Showing 48001 words to 51000 words out of 124441 words
cikin nutsuwarta sosai hakan ya sa ba ta kula ba.
Sai da suka kammala komai Malam ya kama hanya suna tafe yana jan su da hira, ita dai Sadiya ganin ba hanyar gidan Yayansu Hashim aka ɗauka ya sa ta kasa shiru ta ce.
"Malam an fasa zuwa gidan Yaya Hashim ne? Ko wani wurin zamu biya?"
"Aa Sadiya, gidan Yayarki Hajara za ku je nan da sati kafin Innarki ta dawo."
"Innalillahi..." Ta kasa ƙarasa saboda ba ta ma san cewa a fili ta furta ba, ƙirjinta sai da ya bada dam, wani baƙin ciki da tsoro ne suka dirar mata lokaci guda.
Shi kuwa Malam da tsananin mamaki ya ɗan waigo kujerar bayan ya dubi Sadiya kafin ya maida duba ga kallon titi.
"Innalillahi fa ki ka ce? Akan zuwa gidan ƴar uwarki? Sadiya?"
Haba ai sai Malam ya shiga faɗa, yi yake kamar ya ari baki wai bai san haka Mairama ta yi nisa a ginamata tsanar Hajara ba sai yanzun! Ya kuma rantse ba don ba ta kammala gaba ɗaya jarrabawarta ba da sai ya ce ta koma gidan da rayuwa ya ga ta tsiya. Ita dai Sadiya hawaye kawai take fitarwa tana ba shi haƙuri. Husna ma ta shiga taya ta lallaɓa Malam ɗin da ban hakuri amma a can ƙasan ranta kamar ta kwashe da dariya ta ke ji. Koda suka isa ajiye su kawai ya yi sannan ya juya, a farfajiyar gidan Husna ta dube ta fuskarta itama duk ya jike da ruwan hawayen da ta ƙaƙalo tun kafin su sauka a motar ta riƙo hannunta tace.
"Don Allah ƴar uwa ki yi haƙuri, na rantse ba ni nace mu je ba. Ashe wai Anti Hajara ce ta kira ta roƙi Malam ɗin mu zo gidanta."
Sadiya ko kallonta ba ta yi ba ta janye hannunta ta goge fuskarta da tuni ya yi jazur saboda kukan da ta ci. Husna ta yi gaba tana share nata hawayen da murmushi ɗauke saman fuskarta.
Hajara dake tsaye a ƴar barandar sama tana hangensu, wani murmushi ta yi na zallar tsana ga Sadiya. A fili ta ce.
"Barkanki da zuwa gidana Sadiya, barkanki da shigowa inda zan tarwatsa dukkan wata alaƙar da ke tsakaninki da Huzaif. A sati ɗaya kacal! A sati kawai komai zai faru ya ƙare. Dukkan abin da zai biyo baya a rayuwarki, ba zai taɓa daidaituwa ba."
Daga haka ta juya da nufin sauka ƙasa don tarbar shalelarta Husna.
Sadiya na tsaye a gefe tana karewa gidan kallo, tabbas babu ƙarya an zuba uban dukiya a gidan kamar yanda ta ji labari. Tun da take a duniyarta ba ta taɓa kawowa ma akwai rana irin ta yau da za ta zo wai ita da kanta, da rai da lafiyarta ta taka gidan Anti Hajara ba.
Tana kallon yanda Husna ta ruga a guje kamar wata ƙaramar yarinya suka rungume juna da ita, da ace da hurumin dariya a lokacin da tana da tabbaci zai suɓuce mata sakamakon riga da wandon da Hajara ta tsuke a ciki ita a dole ƴar gayu ta ƙarshe. Fatarta dai ba ƙarya ta ƙara gogewa sosai, kana kallonta ka san tana cikin ni'imar daula. Ko kallonta ba ta yi ba, ta ja hannun Husna suka haye sama. Dama ai ta san ta gayyace ta ne don ta wulaƙanta ta, sai da ta ji ƙafafunta na neman sagewa saboda tsayuwa ta nemi gefe guda a kasan kafet ta yi zamanta gami da fidda wayarta, har a lokacin Huzaif bai ce mata uffan ba kuma yana online, har status ta ga ya ɗora na bidiyon wasu kifaye a ruwa. Sai ta ji jikinta ya yi sanyi, amma kuma ta tsinci kanta da yi mishi uzuri, wasu lokutan mutum zai ga sako har ya buɗe sai wani abin ya ɗauke hankalinsa ya manta da saƙon. Wasu lokutan kuma saƙonnin ke yawa don haka ta sauke ajiyar zuciya ta yi mishi sallama. Akan idanunta ya buɗe har ta ji wani sanyi, shiyasa yi wa mutum uzuri ke da daɗi, wataƙila ma jira yake ta yi mishi magana.
