Showing 15001 words to 18000 words out of 150033 words

Chapter 6 - Rabo Ya Rantse Book One Complete Hausa Novel

*NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

*11*

Zagaye Ƙaton Parloun shi yake hannun shi Goye a bayan shi Sam ba zaka fahimci inda Halin da yake ciki ya dosa ba Idanun shi ya rintse Har yanzu sautin Muryar yarinyar da take Labaran bai bar amsa kuwa acikin Dodon Kunnen shiba.

"Iya sanina bani da abokin faɗa a Wajan sana'ata Bani da Abokin Gaba bani da wanda na taɓa Musayar Harshe dashi a ko ina Why zaku Min haka mai nayi Muku zaku ɓata min suna a idanun al'ummah idan wasu sun yarda wasu ba zasu yarda Ba"

Da sauri ya Zube a gaban Ammi wadda ta tallafe haɓa da hannunta hawaye nabin Idanunta.
Ya kamo ƙafafunta ya ɗora kanshi akansu.
"Ammi ki yarda dani wallahi bani da Hannu a zubewar Cikin Mami, Arziƙi Allah ne yayi Minshi nima ina mamakin Yadda duk abin da na taɓa sai Allah ya saka mai nasibi Ke shaida ce ammi kinsan yadda Muka taso"
Yana fara maganar Muryarshi ta shaƙe ya soma tari da gudu Ammi Ta buɗe Frij ta ɗauko ruwa ta ɓalle Gorar ta fara bashi Musa na masa sannu.

"Nina haife ka Nina san waye kai Allah ya tsareka daga dukkan wanda ya nufoka da sharri Allah ya kare ka daga dukkan sharri"
Ammi ta faɗa cikin kuka.

Da gudu ɗaya daga cikin masu gadin Gidan ya shigo falon Ammi ta zaro ido tana cewa.
"Sun shigo su kashe min shi ko? ku taimaka Ku Ɓoye min shi kada a far masa"
Mai gadin yayi Murmushi.
"Hajiya ku godewa Allah, Haƙiƙa baka Alkairi ka taɓe kamar yadda baka sharri ka gama lafiya, Dama zaki fito waje da sai Kin mayar da kukan ki Dariya sabida Ilahirin matasan Dake garinnan sunyi dafifi a ƙofar Gidannan domin bawa mai gida kariya, Yanzu haka mai girma gwamna ya turo da Motocin Ƴan sanda kusan Goma suna nan tsaye da Bindigu domin su bawa wannan Bawan Allah kariya Sannan matasan gari sun Je sun ƙona gidan Radion yanzu haka neman Mai gidan Radion suke ruwa a jallo dan dai basu sami Mutum Ko ɗaya bane daga cikin ma'aikatan sabida kowa ya gudu"


Ammi ta sauke ajiyar zuciya tana shafa kan Aliyu wanda ya kwantar dashi akan cinyarta.
Ya kasa magana Har Ammi ta sallami su Musa Falon yayi saura daga shi sai ita.
"Ka ɗauka hakan wata nasara ce daga Allah in sha Allah hakan ba ze zama sharri gareka ba sai Alkairi kuma bana son kai fushi ka daina taimako wannan ma ya zama ƙara ƙarfin ka wajan taimakon al'umma domin kaga ranar hakan da idanunka inda baka taimako da bamu san yadda abin zai zama ba, amman albarkacin al'ummar Annabi gashi kana ta samu kariya"
Aliyu yaƙi magana sabida zuciyarshi yadda take a karye ta yaya za'a ce shike salwantar da Cikin Mami dan ya ƙara arziƙi ta yaya za'a dangana dukiyar shi data tsafi shida ya sha wahala kafin ya tarata.

Duk yadda ake kiranshi a waya ya kasa ɗagawa Ta ya sadik kaɗai ya ɗaga data bashir waɗanda suka ɗaga hankalinsu akan Labarin da suka ji ya tabbatar Musu da cewa yana lafiya ya kashe wayar sai ta mai girma gwamna wanda ya bashi haƙuri yace kada ya saka abin aranshi hakan ma matakin nasara ce Kuma gwamnati zata ɗauki mataki akan shugaban Gidan radion dan zata binciko shi harma wadda tai labaran.

Bayan ya gama jin jawabin gwamna yayi godiya sai dai yace wa gwamna yabar Batun tuhumar mai gidan Radion shida kanshi zai Bibiyi Lamarin dan ya ɗauki matakin daya dace sosai sukai magana da gwamna kafin yayi masa sallama bayan yace ga Jami'an tsaro nan ya Turo masa dan su kare lafiyar shi data iyalin shi yayi Godiya ya katse wayar.

