Showing 81001 words to 84000 words out of 155892 words
d'insa,
Ganin ba abunda zaiyi yanzu a Office d'in yasa ya shiga Motansa ya nufi Gidansun,
Tanaji anbud'e gate ta lek'a ai tana ganin Motan Kb ta daka tsale ta shiga d'akin Mamanta ta fad'a jikinta, bata tab'a k'iransa yazo ya d'auketa yazo akan kariba lokuta dayawama kai tsaye yake cemata shifa ba driver bane, sai dai yasa azo a d'auketa, "Mama Magani yaci wlh gashi ina k'iransa ko 10 minutes baiyiba ya iso,
"Mamnta tana dariya tace "aifa Nasan Boka sam baya wasa indai zaki sakar masa kud'i zaki ga aiki,
Tam bud'e kunnenki da kyau kiji abinda zance miki, ta fad'a tana k'asa da Murya, "karkiyi wasa bawai kawai kisashi ya rabu da Matarshi shikenanba, kud'i ki dinga karb'o mana mak'udan kud'ad'e ahanunsa, saboda bazamuyi sanyaba zamuke yawan zuwa gun Bokannan yana bamu magunguna,
Dai2 Lokacin wayan Nafisa ya hau Ruri, ta d'aga yace
"Ganifa na iso,
"Haba Kb kashigo mana sai kace Gidan Bak'onka? Ok ta fad'a, Sannan ta kashe wayan, a Falo ta sameshi ta zauna Gefe tana Murmushin Kissa, "My Luv ko nimana bakayiba yau da safe why?
Ciki dakewa yace
"Na nimeki mana duba wayan kigani cikin kissa tace Oh nabar wayanma acan Gida, nasan wancan Layin ka k'ira,
Kallonta yayi "Naji kin k'irani any problem? "Nothing kawai inason inkoma can gidanne yasa Nak'iraka ka maidani, sannan Gaskiya nayi missing naka sosai jinayi kaman na shekara bangankaba.
Ya sauk'e ajiyan zuciya cikin yarda da Magananta, "Oh nazaci wani abunne,
"Ba komi barin fito Mu tafi, kar inb'ata maka lokaci my luv, ta mik'e tayi ciki shima mik'ewan yayi
"Kisameni a Mota, ya fad'a atak'aice,
Suna tafiya sai kallonsa takeyi ta gefen ldo aranta tanaga tagama yin sa'a ace ta mallaki Kb ita kad'ai a Duniya.
D'an gyaran Murya tayi tana kallonshi, "Kb Maganan Kud'in pertyn nan,
"Oh bance kiyi list ki fad'amin nawa bane,
"Eh nayi naga zai ci kaman Dubu d'ari 4
D'an jim yayi yana Tunani, sai kuma yace
"Ok Gobe zan turomiki,
"Gud My Husband i luv u Murmushi yayi sam Hakanan kawai yaji bata Burgeshi, Magananma basonyinta yakeba,
suna tafiya tana jansa da Hira, jifa2 yake amsawa, har suka isa,
A bakin gate ya Hango Dijah Ta rako K'awanta Jamila suna Gaisawa da Saurayinta daya kawota,
Dukansu sai Murmushi sukeyi Musammanma Dijah, wani lrin takaicine ya ziyarceshi, aranshi yana tunanin tsawon zamanta dashi bazai iya tuna Rana d'aya da ta masa Murmushiba, sai dai yaga tanayi ma wani, shidai tsakaninta dashi tsiwa da Rashin Kunya,
Wani lrin Horn ya dinga dannawa ba k'ak'kautawa, har sai da Mai Gadin ya razana aguje ya fito ya Bud'e gate d'in,
Nan ya bad'esu da k'ura ya shige, ranshi kaman Wuta yanasane Wannan Jamilance ta kawo mata wani yaro da ta k'irashi Da surayinta yauma gashi ta kawo wani, "I hate this Girl ya fad'a afili, yana Huci,
Wayyo Nafisa ji tayi kaman tayi Hauka tsaban Murna, a tunaninta Dijah ya tsana, har yakasa B'oyewa,
Lallai Bokannan ya iya aiki ta fad'a tana Bud'e Motan, kusan tare suka fito a lokacin Idon Dijah yana cikin Gidan, nan idonta ya sauk'a akansu, tsananin B'acin Rai taji, dan haka tayi saurin janye ldonta, tanayi ma Jamila sai anjima ta shiga cikin Gida, ji tayi kaman kar ta shiga ciki ganin nan sukayi, sai dai tunawa da tayi yanzu zaya fito taje Gidan Sauda yasa da sauri ta shiga,
Ko Kallon inda suke a falon batayiba ta shige d'akinta ta d'auko mayafi da jakanta, taje tayi wa Mami sallama,
"Khadijah karfa kidad'e kigayawa driver ana la'asar yaje yad'auko ki, ki gaisheta, ta amsa da to tafito,
Wannan Karon Nafisa kad'ai ta tarar a falon ta fita.
