Showing 21001 words to 24000 words out of 176868 words

Chapter 8 - Nakasa Ba Kasawa Bace Book 1 Complete Hausa Novel

muka juya rigingine ya kuma yi mik'a still ba sauyi ajiyan zuciya yaja tare da barin abin a ranshi kana ya fara tasbihi dan ya samu bacci ya saceshi cikin k'ank'anin lokaci kuwa yayi bacci abunshi.

Washe gari kuwa kamar kullum da sassafe suka tafi gombe shida Salisu nan suka wuni kasuwancinsu,
bayan sallan isha suka koma Dukku.

washe gari wanda ana gobe za'a d'au Azumi sabida ana zaton ganin wata yau,
wanda ranar ne kuma Baba bello zai sallami kasuwa sai kuma bayan salla.

Ranar sammako sukayi sosai shida Salisunshi k'arfe bakwai dai-dai na safe suka isa birnin bubayero,
bayan Salisu ya sauk'eshi sai ya tsallaka bakin tashar gombe line,
ya fara d'aukan irin masu kai aike tasha da sanyin safiyan nan.

Shi kuwa Saifuddeen yazo dai-dai mashigar kenan yaga Jabeer ma,
da sauri Jabeer ya iso gabanshi tare da bashi hannu cikin fara'a yace.
"Tab Lallai wannan balaraben dukkun da himma kake wato in junin wani sammako kai a tafe ka kwanako?."
hannu yasa ya d'an bugi k'eyar Jabeer irin ya cika surutu nan.
shi kuwa Jabeer kama hannunshi yayi suka nufi cikin kasuwar da yanzu ake shirin bud'eta sai ya kuma kalli Saifuddeen tare da d'aga mishi gira kana yace.
"Ko dai kudin aure kake nema ne wannan iya sammako haka har ka rigamu mu yan cikin gari,
nima dana fito yanzu yaseen Ya Adamu ne ya matsa wai inzo in kimtsa shagon yau zuwa jibi kayanmu zasu iso zamu fara baza hajar cinikin salla ne."
murmushi ya d'anyi kana ya jinjina mishi hannu alamun mgninka ai.
suna isa shagon Jabeer ya bud'e sannan ya fara kikimtsa wurin,
yayinda Saifuddeen ke taiyashi,
tuni suka kimtsa shagon suka gyara komai yayi ras,
kafin su gama tuni kasuwa ta fara cika duk masu shaguna sun firfito da kayayya kinsu
cikin yin mik'a alamun gajiya.
Jabeer ya kalleshi tare da cewa.
"Yauwa Balarabe jirani bari inzo."
kai ya gyad'a mishi kana ya konta bisa tattausan sallayan daya shimfid'a cikin shagon ga iskan fanka na kad'ashi ido ya lumshe tare da gyara kinciyarshi.
Shi kuwa Jabeer yana fita bakin tashar ya nufa inda wasu masu saida abinci suke,
soyayyan dankali da kwai,
sai gasashiyar kaza ya sai musu kana ya shiga shagon gefen wurin ya saya musu Faro k'ananun roba guda biyu, sai molt,
kana ya juya rik'e da ledojin ya nufi cikin kasuwar.

