Showing 144001 words to 147000 words out of 155892 words
fita, ta fad'a jikinsa tana sake fashewa da Kuka,
KB yaji Wani irin....
*Ummu Fatima ce* π
πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦
*DIJAH* *QAYA*
πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦
*BY ASMA'U GALADIMA*
π¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏ
π¦ π¦
π¦ π¦ π¦ π¦
*UMMU FATIMA CE*π¦π¦
π *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......π
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHMAH MAI JIN K'AI*
_GODIYA DA YABO SUN TABBATA GA SARKIN SARAKUNA, KAD'AICACCE WANDA BAI HAIFABA BA AHAIFESHIBA, RAYYAYEN DABAYA MUTUWA, TSAYAYYEN DA BAYA GAJIYA, MAI TASKAR DA BAYA K'AREWA UBANGIJIN SAMMAI DA K'ASSAI_
*TSIRA DA AMINCIN ALLAH SU TABBATA GA FIYAYYEN HALITTAH, SHUGABAN MAZONNI, D'AN GATAN ALLAH, DASHI DA AHLINSA, DA SAHABBANSA,*
_jinjina gareku masoyan Dijah Qayah Bani da bakin godiya gareku, Ina muku fatan Alkhairi a duk Inda kuke, Al'amarinmun daga Rabbine_ π
_Gwiwana Ak'asa tsananin kunyanku yasa nakasa bud'e ido inganku, dafatan za'a gafarci Ummu Fatima jirgin dank'aro_ πππ
_Masumin fatan Alkhairi da masu k'irana awaya da massage, nagode matik'a da gaske dazan iya da na zayyanoku Allah yahad'a fuskokinmu a Firdausi_
*Wa inda suka rubutomin zagi da cin mutunci na yafemuku Allah ya had'a fuskokinmu a firdausi*
_pls, pls, wa inda kuke k'irana ban d'agaba, da masumin magana a watsap ban amsaba kuyi hak'uri ba walak'ancibane wlh, akasi ske samu_
_Aunty Fauxa Yar Amana_
_Mrs Adams_ Yar mutan kagara
*Dota Hauwa ('Jiddah)*
_the page is urs guys_ ππ
7β£5β£
KB yaji Wani irin k'arni dake fitowa ajikinta, da sauri ya d'agata ajikinsa yana ya mutsa fuska, adak'ile yace "Malama meye hakan? Kinshigomin d'aki baniman izini, sannan kinason kawomin rainin hankali, me kike nufi?
Nafisa ta tsuguna a gabanshi ta had'e hannunta tana kallonsa cikin kuka tafara masa magiya,
" Dan Girman Allah KB kayi hak'uri, ka yafemin bazan k'araba,
Rai ab'ace yace "ke kinsan Allah ne Nafisa? Da Har kikasan girmansa? Anyah akwai Allah a zuciyanki?
Tana sheshshek'a tace
"Kayi Hak'uri Kabir bazan sakeba, ka yarda dani Zan canza halayena,
Kallonta kawai yatsayayi cikin zafi, yana tuna abubuwan datayi ta aikatamasu agidan,
Tsananin kukan da takeyine yak'ara karyarmasa da zuciya,
Ya zauna kujeran da yake daf da ita, ya sauk'e ajiyan zuciya gami da fad'in, " is oK naji, share Hawayenki Nafisa, ki nitsu ki zauna muyi magana, ba musu tayi yanda yacen,
Yad'an zuba mata ido na d'an lokaci, kana ya nisa, "Nafisa meyasa kikeson jefa Rayuwanki cikin matsala? Duk da adalcin danake yi a tsakaninki da yarinyannan, Baku daina shiga da fitaba, Me namiki? Meyasa kika had'a kai da Meenat kukeson kashemin mata? Da d'ana? Dan Allah kigayamin meyasa kika tsani Khadijah? Metamiki dakike nuna tsananin gaba da ita Haka?