A k'ofan falo sukayi karo da Kabir da sauri tarab'a ta wuce ganin alaman fita zatayi yasa yabi bayanta, yana Magana "ke ina zakije?" cigaba da tafiyanta takeyi bata ko nuna alamun tajishiba,
Mayafinta ya jawo yana kallonta hawaye taf idonta, "Ba magana nake mikiba, k'wace mayafinta tayi dai2 lokacin hawaye yafara zirya a fuskanta, ta juya binta yayi niyanyi, wani sashi na zuciyansa kuma yana mamaki Hawayen da yagani afuskanta, Wayarsa ce ta hau Ruri.
Yakoma gefe yana Amsawa yana gani driver yafita da ita,
Har bakin gate ya isa ya lek'a da niyan yadakatar darivern har sai ya san inda zata,
Sai dai ko alamansu bai ganiba,haka ya dawo ya shiga pert d'insa,
Yau Juma'a yakasance Gobe ne Ranan Engagment d'insu,
Yana Zaune a k'ofan pert d'insa yana tunani Rabonda yaga Dijah a idonsa tun Ranan da tafita tana Hawayennan, "ko ina taje?
Yafad'a a fili, yana zaune awajen Motan wasu daga cikin freinds d'insa guda 2 suka shigo da 'yan Matansu, kai tsaye gunsa suka nufa,
Cikin Murna ya taresu gami da ba wa Mazan wajen zama, Wayansa ya d'auko da sauri yana fad'in barin k'ira Nafisan ta shiga daku ciki ya fad'a yana kallon 'yan Matan dasuke tsaye,
Tana d'auka yasanar da ita tazo tashiga da Bak'i,
Cikin tsantsararren kwalliya ta fito tana taku d'ad'd'ai cikin farin ciki yayi dai2 da shigowan Dijah, kanta ak'asa take tafiya, Dai2 zata shiga cikin falon Nafisa da 'yan Matan suka iso suma zasu shiga,
Nafisa ta ciza Baki aranta tace "b'uyanki agidannan nabanzane yarinya nasan bakin cikin bikinmu yasa kike k'in fitowa yanzu zan k'aramiki bak'incikin inyaso kiyi Bindiga,
"Ke Dije Maza ki had'a min abun Motsa baki kikawo ma bak'ina in akasamu matsala ina mai tabbatar miki yau tsohon k'auyennan zaiyi Mummunan Gani.
Har Ranta taji Maganan anma ta d'auke kanta kaman batajiba zata shiga, jawota Nafisa tayi tayo baya da ita "Bakiji.... Aibata fad'i abinda zata fad'anba taji sauk'an Magigitan Mari har biyu a fuskanta, "Kafin tsohon k'auye yaji Mummunan labari na Birni sai yafara ji, daga haka ta wuce cikin matsanancin Borin Kunya tayunk'ura tayi bayanta "wlh yau sai na halakaki, d'aya daga cikin 'yan Matan ta rik'o Hanunta "No Nafisa ba girmanki bane pls stop it, ince k'anwar wanda zaki aurane?
