Showing 15001 words to 18000 words out of 124441 words
me ba zai yi shawara da su ba kafin ya kai mata. Har da cewa ba zasu ba shi komai na gudunmuwa ba.
Haka har biki ya zo aka yi shi cikin rufin asiri, Inna Mairamu wasu abubuwan ita ta yi mishi da kudin ɗaya cikin tumakanta da ta siyar wanda take kiwo a wajen Kawu Jibo na gadonta. Ya ji dadi sosai da abinda ta yi hakanan Malam har godiya ya yi mata.
A Daura ya auro matarsa yar fulani da ita, har fulatanci tana ji hakan ya sa ta shiga ran Inna Mairamu sosai, sunanta Hameeda. Iyakarta sakandire. Yarinyar na matukar girmama Inna, kuma tana kaunar Sadiya da Husna. Su kuwa su Hajara sai ta yi bakin jini a gurinsu tunda ita kadai ce a matan yayyun ke shiga lamarin Innar. Sauran duk basu wani damu da lamarinta ba.
***
Daga wannan lokacin kuma sai tashin hankalin da ya biyo baya na fasa auren Hajara.
Mutum na farko sun haɗu ne sanadin mahaifiyarsa da ya kai asibiti ba lafiya, yanda Hajara ta tsaya wajen nuna kulawa sosai gareta ne ya sa ya ji nan duniya ta burge shi kuma zai iya aurenta, haka ma a ɓangaren mahaifiyartasa ta yi na'am da Hajarar matsayin matar ɗan nata. Saboda har suka bar asibitin Hajara kan je har gida ta gaishe ta. Ita kuwa Hajara ganin irin kudin da suke facaka da shi a asibitin da ma yanayin wayoyin da yake amsawa yana batun ƙasashen waje, inda ya je da kuma dawowar da ya yi daga London saboda jikin Mahaifiyarsa da ya motsa duk su suka ruɗa ta, ta maida kanta wata salihar gaske a gabansu.
Ranar da Sunusi ya fara zuwa gidansu ya nemi iznin zance wurin Malam kuwa, ai kwanan farin ciki ta yi. Har tana cewa Malam ita fa ta gaji ta gani shi take son aure. A gaban Inna Mairamu ta cewa Malam kuma duk sadda ta yi aure da Husnarta za ta tafi. Malam dariya kawai ya yi, ya sani babu kunya ko kadan tsakaninsu da yaransa don yakan yi hira da su sosai. Ya sakar musu fuska hakan yasa wasu lokutan yake gane damuwarsu da ma wasu abubuwan. Sai dai duk irin ganiyarsa, yarda da ya yi da Hajara ya sanya bai taɓa hasaso wai tana bibiyar maza a waje ba da sunan soyayyar shan minti. Ba dai ta taɓa bari a kusanceta kusanta irin ta mata da miji, amma ban da hakan, komai ta aminta namiji ya yi da ita.
Watansu hudu tare da Sunusi, bayan sallah ƙarama ya turo aka sanya ranar aurensu har da kuɗi dubu dari mai matukar daraja a wancan lokacin. Kawayenta suka cika gida da yan uwa aka yi ta murna da farin ciki, Inna Mairamu ta sha habaici a wajen dangi inda wasu ke fadin ai fa Hajara ta yi goshi, kaf a yaran Malam ma babu wanda aka kawo kudin aurensa kamar nata, kuma an yi an gama ba za'a ƙara ba.
Abba ne ya dauki nauyin yi mata komai na kayan daki, Malam ya rasa kalmar da zai yi amfani da shi wajen godiya gareshi, ga kuma kayan abincin da za'a girka na gida yan uwansa maza sun ce basu yarda ya siya ko gishiri ba, su zasu yi. A cewarsu Hajiya Asma'u mutuniyar kirki ce ta mutane wacce ba ta da rowa sam, don haka burin da ta ci na bikin Hajara idan babu idanunta, to su za su bugi kirji su cikamata shi. Ga kuma uwa uba shi Malam din mai kokarin zumunci ne da kyautatawa yan uwa daidai gwargwado. Watan tafiyar Alhazai na shiga aka kawo lefe na gani na faɗa a lokacin, wanda sai ɗan wane da wance.