Bayan ya isa ya tsallaka wani dandamali da akayi wanda yake shamaki tsakanin masu shago da masu sayan kaya,
kusa da Saifuddeen d'in ya zauna bubbud'e musu takardun abincin yayi kana ya kalli Saifuddeen dake konce yanata tab'e baki cikin tsuke fuska yace.
"Ka tashi muyi breakfast."
fuskar ya kuma ya mutsawa tare da jujjuya mishi alamun bazai ciba ya koshi,
ido Jabeer ya tsura mishi domin tabbas yasan wannan d'abi'ace ta fulani yin fulaku wa kowama.
shi kuma Saifuddeen tashi zaune yayi ganin kamar ran Jabeer ya sosu sai ya d'auki ruwa kana ya b'alle marfin sannan ya d'an sha ruwan har kusan rabin robar,
a hankali yayi gyatsa kana ya ajiye goran ruwan sannan ya d'auki na molt,
ya fara k'ok'arin mik'ewa da sauri Jabeer ya rik'o hannunshi kana yace.
"Meyasa ne kake min haka shin baka d'aukeni aboki bako bare in kai matsayin amini."
kai ya jujjuya mishi kana ya zaro bironshi tare da ballan takarda ya rubuta mishi.
"Am so sorry my friend, wlh a k'oshe nake Ummi ta cika min ciki da d'umame yau da kanta taimin dan Adda Rahma taje gidan Goggo Dada can ta kwana,
kana ni bana cin kaza,
shiyasa,
sannan dankalin kuma ba irin suyan da nake so bane akayi shiyasa bazanci ba,
ai dani da kai yanzu mun zarta abokai mun zamma aminai,
ka fahimceni."
yana karantawa yace.
"To gaya min me Kakeso in sayo maka?."
amsar takardar ya kumayi ya juya bayanta kana ya rubuta mishi.
"Am sorry Jabeer ba wai nak'i ci bane haka nan badan wani abu ba because inada wani banzai kyakk'yani wanda ni kaina yana damuna ba ko ina nake iya cin abinciba.
Kaga zansha molt baka tab'a lura daniba haka nake wuni bani cin komai wani lokacin sai dai in had'a molt da pic milk sai insha."
tabbas Jabeer yasan hakane so duk da haka baiji dad'in rashin cin nashiba,
amman dole ya hak'ura dan Saifuddeen da wuya yaci, shi kuwa Saifuddeen tsallaka madandalin yayi kana ya nufi shagonsu Hisham wanda yau cikansa ya zarta na kullum,
bayan sun gaisane yaje ya amshi botikinshi sabida lokacin wasu nata karya kumallonsu so zasu buk'aci ruwa da kayan zak'i.
cikin sa'a kuwa a safiyar yayi ciniki kusan na 3,500
sha d'aya dai-dai ya kuma komawa da nufin k'aro ruwan sai ya samu Baba Bello ya iso yazo wurin yana nemanshi,
haka yasa ya ajiye botikinshi anan shagon su Kabir kana suka juya suka nufi dilan ledodin.

