Showing 1 words to 3000 words out of 116366 words

Chapter 1 - Tmw Book 3 Complete Hausa Novel

26 Oct 2025

302

*TMWBK301*


*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/IhAz8h8nRy250ZnGGXwM65


*LAME NIG!*

*KASAITATTUN MATA MUN GAISHE KU*.
*AISHA LAME TA KAWO MUKU DUKKAN NAU'IN KAYAN KWALLIYA*.
*KUNSAN GWANAACE WAJEN BAWA FATA HAKKIN TA*
*KUN TUNA KYUAN FATAR GUDUYO KO?*
*KUN TUNA DAI YADDA BULKACHUWA KE SIYAWA YABI KAYAN KWALLIYA NA ORIFLAME KO?*
*TO KEMA GARZAYO KI ZABI NA KI, KO TA ZABA MIKI WANDA ZAI FI DACEWA DA FATARKI*.
*BA IYA KAYAN ORIFLAME BA KAD'AI.*
*TANA DA PRODUCTS DABAN DABAN MASU KYAU, MASU MASTAKAITAN FARASHI*.
*KU TUNTUBE JIKAR DADAR MARINA A WANNAN LAMBAR 07036662633*.
*ADO DA KAMSHI NE SIRRIN GAYU*


Ina tafe ina hard'ewa kamar zan Fad'i saboda sauri da waige waige, burina kawai na yi nisa da gidansu Assadiq kafin abunda na ke gudu ya faru dani.
Ni dai a sanina babu wanda yaga fita ta sannan har na fara nisa ban ji takun wani na bin bayana ba.
Har na cire mayafina a saman fuskana na saki jiki na fara tafiya ina Duba abun hawan da zan samu ya kaini tasha.
Kamar daga sama naji an kira sunana da karfi

"HASIYA..!"

Gabana ya fad'i ras! Jikina ya fara rawa na kasa juyawa Saboda Tsabar Rude'wan da na yi sai naji kamar Muryan Assadiq.

Tahir bai jira sai Hasiya ta juyo ba ya taka ya sha gabanta, cikin mamaki na Dago ina kallonsa da sakin baki da mamakin me yasa ya Biyo ni?
Kuma daman yaga Lokacin da na fita ne? Sai wata zuciyar ta ce min kila Assadiq ne yaga fitar ki ya kuma aikosa wajen ki.
Sai naji na samu yar salama kad'an sai dai Lokaci d'aya in ka kalleni zaka san ina cikin yanayin Tsoro da Firgici.
Daga sama har kasa ya ke kallona Cikin kallon kaskanci da wulakanci.
Sai na sha jinin jikina na maida kaina kasa ina rawan baki na kasa mgana.
Cikin kaushin Murya Tahir yace"Ki gayamin gaskiya shin da gaske ne har yanzu akwai aure tsskanin ki da Sadiq?
Gabana ya kara bugawa Dam! Da Sauri na Dago ina kallonsa cikin mamakin kalamansa, kara had'e rai ya yi ya na kara kaurara Muryansa yace"Ki gayamin gaskiya in kina so ki Tsira da mutumcinki, in kuma kika yi min karya sai kin raina kanki wlh."
Jikina ya fara rawa na fara kokarin ja da baya, da ya ke yadda muke Tsaye ba wanda zai fahimci wani abu za'a yi Tunanin ya Tsaidani muna magana ne.
Na rasa me zan ce masa Tunda Assadiq bai bani wannan Hurumin ba, Sannan bazan so na zama mai Tona masa asirin da Allah ya Rufa masa ba gwara na bari in za'a ji komai a ji a bakinsa, kila ma zamana da Assadiq ya zo karshe in na fad'i abunda ke Tsakaninmu zai zo ya lalata komai tunda a kalaman Abokinsa na Fahimci shima ya yi Tunanin Assadiq ya sake ni Tuntuni.

Ina cikin wannan Tunanin naji ya Dakamin Tsawa ya na kara fad'in"Kina batamin Lokaci malama ki fad'amin gaskiya ki yi tafiyarki cikin salama in kuma ba haka ba? Umh!"
Ya fad'a ya na wani Cije baki, ganin haka yasa idanuwana suka kawo kwallah cikin rawan baki da na gabban jiki nace"Ba ba. Ba komai a tsakanina da shi."
Kallon da naga ya na yi min ne yasa na kwaso rantsuwa ina fad'in"Wallahi gaskiya na.."

