital zanyi k'ok'arin hadaku da d'aya daga cikin manyan doctors d'in.
Physiotherapist domin sune suk'eda gwarewa da k'ok'arin farfad'o da aikin lakar jiki ga wad'anda akayiwa aiki dama wanda ba'a samu damar yi musu aikin ba.
To shiyasa nake son turaku garesu in munyi sa'a zai samu sauk'i cikin k'ank'anin lokaci tunda an mishi surgery sannan an sama mishi kular likitocin fisiyo to muna da k'arfin guiwar samun sauk'inshi."
cikin gamsuwa Dr Adnan yace.
"Ba matsala in dai hakan ya kamata ayi duk abinda ya dace kawai."
shima bappa Ali cikin gamsuwa ya gyad'a kai,
sai kuma suka nitsu jin Dr Malik Khan na cewa.
"Alhamdulillahi ko yanzu muna ganin alamun sauk'i sosai a jikinshi alamun aikin da akayi mishi yayi kyau to amman yana da kyau ku kaishi Mumbai d'in domin acan zai samu duk abinda ya dace a sauk'ak'e, likitocin zasu rink'a kula dashi sosai dan canma asibitin mune, munfi zama a canma nan duk wata sa huɗu muke zuwa muyi aiki,
so a can akwai.
Orthopedic surgeon likitocin da suka k'ware a fannin k'ashi, ga kuma neurosurgeon da suka kware fannin k'wak'walwa, to suke kula da masu larurar. So zai samu wadacecciyar kulawa da treatment mai kyau da ink'anci, da taimaka musu wurin movement motsa jiki da da kuma yin exercise a rink'a strengthen muscles d'in manual therapy. koyar dashi duk wani abinda ya dace tare da bashi shawarwari yadda zai kula da kanshi bayan an sallamesh.
Sai dai kam akwai cin kud'i amman in sha Allah zai samu lfy."
cikin gamsuwa Bappa Ali ya kalli Doctors d'in tare da cewa.
"Ba matsala aiyi duk abinda ya dace fatana samun lafiyar d'an d'an uwan na."
murmushi Dr Malik Khan yayi tare da cewa.
"To Alhamdulillahi yanzu dai muna bashi Drugs masu rage mishi symptoms d'in ciwon sosai, kuma Alhamdulillahi yana jin dad'insu, so yana gama shansu zamu yi muku transfer zuwa can d'in."
sosai Dr Malik Khan ya musu cikekken bayanin da zai sama musu nitsuwa har saida yaga hankalin su ya kwanta sannan ya sallamesu suka fita suka tafi.

Daga ranar ba'a sake barinsu sun ganshiba sai bayan kwana hud'u wanda kuma a ranar ne Bappa Ali zai koma gida Nigeria.
Da sanyin safiya suka nufi cikin asibitin bisa jagorancin Dr Malik Khan suka samu suka shiga suka ganshi, kuma Alhamdulillahi sosai suka samu nitsuwa dan sunga alamun d'an sauk'i a jikinshi,
suna fitowa Bappa Ali ya shiga taxi ya nufi airport k'arfe sha d'aya dai-dai jirginsu ya tashi.

Su kuma kai tsaye masauk'insu suka koma.

Bappa Ali kuwa komawarshi ya samawa Ummi nitsuwa sosai dan ya kontar mata hankali ya b'oye mata batun sauyin asibiti ya samu kuma ya hanata tafiyar yafi son sai sun koma Mumbai d'in taje.

Warisu da Mudassir da Bello kuwa suna kula da kasuwancinsu yadda ya kamata.

Bappa Ali ya dawo da kwana biyar Salisu yaje India ya duba jikin abokin nashi kwana biyar yayi ya dawo gida Nigeria shima ya k'ara kontarwa Ummi hankalinta sosai.

Sai dai sunyiwa Ishaq bayanin komai,
yaso yaje sai suka hanashi a kan ya bari sai sun koma Mumbai d'in sai yaje da Ummin dan dole ya hak'ura.

***
Yau watan su Saifuddeen d'aya da kwana goma kwanansu arba'in kenan a can,
kuma yau ne zasu wuce Mumbai tare da jagorancin Dr Acash prasat.

K'arfe biyar dai-dai jirginsu yayi sauk'an ank'ulu a babban filin shige da ficen.
Hilton Mumbai international Airport.

Daga nan Airport d'in kai tsaye asibiti suka wuce.
*Nanavati super speciality hospital*.  
Shine sunan dake liƙe asaman asibitin da akayiwa su Saifuddeen transfer. Asibitine da haɗuwarsa ya zarce misali don ya ƙawatu sosai, komai na cikinsa gwanin burgewa ne, ko ina kakai dubanka zakaganshi ya ƙawatar gwanin ban sha'awa, don sosai haɗuwarsa ya zarce na garin New Delhi.