Bayan an gama warewa Baba Bello adadin da yake amsa kullum,
sai aka rubuta sunan Saifuddeen dasa hannun shi dana baba Bello kana akasa kud'in kayan da akabashi ganin yawan kayanne da yawan kud'in yasa Saifuddeen yiwa Dottijon alamun.
"Kayan basuyi yawaba kuwa?."
Murmushi Baba Bello yayi kana ya fara loda ledodin a k'aton kwalin dake bayan kekenshi,
saida ya loda kusan rabin ledodin kana ya hau kekenshi sannan ya kalli Saifuddeen cikin yin kasa da murya yace.
"Kada Ka damu ai zan had'aka da customers d'ina duka,
kaga duka-duka kayan dubu hamsin nake amsa dama,
nakan sa na ishirin da biyar,
in fita inje in rarraba in ya k'are inzo in kuma kwasar rabin.
Yanzu muje duk zamu rabashi sai mu dawo mu debi sauran."
cikin gamsuwa ya gyad'a kai kana yabi bayanshi.
tafiya kad'an suka isa shagon wani mai saida takalma bayan sun gaisa Dottijon nan ya d'ebo banduran leda takwai,
ya bawa Saifuddeen kana ya juyo ya kalli mai shagon tare da cewa.
"Alhaji bala ga Jikana ya fara kawo muku daga yau,
insha Allah kullum zaike kawo muku kamar yadda nakeyi daku sai in Allah ya kaimu bayan salla."
wanda aka kira da alhaji bala kuwa cikin kula ya irgo dubu 4 ya bawa Dottijon kana yace.
"To baba Bello Allah ya kaimu bayan sallan, Allah ya sadamu da al'khairi."
Amin Amin, yace kana suka shige shago na gaba nanma ya basu kaya suka bashi kud'i.
haka dai sukayi tayi har suka gama wanda suka kwason kana suka koma suka kwaso sauran kashi d'ayan.
Kai tsaye shagonsu Jabeer sukaje inda sukace a basu na dubu 5, nanfa Saifuddeen ya basu suka bashi kudin na jiya ya bawa baba bello,
Jabeer nata musu tsiya wai.
"Tab ku dai kam kun more dan ko bamu sayarba ku dai kun sayar."
dariya sukayi kana sukaci gaba dan inda sabo sun saba da shek'iyancin Jabeer.
daga nan suka zagaya har layin masu kayan kitchen nanma shagonsu Hisham suka saya,
sai kuma suka mik'e babban layi har kan shagunan ba miskila,
cikin sa'a suka sameshi shida kanshi bayan baba bello ya mishi bayanin Saifuddeen ya gamsu kana yace.
"To Baba Bello Allah ya taimaka mana,
yanzu ni daga gobe ya rink'a kawo min na 15k dan shaguna na babbar kasuwama za'a rink'a kai musu da na kasuwar mata da shagunan cikin unguwanni dan naku ledodinku suna da kyau, muna jin dad'insu."
shiko Saifuddeen murmushi yakeyi yana ganin darajar mutumin sabida duk inda yaranshi sukayi awu sai ya amshi kwanon awun ya kamfata ya zuba a ledan wanda aka gamawa awun,
yara sai godiya sukeyi.
daga nan suka ci gaba da rabawa har layin masu kayan kolliya.
Wasu na 5k wasu 4k wasu 3k wasuma na 1k wasu ma na 500 yayinda wasu 6k ko 7k kowa dai dai-dai cinikaiyarshi yake karb'a
Koda suka gama sai suka tafi can dilan nasu,
a hankali baba Bello yaja hannunshi suka d'an koma gefe,
kana ya fito da kudin da suka tattaro ya had'a kansu,
sannan ya irga inda ya samu kud'in dubu hamsin da shida ne da d'ari uku.
Gyara zama yayi kana ya ware dubu hamtsin sannan ya kira d'aya daga cikin yaran shagon ya bashi kudin ya irga,
sannan ya d'auko wani babban littafi yaja gud a kan sunan baba bellon tare da rubuta bama binshi ko asi,
sai bayan salla in ya dawo.
Sai kuma yasa sunan Saifuddeen k'asan na Baba bello tare da rubuta .
"Munada kayan dubu hamsin a wurinshi."