Ya jeromata Tambayoyin araunane,
Tasa bayan Hanunta tana share Hawayen da yagama wankemata fuska, zuciyarta sai zogi take mata,
Yaushe zata raba Zuciyarsa da Dijah? Meyasa duk laifin da take masa bai cika d'aukansa da zafi kaman in abun ya shafi Dijahnba, Duk yanda akayi Bokansu yafi namune, ta fad'a a k'asan Ranta, a fili kuma tace
" kayi Hak'uri KB, sonkane ya jefani a duk yanayin da nake ciki, takuma fashewa da kuka, wlh tsaban sonkane yasa na tsani yarinyannan ko sunanta banason inji, Anma ka yafemin bazan sakeba,
Kabir bakamin Adalci akanta, A fili kake gwada Bani bace agabanka, taya bazan ji zafiba, ka tunafa ni nafara Sonka aduniya duk son da wata mace ta maka a bayanane KB,
KB ya jijjiga kai yana kallonta cikin son kwantar mata da hankali, lura da Yayi bata hayyacinta, dan ya lura ko wanka takasayi, a mizanin shirme ya ajiye maganganunata,
"Kar kimanta Nafisa ke 'yar'uwa tace ko ba komi kina da hak'k'in Zumunci akaina, dole inmiki adalci, pls pls, banason tashin hankali kinsani,
Ya duba agogon Hanunsa, sannan ya mik'e da sauri ya rab'ata ya wuce yana fad'in "shikenan kikula da kanki Sannan ki Danni zuciyarki kada ki kuskura ki kuma aikata abunda kika aikata, ba ruwanki da Matata, daga haka ya wuce, tayi saurin mik'ewa, tana kallonsa da son yin mgana,
Ya had'e rai " So yanzu kuma meye?
" Mamata KB Dan Allah ka taimakamin ta samu lfy pls Dr,
"Bani ke bada lfy ba kiyi mata Addu'a inda Rabon sai ta girbi a bunda ta shukane ta wuce, sai kiga tayi lafiya,
Ya fice ba tare da ya kuma bin ta kantaba,
Jiki asanyaye ta koma sashinta, Dan bata gano nasara ba,
Rayuwa sannu a hankali take nausawa, da kad'an2 Mmn Nafisa take samun lfy yau watanta guda kenan a Asibiti, tana fama da Guntulallen k'afanta, da aka Yanke, da idonta guda d'aya, dan d'ayan ya mutu,
Allah kenan mai talala ma Bawa, ba tare da Bawan ya luraba, ayanzu har takan tashi ta zauna, bata da buri da yawuce, tasamu lfy ta koma wajen Boka, dan tayi Rantsuwa sai ta karb'ama 'yarta 'yanci agidan KB, sannan zatayi maganin Mijinta, da yayi watsi da ita a Asibiti, Momi ce kad'ai ke tsaye akan jinyanta, kama daga magungunanta, da duk goje gojen da akeyi, Sam takasa lura da halin da Rayuwan ya k'unsa, takasa zama tayi ma kanta karatun ta nitsu.
Yayinda shima Alhaji Ya'u yake ta fafutukan Kashe KB, musamman dayaga Mami ta dage ta kashe case d'in cin Guba da Kabir Yayi, ganin wacce take da Hanu dumu2 Cikin iftila'i,
A daidai lokacinne kuma Cikin Dijah ya cika wata Tara, Wanda yak'ara jefa Nafisa cikin matsanancin Tashin Hankali, babban damuwanta ace yau Dijah ta haifarma KB d'ah, ba itaba, kullum taje Asibiti gurin Mamanta maganan da sukeyi kenan, tana bata k'arfin gwiwan cewa Dijah bazata haife cikinba, muddin tana Raye,
Ab'angaren Kabir da Mami kuma sun tattara duk kulawansu sun mayar kan Dijah, Mami taso k'warai ta dawo da ita wajenta,
Kabir ya dunga mata magiya Dole ta hak'ura ta barmasa ita, sai dai kullum sai taje ta dubata.
Sosai yake bata kulawa, kullum yana mak'ale da ita, gani yake kamar wannan rana baza tazoba, ranan da Maminsa take burin gani arayuwarta,
Wato Ranan da Allah zai azurtasu da Baby,
Ab'angaren Dijah kuwa sai buga shagob'anta takeyi son ranta, shi kuma gogan yana biyemata, Dan ko fita bai cikayiba,
π΄π΄π΄π΄π΄π΄π΄π΄π΄π΄
Wani daran juma'ah, Kabir yana zaune a falo cikin kayan Bacci tree quatern wando da gutunwar Riga mai gajeren Hanu farare tas, sai baza k'amshi yake mai ratsa zuciyan Wanda yashak'a,
Lap top ne agabansa da wasu takardu, yana aiki dasu jifa2 yana kallon Dijah da take kwance agefensa, cikin light pink d'in kayan Bacci masu yauk'i, danne2 waya take fuskanta ba wall wala,
Yad'anyi Murmushi, a k'asan Ransa, yace "sark'a kenan mai rikicin gangan,
Fushin nata tun na jiyane bata huceba,
Dan duk randa Bana girkintaba, da fushi suke rabuwa,
Ya ture lap top d'in gefe, ya jawota jikinsa,
Cikin murmushi yake kallon fuskanta,
"Haba 'yan matana, har yanzu baki hucebane?
