Showing 21001 words to 24000 words out of 150033 words
Chapter 8 - Rabo Ya Rantse Book One Complete Hausa Novel
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*15*
Lumshe idanunta tayi ta saki wata irin ɓoyayyar ajiyar zuciya, Yayi mata masifaffan kyau Ƙura masa idanu tayi babu ko ƙiftawa sanye yake da wani irin lallausan yadi Coffee colour wanda ya haska farar fatar jikin sa sai yanzu ta kuma ƙare masa kallo dogo ne sosai dan yadda ya mata tsaye akan ta har rumfa tsayin shi yayi mata Yana da manyan lumsassun idanuwa masu kama dana wanda yake jin bacci Yana da cikakken gemu wanda ya haɗe da ƙasumba ya cika fuskar tashi Sai Ƙaton tabon Abin sallah wanda yay baƙi sosai a saman Goshin sa.
Numfashin ta ne ya kusan ɗaukewa lokacin da taji ya hura mata iskar cikin bakin shi mai ƙamshin Mint.
"Kallon fa?"
Ya faɗa da tattausar Muryarshi.
Tsintar kanta tayi da jin matsananciyar kunyar shi.
A hankali ya furta.
"Do you feel what I feel when you are with me?"
Ya kuma matsowa gabanta ya maimaita mata abin da yace da yaran hausa.
"Kema kina jin abin da nake ji atare dani?"
Matse katin asibitin dake hannunta tayi gam aranta tana cewa.
Wannan Bawan Allah zai halaka ni.
Jikinta ko ina rawa yake muryarta na rawa sosai tace.
"To ka matsa baya sai muyi magana"
Aliyu ya zira hannunshi saman nata hannun ba zato taji ya fisge katin asibitin data riƙe a hannun nata.
Zubawa katin idanu yayi yana gama karantawa ya saki murmushi.
Bai miƙa mata katin ba ya zira shi acikin aljihun shi.
Hannun nashi tabi da kallo wanda yake shinfiɗe da wata irin baƙar suma tai luf kamar ka taɓa jini ya fito.
"How do you feel about your body?"
Ya faɗa yana ƙoƙarin saka ƙwayar idanun shi cikin tata wadda ita kuma taƙi yarda ta haɗa idanun dashi sabida duk kunyar abin da ya gani ajikin katin tagama kamata.
"Shike nan tunda baza'a min magana ba oya shiga gida"
Kamar jira take da sauri ta kama ƙofar gidan nasu zata shiga ciki.
Hannu ya zira cikin Aljihunshi tare da fesar da iska mai zafi.
Tsadaddiyar wayarshi wadda bai cika amfani da ita wajan hulɗa da jama'arshi ba ya fito da ita ya damƙa ta a hannun Farha wadda harta kai da shiga soron gidan nasu.
A hankali ya rage tsayin shi ya Sunkuya daidai kunnenta ya raɗa mata.
"Saura ki ƙi ɗaga wayata, zan kira ki anjima"
Daga haka ya juya ya fice daga soron gidan yabar mata ƙamshin turaren shi.
Gaba ɗaya Jikin farha rawa yake sai faman kaiwa da komowa numfashinta yake Ta kasa jan ƙafafunta zuwa cikin Gida gefe guda ga tsoron wannan waya daya bata Ya cika mata zuciyarta.
Da ƙyar ta aro jarumtar jan ƙafafunta da suka mata nauyi ta shiga cikin Gidan Duk matan gidan da ƴaƴan suna cikin ɗakunan su yanayin sallamar datai ne a hankali yasa ba wanda yaji sallamar tata.
Ta ɗaga labulan ɗakin umma ta shiga ɗakin da sallama, Umma ta zuba mata ido cike da tausayinta zaton umma duk jikin nata ne yasa ta koma haka.
"Sannu farha ina nan ina tunanin ki Yaya ƙarfin Jikin naki?"
Ta damƙe wayar tana Cewa.
"Alhamdulillahi Umma"
Daga haka ta nufi uwar ɗakan su ta aje wayar a saman sif gudun kada Umma ta gani, Ta zare hijabin Jikinta Ta fita tsakar gida banɗaki ta shiga ta gyara jikinta sabida priod ɗinta daya zo mata a yanzu.
Tana shigowa ɗaki taji Muryar yaro yana cewa.
"Wai ina fatima?"
Umma ce ta ɗaga murya tace.
"Shigo mana menene"
A lokacin Farha ta zauna a gefen tabarmar ɗakin yaron ya shigo da ƙatuwar leda a hannun shi fara mai ƙyalli.