"Anti Sadiya, ki taso muje ɗaki."
Muryar Husna ta ɗauke hankalinta. Sam ba ta ji dawowarta falon ba daga benen da suka bi suka haye sama a ɗazun, Sadiya wacce har lokacin take jin zafin Husna don ta kasa yarda ba ita ta cewa Malam ya kawo su nan ba saboda a iyakar tunaninta babu wani dalili da zai sa Hajara ta neme ta a gidanta.
Mikewa kawai ta yi ba tare da ta ce mata uffan ba tana jan akwatin kayansu. Hannunta Husna ta riko gani da marairaicewa. Rantsuwa ta shiga yi akan ba ta da masaniyar ya hakan ta faru, Sadiya ta ɗauke kai.
"Ya wuce ai. Muje."
Daga haka ta ɗan yi gaba, Husna ta harareta ta baya kafin ta bi bayanta su jera suna hawa matattakalar. Sai a nan Sadiya ta ga wata sabuwar duniyar, ashe dai ɗazun ba ta ga komai ba. Tafkeken falo ta gani wanda ya sha kayan alatu, sai ƙofofi har biyar da ba ta san meke cikinsu ba. Babu ɗaya da suka shiga ta ga sun nufi wani ɗan ƙaramin lungu, wata ƙofa Husna ta buɗe mata suka shiga. Sanyin ac ne ya soma ratsa Sadiya kafin ƙamshin Airfreshner ya mamaye ƙofofin hancinta. Gadon da komai kwalliyar fari da ruwan hoda aka yi.
Cike da walwala Husna ta dube ta.
"Wannan ɗakina ne a gidannan. Komai da ki ka gani a ciki, da sunana aka sanya shi."
Sadiya ta yamutse fuska.
"Wannan bai dameni ba Husna. Sallah nake son yi."
Husna ta yi dariya tana ɗan riƙo hannun Sadiya.
"Haba mana ƴar uwata, please ki saki jikinki da gidannan. Na rantse Anti ba ta da matsalar komai. Za ki ji dadin rayuwa a gidannan. Kamar a turai haka za ki ji, babu wanda zai takura maki, sai abin da kike so za ki..."
"Ya ishe ni haka Husna. Kar ki ƙara sanya ni tunzura. Na ce maki sallah zan yi ko?"
Husna ta ɗan turo baki kaɗan ita a dole ba ta ji dadi ba. Da muryar shagwaɓa ta nuna ƙofar banɗaki da yatsa.
"Ga fa toilet ɗin can."
Girgiza kai Sadiya ta yi, Husna ba za ta taɓa sauyawa ba. Ta shige banɗakin, abin duniya duk ya ishe ta don ita kam har ga Allah komai na Hajara bai burge ta, ciki kuwa har da wannan daular. Wane jin daɗi za ta samu ta ɓangaren matar da ba ta girmama mahaifiyarta? A jikinta take ji ma yadda Hajarar ke yi wa Innar ladabi a yanzun na ƙarya ne.
Husna ganin ta shige da sauri ta ɗauki wayar Sadiy, dama ba ta saka lock a wayar. Kai tsaye saƙon Huzaif ta shiga a whatsapp. Ganin ya aiko da saƙo ta buɗe da sauri. Sallama ce ya amsa kawai, cikin hanzari ta goge ta bar iyakar maganar Sadiya. A yadda ta san ƴar uwarta sam ba ta da naci akan komai, idan har ta ga bai amsa ba zai wahala ta ƙara magana duk kuwa da ta lura tana son Huzaif ɗin sosai.
Kai tsaye ta fice daga ɗakin ta koma wurin Antinta don soma aiwatar da abin da ya kawo dalilinsu na matsawa da zuwan Sadiya gidan.