Ba gani na dawo garekiba,
Tazame jikinta kaman zatayi kuka tace " kaga ba Ruwanka da ni,
"Why Khadijah laifin me na yi?
Dolena ne inyi Adalci gareku inba wa kowacce hak'k'inta, Khadijah ki taimakamin in kub'uta a gaban mahaliccina, kinsan matsayin mai nuna fifiku tsakanin matansa,
Banason ganinki cikin damuwa ko kad'an, ki taimaki Mijinki kar ya tashi da gefe d'aya ashanye ranan k'iyama, Khadijah pls, ya k'arashe maganan cikin rauni.
" Ni bance ka nuna fifiku a tsakaninmuba Likita, So nake kabarni inkoma gidan Mami, wlh yanzu tsoron kwana ni kad'ai nake, kabarni in koma inyaso sai Ku cinye kanku tsaban soyayya bana nanma bare in takuramuku, ta fad'a kaman zatayi kuka,
'Yar dariya Yayi Sosai Dan ya lura tsaban kishine ke d'awainiya da ita,
Ya nisa asanyaye yace "gaskiya bazan iyaba Dijah dole ce kawai zata rabani dake, ba son rainaba, bazan iya wal walaba muddin baki kusa dani, ki yarda dani, ki daina shakku cikin Son da nake miki Khadi na. Ina sonki,
Lafewa tak'arayi ajikinsa tana jin bugun zuciyansa,
" Khadijah! Yak'ira Sunanta cikin wani irin yanayi, "Dan Allah inkin haihu kar kibari Mami ta d'aukemin ke, kinji!
" Tom kawai tacemasa cikin sigan da yamata maganan,
" Likita tunda kaje Ruganmu bakace dani komi game da zuwanba, ya BAFFAH da INNA ta? tayi tambayan dan son kawar da zancen da yake son mata,
Yaja hancinta yana murmushi, "Duk suna lfy Khadijah, sunce agaidaki,
Nagama gyara gidana na bayan low coast da Sunan Baffah, abunda yakaini kenan, naje sosai mukayi artabu da Baffah, fir yace bazai dawo garinnanba, na kad'a na rawa Khadijah Sam yak'i,
Dijah ta sauk'e ajiyan zuciya " ai Dana San abunda yakaika kenan da nace karma kaje Dan nasan Baffah bazai tab'a yarda yadawo garinnanba, tayi maganan a raunane,
KB ya shafi cikinta cikin sigan Rarrashi, yace "kar kidamu zamu San abunyi, idan kin haifu, Baffah ya girma yana buk'atan Hutu yanzu shiyasa nake son dawowa dashi kusa da mu,
D'an ajiyan zuciya kawai Dijah ta sauk'e tana sauraron salon da ya koma mata,jin yana niman zarcewane yasa ta mik'e zata gudu, ya tashi ya bita, nan suka Shiga zagaye falon suna k'yata Dariya, sai da ta gaji ta tsaya ya kamata, ya nufi d'aki da ita.
