Showing 30001 words to 33000 words out of 150681 words
bude baki a hankali tana kokarin boye yanayinta duk da dukkaninsu sun gama sanin tana cikin rashin nutsuwa me girman gaske dan haka akwai abinda take boyewa.
"Ban yadda kowa ya fadawa AZIZ abinda ya faru ba,
Idan nace AZIZ ina nufin Sayd sbd shine kunnuwa da idanuwansa,
Ko a bisa tsautsayi karya taba sanin abinda ya faru,
Ko sunan masu aikin Nan da komai ya faru sanadinsu ban amince ya isa kunnuwan AZIZ ba har abada"
Dago idanuwanta tayi ta saukar akan fiddausi da nata idanuwan sukai jajir itama ta sauke kanta qasa a sanyaye cikeda mamakin menene ya fito da Maman bayan ko kaunar ganin Zaadens batayi hakama batason ko kadan su San a inda suke.
Da kakkauran kalami Maman tace
"Kin Sani isar wannan maganar a kunnuwan AZIZ ko Falaq daidai yake da abinda na fada Miki a baya sbd naga alamar kina son zabar zama a wajen LIMBAs Wanda babu nasara ko kadan a bangaren da kikeson zaba"
Nicky idanuwanta ta juya ta kalli fiddausi kafin ta dawo da idanuwanta akan Mama tana kokarin fahimtar abinda yake faruwa amma dai koma menene tasan yanada alaqa da abinda baa son ta Sani sbd babu abinda Mama ke boye mata bayan duk abinda ya shafi Matar LIMBA ta baya.
Fiddausi kuwa hadiye hawayenta tayi zuciyarta na daci da baqin samun kanta a tsaka me wuya irin wannan ta gyada Kai tana bude baki muryanta a shaqe tace
"Insha Allah Mama"
Kallansu tayi ahankali tace su tafi taji sauki tana buqatan kasancewa ita kadai.
Wani kallo tayiwa fiddausi wanda fiddausi ta fahimci abinda take nufi dan haka ta fara wucewa ta nufi kitchen ta fara jingina da bango tana sauke numfashi me tsananin zafi kanta na toshewa gabaki daya.
Tea me zafi sosai ta hadawa Maman ta fito kitchen ta nufi dakin sbd ta tabbatarda Nicky ta fice.
Tana shiga tura kofar tayi ta rufe ahankali ta iso gaban Maman ta ajiye tray din hannunta tana durkusawa ta dauka ta miqawa Maman a natse.
Kofa Maman ta kalla ta tabbatarda fiddausin ta rufe ta bude baki tace
"Na tabbatarda bayan abinda ya faru baa barsu sun fice daga mansion din ba suna nan haryanxu??
"Eh suna nan Mss Nicky tace kar abari su tafi sai kin tashi"
Ajiyan zuciya boyayya Maman ta sake tana ajiye cup din hannunta batareda ta iya shan tea din ba dan gabaki daya a cunkushe cikinta yake tace
"Shikenan kije zan saka a sallamesu da kaina ki sanar da securities nace idan baniba Kar Wanda ya bada umarnin zamansu ko tafiyarsu a gidan nan"
"To" tace tana juyawa ta fice daga dakin.
Nicky yau bata fita koina dan haka bata sake sauka ba hakama su Maman babu Wanda ya sake fitowa abinci ma a sama fiddausi ta kawo musu.
Mama wuni tayi a tsaye da zaune sbd gabaki daya nutsuwarta bata tattare da ita,
Duka AC dayake buga koina na cikin inda suke rayuwa zufa take yi bata iya cin komaiba sai tea da ruwa kadai datake Sha,
Bugawa zuciyarta takeyi wadda take hana numfashinta tafiya daidai sbd kasa zuwa ta tabbatarda fatimace a gaban idanuwanta hakama akan wane bagiren zata dauki lamarin.
Daga Mama har Zaadens wunin tsaye sukai babu Wanda baya cikin tsananin tinani me zurfi da baqin cikin kasancewa guri daya da juna har lokacin.
Duk yanda sukaso tafia sun kasa samun dama gashi basuda labarin halinda ake ciki Maman ta tashi kokuwa haryanxu tana can a sume.