Yawan ƴan jaridar dake ƙofar Gidan ya kai ya kawo dan ƴan jarida kamar su fasa gidan su shiga su ɗauko rahoto haka suka taru ga jama'a kota ina wannan tasa aka rufo gidan ma gaba ɗaya ya zama ba shiga ba fita daga gidan Madaki ma sosai ƴan uwan su Aliyu suka girgiza nan da nan Baba Usman Ƙanin Mahaifin Aliyu ya saka malamai aka hau sauke alkur'ani mai girma.

Mami kuka take tana kiran layin Aliyu dan hankalinta gaba ɗaya yana kanshi Ko kaɗan bata yarda da wannan labari ba sabida tasan waye Mijinta har ya fita damuwa akan asarar Cikin da suke yi Suma gidansu Mami sai rufe Ƙofa sukai sabida Yadda jama'a ke dafifin shigowa jaje.

Yana rangaji ya miƙe da sauri Ammi ta taimaka masa ya haye saman shi ya faɗa saman gado yana Lumshe idanunshi Ammi ta rufo masa ƙofar Ta nufi sashin sa da ƙyar ta rarrashi su sajeeda waɗanda suke Kukan abin da aka wa yayan nasu.

Wayar shi dake Ringing a karo na ba adadi ya laluba ya ɗaga Muryar mami ke sauka cikin kunnen shi.
"Yaya dafatan kana lafiya? wallahi ni na yarda dakai Mijina sabida haka ka kwantar da hankalin ka wannan shiri ne na maƙiya"
Da.
"Umm"
Ya amsa mata ya kashe wayar yayi shuru yana sauraran Bugun zuciyar shi.

Ƴan jarida da sauran jama'a gajiya sukai suka bar ƙofar gidan har zuwa dare ba aji ɗuriyar shiba amman an tabbatar yana cikin Ƙoshin lafiya dama shi haka tsarin sa yake in yana cikin damuwa shuru yake In yana cikin ɓacin rai shuru yake ya killace kanshi wannan tasa Ammi bata sake komawa wajan shi ba tasan yana tunanin mafita ne na wannan matsala data afko masa.

***********

Gaban Farha ne ya faɗi sanda taji kawu na Allah wadai da Wannan tasha ta garkuwa wadda ta ɓata sunan Aliyu Matan gidansu kuwa masifa suke suna kumfar bakin cewa baƙin ciki ne yasa akai masa sharrin ba wani abu ba Ƙara jan abin rufa tai tana Sakin Hamdala da Allah yasa babu wanda yasan a tashar take aiki kuma ba sunanta a labarin sannan bata can aka ƙona gidan rediyon kamar yadda taji labarin a tsakar Gida cewa an ƙona gidan rediyon.
Damuwar ta ɗaya wannan sharrin data ja gaba wajan yaɗawa Ina zata sami wannan bawan Allah ta roƙe shi gafara tsananin tsoro da damuwa sune suka ƙara haddasa mata zazzafan zazzaɓi zuwa dare Jikin Farha ya ƙara rikice wa wanda hatta Ƴan gidansu sun tsorata dan kuka take tana cewa umma ta yafe mata mutuwa zatai Duk zafin kawu sai da ya ruɗe Salim ne ya kirawo Nurse aka saka mata ruwa aka mata Allura Wanda bacci yayi awon gaba da ita.

***********
Daran ranar Aliyu bai bacci ba yadda yaga dare haka yaga rana, Ba abin da yake sai sallah yana ƙara neman gafarar Allah akan dukkan laifukan sa tare da neman tsari da kariya daga dukkan sharri sai da yayi sallar asubah sannan ya sami bacci Ƙarfe goma ya farka ba laifi ya sami nutsuwa sosai harya fito Parlou yana amsa jajen ma'aikata yana kuma ɗaga wayar mutanen sa masu yi masa jaje.
Ƙarfe sha ɗayan safe Musa ya ƙaraso Parlon nashi bayan sun gaisa ya dubi Musa........*RABO YA RANTSE! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne mtn card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
*RABO YA RANTSE...!!*🌹
          
           *NA*
*AUTAR MANYA*

ADABI WRITTER'S ASSOCIATION

                     *12*

Muryar shi a kausashe wadda ta nuna zallar Ɓacin ran daya kwana dashi.
"Musa ina son lallai a yau ka gano min  inda mai gidan radio ɗinnan yake inda hali katafi da jami'an tsaro cikin fararen kaya, su Kama min shi tabbas sai ya gaya min meye nufin shi akaina zan nuna masa ni ɗin wanene in aka shiga gona ta"
Ya faɗa yana fesar da numafashi mai ƙarfi.
"Sannan ita ma yarinyar datai labaran lallai ina son sanin wacece"
Ya faɗa yana jingina kanshi a jikin kujerar da yake kan ta a zaune.