A tsorace kuma ido a waje take duban Antinta Hajara, girgiza kai ta shiga yi tana mai ja baya. Riƙo hannunta Hajara ta yi ta maido ta gami da jan ta su zauna gefen gadon.
"Anti asiri fa? Wannan ai asiri ne."
Jinjina kai Hajara ta yi.
"Yes Husna, asiri. Idan har kina son ki cimma manufarki a kan Huzaif, to ina mai tabbatar maki wannan kaɗai ne hanyar da za ki yi nasara. Ni kaina a sanadinki na soma yarda da ire-iren waɗannan abubuwa, a baya sam ganinsu nake yi shirme sa ɓata lokaci amma fa ban da yanzu. Ko kin san wannan rashin jituwar da ke yawan afkuwa tsakanin Huzaif da Sadiya sanadin asiri ne? Ban faɗamaki komai zai tafi daidai ba? Ko kuwa a zatonki ƴar dabararki ce ta yi sanadiyyar faɗansu ya yi ƙarfi sadda zai tafi? To ki saurare ni dakyau, aljani ke tasiri a jikin Huzaif. Shi ne musabbabin komai dake gudana tsakaninsu, Huzaif a yanzu koda yana son Sadiya, lokuta da dama ba ya jin komai sai haushinta a dalilin wancan shaiɗanin da ke jikinsa. A nan gaba kuma hatta da sunan Sadiya ba zai so ya ji ba. Zai kasance hirar da ya kamata ya dinga yi da ita, da ke ya ke yi, a lokacin da zai dawo garin nan, soyayyarki ce za ta maye gurbin ta Sadiya a ransa. Don kawai maganin da za ki tabbatar kina mata barbaɗensa a abinci shi ne zai sa ki tashi hankalinki? Kin san ba zan cutar da ita ba, ƙanwata ce fa ko na ƙi ko na so, maganin ba na komai ba ne sai na mantar da ita zancen Huzaif gaba ɗaya. Ta yadda za ta rufe babinsa a rayuwarta."
Hajara na kai wa nan ta tsaya tana nazartar yadda maganganunta suka yi tasiri a wurin Husna daga ma yanayi na fuskarta da ya sauya ba kamar a farko ba. A haƙikanin gaskiya kuma maganin ba na komai ba ne face na baƙin jini. Babban burin Hajara ko bayan kawar da Huzaif daga rayuwar Sadiya, to ta yi baƙin jini wurin samari, Bokanta ya tabbatar mata aikin a hankali zai ci, akwai aiki mai kyau da zai mata na turen baƙar aljana ga Sadiya wanda ba zai sa wani namiji ya kalle ta da sunan so ba duk kuwa da kyanta.
"Shikenan Anti, idan dai ba zai mata komai ba, aikin kuma zai sa na samu Yaya Huzaif. Zan bi umarninki."
Sauke nannauyar ajiyar zuciya Hajara ta yi gami da murmushi, a hankali kuma ta shafi gefen fuskar Husna.
"Haba Momina, babu cutarwa tsakanina da Sadiya, koda ace ba na kaunarta, hakan ba zai ban damar na cutar da ita ta kowane ɓangare ba. Ƴar uwata ce fa, jinin dake yawo a jikina yana yawo a nata."
Murmushi Husna ta yi ta jinjina kanta cikin gamsuwa da bayanan Hajara. Nan ta karɓi maganin ta kuma ci alwashin za ta fara aiki da shi daga yau.
Sai dai kash, duk yadda ta so Sadiya ta ci abinci a ranar cewa ta yi ta ƙoshi. Gudun kada ta zargi komai sai ta basar ta maida abincin kicin ta zubar a bola tana jan guntun tsaki.
***
Washegari gaba ɗaya Sadiya ta tashi zuciyarta a jagule, haka zasu yi rayuwa da Huzaif? Babu kira babu amsa saƙo? Ko dai wani abin ne ya ɗauke hankalinsa ne? Sai dai kuma ta ƙaryata tunaninta a take ganin har Status yana ɗorawa abinsa a whatsapp. Ita ce dai ba zai kula ba. Wannan ya yi mata zafi ainun, ta saka a ranta ba za ta ƙara kula shi ba don ba za ta iya rantsuwar da zai janyo mata kaffara ba. So ne tana yi mishi, a kansa ta san ma'anar wannan kalmar, kuma ta sani, bai mata kamun wasa ba. Don haka batun ma ta yi rantsuwa akan ba za ta ƙara gwada yi mishi magana ba sam bai taso ba.