Ga yunwa a cikinsu Amma damuwa da qunci sun hana suji yunwar yanda ya kamata dole a cikin kayansu suka hada tea kowa yasha suka ci gaba da zaman radadin zuciya.
Da daddare sawu ya dauke tsaf kowa a mansion din yayi bacci Banda su Dad da suke zaune daram har lokacin baqin cikin rayuwa ya gama rufesu sbd ayau sun sake tabbatarda su din ba kowa bane a yanzu sbd yanda aka tsaresu a inda sukejin gwara zaman cikin inda ake gasa bread dashi...
Karfe daya da mintina kamar yanda Dad yayi tinanin akwai dalilin hanasu tafiya hakan ce ta tabbata sbd sak a mutum hajiya sakina ta bayyana a palon da suke zaune su dukansu har Fatma da Ummah harma da Garba sunyi nisa sosai a bacci.
Ita kadai ce ta taho babu kowa a tareda ita hakama ta tabbatarda babu wanda baiyi bacci ba a mansion din dan haka kai tsaye ta qaraso har tsakiyar palon idanuwanta kafe akan fuskan Ummah dake bacci a jikin Dad hankalinta kwance hannuwanta duka biyun ta sarke hannuwan Dad din dasu wanda hakan ya saka Mama rikicewa ganinta na neman daukewa ta fada cikin kayansu dake gefen ajiye batareda ta saniba tsabar rikicewa.
Babu Wanda yayi yunqurin taimaka mata sai Jannah data tashi tareda miqa hannu zata kama ta Maheer ya riqo hannunta a natse tareda dawowa da ita gefensa Yana girgiza mata kai ahankali cikin sanyi yace
"Karki taba ta ace mun sake mata wani abin Jannah"
Sauke kanta tayi ahankali tana jin batajin zafin Maman sbd ba itace ta lalata rayuwarsu ba 'danta ne Amma kuma dole indai tana Zaadens kuma jininsu ne a jikinta zata tsaya dasu ako wane hali kuma ta tsaya su fuskanci duk wani wnada suke ganin abokin gabarsu ne.
Miqewa Maman tayi tana kasa dauke idanuwanta akan hannuwan Fatima da Dzad...
Bakinta na rawa idanuwanta na cikowa da hawayen da batasan ma na menene ba ta kalli Dad a rikice tace
"FATIMA"
Dukkaninsu kallanta sukai suna miqewa tsaye daya bayan daya ahankali kafin Jannah ta isa kusada Ummah tana kokarin riqota Mama ta riqe hannun Jannah din cikin tsananin tashin hankali tace
"Ina kuka hadu da Fatima?
Dad sake riqe hannun Ummah yayi wadda ta bude idanuwanta ahankali tana miqewa tsaye ta sake riqesa da kyau batareda ta kalli Mama ba.
Ganin hakan Mama ta sake ambatar sunanta da dan karfi tana kokarin isa gurinta ta fizgota daga jikin Dad Amma a lokaci daya Umman taja da baya tana riqe Dad da Jannah da kyau kuma a daidai lokacin Ammar da Maheer suka sha gaban Maman suna kallanta cikeda dukkanin tsanar duniya da baqin cikin sake ganin wani daga cikin LIMBAs a rayuwarsu.
Da tsananin mamaki Maman ta kallesu kafin ta tsayar da idanuwanta akan Fatiman dake kallanta fes Amma ta kasa sakin Dad bare Jannah da dawo da idanuwanta akan Dad cikin tsananin tsanarsu datake jin tana qaruwar mata tace
"Kunsan waye ita??
Sai alokacin Dad ya bude baki a natse yace
"Nine nafi kowa sanin ita waye sbd ita din matatace,
Idan kuma kinada wani bayanin akanta ki zaki iya sanarwa kafin mu wuce tinda gashi naga harkin tashi akan kafafunki bamuda sauran abinda ya rage mana anan"
Wani qaton qullutun baqin cikin dayafi kowane a rayuwarta ta hadiye tana kallansa da tsananin mamaki tace
"Matarka?
Fatiman ce ta zama Zad itama?
Tayaya ta ina?