"Wai wanine yace in kawowa Fatima amman ya tafi"
Umma tace.
"Wani yaya kamannin sa yake?"
Sabida duk ta ɗauka ko Salim ne.
"Dogo ne sosai fari amman banga fuskar shi ba"
Umma tai jimm dan Salim baƙi ne kakkaura.
"Ka mayar masa da ledar kace ba'a nan gidan take ba"
Yaron yace.
"Ai ya riga ya tafi tunda ya bani"
Daga haka yaron ya aje ledar yayi tafiyarshi.
Ikram ta buɗe baki cike da Ɗaga murya tace.
"Wallahi umma da gaskiyar yaron nan nima tunda kika aiken siyo suga ɗazu na ga Mutumin a ƙofar gida wai yace ina Masifaffiyar yayata, Kuma Umma mutumin kamar balarabe Duk da fuskarshi a rufe take"
Umma tai shuru ta zubawa Farha idanu wadda tai ƙasa da kanta Jikinta na rawa.
"Farha wanene kuma wannan Mutumin kada ki Ɓoye min gaskiya?"
Farha tace
"Wallahi Umma ban sanshi ba nima, Yace min wai a hanyar wajan aiki yake ganina in zan tafi, Amman umma ni ban sanshi ba Allah da gaske nake miki"
Umma ta janyo ledar ta buɗe.
Magungunan da aka rubutowa farha ne masu tsada amman ba a sako katin ciki ba, Sai Kaji manya gasassu Guda Uku da Lemuka masu sanyi.
"Baki san shiba ta yaya kika bashi katin maganin ki? Farha ba zaki jamin Cin mutuncin mahaifin kiba wallahi sai na tattare kayana na bar muku gidan in banda ke da Ikram da tuni na mance da barin wannan gida Salim bai cancanci haka daga gareki ba kada ki bari ruɗin Shaiɗan ya shiga zuciyar ki, Maza ki tattare masa kayanshi Kisan yadda zaki ki mayar masa dasu ni babu ruwana kuma ki kuka da kanki idan mahaifinki yaji"
Farha tahau kuka tana bawa Umma haƙuri.
"Allah umma ki yarda dani shine ya ƙwace Katin a hannuna ɗazu"
Umma miƙewa tayi tabar mata ɗakin.
Farha tasha kukanta Daga ƙarshe ko kallon ledar bata yi ba ta miƙe ta shige ɗaki ta kwanta.
Umma banɗaki ta shiga bayan ta fito Ikram tai musu shinfiɗa a rumfa suka kwanta dama su a rumfa suke kwanciya Farha ce ke kwanan Cikin uwar ɗaka dan komi zafi bata fitowa.
Umma ta jima batai bacci ba tsoron ta Ɗaya shine kada Allah yasa wannan Mutumi ya yaudari Farha ya rabasu da Salim dan so wani bin shu'umi ne Musamman ga zuciyar mace mai rauni.
Cikin baccinta taji Nishin wayar daya bata wadda ita Fushin umma ma yasa ta mance da ita.
Da sauri ta miƙe ta ɗauko wayar ta katse kiran.
Can wani sabon kiran ya kuma shigowa Numbern ba suna sai dai special number ce ta ƙurawa Numbern idanu kafin a hankali ta ɗaga kiran.
Wata irin Ajiyar zuciya Aliyu ya saki ta cikin wayar.
"So kike yau na kasa bacci my princess ina ta kiranki baki ɗaukar Min kirana ba Why?"
Ƙara damƙe wayar tayi tana Zare idanu tsoronta ɗaya kada Umma ta jiyo ta.
"Dan Allah ka rufamin asiri bawan Allah kazo ka amshi Abin da ka aiko kasa ummata tana fushi dani"
Ta faɗi Murya can ƙasa Kamar mai yin raɗa.
Aliyu ya Narkar da Murya kamar zai mata kuka ya soma Gaya mata mayaudaran kalamai wanda shi kanshi bai san ya iya suba Luf Farha tai tana ƙara nutso a saman gado Wayar kare a kunnenta wani irin Baƙon lamari ke bibiyar dukkan sassan jikinta.
Aliyu sai da ya tabbatar ya mata illah a zuciyarta sabida yadda yaji tana sakin Numfashi da alama kokawa take da zuciyarta Manna wa wayar Kiss yayi ya kashe kiran.