sai ya kuma basu littafin sukasa hannu shima yasa hannu daga nan ya koma bakin aikinshi.
Su kuwa su Saifuddeen cikin nitsuwa Baba bello ya kalleshi tare da bashi 2k sannan yace.
"Kaga wannan ribanane na jiya,
ladan yawon da nasha yi cikin rana,
kuma kaima zaka iya samun haka a kullum koma fiye da hakan cikin duk kayan dubu goma ina samun ribar dubu d'aya da dari biyu,
wani lokacin in naga kasuwa bata gudu duk bandir din dubu goma sai inbi dubu d'aya rak kaga kenan duk fakitin dubu d'aya ina bin nera d'ari d'aya kacal ne,
kuma Alhamdulillahi a cinikin da nikeyi dubu hamsin kullum ina samun dubu shida ko biyar in na rage farashi na,
ta iya yiwuwa kai ka samu fiye da haka tunda kai yanzu ana hidiman cinikaiyan salla,
dole masu shaguna suna k'ara sayan leda,
kaga misali yanzu ba mishkila daga sayan na dubu 5 yanzu yace gobe na dubu 15 zaka kai mishi,
kaga Alhamdulillahi kasuwa ta fara a sa'a, dan haka kai gobe kayan dubu 60 zaka amsa,
yanzu zan gayawa shi Alhajin in dai ka buk'aci k'ari to ayi maka."
cikin jin dad'i da tsananin mamaki Saifuddeen yake kallonshi domin jin k'udurar ubangiji.
Mutun nawa ke raina kasuwar leda rashin sanin al'barkan dake cikinta ne yasa haka da yawa raina riba ke wahal da matasanmu da ganin sunfi k'arfin sana'a kaza sai kaza ko a a su sunyi karatu sunfii k'arfin talla a kasuwa sai zaman office.
cikin kurmanci yayiwa baba bello godiya tare fatan al'khairi.
Shi kuwa Baba bello 2k d'in ya kuma bashi tare da cewa.
"Amshi wannan ka sayawa Mamanka sugar ka kai mata taci al'barkacin sana'ata."
Da sauri ya girgiza kanshi alamun a a bazai amsaba ai ya gama mishi komai ma daya bashi aron sana'arshi ba tare daya mishi hasadan abinda zai samuba.
Shiko Dottijon cikin girma da isa yace.
"Bana son musu a tsakaninmu da mahaifinka ne ya baka zaka k'i amsane?
niko da ace Allah yasa inada d'a da na bashi ai bazaik'i amsaba sai daima yace in k'ara mishi dan haka maza karb'i kud'innan."
cikin tsananin ganin darajar Dottijon yasa hannu ya amshi 2k d'in kana ya mishi godiya.
Shi kuwa Baba bello,
ubangidan nasu yayiwa bayanin kan ba mmki Saifuddeen ya nemi k'arin leda.
cikin mutuntaka ogan nasu yace.
"Ba matsala aimu haka mukeso."
daga nan ya sallamesu, kana ya yafito Saifuddeen sannan ya hau kekenshi,
yana janta a hankali kana Saifuddeen na binshi a baya har sukaje bakin titi,
cikin kula ya bawa Saifuddeen hannu da sauri Saifuddeen ya bashi nashi hannun sai kuma ya zuba mishi ido jin ya rik'e mishi hannun cikin bada shawara yace.
"Ita sana'a bata yiwa mutun yawa,
kaga shi leda cikin awa uku duk zaka gama kaiwa kostomominka ka kuma tattara kud'i har ka biya kana ka zare ribarka.
To in dai ka gama da wuri to zakafa iya saida ruwanka d'in in kaga alamun zai saidu,
in kuma Kaga bazai saiduba tofa kada ka zauna banza ka samu sana'ar da zaka had'a dana ledan kafin bayan sallan ka komawa ruwan."
Cikin gamsuwa ya jinjina kai alamun in sha Allah hakan zaiyi.
shi kuwa Dottijon ya jima yana mishi nasiha da rik'o da amana da tattali,
sannan daga bisani sukayi sallama shi dottijon ya kama hanyar gidanshi kana shi kuma Saifuddeen ya koma cikin kasuwa ya d'auki bitikinshi ya kuma saran ruwa.
Koda Jabeer ya ganshi yai ta mishi tsiya wai shine sana'a goma mgnin baccin safe.