Hajara kanta ya kara fasuwa, gyaran jiki na musamman ta je can makwafciyar Hafsatu ƴar Maiduguri take mata. Ga kayan haɗe-haɗen da ta samu na wata daga Sokoto. Abin har daurewa Hafsatu kai ya yita kasa shiru tace.
"Wai Hajara ina kika san duk wadannan magungunan? Dama kin san ana yin su?"
Hajara dariya kawai ta yi ta basar yayinda mai mata gyaran jiki ke tarewa da fadin
"Ai ba za ta kasa sani ba Malama, kar fa ki manta zamanin kullum sauyawa yake ƙara yi. Ba irin namu lokacin ba ne."
Da wannan Hafsatu ta ji mamakinta ya ragu.
***
Tashin hankalin da ya riski Inna Mairamu ana gobe daurin auren Hajara ne ya sa dole ta nemi iznin Malam a daren ta fita zuwa asibiti don duba Kawunta Jibo da aka ce an kai shi bai san ma wanda ke kansa ba. Haka ta tsallake ta bar yan uwan Malam din da na maman Hajara sai ko yan bikin zuwa asibitin tare da Sadiya da ta dinga magiyar ta tafi da ita. Ita ma ba ta musa ba ta ja ɗiyarta suka bar gidan gudun zagi ko cin mutunci daga yan bikin.
Har hawaye ta yi ganin halin da Kawu Jibo ke ciki, wai hawan jini ne ya yi sanadiyar zubewarsa a dakinsa, Allah ya taimaka Dada da kusa. Da taimakon makwafta da ɗansa wanda bai fi sa'an Safiyyar Malam ba, Sharu, suka kai shi asibiti. Sharu ne ya kira a waya ya sanar da ita.
Jikin da sauki don likitan ya ce zai tashi da yardar Allah. Ta jima anan sai daga baya Dada ta saka Sharu ya tare mata abin hawa ta tafi gida da zummar gobe za ta yi sammakon dawowa kafin a fara hidimar biki.
Washegari kuwa da sassafe ta je asibitin da abin kari, Malam bai samu shiga na sai saƙon gaisuwa da ya bayar yace a yi ga Kawun zai shiga ya duba shi bayan daurin aure, ganin har Kawu na magana hankalinta ya kwanta. Shi ya ba ta umarnin komawa ga hidimar bikin idan yaso daga baya ta dawo tare da mijinta. Da wannan Inna Mairamu ta koma gidan hankalinta kwance, sai dai na mutanen biki a tashe.
Ta yi saroro a tsakar gidan ganin Hajara da Safiyya sun haɗa kai suna runtuma ihun kuka, wasu a manyan ma sharce hawaye suke yi. A bakin Hafsatu take ji wai Sunusi ya fasa auren Hajara kuma ma wai ya bar mata komai na kayan da ya kawo. Salati Inna Mairamu ta saki don ba karamin razana abin ya sanya ta shiga ba. Jin lamarin ta yi tamkar ga ƴar cikinta ya faru. Hawaye ta shiga matsewa. Ta karasa da zummar rarrashin Hajara aikuwa ta yo kanta.
"Munafuka algunguma! Ni dama na sani! Tun ganin da na yi maki ki na safa da marwar shige da fice a daren jiya da safiyar yau jikina ya ba ni wata baƙar muguntar ki ke shirya min. Me na yi maki Mairamu da za ki datse min igiyar farin cikina tun ban kai ga ɗanɗana ba? Allah ya isa tsakanina da ke! Ni dama na san tun da aka kawo kudina ki ke bakin ciki da hakan! Don ba Sadiyarki ce ta samu miji kamar nawa ba! Wayyo Allahna, mutuwa mai yankan kauna ta raba ni da uwata abar sona!"
"Ke Hajara yi min shiru haka, bana son hauka."