Cikin Dare misalin k'arfe 2:00 mata da mijin suna tsaka da Baccinsu mai dad'i Rungume da juna, wani irin k'arane ya farkar dasu daga duniyan daddad'an Baccin da suke,
Jikin Dijah ya saki b'ari a firgice tafara jero addu'o'i tana k'ank'ame Kabir da yake k'ok'arin tashi ya fita, shima bakinsa d'auke da Add'u'a ya cireta a jikinsa a hankali yace "Harbi naji agidannann Khadijah barni infita, tana kuka tace " Karkafita Likita Dan Allah kar kafita su kasheka, ganin yanda tayi mugun tsorata ne yasa ya koma ya zauna ahankali yana Rarrashinta, can kuma kaman a tsakaleta a firgice tace "Aunty Nafisa, Dr tashi muje kar su kasheta, wlh zasu kasheta, ta tashi aguje ta nufi k'ofa yayi saurin rik'ota yamaidata Baya, " koma ki zauna Khadijah ni zanje, karkiyadda ki fito, yafice da Sauri yabarta anan tana b'ari, kasa jure jin hargowan da ke tashi a falon ne yasa ta fito,
K'attine guda shida suka kewayeshi da bindigogi dukansu sanye suke da bak'ak'en kaya sun rufe fuskokin da bak'in abu, baka iya ganin komi na jikinsu, wani irin ihu tasake "Dan Allah ku ji tsoron Allah, kubarmin mijina kar ku kasheshi, jin hakane yasa Nafisa wacce take mak'ale ajikin k'ofan shigowa da gudu, ta k'araso gaban kila Wanda yadakama Dijah tsawan kar takuma musu ihu, "kila ba KB kukacemin zaku kasheba, wannan 'yar k'auyen kukacemin zaku kashe, ta fad'a tana tankad'a Dijah da ta durk'usa tana magiya tana gunjin kukan kar su kashemata Miji,
Kabir da tun fitowansa suka kewayeshi da Bindiga ya tsaya Nad'e da Hanunsa akan k'irjinsa yana binsu da kallo d'aya bayan d'aya, ya yunk'ura zai taro Dijah cikin zafi,
" kar kayarda ka motsa anan inkayi wargi takanta zamu fara,
Rai ab'ace yace "danme zaku fara takanta? Me ta muku da zaku kasheta? Nine mai laifi kuma gurina aka turoku, Dan haka ba ruwanku da matata, Ku gaggauta kasheni Ku fita Ku daina tsoratamin mata,
Kila yayi wani mahaukacin Dariya ya kalli Dijah, " Ina yaushe zanyi gangancin kashe wannan kyakkyawan hallita ban moretaba?
Yasa k'afa ya sharb'e Kabir sai da Ya durk'ushe a k'asa, "D'an rainin hankali ka tsaya wa mutane tsegege, tsawan lokaci Kabir kana bamu wahala sai mungama shirinmu akanka ka b'ata mana, munsha harinka a wurare da Dama da niyan kasheka kana kub'ucemana, yau gaka agabana ahanuna, ba ma kawa yau d'innan zaka bi bayan tsoho duk taurin kanka yau baka da mafaka, ko akwai mai k'watarka? Cike da izzah yace, " Allah shike kashewa ke rayawa, inbai kashenuba ku baku isa kasheniba, bak'in cikin ganina araye shi zaiyi ajalinka kai da uban gudan naka, Kila ya ciza lips cike da isa yace "tom barin gwadamaka cewa baka da wayo bakasan me kakeyiba, kai Ku shigamin da yarinyannan daga ciki na d'an Mora kafin na aikashi,
Da sauri Kabir ya mik'e cikin k'araji yana nunashi da yatsa, "Kayi k'arya wlh sai dai abayan raina k'azami matsiyaci, k'arya kake kaci zarafin mata ta a gaban idona ina Raye, a zafafe Kila ya saita kansa zai harbeshi, Nafisa ta tankad'ashi gefe, " wlh Baku isaba Dijah kukacemin zaku kashe bazaku kashemin Mijiba, dai2 lokacin kuma yaran kila suka kama Dijah zasu cika umurnin Ogansu, "Dan girman Allah kuji tsoron Allah karkuci zarafinmu, me muka muku? Dijah ta fad'a cikin kuka tana tirjewa
Kabir Yayi kukan kura ya watsar da sauran ragowan guda ukun da suka kewayeshi, ya dira agabansu da iya k'arfinsa ya kaimusu Naushi, gami da finceke hanun Dijah yana shirin turata d'aki Kila ya saita kansa da Bindiga, da gudu tasha gabansa ta fad'a akansa ta tare Harbin, facauuuuu kakejin yanda jini yake b'ulb'ula ta d'ago kenan, suka sake harbawa sai da sukayi harbi har Uku, Sannan suka fice a guje Dan tsoron kada a ritsa dasu,
Innalillahi wa inna ilaihirraji'unππππππππππ
Kullu Nafsin za'ik'atul mauttttttπππ