Tashin Hankali Farha a zaune ta raba dare ta kasa bacci duk motsi hoton Aliyu da yadda yake mata magiya ne yake mata yawo acikin idanunta zuwa asubah wata irin Mahaukaciyar soyayyar Aliyu tai mata mugun kamu Ko Motsi tayi shi take gani bata kallon ko wani namiji a zuciyarta sai shi taji ta aminta da Salim kawai kula shi take, amman soyayya yanzu ta fara yi da bawan Allah kamar yadda ta raɗa masa dan bata san sunan shiba.
Aliyu kwanciyar shi yayi ranshi fes batare daya ji dukkan wasu kalamai daya yiwa yarinyar yayi tasiri a zuciyar shiba.
Washegari haka ya shiga harkokin sa batare daya tuna da Farha ba Ranar Alhamis wadda ta kama rabon shi da farha kwana uku jirginsu ya ɗaga ƙasar chaina.
Harga Allah ya mance da ita tunda ya je chaina zirga zirga yake akan yadda sabbin motocin daya siya su zo Kamfanin shi wannan tasa baya samun Lokacin kanshi bacci ma baya isarshi sosai tsayin sati ɗaya ya ɗauka a chaina daga nan kuma ya wuce saudiyya.
Tuni soyayya da tunanin Aliyu sun huda dukkan sassan jiki da zuciyar Farha dama tun washegari da bai zoba Umma Ala dole tai amfani da Kajin ta bawa farha magungunan sai dai sam ta daina sakarwa farha fuska maganar aiki ma umma da kanta tace ita gaskiya farha ta haƙura da fita Tunda dalilin fita aikin wani ya fara biyota ita bata son Su shiga haƙƙin salim wannan hukunci yayi wa farha daɗi sabida haka bata ɗagawa kanta hankali ba suma mutan gidan duk sun ɗauka rashin lafiyar farha ne yasa Bata koma aikin nata ba.
Ba abin da Farha take sai aikin kwanciya Sai kuma zubawa wayar data ɓoye ido kullum Tunanin ganin Kiran Bawan Allah take tun tana sanya rai har ya cika sati ba shi babu wayar shi dole tai shahadar kiran layin nashi sai dai baya tafiya haka zata haɗa kai da gwiwa tana kuka ita kaɗai a ɗaki tana Allah wadai da zuciyarta data kamu da son wanda ko sunan shi bata sani ba ƙila ma Ƙarya yake mata yaudarar ta kawai yazo yayi.
"Ni farha meke damun kine? wannan jarababban bacci da ƙunci ke kaɗai ya isheni idan ma dan na hanaki fita aiki ne to kisha Kurumin ki ɗazu Mahaifin Salim ya turo Ƙanin sa nan da jibi zasu kawo kuɗin auren ki"
Farha bata ɗaga kai ta dubi Umma ba Hawaye ne ke gudu acikin Idanunta Ta kife a saman gado ranar wuni tayi kuka da magariba Salim yazo haka ta fita a zuciye duk haushin salim ya cika mata zuciyarta.
Duk maganar da salim ya gaya mata baƙar magana ce take Biyo baya Cike da mamaki salim ya dube ta dan hakan bai taɓa faruwa a tsakanin suba.
"Farha lafiya kuwa kodai wani ya ɓata miki rai ne?"
Ta ɗago a fusace.
"Kaga salim dan Allah ka rabu dani, Kaga in ka takura sai ka aure ni wallahi zan kashe kaina kowa ya huta"
Daga haka ta shige Gida da Ihu wanda yaja hankali mutan gidan tambayar duniya an mata taƙi cewa komai addu'a Umma ta dinga tofa mata zaton umma ko gamo farha tayi
Abin mamaki kwana tayi tana kuka ta wuni Kawu duk zafin sa sai da ya sauko yana tambayar ta Meke damunta.
"Kawu kada ka aura min salim bana son shi wallahi idan aka aura Minshi zan kashe kaina"
Salati Umma dasu Babarsu Ruƙayya suka ɗauka.
Kawu ya miƙe.
"Zan tanaji likkafani da makara wanda ina ɗaura Miki auren zan haɗaki da kaina na kaiki kabari amman ki sani ko gawarki ce sai taje gidan salim Butulu Dama nasan za'ai haka tunda uwarki ta ɗaure miki gindin aiki To duk baku isaba ni ba ƙaramin Mutum bane"
Kawu yabar ɗakin
Umma a zuciye ta rufe Farha da duka tana cewa.
"Ni zaki wulaƙanta to bara na kashe ki da kaina kafin Ki kashe kan naki"
Da ƙyar aka ƙwaci farha a hannun Umma Babarsu Hadiza ta kaita ɗakinta Ranar kowa ya wuni ba daɗi agidan.