Cewar Haj Mariya a tsawance kafin ta ja ta su yi daki tare da wasu a yan uwa. Wasu kuwa suka yi wa Inna Mairamu caa wacce ta yi tsaye tana ɗigar da hawaye ta ma rasa kalma ɗaya da za ta yi amfani da ita wajen kare kanta. Kai ka ce ba ta sanar da su halin da ɗan uwan mahaifinta ke ciki ba har ma suka bi ta da addu'ar nema masa lafiya. Kowa ya shiga zaginta daidai gwargwado sai kuwa su Mama Iyabo da wasu a yan uwa masu kare mata. Ranar tashin hankalin da Inna Mairamu ta shiga Allah kaɗai ya sani.
Da zazzabi sosai ta kwana ban da kuka da ta ci ga Sadiya da Hafsatu masu taya ta da kuma ba ta hakuri. Zakari ma shiga da fita ya dinga yi yana ba ta hakuri. Haj Mariya duk da ba wani shiga harkar Innar take yi ba, amma ba ta wani tsane ta, sai da ta shiga ta ba ta hakuri dangane da abin da Hajarar ta yi gami da nunamata ba ta cikin nutsuwarta ne. Karshe ma gidan Abban ta wuce tare da ita bisa umarnin Abban da ya cewa Malam ya dace Hajara ta dan bar layin na ɗan lokaci.
***
A ka yi wannan ta wuce, tsana mai tsanani na Inna Mairamu ya ninki a zuciyar Hajara. Ko watanni biyar ba a yi da faruwar lamarin ba ta ƙara samun wani mutumin. Shi yana da mata amma yace ita Hajarar Lagos zai kai ta inda yake aiki. Shi ma sosai yake sakarmata bakin aljihu, gaba daya ya rude nan duniya ita yake so. Tun tana ɗar ɗar har ta saki jiki ta kai shi wajen Malam, nan fa magana ta yi karfi har aka tsaida rana.
Sai dai shi ma ranar da aka ce za'a kawo lefe, a ranar saƙon fasa aurenta ya riskesu ta hanyar sako na waya da ya yo mata.
Wannan karon har kwanciya asibiti Hajara ta yi. Koda ta dawo hayyacinta bayan tsawon lokaci, sai kuma ta tattara lamarin auren ta watsar. Yayar mahaifiyarsu mai suna Saratu, har gidan ta zo ta yi wa Inna Mairamu kashedi mai kyau akan ta fita a harkar ɗiyar yar uwarta ta bar ta ta yi aure idan ba haka ba za ta maka ta a kotu.
"Abin da na sani Allah kaɗai ke da ikon hanawa da zartarwa ba ni Mairamu ba. Allah shaida ba zan iya cutar da Hajara ba koda kuwa kuma ganin ba ni na haife ta ba. Amma idan ku na tunanin ni nake hana ta aure, ai ina da yara matan, su ma hakan zai faru a kansu tunda ban isa na zalunci ƴar wata ba, ni kuma Allah ya bar nawa."
Iyakar abin da tace kenan daga haka ba ta kara tofa uffan ba sai Gwaggo Saratu da ke faman sababi da jifan yaran Innar da mugun baki da kalami har ta gaji ta fice a gidan ta bar Inna Mairamu da zubar hawaye da kiran sunayen Allah da ma duk wata addu'ar da za ta haifarmata da nutsuwa a zuciya. Babban jin dadinta bai wuce yanda Malam ya yarda ita da ba, har nasiha da jan kunne ya yiwa Hajara da yan uwanta kan su maida lamarin ga Allah, mutum bai isa ya yi musu komai ba amma Hajara ba ta jin za ta bar zarginta har abada.
Hajara ta cigaba da cin karenta babu babbaka a waje tana ba da fuska ga manyan mutane tana musu wayo tana karɓe chanjinsu, an sha ɗana mata tarko don kawai a keta haddinta amma Allah na tseratar da ita sai dai hakan bai sa ta hankalta ta bari ba. Rabuwarsu da Nusaiba ta samu kawayen da suka fi Nusaibar gogewa a harkar a nan asibitin da take aiki. Har ɓata gari a likitocin bibiyarsu suke yi.