"Karya ki ke fad'amin ba gaskiya ba ne malama."

Kalamansa suka katseni ai sai na yi shuru ina raba idanuwana kamar wacce ta yi karya, duk da daman karyan na yi sai kokarin Danne kukan da ke tasomin na ke yi Kada kukana yasa jama'a su fahimci wani abu su taru faruwar haka kuma daidai ya ke da lalacewar komai a wajena ni Hasiya.
Tabbas yasan karya ta ke yi, domin Sadiq bazai taba gayamasa abunda ba gaskiya ba ne, tunda ya furta yasan akwai wani abu a kasa.
Cikin Daga murya yace"Sadiq ya fad'amin komai akan cewa har yanzu ke matarsa ce, kinga kenan karon Farko kin yi min karya kuma sai da na gargad'eki a kan haka."
Ya fad'a ya na nuna ni da yatsa da Sauri na had'a Hannayena waje d'aya ina fadin"Don Allah ka yi hakuri ka Rufamin asiri ka barni na yi tafiyata."
Da Sauri yace"Zaki tafi yanzu ammh sai kin fad'amin wa ya kawo ki gidan nan? Ki ka kara gayamin karya wannan karon bazan Daga miki kafa ba."
Da Sauri nace"Eh Saliha ce, Saliha ce kawata ita ta gayyaceni."
Cikin mamaki ya ke kallona kafin yace"Saliha? Ta ina?
Cikin Rawan baki nace"Saliha yayar Assadiq wacce ke aure a garin Ibadan"
Cikin Dage gira yace"I see garin ya ya? A ina kuka san juna?
Ina goge hanci na fara bashi Labarin farkon had'uwata da Saliha da kuma Dangin Assadiq a kaduna.
Cikin mamaki yace"Ke yar'uwan mijin Salima ne?
Sai na gyad'a masa kai da Sauri ina goge kwallar da kawo cikin Idanuwana.
Cikin mirmishin Mugunta Tahir yace"Wato in na gane kinsan daman Waye Assadiq ammh duk da haka sai da kika zo domin ganin ma idon ki ko?
Sai na kasa mgana shi kuma ya Cigaba da fad'in"Good. na ji dadin haka gwara da kika zo, ki ka ga abunda zaki kara Fahimtar cewa Sadiq ba Tsaran auran ki ba ne, sannan ki kara gane cewa ba rayuwarku d'aya ke da shi ba."
Ya dakata ya na maida Numfashi kafin ya Daga hannu ya na nuna min gidansu Assadiq lokaci d'aya ya na Fad'in"Kinga wannan gidan? Da duka mutanen da ke cikin shi?
Sai na gyad'a masa kai Kamar wacce ta yi karya , bai damu ba ya cigaba da Fadin"To wannan itace hakikanin gaskiyar Rayuwar Sadiq. wacce kika sani a baya ba ita bace Rayuwarsa wannan rayuwar ta karya ce, ita wannan da kika ganin ma idanuwanki itace Zahirin waye Abubakar Sulaiman Abubakar Shinkafi ina fatan kin gane?