A hankali ya furta.
"i will not leave them"
Ya ɗago ya kalli side ɗin da musa yake ya furta.
"kuma a yau nake so ka ai watar da komai ba sai gobe ba"
Musa daya tsorata da yanayin mai gidan nashi jiki na rawa yace.
"I will do my best for that"
Daga haka ya ɗaga ma Musa hannu yana cewa.
"Thank you very much Musa"
Da hannu ya dinga cakuɗa sumar data ke kanshi Duk ranshi a ɓace yake mai yasa mutane suke haka tabbas inda sun san girman laifin da sukai masa da idan ance su ƙara ma wani irin sa baza suyi ba.
Ya cije baki.
ya tashi ya koma bedroom ɗinshi yau ko wajan Ammi bai leƙa ba yana jin wayar shi na ringing bai bi takanta ba.

Musa yana tafe yana tausayawa Mai gidan radion sanin waye Aliyu Sarƙa ne faɗi kirikice Sarƙa ne mai rikicin gangan Dangin zaƙi ne Layin zuma.

Direct police station ya nufa sannan ya buƙaci a bashi ƴan sanda Guda biyu Batare da sun saka uniform ɗinsu ba Haka suka nufi Gidan Radio Ɗin Abin yayi matiƙar bawa musa Tsoro na yadda yaga an ƙona gidan Radio ɗin Ƙurmus ba wani abu na mora aciki Wajan ba kowa sai Mai gadi wanda su Musa suka ƙarasa wajan sa yana zaune a saman Banchi su musa suka ƙarasa suka mai sallama.

Mai gadin Irin Iyamuran nan ne Bayan sun gaisa bai da hausa sosai ya dubi Musa yana tambayar shi.
"What do you need here"
Ɗaya daga cikin Police ɗin ya kalli mai gadin yace masa.
"We will ask you a few questions"
Mai gadin ya zuba musu ido sabida dama tun jiya a tsorace yake dandai kawai son kuɗin shi na albashi shine ya zaunar dashi Kowa yasan ƙabila akwai riƙo da aiki baya wasa dashi.
"I hear you,what is your quesion?"
Ya faɗa yana kallon ɗan sandan daya masa magana.
Musa yaɗan dube shi.
"Gidan mai wannan gidan radion muke son ka nuna mana?"
Mai gadi ya zaro idanu cikin hausar da bata ishe shi sosai ba sabida yana jin hausar sosai amman Mayar da amsar ne take basa wiya.
"i don't know his house"
Ya faɗa yana mayar da radion shi kunnen shi ganin zai Ɓata musu lokaci yasa Ɗaya daga cikin Jami'an tsaron ya buga Masa tsawa tare da Nuna masa Id card ɗinsa Jikin mai gadi ya soma rawa Zufa tana karyo masa Nan da nan ya miƙe yana cewa.
"Let me show you"
Suka bi bayan shi Sai da suka hau Adaidata sabida da ɗan tazara daga nesa da gidan ya dakata ya nuna musu da ya tsansa yana cewa.
"That house with a black gate"
Daga haka ya juya da sauri, Suma basu wani takura mai ba suka nufi Inda ya nuna musun Gidan a rufe yake sai da suka buga Da dutse Md ya Fito yana cewa.
"Waye?"
Musa ya maƙale Murya kamar ta mata yace.
"Nice Hafsa"
Md yayi tsuku daga ciki kafin ya zare sakata caraf Ƴan sandan suka damƙe shi batare da sun masa magana ba suka tura ƙeyar shi Titi suka sami adaidaita suka tafi dashi station Gaba ɗaya Md zare ido yake Jikinsa na rawa wata irin nadama ce ta rufeshi dama tunda ya shiga Gida hankalin shi ba a kwance yake ba Burinshi yaranshi su taso daga Islamiyya ya tarkatasu su gudu Matarshi ta fita Ɗauko yaran duk zaton shi itace ma dayake sunan nata kenan Hafsa wanda Musan yaci sa'ar Ambata shiyasa ya buɗe Iya azaba Md yaji a wajan jami'an tsaron Amman Amsar shi ɗaya ce wallahi ba wanda ya saka shi ƙirƙirar labarin shidai kawai yayi ya saki ne dan tashar sa ta sami Suna.