"yar aiki ce daga k'auye aka kawota, sam ba a dangin mu take ba,
'yar aiki? Suka fad'a dukansu suna kallon juna, d'ayan tace "tokoma yane kiyi Hak'uri Mukanma daganan zamu koma dama bazamu samu attending Hidiman bikinku bane, zamu koma school abroad shine suka matsa akan muxo mu gaisa, Muna muku fatan Alkhairi ga wannan ba yawa, suka mik'a mata k'atuwar Ledan da sukazo da ita, cikin Matsanancin Kunya ta karb'a tana fad'in "Dan Allah kuyi hak'uri mushiga pls
"No karki damu dama ko munshiga ba dad'ewa za muyiba, akwai inda zamuje, tsaban Kunya kasa Rakasu tayi, ta tsaya awajen,
A haka suka k'arasa wajensu Kb da shima gaba d'aya kunya tagam lullub'eshi, dan tun shigowan Dijah yabita da kallo, yana son yace mata takawo masu abun tab'awa dan Ruwa kawai ya d'auko musu, saidai yanayin da yake ganin fuskanta ya dakatar dashi, kallonta kawai yakeyi, kaman yau ya fara ganinta, akan idonsa Nafisa ta tareta, baiyi auneba sai sauk'an Maruka ya gani kan fuskan Nafisa, nan Hankalin abokansan da suke shan Ruwa yayo wajen, ji yayi kaman k'asa ta tsage ya shiga, tsananin kunya,
Kanshi na sunkuye yaji suna masa sallama, asanyaye ya tashi, yana jan dariya,
"Haba har zaku tafi? Baku ko shiga bafa, yafad'a yana kallon Matan,
"Wlh sauri mukeyi suka bashi amsa,
Ya mik'a wa Mazan Hanu, "ok guys thanks so much, sai when?,
"Mukan ai damu gobe za'ayi komi, har jikin mota ya rakasu, yana d'aga musu hanu har suka fita,
Tun ahanya yake k'iran watan Nafisa tana d'agawa cikin kakkausan Murya yace "maza ki fito ina jiranki,
Sai kaiwa da kawowa yake agun tafito aranta tana fad'in yau zaman Dijah agidan ya k'are,
Yana jin motsinta abayansa ya juyo, yanayinsa ba k'aramin tsoratata yayiba,
"Ke Nafisa ashe baki da Hankali bansaniba? Ashe ke mahaukaciyace nake miki kallon mai hankali, Meye Had'inki da Khadijah? Ina Ruwanki da ita?
Cikin jin zafin Maganansa tace "Kai Kabir ya haka kake niman kazageni akan wancan banzar 'yarqauyen? Kasan me tamine? Daga ce ta had'a ma Bak'in mu Abinci sai tanimin min Rashin kunya? Meye amfaninta agidan? Wlh bazan bartaba ta rainaniba nida gidanmu sai naci Ubanta, nibana tsoronta dan naga ka maidata kaman wata ita tahaifeka, sai na halakata shegiya 'yar matsiyata tasss taji sauk'an Mari afuskanta,
yanuna ta da yatsa "yaushe kika fara rainani irin haka? Wace ce ke dahar zaki furtamin magana haka? Nidake waya riga wani sanin Khadijah? Ni nafiki sanin wace ce ita, duk da nasan akwai bashin Mari atsakaninku inda baki shiga sabgartaba bazata kulakiba, zakice ta had'o miki Abinci ma Bak'i ancemik 'yar aikice ita? Ko dakike cemata 'yar qauye yanzu keda ita wace ce tanuna qauyanci da dabbanci ma? Kin kunyatani kin kunyata kanki, Khadijah yarinyace k'arama agabanki ko a'ina kukayi haka ansan kece bako da hankali, sannan da kike wani fiffik'an sai kin mata kaza2 ke kin isa da Khadijah? In abaku guri da ita sai kin raina kanki ke kanki kinsan wannan, shine dan tsaban rashin kunya zakicr min nad'auketa kamar uwata, to ba Uwata bace ita, Mata tace ta aure ko dakike yawan cewa sai tabar gidan saidai ke ki bari dan kinsan ayanzu nine mai gidan kuma zaman aure takeyi, ko kina tsammanin matsayinki na k'anwata yazarta na mata tace, ko kina tunanin dan ansa ranan aurena dake shikenan har kinfara bearing matata ce? Nonses kawai, yafad'a tana jifanta da wulak'ancaccen Kallo, yajuya kaman kumurcin Maciji yayi nufi pert d'insa zuciyansa sai suya yake masa,
Nafisa da ta daskare awajan dafe da k'uncinta da tunda taji sauk'an mari idonta gaba d'aya sukayo waje tana kallon Kabir da take kokonton anyah kuuwa shine? Tasan Kabir tuntuni in Ransa ya b'aci yakan zama abun tsoro amma bata tsammaci hakanba,
Musamman ita da tasan aikin Boka na jikinsa,
Tana jin ya rufo k'ofa ta juya aguje tayi bayan d'akin Mami ta dirk'usa kaman mai niman gafara tana kuka kaman ranta zai fita tana fad'in "Wayyo Na shiga Uku aikin ya karye Boka aiki ya karye ya karye kalman da take ta maitawa kenan kaman sabuwar mahaukaciya.
🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣🤣
*Tofa Mari Uku ana Gobe Engagement* wai yazata kasance ne?