Ku biyoni insha Allah gobe zakujini
Ummu Fatima ce πππΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦
*DIJAH* *QAYA*
πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦
*BY ASMA'U GALADIMA*
π¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏπ¦πΏ
π¦ π¦
π¦ π¦ π¦ π¦
*UMMU FATIMA CE*π¦π¦
π *KAINUWA WRITTES ASSOCIATION*.......π
7β£6β£
A firgice Dijah tayi Kansu dukansu biyu sunjik'e da jini sharkaf, Sam takasa gane Wanda aka harba acikinsu, abunda ta gane dai shine Kabir rik'e da Nafisa yana jijjigata cikin tashin hankali yana k'iran sunanta,
"Innalillahi wa inna ilaihir rraji'un kalman da Dijah take iya maimaitawa kenan, ta gama fita a hayyacinta,
Ta k'araso ta dafa goshin Nafisa, ta fashe da wani irin kuka mai cin rai, "Aunty Nafisa, ki tashi pls bud'e idonki kar ki tafi ki barmu,
Sosai jikin Kabir ya d'auki kyarma, yarasa yadda zaiyi zufane yake ketomasa ta ko ina, ya kalli Dijah, da gaske take rafzan ihu kaman kanta zai tsage, ya kalli Nafisa da take gurnani cikin wahala kaman rai zai fita, bai San lokacin da ya fashe da kukaba, yasan ba Asibitin da zasu karb'eta sai da Hukuma, to ta inama zai fara? ya jingineta ajikin kujera ya tashi ya shiga d'aki ya d'auko waya, gaba d'aya yarasa Wanda zai k'ira awayan, kimanin minti lshirin yana kaiwa da kawowa da waya ahanunsa cikin matsanancin tashin Hankali,
Can Yayi k'arfin halin k'iran Habib, wayan har ta yanke bai d'agaba, ya k'ira Sanima bai d'agaba,
"Likita Dan Allah kazo mukaita Asibiti kar ta mutu, ka duba halin da take ciki Dan Allah, Dijah ta fad'a cikin kuka,
Cikin k'arfin hali KB yazo zai ciccib'eta, Nafisa tayi saurin dakatar dashi ta hanyan kamo Hanun Dijah, suna had'a ido ta sakarma Dijahn murmushi tare da gangarowan hawaye a fuskanta, Cikin muryan tausayi mai d'auke da Nadama da Dana Sani kala2 tace " Khadijah inama ace nice nasmu rayuwa mai kyau da tarbiya kamarki? Inama ace ak'auyen da tafi taku nayi Rayuwa har abada na tsira da mutumci da imanina,
Khadijah kin kasance 'Yar k'auye anma Rayuwarki tafi ta wainda aka haifesu a birni sukayi Rayuwa a birni, kina da kyawawan d'abi'u da Addini, tarbiya, sanin ya kamata hak'uri da tawwakali, kin mik'a dukkan lamuranki ga Allah, sab'anin nida NA mik'a nawa ga wanin Allah, Kullum kece da Nasara akaina, Khadijah ki yafemin na miki abubuwa da yawa dani kaina bansan yawansaba, ki yafemin ko Allah zaisa incika da imani, cikin Kuka Dijah tasa hanu ta rufemata Baki, "Nayafemiki Aunty Nafisa dama ni ban rik'ekiba, fatana kullm shine Allah yaganar dake Gaskiya, ki gane kishi ba gaba bane, Allah ya baki lfy,
"Nagode Khadijah Dan Allah ki rik'a nimamin gafara a wurin Mahaliccina, nikam nasani tawa tazo k'arshe,
" Bazaki mutuba Aunty Nafisa zakiyi lfy insha Allah zamu cigaba da Rayuwarmu mai tsafta,
Wayan KB da Yayi kasake yana kallonsu da sauraronsu ne ta hau ruri, a kasale ya d'auka,
"Helo Habib..... Narasa me na musu? Meyasa suke bibiyan Rayuwata, duk lokacin da suka kawomin hari sai sunyi illa ga wani da muke tare, sun Harbi Nafisa.... Dan Allah kazo ka taimakamin,
Abunda yake futowa Bakinsa kenan ba tare da ya tantanceba, ya ajiye wayan ya kalli Nafisa itanma shi take kallo cikin d'unbin nadama da kaiton Rayuwar da tayi,
" Nafisa meyasa kika tare Harbin? Meyasa baki bari sun harbeniba? Da burinku ya cika, Ince dama nine bakuson gani? Meyasa baki barsu sun kasheniba,
Tayi wani Murmushi mai ciwo tace "wannan shine ake k'ira tsautsayi koma kan mashek'iya Yaya Kabir, Ba Haushe Yayi gaskiya da yace inzaka Gina ramin mugunta ka ginashi dai dai tsayinka, ba mamaki kai zaka afka cikinsa, Nayi matik'ar farin ciki da wannan Rana, na farko na samu daman niman gafaran Dijah ta yafemin, sannan inata istigfari ma Ubangijina, nagane