Showing 27001 words to 30000 words out of 124441 words
customers dinku delivery cikin sauki acikin Leda gari yayi zafi*🤣
*Muna aika kaya ko'ina cikin aminci d Amana*
***
*Kazar Kwanci...*
Duk irin yadda Sadiya ta so ƙin bin su zuwa liyafar hakan bai samu ba tunda Zahra da su Meenat ɗiya ga Anti Amarya (Zulfa'u, matar aminin Malam, Alh Abubakar da suke kira da Abba) sun matsa akan ta shirya su wuce, a dole bayan Inna ta sanya baki ta miƙe ta shirya cikin ankon da kowa ya saka. Ba ta shafa komai a fuskarta ba amma ɗinkin ya zauna ƙwarai a jikinta, ya fiddo da ainahin surarta mai kama da na cocacola.
A can kuwa biki ya yi biki, duk irin nishaɗin da ke saman fuskokin jama'ar wurin babu wannan farin cikin a ɓangaren Hajara don har a sannan da take zaune saman wuri na musamman da aka tanada dominta kaɗai a wannan rana, ta kasa mance barazanar da Nusaiba ta yi mata. Saƙe-saƙe take yi na yadda za ta ɗau mataki a kai.
 Hankalinta bini-bini yana kan wayarta, kula da rashin nutsuwarta ne ya sa Safiyya da kanta ƙarasawa ta yi mata raɗa a kunne.
"Wai meke faruwa? Don Allah ki saki jikinki hankalin kowa fa yana kanki. Wasu sai su É—auka ko akwai matsala ne."
Hajara da ta ji abin ya haÉ—e mata da kewar Mamanta, kawai sai ta marairaice fuska.
"Mama nake tunowa."
Safiyya ta ji hakan a ranta ita ma, dama kuma ta yi wannan hasashen. Kwalla suka cika idanunta, ta yi saurin dauke su da yatsu.
"Addu'a da haƙuri zamu cigaba da yi Autar Mama."
Daga haka ta bar wajen. Ba jimawa Ango ya iso da tawagarsa, ranar dai an yi ruwan kuɗaɗe na liƙi. Abin da ya baƙanta ran ire-iren su Sadiya bai wuce zagewar da ya yi yana tiƙa uban rawa ba. Ta kula ita Anti Hajarar ma rangaji kawai take yi don dama gaskiya can ita ɗin ba ta kasance mazari ba. Don haushi ko tashi ba'a yi ba suka bar wurin ita da Zahra'u.
Bayan tashi daga taron, a daren kowa ya watse sai na jiki sosai kuma na nesa da suka kwana a gidan Malam da zummar rakiyar Amarya É—akinta a washegari.
***
Kowa ya yi zaman kari, kofuna É—auke da kunu da fanke kawai kake gani yana gilmawa ana yi ana hira.
 Shigowar Malam tsakar gidan daga shi sai doguwar jallabiyarsa ya sanya aka hau gaishe shi. Babu wacce ya amsawa, anan suka kula ransa a tsananin ɓace yake don jikinsa har rawa yake yi sosai.
"Hajara! Hajara!! Kina ina!"
Sunan Hajara da ya ambata sai da ya sa dukkansu miƙewa a ɗan firgice, kowa na neman ba'asin.
Hajara wacce kamar a mafarki ta ke jin kiran na Mahaifinta ga kuma muryar Husna na kiran sunanta da jijjiga ta, kusan a razane ta buɗe idanun. Ta miƙe zaune, ba tare da ta ƙarasa sauraron Husnar mai shaida mata Malam na kiranta ba tunda babu buƙatar ƙarin bayani.
"Na'am." Ta amsa sadda ta fito daga ita sai doguwar rigar bacci iyaka gwuiwa mai kauri. Malam wanda a lokacin har Inna na tsaye tana tambayarsa ko lafiya amma bai kalli kowannensu ba. Ransa ya yi ɓacin da idanunsa suka makance, kunnuwansa suka toshe, ba ya tuna su waye a wurin. Hajara kirjinta ya faɗi sadda ta ke duban Malam wanda idanunsa suka kaɗa jawur, wayar hannunsa ya buɗo bidiyo ya ɗaga da hannunsa zuwa saitin fuskarta yanda za ta gani dakyau.
"Ke ce wannan? Dagaske ke ce?"