*shin Kabir ya manta ne yayi irin wannan hukuncin wa matan da yake ta lissafa ranan aurensu?*
🤔😅😅😅
Yaukam sai kungaji da karatu😉
*Ummu fatima ce* 😘
[7/22, 7:21 AM] +234 816 155 6998: 🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
*DIJAH* *QAYA*
🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋
*BY ASMA'U GALADIMA*
🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿🦋🌿
🦋 🦋
🦋 🦋 🦋 🦋
*UMMU FATIMA CE*🇳🇬
🌈 *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......🖊
4⃣5⃣
*Dijah* da tun fara maganan *Dr Kb* ta ke kallonsu ta Window ne ta sake labulen tana tab'e Baki taja tsaki ta koma ta kwanta tana jiyo kukan Nafisa,
"Ke Nafisa" Mami da tun tana toilet take jiyo tane ta lek'a Window ta k'irata, da dauri tasa Hanu ta toshe bakinta tana mayar da kuka da maganganun da yakeyin tana Mai Addu'an Allah yasa Mamin batajiba,
"bada ke nakeba ne Nafisa tashi kishigo yanzu2 inajiranki,
Asanyaye ta tashi tana had'a hanya ta shiga, a fallo tasami Mami ta zube a jikinta tana sake sabon Kuka ita sam ba Marin da aka matane ke damuntaba, illah aikin bokan da baiyi tasiri ba tanaganin samu sai gashi taga rashi, yanzu haka ita sam basan makoman aurenta da Masoyin nataba, tabbas da tasan cewa Asirin bai yiba ko da gigin wasa bazata tab'a gigin d'aga harshenta ma Kabir ba mutumin da ta d'auki lokaci tana dakon soyayyansa bata da buri da yawuce taganta matsayin Matansa, kuka take kaman Ranta zai fashe, tun Mami tana k'o'arin binta da lallami har ta fusata tafara fad'a,
'inbazaki sanar daniba shikenan tashi kije ki cigaba da kukanki inkina ga zai miki Magani, Mami ta fad'a tana k'ok'arin tashi, ta rik'o Hanunta tana fad'in "Kabir ne Mami Kabir ne baya sona ya tsaneni bansan me na masaba, Nan ta kwashe duk yanda sukayi ta fad'a mata sai dai bata sanar da ita cewa ita tafara tsokano Khadijah ba,
Hab'a Mami ta rik'e tana kallonta tace "Mari? Khadijah ta mareki shi ya Mareki sunyi Haukane? Ko ke 'yarsuce?
Ta jawo Wayanta ta k'ira Kabir alokacin har yayi Wanka ya shiryo zai fita, yana d'agawa tace "Maza ina nimanka yanzu2
Nafisa tana sheshek'a ta kalli Mami "wlh Mami na lura yarinyannan bata bar Kabir hakaba, wlh Asiri suka masa mai k'arfi,
Cike da Mamaki Mami ta kalleta, tad'anyi Murmushi ta gyara zama,
"Nafisa Rayuwa da kika ganta wanda ya d'auketa da zafi da zafin take zuwa masa, Babu wani Riba cikin sab'on Allah sai tab'ewa da wahala, aduk cikin sab'a ma Allah kuma ba kaman had'a Allah da wani, danshi laifine da matik'ar ka mutu kanayinsa Allah bazai tab'a yafe makaba, sai ya hukuntaka akai,
Kuma bakisan wani abuba inma niman wani abun kikayi awajen wani yamikishi ta hanyan sihiri In Allah yaga dama sai ya miki talala, sihirinki yaci anma kisani akwai ranan k'arshen abun watak'ila kuma k'arshensa yazo miki da matsaloli fiye da wanda kika guda kiyi danasani mara amfani, inkuma yaga dama sai kiyi tayi amma bazaki tab'a ganin biyan buk'ataba, sai akasin hakan,
Ta d'an k'ara muskutawa tana kallon Nafisa da gaba d'aya jikinta yayi sanyi, danji takeyi kawai da ita Mami takeyi,
"ldanma Su Khadijah asiri sukeyi ma Kabir to da da Hali ki dakatar da ita ta hanyan bata shawara dani da Kabir sam bama wasa da Addu'o'i da yardan Allah bawani sihiri da zai kama waninmu ta hutar da kud'inta, ta fad'a tana nazartan yanda sak'on nata ke shigan Nafisan, dai2 lokacin Kabir ya shigo da sallama, fuska a murtuk'e yazauna a kujeran dake fuskantan Mami, "Tashi ka shiga d'akin Khadijah ka k'irata Mami ta bashi Umurni, tura k'ofan yayi ya shiga da mak'alalliyan sallama yatsaya yana kalle2 can ya hangota a kan Gado ta takure waje d'aya acikin Bargo, ahankali yak'arasa jikin Gadon yana kallon Fuskanta da hawaye ke ta sintiri,