Salim durƙushe a gaban Babansu wanda ya kirashi akan Batun kai kuɗin auren shi gidan su Farha.
"Baba ina ganin abar batun kai kuɗin nan"
Baban salim yace.
"Dalilin ka kana son naji kunyar aminina?"
Salim yay ƙasa da kanshi.
"Baba muna jin case a radio da kasuwa na illar auren dole Jiya naje wajan Farha da kanta taci alwashin na aure ta zata kashe kanta"
Subuhanallahi.
Baban Salim ya faɗa yana tafa hannun shi.
"Jeka zan nemeka"
Babar salim dake bakin Ƙofa tahau bala'i
"Tsinannu dama nasan za'ai haka sun gama ta tsar shi shine zasu zugata to Allah ya isa"
Baban Salim ya dube ta.
"Amman baki da hankali In da kin san waye Abubakar akan ƴaƴan sa da baki ce haka ba, Ɗane ka haife shi baka haifi halin sa ba mu dai addu'a zamu yi duk abin da yafi alkairi Allah ya zaɓa bama son ai abin da za'a zo ana kuka"
Baban Salim Mutum ne mai sauƙi wanda halin shi salim ya ɗauko ba irin mahaifiyar shi masifaffiyar mace ba.
A ranar Baban Salim ya sami kawu a Gida bayan sun gaisa yace masa.
"Malam Abubakar nazo ne da maganar yarannan ɗazu salim yace Min fatima tace in ya aure ta zata kashe kanta, To duk maganar haka bata taso ba ka zaunar da ita ta gaya maka wanda take so in yaso sai ayi dashi ƙila rabo ne ke kiranta in aka ja za'a iya rasa rai"
Kawu ya dubi Baban salim.
"Duk wanda aka rasa kwanan shine ya ƙare nifa ba zata mayar dani ƙaramin Mutum ba Munafurci ne nata dana uwarta Sabida haka bama kawo Kuɗi ba gobe gobannan ina son ka turo da sadakin salim na ɗaura musu aure da fatima"
Baban salim yace.
"Nagode nasan duk ƙauna ce ta saka kace haka ni nafi ka hange akan wannan matsalar, saboda haka ayi haƙuri a tuntuɓi yarinyar wa take so a bata shi ni dai nine mahaifin salim to in dai daga wajena Auren shi zai Ɗauru da fatima to na janye Allah ya haɗa kowa da rabon shi"
Duk yadda kawu ya kafe Baban salim yaƙi sabida Yaji tsoron furunci Farha haka sukai sallama da Kawu abin ba daɗi dan kawu ya zuciya haka yayo gidan ya faɗo ɗakin Umma A ranar anga tashin hankali agidan dan kawu cewa yayi umma sai ta bar masa gidan shi ita da Farha da ƙyar su Halifa dasu Babarsu Ruƙayya suka janye kawu Daran Umma kuka Farha kuka Ikram kuka umma taiwa farha dukan da har sai da tai mata tarkaɗe Amman zuciyar farha bata saduda ba zuwa asubah kawu ya tara kaf Matan shi.
Da Ƴaƴan ya dubi farha.
"Na baki daga yau zuwa gobe Kiwa wanda kike so magana yazo gobe da sadaki na ɗaura muku aure idan ya wuce gobe kuma zan bawa duk wanda naga dama sadakar ki Burunku ya cika keda mahaifiyarki"
Daga haka yabar wajan.
Umma bata ko kalli farha ba tayi ɗaki Farha ta rasa yadda zatai Haka ta shige ɗaki taita gwada numbern Shi yaƙi shiga.
Har Yamma abu ɗaya take taƙi fitowa waje sabida tana tsoron Hararar umma.
Kamar da wasa Ana kiran magari ba ta kira Numbern tana ringing amman ba'a ɗauka ba.
Aliyu daya sauka yau da rana tunda ya shiga part ɗin shi da yayi wanka bacci kawai yake bai tashi ba sai la'asar yayi sallah Ya Nufi Gidansu Mami abisa tirsasawar Ammi har Magariba suna tare da Mami yana kallon wayar shi na ringing da tsohon layin shi daya bawa wannan yarinyar wadda ya manta ta kiranta ne ma ya sanya shi tuna ita ɗin wacece yana kallo kiranta yana shigowa amman yaƙi ɗauka sai da yayi sallar magariba sannan ya baro gidan su mami wadda tace cikin satin nan zata dawo ɗakinta.
Yana driving yaga wani kiran nata ya ƙara shigowa wayar shi yayi parking a gefen titi ya ɗauki kiran.