Ya tambaya murya a dusashe. Ji ta yi jiri ma neman kayar da ita, kowa a gurin kuwa ya hau salati, waɗanda ba su gani ba suna zuro kai, yayinda Gwaggo Atine hannu ta saka ta karɓi wayar a hannun Malam.
"Innalillahi wa inna ilaihir raaji'un! Na shiga uku ni uwar Gambo, wallahi Hajara ce."
Sai kawai ta fashe da kuka tana kai wa nan, Inna wacce ta ga bidiyon don a gefenta Hajara ke tsaye ba a hayyaci ba. Safiyya ita ma kukan ta saka ga wani irin tsantsar mamaki da ya rufe ta. Malam ya shaƙo wuyan Hajara.
"Don ubanki abin da kike yi kenan idan kin fice a gidana da zummar aiki? Kin cuce ni Hajara! Kin kuma cutar da kanki! Allah wadaran wannan halin naki!"
Daga haka ya hankaɗe ta ya fice zuwa falonsa. Hankalin kowa ya tashi, Inna ce ta karɓe wayar ta bi bayan mijinta ranta babu dadi ga hawayen da take fitarwa. A tsakar gidan kuwa aka yi wa Hajara caa kowa na faɗa. Kowa faɗi yake ta ɓata wayonta.
"To kodai dama wannan ne dalilin da yasa ake fasa auren nata a baya?" Maganar ta fito daga bakin wata matar ƙanin Malam da suka hada Uba wacce bakinta ba ya shiru.
"Uhum, ai zai ma iya kasancewa hakan ne. Baiwar Allah Mairamu an ɗauki haƙƙinta babu gaira ba dalili, ana zaton wuta a maƙera..."
"Sai aka gan ta a masaƙa." Wata ta ƙarashe zancen da wata da suke kira Iya Sarai ta ɗauko. Nan da nan hayaniya da cece-kuce ya shiga tashi kowa na faɗin albarkacin bakinsa, ita kuwa Hajara sai Safiyya ta ja hannunta suka shige ɗaki ta rufo.
***
"Haba Malam, ya kyautu ace ka fallasa wannan zance a bainar jama'a? Yanzu..."
"Mairamu ki bar ni da zancen nan don Allah. Ki bar ni na ji da abin kunyar da yarinyarnan ta jima tana jaza min." Faɗin Malam ɗin har sannan fidda huci yake kawai na zallar ɓacin rai.
"Assalamu alaikum."
Inna da Malam suka dubi mai sallamar, Hashimu ne wanda Malam din ya yi wa kiran gaggawa, ba ma shi ɗaya ba, gaba ɗayansu ya yi wa wannan kiran. Ya ƙaraso kana kallonsa ka san cewa a gigice ya ke don ko wanka bai yi ba, riga ce tshirt a jikinsa sai wandon shadda da ya zura a saman gajeran wando na ciki. Allah ya taimaka ma a mashin yake.
Ya gaida Inna ta amsa gami da miƙewa ta ba su wuri. Malam ya fiddo wayarsa, jikinsa duk ya mutu a sannan saboda damuwar da ke cin zuciyarsa da tsananin baƙin ciki. Abin da ya fi masa ciwo ma bai wuce na samun irin wannan banzan halin daga wacce bai taɓa zato ba a yaran. Hashim ya sanya hannu ya karɓi wayar, nan ya shiga kallon bidiyon ƙanwarsu Hajara tana ta shafa jikin wani namiji ita ma ana shafa ta ɗin. Ba a nan abin ya tsaya ba, sauran abubuwan ma da suke biyo wa baya babu kyan gani.
"Innalillahi..." Hashim ya furta har ƙarshe yana mai miƙawa Mustafa wayar wanda tuni ya gama gani tun wayar tana hannun ɗan uwansa. Yana tsaka da kallon ne ya shigo falon, ganin yanayinsu bai ko iya kwakkwarar sallama ba ya zauna gefen Hashim yana kai idanunsa kan abin da yake kalla.
Gaba ɗaya zuƙatansu suka ɗauki zafi. Hajara ce dai? Har a lokacin Mustafa tantama yake yi dalili kenan da ya ƙara buɗo bidiyon yana kallo sai ya yi maza ya kife wayar. Miƙewa ya yi jikinsa har wani rawa yake.
"Koma ka zauna."