Sai da ta shekara ba ta ko kara kallon wani namiji da sunan aure ba, wani mai suna Yusuf ya dinga nacin yana son ya turo gidansu. Ma'aikacin banki ne, babu laifi yana da rufin asiri daidai gwargwado amma bai kama ƙafar wadanda suka tafi a baya ba, ta ƙi ba shi dama saboda tana tsoro amma kuma tana son abin. Sai dai koda ta tuntuɓi Gwaggo Saratu ta ja ta suka je wajen wani Malami ya ba su magani akan Hajara ta dinga amfani da shi babu wanda ya isa ya hana aurenta a wannan karon. Hajara sam ba ta yarda da wadannan abubuwan ba saboda ita ta sani ƙarya ne, sam a tsarin rayuwarta babu bin bokaye da malaman tsibbu tunda ta sani ba a haka a gidansu. Ta sha mamakin ma da ta ga Gwaggo ta yi amanna da su har haka.
Don dai kar Gwaggon ta ga kamar ba ta yabawa kokarinta ba, ta yi amfani da shi sannan Yusuf ya turo gidan neman aurenta.
"Wannan karon ko uban kuturu ya yi kaɗan ya hana min aure. Kuma mutum ya gwada ya gani."
Haka shi ne furucin da Hajara ta bi Inna Mairamu da shi ranar da aka tsaida lokacin bikinta da Yusuf. Inna ban da murmushi ba abin da ta yi.
"Hakurinki yana yawa a gidan Sa'adu, Mairamu sam ba na son wannan shirun naki, ni na san suna cutar da ke yawa."
Abin da Dada ta taɓa furta Inna kenan a wata ziyara da ta kawo mata sa'ilin da Sadiya ta yi fama da rashin lafiya. Ganin yanda Hajara ke habaice-habaice ba ta ko girmama Inna a gaban mutane ya sa Dada yin maganar.
"Babu komai Dada, komai mai wucewa ne. Rayuwar duniyar ma duka nawa take? Har yanzu yara ne, zafin rabuwa da mahaifiyarsu bai sake su ba. Ke ma ki yi musu uzuri. Watarana sai labari."
Dada ta kalleta sosai a wancan lokacin ta jinjina kai.
"Uhum! Kazar kwanci kirjinki ya saba da danna! Ki cigaba da hakuri, mai hakuri kan dafa dutse har ya sha romonsa Mairamu. Watarana za ki yi dariya sosai."
Murmushi Inna Mairamu ta yi tana hasko wannan ranar a idanunta, tana da yaƙini lallai idan da rai da lafiya zai zo watarana. Ai babu abin da ya fi karfin iko na Allahu.
***
Zaman taron zuri'a aka gudanar wannan karon a can gidan gado na Malam duka kuma akan fasa auren Hajara da aka ƙara yi karo na uku don wannan ma taron bai watse ba sai a ranar daurin aure duka an taru amma Ango Yusuf ya miƙe ya ce ya fasa. Hakan har faɗa da cece kuce ya jawo inda Mustafa da Baba Habu suka kusan yi doki in doka da dangin Yusuf din. Rabuwa dai aka yi babu dadi kuma dangin Ango suka ce lallai duk abin da suka kashe sai an biya su abinsu.
Wannan lamari ya girmama inda Gwaggo Saratu ta daukowa Inna Mairamu ƴan sanda. Dakyar aka kashe zancen bayan Abba da wasu a makwafta sun je sun yo belinta. Dole aka yi zaman sulhu a gidan su Malam din.
Nan fa wasu suka dage akan lallai sai Inna Mairamu ta yi rantsuwa cewa ba ita ke yin kullin da ake fasa auren Hajara ba. Wannan karon ƙirjin Inna Mairamu har zafi yake yi ga wani jiri dake kwasarta a zaune. Ban da innalillahi babu abin da take bita a zuciyarta. Ta lashi busassun lebbanta tana jin wani raɗaɗi a maƙogwaronta. A hankali ta dubi Malam wanda ba shi da ta cewa kansa yana sunkuye ya zabga tagumi. Sai ta kauda kanta ta kasa magana, ta maida duba ga Alkur'ani mai tsarki da aka ajiye a gabanta kan cewa ta rantse ba ita ce ke korarwa Hajara maza ba. Hawayenta suka zubo har suna ɗiga a saman alkur'anin ta goge su.