Da Sauri na gyad'a kai na cikin mutuwar jiki da na zuciya.
Shi kuma ya cigaba da fadin"Kinga Iyayensa da Ahalinsa tare da yan'uwansa Uwa uba matarsa, to ina so ki saka a ranki Assadiq din da kika sano a zariya karya ne, Sadiq da kika gani a Gusai shine zahiri, shawara da zan baki guda d'aya ne ki yi nisa da Rayuwarsa domin baki da kofa ballatana Muhalli ki je ki nemi daaidai da ke, daman kuma Daga taimako ne sai kuma abu ya zame masa karfen kafa, Sadiq ya aureki ne Saboda mahaifiyarki ta fad'i Gabansa ta rokesa ta na kuka, ammh bai taba son ki ba, Sultana ce matarsa tun ba yau ba shaidu ne kad'ai ba su shaida ba sai yau, kuma ya yi min alkwarin sakin ki tun a lokacin da zaman mu ya kare a zariya, sannan ya tabbatar min da ya sake ki, ban kuma san me ya faru yanzu naji wani Labari na Dabam ba, to ko ma menene wannan ba shi ba ne a gabana, abunda ke gabana shine ki yi nesa da Rayuwar Sadiq aduk in da ki ke zai aiko miki da Takardan sakin ki"
Ya karishe fad'a ya na kallona, nima Tunda ya fara mgana shi na ke kallo cikin mamakin kalamansa.
Da gaske ya ke yi Assadiq baya so na? Kuma yace daman in ya aureni zai sakeni?
Kamar Tahir yasan abunda na ke Tunani ya fara gayamin yadda suka yi da Assadiq a daran da aka Daura mana aure har zuwa ranar da zasu koma Garinsu bayan sun gama Bautar kasa da ce masa da ya yi ya riga ya Rabu dani bayan ya bani jari mai Tsoka.
Bansan ina hawaye ba, sai da naji saukarsu a saman kumatuna, sai dai daga saman lebena ina mirmishi a raina ina fad'in"Tabbas ya bani jari kyakyawan jari a rayuwata."
Batare da wani Tunani ba na kalli Tahir ina fad'in"Naji shawaran ka, kuma in sha Allahu zan yi amfani da ita nagode."
Da haka na share hawayena da gefen mayafina na rab'a ta gefensa na Cigaba da tafiya, sai da na yi nisa da shi kad'an na tsaida adaidaita na gayamasa tasha zai kai ni yace na Shiga, ina kallon abokin Assadiaq har Adaidaitan da na hau ta fita daga Layin gidan su Sadiq bai bar wajen ba, inaga ya na so yaga tabbacin yin nisa da Rayuwar Assadiq gabadaya.
Muna tafe cikin Adaidaita ina Tuna yadda nazo garin Gusau a jiya ina mai Nadamar me yasa na Biye ma zuciyata na zo?

Har wajen la'asar ina zaune ban samu mafita ba shed'an ne da kuma kishin Assadiq suka Ingizani na kira Saliha nace ta turomim adireshin gani nan zuwa, nan ta ke ko ta turomin ta na mai Farinciki batare da sanin mijina ko yan'uwana ba na shirya tafiya Gusai a gidan mu Maman suhailat kawai na yi ma sallama itama ban ce mata tafiya mai nisa zani ba, sai ita kuma ta yi Tunanin wajen Amma zani har ta na min fad'an na yi yamma, ballatana yadda Rayuwarnan ta lalace na rashin Tsaro.

Sai da na je tasha na hau Motar gusai har mun dau hanya sannan na fara nadama naji kamar na Dawo ammh kuma zuciyata na ingizani zuwa ganin abunda na ke so na gani ko kuma nace na kara samun Tabbaci.
Abunda ya faru dani, yau shine abunda Amma ke ta min gudunsa ta fad'amin kada na matsa da sanin abunda ba'a so na sani ba, in na matsa to zan zo na san abunda zai zama tashin hankali a gareni.
Shiyasa akace abunda Babba ya Hango yaro ko ya hau kan Rimi bazai hango shi ba.
Bansan Lokacin da na fashe da kuka ba, ina tuna Kasadar da na yi sai wajen goma saura na Dare muka iso mota ta lalace mana a funtua sai da aka dad'e sannan aka gyara.
Saliha na ta kirana nace mata muna Hanya, sanda muka shigo gusai na kirata na gayamata sai tace na tsaya a tashan tunda dare ya yi zata zo ta Daukeni.
Sun zo tare da wata itama yayar Assadiq ne tunda suna da yawa naji dai ta na ambatan sunanta da Yaya Saddiqa, sannan kuma inaga ta riga ta fad'a musu ni yar'uwar mijin Salima ne shiyasa suka saukeni Shashen Mama cikin kyakyawan Tarba.
Sai a lokacin naga Salima muka gaisa, yadda ta nuna bata sanni ba, ammh dai ta san Dangin Uban mijinta yan zariya ne.
Saliha ke tafe fad'in ta na da kawa yar'uwan mijin Salima, a kaduna muka had'u ga shi har na zo mata Biki, daga dare zuwa wayewar gari na kara yardan ma kaina Rayuwar Assadiq a zariya karya ce wannan itace Zahirinsa, naga ahalinsa gabadaya na kuma kara tabbatar ma kaina cewa shi d'in dan gata ne kuma ya ci sunansa Magajin gida.