Umarnin da Malam ya ba shi kenan. Ba da son ransa ba ya koma ya zauna, Hashim tsabar ɓacin rai ma kalma ɗaya ya gagara furtawa.
Ko mintuna goma ba a cika ba suka haÉ—u gaba É—aya mazan har Zakari da Anti Hafsatu wacce dama ta gama shirin tahowa gidan, kiran Malam ya tashi hankalinta ba kaÉ—an ba. A sannan har Hajara É—in da Safiyya sun shigo har da Inna da Malam ya sa a ka kira ta.
"FaÉ—a min Hajara, faÉ—a min da bakinki cewa ke ce a wannan faifan ki ke cuÉ—anya da wani namijin da ba muharraminki ba."
Malam ya ƙara furtawa da wani irin sanyi na murya wanda za ka fahimci tsananin ɓacin rai ne ya haifar. Hajara da ta ci kukanta ta ƙoshi ta rarrafa gaban Malam.
"Don Allah ku yafe min. Na yi kuskure, sharrin shaiɗan ne na tuba ba zan ƙara ba."
Wannan ya ƙara wankewa yayyunta tantamarsu, dagaske ita ce, ba wai gizo idanunsu ke musu. Kuma ba wai kamanni ba ne ko kuwa a ce haɗawa aka yi. Ta amsa laifinta tabbas, wannan ya na nuni da cewa ita ɗin ce. Anti Hafsatu ta furta kalmar La'ilaha illal lahu har ƙarshe, Inna kuwa lamarin ya gama sanyaya jikinta. Ta tuna sadda ta ke jin rashin nutsuwa a yanayin irin yadda Hajara ke tafiyar da rayuwarta, har Malam ɗin ta yi wa ƙorafi amma ya hau ta da faɗa sosai tamkar zai ari baki wai don me ta ke zargin ɗiyarsa. Shi ɗin ya yarda da tarbiyyar da ya yi wa yaransa ba za su taɓa aikata mummuna ba.
"Mairamu ki gafarce ni, ki yafe min. Haƙiƙa ke ce kika ankara kamar da sauyi a yanayin da Hajara ke gudanar da rayuwarta har ki ka sanar da ni sai dai ni kuma makahon yardar da na yi wa yaran ya rufe min idanu na kasa yarda, na kasa ganin cewa akwai kaddarar da za ta rigayi fata."
Malam ke zancen kamar ya shiga zuciyar Inna ya ji tunanin da ta ke. Hajara wannan abu ya yi mata zafi ainun, wai yau a kanta ne ake wani ba matar nan haƙuri. Wato munafukar ta gano wasu abubuwan shi ne don munafunci ita ba ta ce mata komai ba amma har ta kai wa Malam ƙararta.
"Bakomai Malam, yanzu duk maganar nan ya dace a yafe wa yarinyar nan tunda dai ta yi aure kuma gidan mijinta za ta shiga. Don Allah kar ka zafafa a kanta har ka kasa sanya mata albarka a aure."
Faɗin Inna cikin kwantar da murya. Safiyya dai wannan karon ba ta Inna take yi ba, ita kunya ma take ji na yanda duk ta dinga zagi da zargin Inna kan hana ƙanwarta aure ga shi nan gaskiya ta yi halinta.
Malam faɗa sosai ya yi wa Hajara ya kuma ƙarashe da faɗin.
"Na rantse maki kuma, babu inda za ki je da Husna kamar yanda a farko kika roƙi wannan alfarmar a wurina na amince. Kuma kaf cikinku idan an miƙa ta ɗakinta ban yarda waninku ya koma ba idan kuwa ku ka tsallake umarnina ban yafe ba. Sannan ki gaggauta neman gafarar Mairama game da zargi da mugun ƙazafin da ki ka dinga jifanta da shi cewar ita ke yin surƙullen da ake fasa aurenki. Hajara, ki ka taka ki ka bar gidan nan kar ki sake ki dawo sai idan ni da kaina na neme ki. Maza tashi ki gurfana gaban Mairama ki nemi gafararta!"
Ya ƙarashe a tsawance. Inna ta girgiza kai. Za ta yi magana Malam ya dakatar da ita ta hanyar ɗaga mata hannu dole ta yi shiru. Hajara da ke kuka kamar ranta zai fita babu abin da ya fi baƙanta mata irin wai da Malam yace ba za ta tafi da Husna gidanta ba. Sannan ta durkusa ta ba Inna haƙuri.