Sai da ta yi wanka ta shirya cikin doguwar rigar atamfarta sannan ta bi Husna dake nacin ta fito su sauka ƙasa su yi karin safe. A ƙasan suka iske Hajara da maigidanta Alh Nuhu suna kari suna taɓa hira. Zuwansu ya sa gaba ɗaya suka ɗago kai. Sauke idanun da Alh Nuhu zai yi kan Sadiya ya ji wani irin maganaɗisu na fisgarsa. Ita kuwa Sadiya sai da ta fito ne ta ga ashe Antin nasu Hajara da mijinta na falon, ta ji kamar ta juya don ba ta iya sakin jiki gaban kowane namiji balle kuma Antin da mijinta da ganinsa sai dai daga nesa. Za ta iya cewa bai san ta ba kuma ita ma ba ta san shi ba a fili sai ko a hotunan biki.
Hajara da ke jin kamar ta shaƙe mijin nata dake duban Sadiya, har ita ma Sadiyar da ta fito mata sakaka babu hijabi. Wani irin mahaukacin kishi take ji na taso mata ba ta san sadda hakurinta ya kare ta dakawa Sadiya tsawar da ta yi mugun razanata ba.
"Ke!" Husna ita kanta sai da ta firgita, Alh Nuhu da ya shagala wajen kallon halitta mai jini a jika a lokacin ne ya dawo cikin hayyacinsa ya ɗan soma kame-kamen ɗaukar cokali ya hau shan farfesun dake gabansa har yana kona harshe.
"Ba ki da hankali ne za ki fito min babu mayafi balle hijab? Haka Inna ta koyamaki? Maza ɓace min daga nan!"
Sadiya da idanunta tuni suka cicciko da ƙwalla ta juya da sauri ta fice har tana haura matattakala bibbiyu. Husna sam abin bai mata daɗi ba musamman la'akari da nata shigar na riga da siket ƴan kanti ga babu ko hula a kanta balle ma a kai ga wani mayafi ko hijab.
"To ni bari na wuce kar na makara, muna da meeting da..."
"Ban tambaye ka ba don Allah. Jeka kawai."
Hajara ta dakatar da shi da faɗin hakan bayan ta ɗaga masa hannu. Ya san halinta sarai, tana shakkarsa, amma kuma akan kishi idan ya yi wasu abubuwan a gaban idanunta ko kuma ta ganewa kanta a wayarsa to fa babu zaman lafiya. Inda Uwargidansa ke burge shi kenan, ita dai idan zai ba ta kuɗi to fa babu ruwanta da sanya mishi idanu akan komai nasa. Rayuwa suke yi na ba ruwan wani da wani, yaransu uku waɗanda gaba ɗaya suna ƙasar waje karatu.
Hajara ta bi shi da harara da tsaki sadda ya sa kai ya bar falon gaba ɗaya. A fili ta ce.
"Namamajon banza kawai."
"Kai Anti. Me ya yi zafi haka? Laifi ne don Anti Sadiya ta fi..."
"Husna kar ki ce komai a abin da ba ki sani ba kin ji ko? Don me za ta fito haka alhalin gidan nan akwai mijin da ba muharraminta ba? Shi kuwa kamar wani tsohon kwarto ya gwalalo idanunsu yana kare mata kallo. Uhum."
Ta ƙarashe da ƙwafa.
"To Anti ni kuma da nake yin kowace shiga a gabansa fa?"
Hajara ta dube ta dakyau, ta kula yarinyar kamar ranta a jagule yake don fuskar babu ko alamun fara'a don haka ta ɗan numfasa da murmushin yaƙe.
"Ke yarinya ce Husna, eh kina da sura daidai gwargwado amma fa kar ki manta Sadiya gaba take da ke. Kuma ke ɗin ai yana maki kallon ɗiyar cikinsa ba ma a matsayin ƙanwa ya ɗauke ki ba. Sadiya kuwa ta girme ki kuma ta fiki cikar halitta ta ko'ina, sannan gyara ai a na fara wa ne daga kan babba. Yanzu dai na gane ban kyauta mata ba, toh ki ba ta haƙuri, ɗauki abincin ki bi ta da shi ɗaki ki lallaɓa ta."