D.p.o ya dube shi.
"Wato irin kune ɓata gari masu tada zaune tsaye acikin al'umma kawai dan son zuciyar kanka da biyan Buƙatar kanka zaka Ƙirƙiri labarin ƙarya dan ka sami ɗaukaka a tashar ka"
Ya kalli ɗan sanda guda ɗaya yace.
"Officer ku shigar dashi Bayan kanta har sai ya bamu amsar abin da muka nema a wajanshi ta yaya za'a ce babu wani dalilin shi na fitar da labarin kuma an tabbatar shine mai tashar"
Md cikin magiya yake cewa ai masa afuwa.
Musa bai bar station ɗin ba sai bayan sallar magariba Kai tsaye Waya ya kira Aliyu ya tabbatar masa da cewa an kama Mai gidan Radion an ɗamƙawa hukuma.
"Ita yarinyar fa?"
Cewar Aliyu.
Shaf Musa yama manta da wannan Sabida haka komawa yayi cikin station ɗin ya nemi daya ga Md.
Bayan ya shiga Inda Md ɗin yake tambayar shi yayi ina ne inda Wadda tai labaran take matar aure ce ko budurwa.
"Wallahi Ranka ya daɗe nina tirsasata bata da laifi yarinya ce ƙarama"
Musa ya buga masa tsawa.
"Ba wannan na tambayeka ba kwatancan ta kaɗai na tambayeka?"
Md yace.
"Gaskiya ni bazan ce ga inda ta fito ba amman Yarona daya taɓa min aiki ɗan nan ƙofar nasarawa ne duk inda ka tambayi gidansu Gali anan layi na Biyu cikin ƙofar nasarawa za'a nuna maka gidansu Tare da ƙanwarshi ya kawo min su tun last week"
Musa yace.
"Na fahimta"
Ya miƙe ya fita daga Wajan kanshi tsaye adaidaita ya kuma hawa sabida yadda Aliyu ya bashi tsoro ne yasan ya ko mota bai ɗauka ba Ƙofar nasarawa ya sauka yaci wiya kafin ya sami gidan wanda Ya sami Gali zaune da matasa a ƙofar gida ana hira Hannu ya bashi suka gaisa sannan yace.
"Da Allah ina son ganin ƙanwarka"
Gali bai kawo komai aranshi ba ya shiga gida ya kira Shema'u duk zaton shi Ko Musa saurayin shema'u ne.