Babu wanda ya tanka ta ta nufi Fatiman da sauri ta riqota tana janyota da karfin gaske tana cewa
"Wlh bazai taba yiyuwa ba"
Fizge hannuwanta Ummah tayi daga na Maman tana komawa bayan Dad
A lokacin ne Dad bacin ransa ya bayyana cikin fushi ya kalli Maman yace
"Ko zan iya sanin alaqarki da ita idanma har kin Santa"
Kallansa Mama tayi bayan ta dauke idanuwanta daga kan Ummah tanajin wani irin zafi da radadi sedai kuma idan har basusan wacece ita din ba kenan da gaske basusan wacece itaba kuma a yanda take gani Fatiman haryanxu duk tsawon shekarun nan bata warke ba dan haka bazata taba barin su San wacece itaba barema AZIZ ya San Fatima tana cikin Zaadens kuma ma a matsayin Matar dzad.
Duk yanda take tsananin so da kaunar Fatima bazata taba iya barin AZIZ yasan tana hannun Zaadens ba bare kuma wai ace ta zama Zaaden din itama,
Tayaya ma zata iya barin hakan?
Hakama suma Zaadens bazata taba barin su San wacece fatima ba bare suyi yunqurin wani abin sbd zasu samu kaman power ne a hannunsu ta yaqarsu.
Dago jajayen idanuwanta tayi da sukai jajir hatta fuskanta tayi ja ta kalli Dzad ta bude baki kai tsaye tace
"Na taba saninta ne baya kuma nasan yan uwanta dan haka inason ka bani ita zan baku dukiyar da zaku Gina sabuwar rayuwar da kuka rasa a baya ta dukkanin daula wadda zamuyi nesa da juna babu haduwa har abada."
Wani irin kallo Mai cikeda tsananin mamaki da tsana me karfi dukkaninsu suke mata Wadda saka zuciyarta sake bushewa itama tana gyada Kai alaman tabbas abinda sukaji take nufi.
Ita kanta Jannah da tsananin mamaki da takaici take kallan Maman sbd kaman da akwai jahilci a cikin zancen.
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS
07019691719
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee
Book 2
Chapter 18
*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa niβima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah π₯°ππ»
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi 1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
π£οΈπ£οΈπ£οΈπ£οΈπ£οΈπ£οΈ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALAππ½ππ½ππ½πππ da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata ππ½ππ½ππ½ππKazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadΔ±π 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection 1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.
******************
Dad cikin tsananin mamakin dayafi kowane mamakin daya shiga a dan wannan lokacin na rayuwarsu ya dago ya kalli Maman Wadda ta sauya lokaci daya dukkanin annurin fuskanta ya kawar ya zuba mata ido yana nazarin ko dai bata hayyacinta ne,
Kodai dukan da Ummah tai mata ya taba kanta ne a lokaci daya?
Maheer ma kallan ba lafiyar tinani yake mata sabanin Ammar da hannuwansa suke dan rawa Yana jin kaman ya shaqe Maman harsai ranta ya fice jikinta koma zasu samu sassaucin abinda sukeji gameda LIMBAs din.
Jannah ma kallan mamakin takewa Maman ta bude baki ahankali zatai magana cikeda kasa gasgata Maman ce kokuwa Dad ya tareta ta hanyar takowa ahankali ya fito fili daga kariyar da Maheer da Ammar suka bawa Umman.
Tsayawa yayi a gaban Maman tareda waiwayowa kadan ya kalli Ummah Wadda itama shi ta kalla ganin ya kalleta tana sake qanqame hannunsa da dukkanin zuciyarta batada niyar sakinsa ko Jannah.
Wata sabuwar soyayyarta ce ta sake cike dukkanin zuciyarsa sbd yanayin rashin lafiyanta ya saka da gasken gaske take tsananin sonsa da yayansa wnada ya Sani babu abinda zai taba sauya hakan daga zuciyarta to bare su,
Idan har ita mara lafiya tana musu tsananin wannan son to su masu cikakkiyar lafiya nasu ya wuce hakan bare daga lokacinda ta riga ta amsa sunan Zad to sun hadu kenan dan mutuwa ce kadai take cire Zad daga Zaadens.