Husna ta gyaɗa kai cike da gamsuwa, zuciyarta ta dan saki amma ba duka ba. Ta ɗauki babban tray dake saman tebur ta haɗa komai da zasu buƙata na karin safe sannan ta shiga ƙwalawa Atine kira, dattijuwar ta fito da sauri tana amsa wa cikin ladabi.
Husna ta yi mata nuni da shi,
"Ɗauki ki kai min ɗakina ba zan iya ɗaukar kayan nauyi ba."
Ba musu kuwa Atine ta ɗauka ta yi gaba. Ita kuwa wayarta ta dauka da ruwan filas ta yi gaba.
"Momina."
Ta juyo jin Hajara ta dakatar da ita. Da murmushi saman fuskarta ta ce.
"I am sorry, sannan ki yi bakin kokarinki wajen ganin komai ya tafi daidai."
Sai lokacin Husna ta yi murmushin da ta ji komai ya wuce. Ta amsa da Ok sannan ta fice.
Duk yadda ta yi ƙoƙari wajen ganin haƙanta ya cimma ruwa abin ya faskara don Sadiya kuka take yi sosai, dama ga damuwar Huzaif a gefe, wannan ya sa kukan ya zama biyu. A lokacin dai Husna ba ta iya ta shawo kanta ba sai da tace za ta kira Malam ta sanar mishi idan ya so su tattara su koma gida a ranar. Wannan ne dalilin da yasa Sadiya tsagaitawa, ta kuma karɓi roƙon Husna ta haɗa shayi. Amma ta kasa cin wainar ƙwai da ma farfesu waɗanda duk ta bi ta barbaɗe su da garin magani.
Sai a abincin daren ne ta samu yadda take so domin Sadiya sosai ta ci abinci sakamakon cin da ba ta yi da rana ba gaba ɗaya.
***
Kwanansu biyar a gidan, ba ta kara gangancin bari ta fita ko falon sama ba balle a kai ga na ƙasa, duk don gudun kar su haɗu da Mijin Antin nata don ta san a kansa ne ake mata tsawa mai kaɗa ƴan hanji. Shi kuwa Alh Nuhu kasancewar gangar siyasa na dokawa a lokacin hankalinsa gaba ɗaya yana kan taimakawa abokinsa kuma ɗan jamiyyarsu don ganin ya yi nasarar samun kujerar Sanata karo na biyu. Ba su da aiki sai ziyartar Bokaye da Malaman Tsibbu iri-iri kuma Jaha daban-daban, hakan ya sa ya ɗan mance da Sadiya da shirginta. Har suka kammala satinsu ɗaya cif suka bar gidan bai dawo daga tafiyar da suka yi zuwa can kudu ba wurin wani Boka. Ita kanta Hajara karɓar kuɗaɗe sosai take a hannunsa da sunan akwai waɗanda take sanya wa su yi musu aiki kuma sun tabbatar mata za'a dace sosai. A farko sai da ya ɗan yi mamaki daga baya kuma ya watsar da mamakin, mace mai bin maza a baya, ai babu lokon da ba ta faɗawa duk don samun kan abokin hulɗa.
"Duk da haka wannan ya zama sirri, ba na so ko ƙawayenki su ji."
Shi ne kaɗai abin da ya ce mata. Ita kuwa Hajara fantamawarta kawai ta ke yi, a gefe kuma aiki tuƙuru take gudanarwa don ganin ta gogawa Sadiya baƙin jini sosai ta yadda za ta fice a ran kowane namiji ciki kuwa har da nata Maigidan.
Husna ta yi iyakar yin ta, an kuma yi nasara Sadiya ta ci abinci da garin magani har sau biyar a zaman kwanaki bakwai a gidan. Hajara ta ce kar ta sake ta damu tunda ba a iyakar wannan kawai suka dogara ba. Kudaɗe ta zuba a asusun banki na Husna ta saka direba kai su wani katafaren shago don su yi siyayyar tafiya gida. Sadiya ta