Muryar Farha cikin kuka take cewa.
"Ina ka shiga bawan Allah ka barni cikin bala'i dan Allah ka dawo gare ni"
Kuka ne yaci ƙarfin maganar tata.
Kukan mace yana ɗaya daga cikin abin da yake san yashi Jin rauni fiye da zato.
"Ki haƙuri bari na zo"
Daga haka ya katse wayar ya tada Motar yayi unguwar su a bakin layin su yayi parking Yaja Face mask Ɗin shi ya rufe fuskarshi ya taka da ƙafar shi har bakin Ƙofar gidan ya fito da wayar ya kira ta.
"Gani nazo"
Daga haka ya kashe.
Sum sum Farha ta fito daga ɗakin su tayo ƙofar gida wajan shi da sauri............*RABO YA RANTSE! littafin kuɗi ne 500 naira zuwa wannan asusun bankin 0078174806 Sterling bank, idan kuma kati ne mtn card na 500 hoton sa za'a ɗauka a turo,shaidar biya 09022260850*
*RABO YA RANTSE...!!*🌹
*NA*
*AUTAR MANYA*
ADABI WRITTER'S ASSOCIATION
*16*
Tana zuwa gaban shi ta zube a ƙasa tana sakin marayan kuka, Hankalin shi a matiƙar tashe ya tsugunna a gabanta ya sanya hannun shi ya kamo Tattausan hannunta ya zuba mata Girman idanun shi batare daya ce mata ko mai ba sai binta yake da kallo kamar zai cinyeta ɗanya.
Kukan take Babu ƙaƙƙautawa Tuni Kan Aliyu ya fara juyawa in da abin da yafi tsana a duniya bai wuce kukan mace ba sabida tafarar ɗaya yake sanya masa Rauni.
Da ƙarfi ya damƙe hannunta wanda Hakan ya sanya ta sakin wata irin ƙara tana yarfe hannun sabida tun Dukan da umma tayi mata take zaton Hannun nata Ya sami targaɗe.
Kula da yayi hannun na mata zafi ya sanya shi ya sakar mata shi.
"Shiii Be quiet and let's talk"
Ya faɗa yana sakin numfashi mai ƙarfi.
Sannu a hankali take rage sautin kukan nata kamar yadda ya buƙata.
Muryarshi can ƙasan maƙoshi ya furta mata.
"What made you cry?"
Goge idanunta take da hannunta mai lafiya muryar ta a dashe ta soma yi masa magana.
"Kawu ne yace in baka aiko an ɗaura min aure da kai gobe ba, zai ba dani sadaka"
Aliyu ya zare ido with full surprise.
Kafin yayi magana ta cigaba da cewa.
"Tun jiya umammu take dukana har targaɗe tai min"
Tana faɗin haka ta kuma fashe masa da kuka.
Yayi ƙasa da murya kamar mai raɗa Ya ƙara matsowa gaban ta a yadda yake a tsugunnen.
"Duka garin yaya akai haka? dama shi kawu ya sanni ne?"
Ƙunshe fuska tai Cikin jin kunya tace.
"Dan nace bazan auri Salim ba"
Cikin Tattausar Muryar shi yace.
"Dalilin ki? kodai kina sona ne kema?"
Ƙasa tai da kanta ta ɓoye fuskarta da hannunta wanda ya bashi tabbacin zargin dake zuciyarsa na ta bijirewa mahaifan tane akan shi.
Ya saki wani ƙasaitaccen Murmushi ya Leƙa fuskarta data ɓoye.
"Baki sanni ba Fatima, Ko sunana bani tunanin Kin sani bare anguwar mu bare sana'ata kawai tashi ɗaya ki bijirewa wanda da bakin ki kika ce tun kina ƙarama yake miki hidima Why are you doing this, Fatima?"
Ya faɗa mata hakan cike da mamakin ta tare da jinjina girman wauta da ƙuruciyarta.
Muryarta har zuwa lokacin bata Dawo daidai ba may be kukan data sha ne yayi Mata haka da muryar tata.
"Bawan Allah! Koda acikin Bukka kake rayuwa namun daji suna kewaye ka ni zan bika mu rayu tare, Ni dai na san ba zaka cutar dani ba, Kawu yace in baka aure ni ba zai bada ni sadaka kuma kai da bakin ka kace kana sona zaka aure ni"
Shuru Aliyu yayi gaba ɗaya ta gama kashe masa jiki da kalamanta wani irin tausayi yarinyar ta bashi amman daya