Mama ya juyo ya saukewa wani irin kallan tsanar da yake ganin batama cancanta samu daga garesu ba sbd sunfi son masifa da duk Wanda yake cikin familyn LIMBAs dan haka dan dauke idanuwansa ma yayi daga kanta yace
"Sakina kina mantuwa Amma ki tambayi shi 'dan naki bazai taba mantawa da babu abinda duk duniya yake raba Zaadens bayan mutuwa,
Allah dayayo mu ahali daya shine kadai yakeda wannan ikon na rabamu ta hanyar daukan rayukan daddaya daga cikinmu Amma babu mutum ko wata dukiya bare daular duniya da zata rabamu,
Fatima da kika magana ta riga ta zama Zaaden,
Sunan Zaadens take amfani dashi,
Shine a bakinta kuma shine a zuciyarta,
A ganin ido Bata isa haihuwanki ba kaman yanda baki isa haihuwanta ba Amma duk da hakan ko a matsayin uwa da ya kuke koma uwa daya uba daya kuke wlh ni bazan baki matata ba har abada idan kuma kina son tabbatarda zancen saninta ko alaqardama duk take tsakaninku ina buqatan cikakkiyar sheda da bayyanarwa duniya da zancen bawai iya mu Nan a daki ba a cikin tsakiyar dare sbd magana ake akan Matar dzad uwa ga Zaadens a yanzu,
Bayan wannan duka idan bakida wani abin bama buqtaan son kai safe a cikin gidan nan bcz we are suffocating "
Dago jajayen idanuwanta da suka qara jajir Mama tayi tana kallan Fatima datake jin tsananin ciwon yanda take zabar makasan Yarta a gaban idonta sbd kawai ciwon hauka Wanda ko hauka tasan nata yakamata ace a jikinta taji tsanar Zaadens koda bata hayyacinta.
Akan Jannah Mama ta maida idanuwanta tana tsayar da dasu akan kirjin Jannah din tana kallan yanda kirjinta ke harbawa tanajin sabuwar tsanar Jannah din na rufeta sbd tanada tabbacin zuciyar dake kirjinta ce ta samu kauna daga Umman wanda ta take feelings na tsanar daya kamata taji tai musu sai kaunar tayi nasara akan tsanar,
Har xuwa yaushe ne Zaadens zasu ringa samu da mallake komai na Fatima data ita kanta Fatiman,
Sun mallake zuciyar Ummitah sun qwace,
Sun qwace mata AZIZ dinta Wanda bai taba fada ba Amma ta gani da idonta ta Sani ta qara Sanin Soyayyar Jannah tayi nasara akansa da fansarsa,
Soyayyar Jannah Zad ta sauyasa daga AZIZ LIMBA dinta na baya,
Soyayyar Jannah Zad tayi nasara akan Soyayyar Ummitah tinda har ya zabi Jannah akan fansar ran Ummitah,
Ayanxu data riqesa ta dauresa daga dukkanin Soyayyar da babu amfani a cikinta tayi nasarar shiga tsakanin Soyayyarsa da Jannah har abada kawai rana tsaka sai Fatiman da zai iya komai akanta,
Fatiman da tin yana qaraminsa haryanxu bai taba dena nema da quncin rashintaba,
Fatimar da itace rayuwar data rage masa yanzu dazai iya sadaukar da komai akanta,
Fatiman da batasan tsakanin ita da Ummitah waye yafi tsananin so ba
Shine kwatsam ace ta bayyana a cikin Zaadens kuma a matsayin macen Dzad??
Wannan shine abinda har abada bazata iya yadda dashi ba sbd AZIZ zai zabi Fatima ya kuma zabi wanda ya kawo masa Fatima,
Tasan har abada AZIZ bazai taba barinta ba amma kuma bazai taba barin wanda suka kawo fatima garesa ba amma kuma shi kansa zai shiga mummunan baqin cikin samun mahaifiyarsa a hannun Zaadens.
Zata karbi Fatima bazata taba barin su tafi da ita ba sbd koman Daren dadewa zata bayyana tinda tana hannunsu ta Sani zasu sake daga kansu sbd bazasu taba zama ahakan ba a wannan lokacin ne duniya zatasan Fatima a matsayin uwa a Zaadens kuma AZIZ zai gani kuma zai san ta sani dan haka bazata taba barin hakan ba.