Mutane ne keta hada-hadan shiga da fice daga cikin asibitin.
Koda suka ƙaraso cikin asibitin ɗaki na musamman aka samawa Saifuddeen tare da taimakon Dr Acash prasat,   Dr.Adnan da Ahmad ne suka ɗaga Saifuddeen daga kan weelchair ɗin da suka turosa akai, kan faffaɗan gadon dake cikin ɗakin wanda yaji lallausan katifa suka shimfiɗesa, ahankali ya maida kyawawan idanunsa ya rufe tare da ɗan sauƙe ajiyar zuciya.  Kafaɗansa Dr.Adnan ya ɗan dafa a hankali, jin an dafa kafaɗansa ya sanyashi buɗe idanunsa ya sauƙesu akan laɓɓan Dr.Adnan,
Dr.Adnan kuwa ganin Saifuddeen na kallonsa ya sanyashi cewa.
"Yajikin naka?" 
Kyakkyawan murmushine ya bayyana akan kyakkyawar fuskarsa, kansa yaɗan jinjina alamar da sauƙi, tare dakai dubansa ga Hayatuddeen dake tsaye ya kafesa da ido, murmushinsa me kyau yayiwa Hayatuddeen tare da miƙo masa hannunsa, ganin haka yasa Hayatudden cikin tsananin ƙaunar da yake yiwa ɗan uwan nasa yataho garesa tare da miƙa masa hannu shima, damƙe hannun Hayatuddeen yayi acikin nasa hannunsa tare da lumshe idanunsa,  sosai yakejin son ƴan uwansa acikin rai da zuciyarsa, tabbas yasan Allah shine gatan kowani bawa, amma kuma yasan duk wani buri da fatan ƴan uwansa akanshi yake, shi musulmine da ya yarda da ƙaddara me kyau ko akasinta, haka kuma yayi imani cewa komai ya faru da bawa muƙaddarine daga Allah,
Sake rufe idanunsa yayi kirif yayinda zara zaran eye lashes ɗinsa suka kwanta luf aƙasan idanunsa, gashin giransa kuwa sai shinning yake kamar wanda aka shafawa mai, uwa uba ga tohon sabon gashi na tattausan sajen da ya fara yiwa fuskarsa k'awanya, sosai fuskarsa tayi fayau da ita hasken fatarsa yasake bayyana, haƙiƙa Saifuddeen kyakkyawane sosai, sannan duk da nakasar dake tare dashi komai nasa abun burgewa ne da so,  ganin kamar yayi bacci ne yasanya Dr.Adnan duban Ahmad da Hayatuddeen cikin kulawa yace.
"Yakamata ace kuje ku nemi masauƙi tunda Dr.Acash yayi mana komai ya kuma sama mana nurses ɗin da zasuna kula dashi, sannan gani ni zan zauna atare dashi."
Jinjina kai Ahmad yayi tare da duban hayatuddeen da har yanzun hanunsa ke cikin na Hamma Saifuddeen ɗinsa. "Mutafi ko Hayatuddeen, naga idanunsa arufe inaga yasamu bacci".
Ahmad yafaɗa yana me kallon Saifuddeen.

Kallon Hamma Saifuddeen ɗin hayatuddeen yayi,cike da tausayin ɗan uwan nasa ya soma yunƙurin zare hannunsa dake cikin nasa,  har acikin ransa yakejin tausayin Hamman nasa, tabbas shikam da ace ana sauya ƙaddara, to da tuni ya sauya ta hammanshi daga mummuna izuwa kyakkyawa.
  Haka Hayatuddeen da Ahmad suka baro cikin asibitin don nemawa kansu masauƙin da zasu zauna,  taxi suka shiga inda suka ce yakaisu hotel wanda yake mafi kusa.

Tafiya kad'an sukayi kana motar ta ratsa cikin Ƙofar katafaren hotel d'in.
Sahar International Mumbai,  mai taxi din ya sauƙesu, hotel ne ƙawatacce me kyaun gaske wanda yake ɗauke da dogon gine gine gwanin burgewa.
Kallon Ahmad Hayatudden yayi bayan sun sauƙa daga taxi ɗin sun biya me taxi ɗin kuɗinsa, cikin yanayi naɗan damuwa yace.
"Ya Ahmad baka ganin wannan hotel ɗin zaiyi tsada da yawa? ka duba kyawunsa fa".
Ɗan jim Ahmad yayi tare da ɗaga kansa yana ƙarewa hotel ɗin kallo, asanyaye yace.
"To Hayatuddeen ya zamuyi, dole haka zamu kama saboda shikaɗaine zai sauƙaƙa mana wahalan zuwa asibiti, kaga idan bashi ba ko ina muka kama sai munyi ta cacan kuɗin transport, kaga kuma wannan ma ƙarin ɗawainiya ne". 
Kai Hayatuddeen ya jinjina cike da gamsuwa da kalaman Ahmad, atare suka jera har zuwa cikin hotel ɗin inda suka tsaya a receiption.  saida sukayi duk wani abun daya dace kana suka biya kuɗi sannan aka basu makulli da kuma nomban ɗakin da suka kama,   tafiya suke suna me dudduba nambobin ɗakunan har suka iso ɗakin dayake da namba dai-dai da wanda aka basu, Ahmad ne

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login