Ganin idon Malam ya sa ta mike ta je har gaban Inna ta durƙusa gami da furucin.
"Ki yi hakuri." Iyakar abin da ta ce kenan amma ƙasan ranta zagin Innar kawai take yi. Inna ta ce babu komai. Abin da ya ba Hajara mamaki bai wuce ganin da ta yi wa Safiyya ta ƙarasa har gaban Inna ta durƙushe ba tare da an nemi ta yi hakan ba ta ce.
"Don Allah Innar Husna ki yafe min, na yi maki munanan kalamai akan Æ´ar uwata. Na tuba ki gafarta min. Zan gyara zamana da ke daga yau."
Inna jin abin ta yi kamar a mafarki, na Hajara bai shige ta kamar maganganun Safiyya ba. Kalmar nan ta zan gyara zamana da ke ya yi mata daÉ—i ya kuma zo mata a bazatan da ya sanya hawayenta fita. Ta kama hannun Safiyya.
"Ya wuce Safiyya, komai ya wuce."
Mazan ma (idan an cire Zakari wanda dama shi ba shi da matsala da Inna), koda ba su furta wani abu ba, amma fuskokinsu sun nuna tsantsar nadamarsu bisa zargi da cin fuskar da suke yi ga Inna wacce ko gaishe ta sai sun ga dama suke yi idan sun zo wurin Malam. Tsakar gidan ma sai su jima ba su leƙa ba duk don kar su haɗu da ita kawai. A yau kam dagaske suke jin nadamar komai. Komai da ya faru tun mafarin aurenta da Malam.
***
Har aka yi shirin kai Hajara zuƙata gaba ɗaya a cunkushe suke, kan kace me kuma magana har ta yaɗu makwafta sun sami labari. Wai sai ga shi a na zuwa taya Inna murnar fita da zargi har da masu neman gafatarta. Husna jin hukuncin Malam ta yi bai mata wani zafi ba don ita ma tana cike da mamaki da jin zafin abin da Antinta ta aikata ga kuma tausayin Innarta don a cewarta Antin ta yaudare ta sosai. Koyaushe cikin nuna mata take yi ai Innar ce dalilin da ya sa ake fasa aurenta, ita kuma idanu rufe take jin haushin Innarta. Sai ga Husna ta rungume Innar tana kuka sosai tana kiran ta yafe mata. Abin da ya fi yiwa Inna daɗi kenan, Sadiya kanta sai da ta yi hawayen farin ciki. Ta kuma ji duk wani ƙunci da aka cusa mata a zuciya lokutan auren nan duka sun wanku tas. Allah ne dama mai wanke bayinsa daga zargi, yau kam ya karɓi addu'arta ya wanke Innarta.
  Haj Mariya da aka yi komai a gabanta kuma har da ita cikin masu kai Hajara a hanya faɗi take.
"Shiyasa munana zato ga ɗan uwa musulmi ba shi da daɗi. Ke kuma Hajara matsayina na Uwa a gareki, ina ƙara jaddada maki cewa ki ji tsoron Allah a zamantakewar aurenki. Abin da ya faru ya riga ya wuce, kar ki ƙara yarda shaiɗan ya yi maki famfo wajen saɓon Allah. Allah ya kyauta ya tsare gaba." Shi ne abin da kawai ta ce sauran jama'ar da suke motar suka amsa da amin idan ka cire Gwaggo Atine da ko magana ma kasa yi take tsabar kunya da nauyi. Har a sannan ta rasa da wane ido za ta dubi Inna Mairamu ta nemi gafararta don ta yi mata wulakanci fiye da zato akan abin da ba ta da haƙƙi.
***
 HUZAIF ABUBAKAR SHARAƊA...
©Rufaida Umar
Huzaif Abubakar SharaÉ—a
"Ga Yaya Huzaif! Ga Yaya Huzaif!!"