Wani nannauyan ajiyan zuciya ya sauk'e aransa yana Mamaki duk da tayi marin bata Huceba kenan ko me? Kodayake kwanan nan duk haka yake ganinta kaman tana cikin damuwa, "To meke damunta? To ina Ruwanka da abunda ke damunta Wani sahin na zuciyansa ya kwab'eshi,
"Khadijah tashi ki zauna, batayi Musuba ta tashi ta zauna tana kallonsa da jajayen idonta, ahankali yasauk'e idonsa k'asa kaman zai tambayeta abunda ke damunta sai kuma ya fasa ya juya yana tafiya yace "Mami ce take k'iranki daga haka ya fita,
Saida ta wanke Fuskanta, ta fito a k'asa ta zauna kusa da Mami,
Ita Mami ta fara tambaya, dalilin da yasa ta mari Nafisa,
Kanta Na k'asa tace "Babu,
"Haka kawai kika mareta Khadijah? Shiru Dijah tayi batace komiba,
Mami tace "tashi kije zanzo insameki, sannan ta kalli Kabir "Meyasa ne Kakeson canza Hali Kabir daga yanda nasanka zuwa wani daban, Naji Nafisa k'anwar kace kana da daman hukuntata, anma inaga abun baikai har da Mari ba,
Murya asanyaye yace "I'am Sory Mami anma inason ta maimaita duk abunda ta fad'a min da bakinta inaga ta cancanci abinda yafi mari awurina, dan niba sa'anta bane, da Harara ya kalleta "ki maimaita abunda kika gayamin kalma d'aya inkika canza sai nafasa miki baki, atsorace ta maimaita muryanta na sark'ewa,
Mami ta jinjina kai "anma da bahaka kika fad'aminba Nafisa komi zakayi kayi gaskiya, rashin gaskiyan bayi da Amfani, nan tayi ta musu fad'a da Nasiha,
mik'ewa Nafisa tayi tace ma Mami zata gidansu, "adawo lfy ta mata ta rakata da ido sannan ta kalli Kabir
"Anyah Kabir haka zakuje kunayi da Nafisa agidan aurenku, sam kai baka iya rarrashi ba, haka zakuje kana mata abu kad'an ta d'ibi jiki tayi gida kaikuma kana kallo, gaskiya da sake zama da mace sai da hikima,
Kabir ya had'e rai "Mami wlh nifa na fara tunanima akan aurennan wlh na lura har yanzu rashin kunyanta na nan,
Mami ta zaro ido "karma ka fara Kabir ko da wasa sai da komi ya kankama zaka tsiro wani abun, ko kamanta nan shekaranjiya muka fafata akan wannan Engagement d'in naku, Nace ku barshi fir kabi bayanta cewa anriga angama tsara komi, kadinga ban baki, shine yanzu zakace mene
to ahir d'inka kar kajangolomin abunda yafi k'arfina, tashi tayi ta nufi d'akin Khadijah shikuma yafita rai ajagule,
Da Daddare Kabir yana zaune ak'asa a falonsa ldonsa na kan T. V amma sam zuciyansa tana can wani wajen Nocking yaji anayi, Nana ya bada izinin shigowa, hakanan ya tsinci zuciyansa, da fad'in Allah yasa Khadijah ce, dan ko ba komi zai d'an rage zafi, idonsa k'yam akan k'ofan ta tura ta shigo da sauri ya janye idonsa yana k'ara muturk'ewa, ahankali kaman wanda k'wai ya fashewa aciki, ta zauna daf dashi kaman zata shige jikinsa,
Ganin ko kallonta baiyibane yasa ta d'an fara shsshek'an Kuka tana kallonsa zuciyanta sai harbawa yakeyi tana tunani wannan karonkan inta rasashi, Mutuwa zatayi, sai dai inta tuno da maganganun Mamanta sai tasamu releif, "Ya Kabir dan Allah kayi hak'uri da abunda na maka d'azu, sharrin shaid'an ne da tsananin sonka, na tuba bazan sakeba tafad'a tana fashewa da matsanancin kukan Makircin da aka training d'inta akai, tun yana sharewa har yaji kukan ya isheshi danshi sam baya son yaga ana kuka, d'an kallonta yayi sai rok'o da Magiya take masa,
"is ok Nafisa har ga Allah kin b'atamin Rai sosai dan nasha jan Kunnenki akan yarinyan nan anma baki ji, Inkin cigaba da