Kallan dzad tayi ta sake bude baki a Karo na biyu tace
"Zan ninka muku abinda nace a farko so biyar ka bani Fatima ku tafi duk Inda zaku tafi dan Gina sabuwar rayuwa"
Tsoki Ammar ya sake Mai cikeda tsananin baqin cikin dayake cinsa ba damar duka,
Maheer ma cikeda mamakin yace mata
"Babu rayuwar dtaake ta siyarwa a Zaadens
Idan da gaske kinsan Yan uwanta ki bamu bayanai da address din komai zamu nemesu da kanmu Amma ki Sani da Sanin danki zamuyi hakan sbd komai ya zama a bude"
Jannah kasa cewa komai tayi sbd lamarin ta kasa yadda kwata kwata da Mama ce ke tsaye a gabansu.
Dad bai iya cewa komaiba ya kalleta yace
"Wallahi tallahi Fatima bazata shiga hannun kowaba sai ranar data samu lafiyanta da kanta ta furta ita din wacece da bakinta dan haka ki Sani ko Banda komai kika sake kwatanta darajar matata da dukiya zanyi sharia dake a kotu koda banda komai kuwa"
Wani irin sarawa kan Mama ya sake yi idanuwanta na sake rinewa sbd ganin komai na neman kubuce mata dan idan yace kotu Fatima zata bayyana kenan sbd ba abu bane da zaa boyewa AZIZ idan aka sakata qara kotun duk da tanada power da kudin da zata hana shariar amma Zaadens bazasu bari ba sai sun tabbatarda sunyi abinda zai janyo hankalin mutane akan case din Wanda hakan ne zai saka AZIZ ji ko gani dan haka bazatai wannan gangancin ba,
Idan har bazasu bata Fatima ba to tabbas bazasu taba barin 4&4 ba kuma bazata taba barin AZIZ yasan Fatima na 4&4 din ba har sai lokacinda ta samu karbeta ta Koresu tukuna ta bayyanar masa da ita.
Juyawa sukai dukkaninsu zasu fice dan barin mansion din gabaki daya ta qurawa hannun Ummah dake cikin na Dzad idanuwanta ki tsaye kaman saukan tsawa sukaji saukan maganarta....
"SALEEM ZAADEN!
cak dukkaninsu suka tsaya babu wanda gabansa baiyi mummunan bugawa ba
Jannah da Ammar ne suka fara juyowa da sauri suna kallan bayanta zuciyoyinsu na wata irin rawar firgici da wani irin yanayi na tsananin kewa.
Dad kasa juyowa yayi sbd yanda zuciyarsa ta cike da wani irin yanayi na tsananin ciwon rashin 'dansa da bai San dalilinta n ambatarsa yanzu ba,
Maheer kuwa ita ya juyo ya zubawa ido sbd kai tsaye yasan tasan ina Saleem yake tinda ta ambaci sunansa.
Numfashi ta sauke a boye sbd ganin ta sara akan gaba dan haka ta sauke ajiyan zuciya a fili tana bude baki cikeda tabbacin abinda zata fada tace
"Saleem Zad Yana raye kuma yana tare da AZIZ LIMBA,
Yana hannunsa,
Ni kadai nasan inda yake,
Ni kadai nasan wane hali yake,
Ni kadai zan iya kubuto muku dashi ya dawo gareku ku taru kuyi rayuwa gabaki dayanku,
Idan har kace dukiya bata siyan daya daga cikin Zads to ai Rai zai iya siyan Rai ko???
Hawayene masu tsananin zafi da tsananin kewa da kaunar Saleem suka gangaro mata ta rintse idanuwanta tana jin farin ciki me tsanani bayan tsawon lokaci jin Saleem Yana raye,
AZIZ LIMBA bai taba mata Saleem dinta ba,
Saleem Yana raye,
Saleem Yana cikin koshin Lfy kenan.
Hawayen farin ciki ne suka cigaba da gangaro mata tana kasa sharewa.
Dukkaninsu farin ciki ne ta wani bangaren me tsananin gaske ya cike zukatansu sedai basu nuna mata hakan ba.
Dad ya sake kallanta jikinsa na mutuwa da jin nutsuwar 'dansa na raye a natse a sanyaye yace
"Saleem idan har Yana