Abin da ya dinga shiga kunnuwan Haj Mariya kenan tun tana kicin tana duba miyar da take yiwa Abba kasancewar ba ta taɓa barin ƴar aiki ta girkawa mijin nata abinci. Abban ma ba ya so, daga ita har Zulfa'u bai aminta su sakarwa ƴan aiki girkinsa ba. Rage wutar miyar ta yi ta fito falon fara'arta ta kasa ɓuya. Ƙarfe biyar da mintuna na yammacin ranar Talata, ta kasa tsayuwa iyakar falon ta nufo ƙofa za ta ƙarasa tsakar gidan don ji take kamar zolayar yaran ce kawai amma kuma da kanta ta ƙaryata tunaninta sadda ta yi arba da Amir ya shigo falon ɗauke da babban akwatin kaya na matafiya, kafin ta kai ga cewa wani abu sai ga su Amira da Meenat da ta rataya jakar makaranta mai adon ja da baƙi ƙatuwa. Sallamar Huzaif ya biyo baya, yana riƙe da hannun Auta Zee Mama da kuma na Affan. Fuskarsa gaba ɗaya yanayinsu ɗaya da na mahaifinsa, ba shi da hasken fata, baƙi ne kuma dogo kakkaura. Yana sanye da dogon wandon jeans baƙi da jan tshirt sai farin madubin idanunsa dake ƙara masa ƙarfin gani (medicated). Wani sassanyan murmushi ya ke kashe Mamin tasa da shi kafin ya saki hannayen yaran ya ƙarasa da sassarfa ya ɗan rungumo ta gefensa.
"Mamina." Ta runtse idanu hawayen farin ciki suka zubo mata. Sai ta share su, yaran gaba ɗaya suka ji sun burge su matuƙa. Ya saki Mamin ya riƙe hannunta yana ta kallo da murmushinsa wanda har kana iya hango fararen haƙoransa reras.
"Sannu da zuwa Huzaifa, barka da sauka. Ashe shiyasa na kasa samunka a waya? To lale marhabin."
Ya yi ƴar dariya. Nan da nan Mamin ta sa Amir ɗauko muƙullin ɗakin Yayan nasu, ta saka su Meenat da Amira zuwa gyara. Ta rasa ma me za ta ba shi, Husna tuni ta yi kicin ta kawo mishi ruwan sanyi da lemon roba da kofi a faranti mai ɗan tsawo ta ajiye a gabansa. Shi kuwa mamakin girman yaran yake yi don gani ya yi kamar waɗanda ake jan su da igiya. Sai ya ga ashe hotunansu da yake gani ma rage musu girman suka yi. Ba kamar a fili ba.
Nan da nan Mami ta ɗauki waya ta kira su Radeeya ta sanar da su dawowar ƙanin nasu. Babu damar zuwa ga kowaccensu don ba su sanar da mazajensu ba, dole ta wayar suka gaisa da zummar za su iso gidan washegari. Mami kuwa hira ce ta ɓarke tsakaninsu har sai da Husna ta yi mata tuni da tukunyarta da ta ɗan fara kamawa, haka ta tashi shi kuwa ya wuce sashinsa don watsa ruwa. Babu sallah a kansa, mutum ne mai kokarin sauke farillah wannan ya sa tun a Airport ya rama sallar dake kansa.
Abba ma sai dawowa gidan ya yi ya ga É—an nasa, sosai ya yi murna. Mami har kunya ta ji don ita shaf ta mance ma ta sanar da Abban ta waya. Nan da nan aka hau shiryawa Huzaif abinci. Ya je har sashin Anti Zulfa'u sun gaisa duk kuwa da cewa tana cikin Æ´ar tarbarsa a tsakar gidan da ya shigo.
Ranar dai ga shi ga iyayen nasa mafi soyuwa a rai, kusan raba dare suka yi hira, a karshe Abba ya ce ya je ya huta tunda ba yau É—in ce kaÉ—ai ta rage musu ba.
***
Kwanaki uku kenan da tarewar Hajara, sai dai har a sannan tabon da ta bar wa mutan gidan bai gama warkewa ba. Koda dai a ɓangaren Sadiya, ba ta taɓa hasko cewa Anti Hajara za ta aikata mummuna kamar wannan ba. Abin da ya yi mata daɗi a gefe shi ne irin yanda jama'a suka bar zargin Innarta da hana ruwa gudu ba. Damuwarta bai wuce alwashin da Malam ya ci ba na cewar babu wata ɗiyarsa da za ta ɗara sakandire ba tare da ta kasancewar tana ƙarƙashin inuwar aure ba. A cewarsa daga ita har Husna babu mai ɗara karatun