Haka dai ranarma ya wuni saida kayan sanyinshi,
saida akayi sallan isha suka kama hanyar dukku wanda tuni anga wotan Ramadan,
gaba d'aya al'ummar annabi gobe za'a tashi da azumi.



Kamar yadda ko wanne gida ke shirin d'aukan azumi hakama gidansu Saifuddeen domin.
bayan yayi wonkane yaje ya samu Umminshi da Adda Rahma da Raihana,
nan ya gayawa Umminshi lamarin kasuwar sai dai bai gaya mata ribar da Dottijon nan ya gwada mishiba don baison ya fad'ad'a burinshi kan ribar gudun kada ya shigar da son zuciya.
Rahma ya kalla wacce ta kawo mishi abinci cikin sanyi tace.
"Yauwa Saifuddeen wannan k'awar Raliyya Salma sun zo d'azu tace wai in gaisheka in ka dawo."
ta k'arishe mgnar tana murmushi da son ganin fuskarshi dan tasan sam Saifuddeen baya shiri da Salma
Shi kuwa yi yayi kamar bai gantaba bare ya gane me take fad'i dama in baya son mgna da mutun haka yakeyi.
Ummi kuwa ido ta zuba musu tana murmushi,
abincin ya d'an tsakura kasancewar shi baida yawan cin abinci.
saida ya d'an gyara zamanshi kana ya kalli Hayatuddeen dake gefenshi tare da mishi tambayar azumi nawa zaiyi?."
cikin d'oki yace.
"30 zanyi ko d'aya bazan shaba."
dariya Ummi tayi jin Raliyya na cewa.
"Ko kuma ko d'aya bazakayi ba ko?."
cikin dariya Rahma tace.
"Ai kam saidai hakan."
shi kuwa Saifuddeen hannun Faruq yaja tare da cemishi shi kuwa nawa zaiyi.
yatsunshi uku na tsakiya ya d'aga alamun zaiyi uku da yake duk sun iya kurmanci.
Raihana kuma tana tsakiyar gida tanata kiciniyar tafasa tea da yin miyar asuba,
miyar dege-dege take musu dan Ummi dubu d'aya ta bada Hayatuddeen ya sayo musu hanta da jan nama,
tofa shine aka gyarashi tayi miyar ganyen albasa da yaji kayan miya dana d'an-d'an dan aji dad'in yin sahur.
koda ta gama tafasa tea d'in da tasa citta da kanumfari,
sai ta d'ura a filas kana miyar kuma ta barshi a tukunyar sai ta dorashi saman kanta sannan taja kitchen d'in ta rufe sai da asuban Rahma zata k'arisa aikin.
tana rufe kitchen d'in taje sukaci gaba da hira,
nan Saifuddeen ya bawa Ummi shawarar a hana Aunty Nina girki dan tana laulayin wani cikin,
to shiyasa yake son a hanata girki su had'a tukunyar,
sosai Ummi taji dad'in haka dan itama taso hakan sabida tasan Bappa Ali mutum ne mai kawaici tana sane cutar mijintane ya medasu basu da wasu yawan kadarori.
koda Saifuddeen ya tashi daga nan k'ofan Bappa Alin ya nufa inda ya samu Aunty Nina tana kiciniyar hura wuta a murhun gawayi yayinda shi kuma bappa Ali,
yake ruggume da Qur'an alamun zai fita masallaci.
nan ya gaya mishi shawarar da suka yanke shida Umminshi.
bawan Allah Bappa Ali sai yake jin kunyar wai shi ya kamata yaci dasu ya gaza sai kuma shima su ciyar dashi,
da fari kamar bazai yardaba to dole dai ya yarda dan Saifuddeen ya kafa ya tsare haka ya hak'uri,
sannan suka kama zance tafsir d'in da zasu fara gobe ya jaddawa Saifuddeen ya shirya dashi za'ake zuwa bayan sun gama mgnane ya fita wurin abokanshi.