Naga Umma da Abba, na kuma kara yardan ma kaina da zuciyata Assadiq ya yi nisa da Rayuwata kaddara ce ta had'a zaman mu waje D'aya.
Kukan da na ke yi yasa har sai da mai adaidaitan da na ke ciki ya juyo ya na kallona, ni kuma ganin haka yasa na yi Saurin shanye kukana, na koma ina faman goge Hawayena.
Ina Tunanin soyayyar da naga ana nun ma Sultana matar Assadiq, ina da yakinin yadda Suke sonta in Labarina ya bayyana a garesu ba za su taba karb'a na ba har Abada.
Mun zo ta sha ana kiran sallar mangariba ammh ban damu ba gwara komai zai Faru dani ya faru da ni a hanya, da na bari ya faru da ni a gidan su Assadiq.
Allah ya taimakeni na samu motar da ta taso daga Sokoto ta sauke wasu mutane a gusai, shi ne ma samu na shiga muka tashi da wuri, muna tafe ina bayan mota na Rufe rabin Fuskata da mayafi ina ta kuka ni kad'ai kamar raina zai fita ba kuma kukan kome na ke yi ba sai na Soyayyar Assadiq da Tunanin yadda Rayuwata zata kare in dan babu Assadiq a cikinta.
Wayata ta dawo dani hayyacina, ina Dubawa naga Saliha ke kirana Sai na kasa Dauka saboda bansan me zan gayamata ba.
Sai da ta yanke sannan na samu Damar Tura mata sakon ta yi hakuri mijina ya kirani yace bai amince na kara kwana ba, shiyasa na tafi ban mata sallama ba ammh ta yi hakuri.
Ina Tura mata sakon sai na yi kokarin kashe wayar gabadaya.

Sai ga kiran ASSADIQ ba kakkautawa, da ta katse kafin na kashe wayar sai wani kiran ya shigo, sai kawai na maida wayar jaka na Tusa kaina a Tsakanin Cinyoyina ina kuka.
Har muka isa zariya ina jin karan wayata a jaka tana virabtion daman Tun jiya na sakata a silent.
Motar ta yi gudu gaskiya wajen tara da wani abu muna zariya.
Daga tasha na samu mashin sai gida, kowa ya kwanta anguwan ma tsit kamar ba Mutane.
Na lalubo key din dakina a jaka na Bude kofa na shiga, nan falo na watsar da komai na kwanta a kasan Tayels ina kuka kamar wata karamar yarinya.

Halin da ni ke yasa na manta da cikina, sai chan da naji yunwa na mukurkusana na mike na saka Ruwan zafi na sha tea, sannan na Diba na yi wanka na Dauro alwala na Rama Sallar mangariba da Isha'in da suka Kubcemin.
A daran na kwana kuka da neman mafita daga karshe na bi shawaran Tahir na yin nesa da Rayuwar Assadiq a wannan Lokacin.
Na yi tunanin naje gidan Adda Fati sai kuma na fasa ta inda aka hau ta nan ya kamata a sauka.
Tun safe na tashi na fara had'a kayana acikin akwatuna, ina kallon kayan Assadiq ina kuka, ina kallon dakin ina Tuna Momemt din da muka yi tare cikin Farinciki.
Wata zuciyar tace karatun ki fa? Sai ma kara gayama kaina Tunda na Rabu da wanda ya yi min sanadin karatun to miye amfanin karatun a wajena? Babu ya zama Dole na tafi tun kafin abubuwa su zo su faru ba daidai ba.
Sai da na gama had'a kaya na duka, na yi tunanin zan tafi da su na bar wasu, sanda na Dauko wayata Assadiq ya kirani yafi sau arba'in sannan ga sakon sa nan na magiyan na Daga wayarsa na kuma Sauraresa.
Ban bi ta kansa ba Sakon Saliha kawai na Bude ta nuna bata ji dadin na tafi ban yi mata sallama ba.
Sai kuma kiran Safiya Ahmad kila mganar makaranta ne, itama ban bi bayanta ba na kashe wayar gabadaya na turata a cikin jaka.
Ban so na kara kwana a garin zariya ba, a niyyata sai a wajen Amma naje na gayamata garejin da ta yi ko nace kuskuren da Soyayyar da ta ke min yau ga abunda hakan ya janyomin.
Sai dai me? Ciwon kai ya matsamin daman Tunda na tashi da shi na tashi sai ban bi ta kai ba tunda daman na kwana kuka daman na yi Tunanin haka zai faru.
Ina ta karfin hali had'a kayana da kauda wasu, sai kuma zazzabi ya Rufeni, na had'a tea domin na sha Tunda ba ni da kuzarin dafa abinci sai amai komai da naci tundaga jiya sai da na Amayar da shi ba komai acikina sai Kakarim Aman na ke yi ba abunda ke fita acikin cikina.