"Ba zan iya rantsuwa da Alkur'ani mai girma ba. Amma ina muku rantsuwa da girman Allahu mahaliccin dare da rana, duhu da haske, fari da baƙi. Maƙagin kowa da komai, ba zan iya cutar da yaran Malam ko ɗaya ba koda kuwa yaran riƙo ya kawo. Me Hajara ta yi min da zan hana mata aure? Mece ce riba ta?"
"Ƙarya kike yi algunguma marar tsoron Allah."
Faɗin Gwaggo Atine ƙanwar Gwaggo Saratu, nan fa Kawu Haruna wanda kusan a maza tsoffi da suka rage a zuri'ar shi ne babba ya tsawatar mata. Nan ya ba Inna Mairamu hakuri ya kuma nusar da zuriar akan su tsoraci Allah saboda shi ne mai yi da hani. Kuma a cewarsa ya dace ma a tuntuɓi mazan a san ko akwai wani abu da suke ji da yake sanya su fasa auren.
Shi ne ya yi dogon wa'azi daga bisani ya kara ba Inna Mairamu haƙuri ya kuma rantse akan duk wanda ya ƙara tayar da zancen zai gamu da fushinsa, dole aka bar maganar anan. Sai dai kuma gutsuri tsoma irin ta mata da bai taɓa yankewa. Don ko haihuwa aka yi ko wani abin idan an haɗu sai an yada wa Inna Mairamu habaici sai dai ta toshe kunnenta.
***
Rayuwar na cigaba da gudu, har aka wayi gari Sadiya ta zama budurwa son kowa kin wanda ya rasa. Dama ga ta nan yarinya ce mai farin jini tun tana ƙarama, a yanzu da take aji na biyu na babbar sakandire sai take ƙara shiga ran mutane musamman yanayin kamewarta da nutsuwa. Sam ba ta da kwaramniya. Husna a lokacin ita kuwa tana aji biyu na ƙaramar sakandire (Jss 2). Yanayin girman jikinta sai ka ɗauka ta girmi Sadiya. Ita Sadiya ƙirarta na fulani ne. Tana da tsayi sai kuma ƙira mai kyau don idan ka kalli cikinta sai ka rantse ba ta cin abinci sau uku a rana. Akwai dai halittar ƙirji da kuma mazauna. Wannan ya sa ƙirarta ya yi kama da wanda ake cewa cocacola shape.
Hajara ta tsani ta ga Sadiya a gabanta saboda wani takaici da take ji. Takan yawaita jan tsaki ta ce.
"Aikin banza, duk wannan kyawun dai na ɗan maciji ne. Yanda ban auru ba haka har abada yarinya za ta ƙare a yawon bariki."
Inna idan ta ji takan nemawa ɗiyarta a tsari a zuciya. Sadiya kuwa kallonta ma ba ta yi tunda ta kula abin na Antin nasu ba na ƙare ba ne.
Lokacin Hajara na da shekaru ashirin da tara cif a duniya. A sannan manema auren ma sun ɗan ja baya sai dai kamar daga sama wani ya fito a karo na huɗu dagaske aurenta zai yi. Murna da daɗi suka kusan kasheta ganin babban Alhaji ne kuma mazaunin Abuja sai dai iyayensa a garin Kano suke, a hanya ya ganta ya biyo ta har gida.
Nan fa aka shiga shirye-shiryen biki. Shi ɗin ma dai bai je ko'ina ba don ana saura kwanaki uku a fara bikin ya ce ya fasa gaba daya. Wannan karon hauka ne kawai Hajara ba ta yi ba. Shi ne a ƙarshe Malama Hafsatu ta ja su zuwa gidanta don Hajarar ta samu nutsuwa ta kuma fita a bakin mutane.
Sai dai gaba daya lamarin wannan karon ma kan Inna Mairamu ya dawo, ga kuam baƙaken addu'o'in da ake fa yi wa yaran Inna Mairamun musamman