Salisu ya samu da Mudasir sai Warisu ganin Saminu baya nanne yasa suka raja'a gidan sarki gidansu Saminun kenan,
a d'akin saminu suka yada zongo sunata hira,
har dai dare ya fara nisa kafin suka fito,
Warisu ya shiga gidansu shima Mudassir yayi hanyar gidansu.
Saifuddeen kuma da Salisu tare suke tafiya dan kusan katangar gidansu d'aya ne.
suna isa bakin masallaci Saifuddeen ya zaro biro kana yayi rubutu a jikin takardar daya b'alla.
"Yauwa Salisu dama inaso in gaya maka an rage balance enka ka rink'a bada dubu biyu duk sati,
sai mu rink'a tasowa biyar dai-dai na yamma kafin a kira magrib kuma mun iso dukku kaga zamuyi bud'a baki a gida kuma zamu dena tafiyan dare,
in kuma gari ya waye in yaso ana fitowa masallaci mu tafi tunda ba batun jiran karyawa."
cikin tsananin jin dad'i Salisu ya ruggumeshi tare da cewa.
"Kai Alhamdulillahi wlh ka kawo shawara mai kyau, amman dubu biyu yayi kad'an gsky zan dai bada 4k tunda du-du du dai awa d'aya da rabine aka rage.
Ngd matuk'a Allah bar zumunci da k'auna my friend."
cikin sanin mutuncin juna ya kuma ce mishi.
"No kai dai kabar 2k d'in ai kaima kanada buk'atun kanka dana iyayenmu."
cikin sanin ya kamata Salisu yace.
"To naji na kuma gode, amman gsky 3k zanke badawa kada ka cemin komai."
jin haka yasa Saifuddeen rubuta.
"To Allah ya musu al'barka."
da haka sukayi sallama,

Koda ya shiga gida tuni su Ummi sunyi bacci acewarsu kada suyi dogon hira su zo su makara.

Shima hakance a wurinshi shiyasa yanayin wonka yayi al'wala yazo yayi konciyarshi.


2:00 Am Ummi ta farka kamar yadda Ummi takeyi ko wanne lokaci in dai cikin Ramadan ne,
kana ta bud'e k'ofa ta fito tsakar gida yayinda iska mai sanyi ke kad'awa, babbar taburma ta shimfid'a kana ta fito da wani d'an madaidaicin cainis carpet amman irin na da fa,
ta shimfid'a bisa taburmar kana ta ajiye hijabinta da carbinta da Qur'an sai lantanta mai wadaceccen haske.
al'wala tayi kana kana taje baki k'ofar d'akinsu Rahma kira d'aya ana biyu Rahma ta amsa.
Itako Ummi tana jin Rahma ta amsa ta koma bisa taburmar ta fara nafila,
Rahma kuwa tana tashi ta tada Raihana Raliyya.
sun jima kafin suka tashi,
suna fitowa duk sukayi al'wala kamar yadda aka sabar musu tun basu kai hakaba,
kana sukazo ko wacce tayi iya nafilar da zata iya daga bisani suka fara karatun Qur'an.
Yayinda tuni Saifuddeen ma ya tashi yazo ya tashi Hayatuddeen sun je bakin k'ofar d'akinshi bisa k'aramar taburma ya shimfid'a musu sallaya,
suka fara nafila bayan sun zauna sun fara tilawa ne ba jimawa Hayatuddeen ya fara gyangyad'i yana rab'awa jikin Hamma Saifuddeen d'in nashi tuni bacci ya sureshi shiko Saifuddeen gyara mishi jinginar yayi kana yaci gaba da tilawarshi.

3:20 Am Rahma tayi addu'a tare da shafawa kana ta mik'e ta cire hijabinta ta ninke ta ajiye gefe sannan ta shiga kitchen ruwan zafi ta d'ora bayan ya tafasa ne ta d'an zuba man gyad'a cikinshi kana ta d'ebo couscous dai-dai misali tazo ta zuba kana ta meda marfin ta rufe,
sanan ta harhad'a kofuna tare da pilet da cokula,
ta fitar taje ta jera bisa babbar taburmar,
kana ta dawo ta d'auki filas d'in duka biyu babban da k'aramin,
sannan ta koma kitchen d'in,
bud'e tukunyar tayi tare da duba couscous d'in yayi lugub yadda akeso kuma yayi wasar-wasar bai kwab'e ba amfanin zuba man gyad'an kenan,
sauk'e tukunyar tayi ta ajeshi gefe sannan ta mik'e ta sauk'o dana miyar ta d'orashi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login