Shema'u cike da mamaki ta ɗauki Hijabinta tabi bayan Gali Jingine da bango taga musa ya ƙaraso suka gaisa tana masa kallon rashin sani.
"Na san zaki mamakin ganina, Sunana Musa ɗaya daga cikin yaran mai Kamfanin Madaki Motors Kuma amintaccen yaron shi"
Shema'u tai jimm dan sunan ya kwanta mata musa yace.
"Ehemm Ina nufin special adviser na gwamna a ɓangaran matasa"
Zabura shema'u tai da sauri sabida ta gano nufin sa yanzu.
"To meye ni nawa acikin case ɗinsu tunda bani nai labaran ba,itama farha duk Nacin danai kada tayi gashi nan son zuciya ya kaita tayi abin zai zama masifa"
Musa ya fito da wayar shi ya saita recording.
"Ko zaki iya gaya mana gaskiyar abin da ya faru?"
Shema'u cikin tsoro tace.
"MD ya nemi ɗaya daga cikinmu akan tai labari akan Shi SA na gwamna ɗin wai muce duk cikin da matarshi ke samu shine yake dalilin zubewarshi ta hanyar bawa matsafa cikin, Ni direct nace bazanyi ba sabida ina gujewa kaina matsala sannan ni ƴar ƙofar nasarawa ce nasan waye shi tunda ina jin labaran alkairan shi a wajan mutane Ƙawata Farha ita tace zatai ba yadda ban da itaba daga ƙarshe ma har faɗa mukai da ita"
Musa ya gyara tsaiwa tare da cewa.
"Ita ƴar ina ce Farha, Kuma budurwa ce ko matar aure?"
Shema'u tace.
"Tare mukai karatu da ita indai ka shiga Lungun Ɗandago kace Gidan Malam Abubakar mai Bulo ba wanda baze kaika gidansu ba, ko kace Gidan cida kai ko gidan yawa Budurwace amman an kusa bikinta a yadda take gaya min akwai wanda yake sonta tun tana ƙarama"
Musa ya mayar da wayarshi Aljihu yana mata godiya.
Shema'u da gudu tai cikin Gida kai tsaye sai banɗaki ta fara fesa gudawar tsoro.
Musa bai koma wajan Aliyu ba sai da ya Je Ɗandago ya sami wanda ya nuna masa har Ƙofar Gidansu Farha sannan ya nufi wajan mai gidan Nashi.
Sai da Musa yasha zaman Jiran Aliyu sabida ƴan uwan mahaifin su da suka cika ɓangaran nashi domin suyi masa jaje Har sai da Aliyu ya sallamesu sannan Musa ya sami damar shiga parlon nashi.
"Musa yaya?"
Ya faɗa yana ɗage girarshi.
"Yallaɓai Mun sami nasarar cafke mai gidan radion duk da yana ƙoƙarin guduwa ne yabar garin, yanzu haka yana wajan ƴan sanda"
Aliyu ya cije baki yace.
"Da kyau musa"
Musa ya ɗauko wayarshi ya kunna yadda sukai da shema'u Aliyu ya Mai da Nutsuwarshi yana sauraran mai shema'u take faɗa.
Murmushi yayi na mugunta bayan ya gama sauraran abin da shema'un take faɗi.
"Yallaɓai gaskiya yarinyar ƴar talakawa ce Irin waɗannan shari'a dasu ma akwai wiya dan in za'a kasheta ba lallai a sami mai belinta ba"
Aliyu ya wara idanunshi.
"Waya ce maka shari'a zanyi da ita musa? ba kace an kusa bikinta ba?"
Musa ya jinjina kai.
"Yawwa Musa ka shiryan tafiyar sirri Gobe In sha Allah zuwa gidansu Yarinyar"
Ya faɗa yana wani irin Murmushi.
Musa daya camfa murmushin uban gidan nashi dana mugunta ya miƙe yana cewa.
"Angama ranka ya daɗe"
Aliyu ya tura hannu cikin aljihun wandon shi ya nufi saman shi bayan sunyi sallama da Musa.
*********
Washe gari Farha ta miƙe da ƙwarin Jiki har Mutan gidansu suna tsokanarta na yadda taita neman yafiya Jiya Tun magariba ta tsala kwaliya sabida salim yace mata zaizo Burinta yazo yau ɗin suyi maganar aurensu tunda dai yanzu ba batun aiki sabida an ƙona gidan radion tasu bababn tashin hankalinta ma shine yadda zata sanar da umma cewar an dakatar da ita a wajan aiki wanda faɗin hakan shine mafitarta, dan kota sha giyar wake bazata dangana kanta da gidan radion da aka ƙona jiya ba, gwara tai aurenta ta huta.
A wayar Umma salim ya kirata akan tai haƙuri baze sami damar zuwa ba jifa tai da wayar tana tura baki gaba.
Umma ta dube ta.
"Ai sai ki tashi ki tafi makaranta tunda baze zo ba"
Takaicin Salim yasa taja hijabin ta tai waje ko jakar makaranta yau bata ɗauka ba.
Adaidai wannan Lokacin Aliyu ya fito cikin Shirinsa jallabiya ya saka Brown Colour wadda tai masifar yi masa kyau ya fesa turare ya Rufe fuskarshi da face mask.
Ya fito compound ɗin gidan musa yana cikin mota yana jiranshi yana shiga motar musa yaja suka bar Gidan masu gadi suka buɗe Musu gate.
A bakin layin su Farha musa yay parking sabida motar ba zata shiga cikin layin ba, Aliyu ya fito daga cikin Motar yana mamakin ƙanƙantar cikin layin ko ina dumɗum ba wutar nepa Musa na gaba Aliyu yana binshi Daga nesa musa ya nuna masa ɗan ƙaramin gidan su farha.
Aliyu ya ƙarewa gidan kallo ya taɓe bakin shi lallai yarinyar nan tai gangancin shiga Hurumin shi dan sai ya tarwatsa mata dukkan wani farin cikinta kamar yadda tai silar shigar shi damuwa shida dangin shi da dukkan masoyan shi.
"Musa koma mota ka jirani"
Da mamaki Musa ya koma Da baya duk da bai san Ƙudirin Uban gidan nashi ba amman Lamarin ya bashi mamaki.
Aliyu ya ƙarasa ƙofar gidansu Farha Adaidai wannan Lokacin ta sako kanta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login