Wasa wasa kafin Dare zazzabi da kasala da Ciwon kai ya kwantar da ni, sai taruwan miyau a bakina, jikina har ya saki ko sallah sai dai na yi a zaune, haka na kwana na yini cikin wannan Halin su Maman suhailat kuma ba su san dawowata ba, balle su lekani su gani kuma tunda na Dawo ban fita ba, sannan kofata na kulle.
Ba na iya cin komai sai Ruwa shima da naci zan yi amansa, ranar talata da naga zan mutu ne na had'a tea da Ruwan sanyi na sha a falo na yi amansa ban iya tashi naje Tiolet ba.
Jikina gabadaya ya saki duk na Rame sai Idanuwana da baki da Hanci daman gashi komai nawa karami ne ballatana ya had'e da cuta.
Ranar Laraba ina falo kwance saman Tayels kamar ruwa ina maida Numfaashi naji muryan Safiya suna mgana da Ummi.
Ta na ce mata kamar ba na nan fa, na yi tafiya, Safiyan na fadin ta yi ta kiran wayata a kashe.
Gani na yi in na bari Safiya ta bar gidan nan zan mutu acikin Daki ba wanda ya sani.
Da Rarrafe na Rarrafo har kofar daki na Bude lokacin har Safiya ta juya zata tafi, ita kuma Ummi daman da ta fito shanya ta koma Dakinta.
Sai dai Safiya taji ina kiran sunanta cikin Dakushewar murya.
Cikin mamaki da juyo ganina kwance a bakin kofar dakina ina maida numfashi yasa ta nufeni hankalinta tashe ta na kiran sunana.
Cikin firgici tace"Hasiya me ya faru? Ba ki da lafiya ne?
Ta na mgana ta na tab'a jikina da taji kamar wuta.
Miyau na bin gefen bakina nace"Safiya ba ni da lafiya, komai baya zama a cikina sai na yi amansa kamar zan mutu."
Safiya na jin haka ta taikamin na mike muka koma cikin Daki, ita ta Daukomim wata Riga na sauya duk da taga kayana a had'e bata damu ba tunda ance na yi tafiyqa kila na dawo kenan na fara rashin lafiya.

Ta daukomin Hijabi da takalmi na saka ta tambayi jakata na nuna mata ta Dauko harda wayata a ciki, akwai Kudi a hannuna sannan ina da shi a banki, daman Akwai Atm aciki Tana Rirrikeni dani muka fito ita ta kulle Dakin nan muka had'u da maman Sulahait ta na ganina ta fara salati ta na fadin"Na shige su Hasiya daman kin dawo? Baki da lafiya ne naga kin dashe kin yi uban fari kamar wata mai yaron ciki?
Ni dai halin da na ke ciki bai barni nayi mgana ba Safiya ce ke fad'amata na dawo kila Ciwon ya kwantar da ni, Sai ta Fara fad'an ana zaman makota kuma sai na yi shuru ban iya kiran kowa ba.
To ni Allah na Tuba ina cikin wani yanayin da ba na iya gane komai ma da komai, Safiya na rikeni da ni muka fita bakin titi muka samu adaidaita, muka hau ta tambayeni wani asibiti muke zuwa nace mata ta kaini kowanne, sai tace muje asibitin musulmi akwai Cousin dinta na aiki a wajen, tun ma muna adaidaitan ta kira ta ta fad'amata sai tace mata tana asibitin sai mun zo.
Saboda ita yasa muna zuwa ba Dadewa naga likita, ita ta yi mana shige da fitan siyan kati da Sauran su, likita na min Tambayoyi ina amsawa daganan ya turani dakin da za'a dibi jinina da Fitsari sannan yace na galabaita zasu Rikeni su gani zuwa yammah.

Ni dai gani nan kwace kamar ruwa a wani office mai Dauke da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login