Showing 42001 words to 45000 words out of 150681 words

Chapter 15 - Kalbim Book 2 Complete Hausa Novel

Mamuhgee   

23 Sep 2025

9081

yagani yasan zaa fito da ita dan haka bazai bari ciwonsa yafi karfinsa ba a daidai wannan lokacin yanason ko fuskanta ne yafara gani kafin yayi loosing control.
#MAMUH
#AZIZ AY LIMBA
#JANNAH ZAD

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 24

*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah πŸ₯°πŸ‘ŒπŸ»
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi 1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
πŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈπŸ—£οΈ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALAπŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ˜πŸ˜πŸ˜ da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ’ƒπŸ½πŸ˜ƒπŸ™ƒKazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadΔ±πŸ˜‹ 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection 1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.


******************
Koda Maman ta isa garesa gabaki daya ya fara loosing control gashi take duk Wanda yake aka maida kowa tsaye cikin qanqanin lokaci securities suka dagawa kowa hankali sai ga masu aiki da duka maaikatan gidan ana fitowa dasu kaman anzo patrol..

Jannah datake qanqame da Ummah a dakinsu data taddata taxo tana kokarin daidaita bugun zuciyarta dayake fita da karfi Yana mata ciwo a kirji me tsananin gaske idanuwanta sunyi jajir sake qanqame Umman tayi Wadda itama take sake rungumeta da kyau tana son tambayarta lafiyanta kuwa Amma kuma ganin yanayin nata sai ta fasa ta rungumeta tanajin kaman ta kurma ihun ganin Jannan ahaka.

Jin ana busa wani irin security whistle na tashin hankali ya saka Fatma dake kokarin tambayar Jannah lafiya ta fito.

Su madam Sisi da sauran kowa duka anfito hankali tashe cikeda tsoro da fargaba jiki na rawa,

Duk wanda ya fito yaga maigidan da kansa a tsaye shiga tashin hankali da sabon tsoro yakeyi.

Mama dake neman mutuwa sbd bugawan zuciya gabansa ta tsaya zatai magana Dzad ya bayyana gaban AZIZ din idanuwansa akan AZIZ din wanda shima nasa idanuwan suka tsaya cak akansa cikin wani irin tsananin mamakin dayake sake tsananta yanayinsa,

Maheer ne ya fito bayan Dad shima idonsa akan AZIZ din kafin Ammar wanda idanuwansa sukai jajir yana kallan AZIZ din cikeda wata irin tsana da baqin wannan lokacin fiyeda kowane lokaci na rayuwarsa..

AZIZ LIMBA duk yanda yaso boye yanayinsa kasa boyuwa yayi Wanda ya saka Sayd dayake cikin mummunan shock shima saurin jansa yana barin gurin dashi sbd kowane lokaci kowa zai iya gane waye AZIZ LIMBA a boye sbd yanayin yafara fin karfinsa.

Falaq ma datake hawaye tinda taga yanayin Daddynta tasan ciwonsa ya motsa gabaki dayane da sauri ta bi bayansu tana kokarin riqe hannunsa daya sedai ba damar hakan sbd gabaki daya ya rikice.

Mama data gama jiqewa da wani irin mummunan gumin tashin hankali da firgici itama kasa tsayuwa tayi sbd tana gab da yanke jiki ne ta fadi gaban AZIZ din Wanda tasan hakanne kawai zaisa a dakatar da wannan tashin hankalin na tsakiyar Daren da a gareta ba alkhairi bane.

Ya riga yaga Zaadens Amma hakan a yanzu bai dameta ba akan yaga abinda yake tattareda Zaadens din.

Toshewa numfashinta yake sake yi sbd bata fita tashin hankalin data shigo b dan haka Nicky ce ta kamata har zuwa dakinta daga Nan kowa ya watse aka koma ciki Banda securities da suka kwana a tsaye kan aiki sbd bazasu iya barin ko mage fita ba indai sun ganta har sai maigidan ya bada umarnin.

Mama na komawa daki ta samu nutsuwanta tafara dawo mata ta sallami Nicky.

Dare har ya raba sosai bata iya rintsawa ba tana zaune Daram cikin rashin nutsuwan xuciya da damuwa..

Sai data tabbatarda har securities sun koma waje ta miqe ta fito daga dakinta cikin rashin hayaniya ko dogon motsi ta nufi bangaren masu aiki ko karfin jiki batada sbd bata gama dawowa daidaiba har lokacin dan ba qaramin tashin hankali da shock ta shiga ba.

Ko data isa cikin kaman yanda tayi tinanin suma suna zaune zasuyi kwanan baqin ciki sbd ganin su da AZIZ sun hadu,

Hakan ta samesu a zaune dan haka kai tsaye ta tsaya gabansu babu bata lokaci ta fidda daurin sabbin Dollars dake hannunta ta ajiye gabansu batareda kwana kwana ba ko batawa kai lokaci ba tace

"Na baku damar tafiya batareda kunban Fatima dinba ku tattara a cikin Daren Nan ko asubar farin kubar nan,

Amma da sharadin zaku sanar Dani duk inda kukaje sbd Fatima zan Aiko masu dubata sbd zan nema mata lafiya"

Ammar da zuciyarsa ke gap da bugawa hakama kansa juyewa yakeyi yana sake juyawa miqewa yayi jikinsa na kakkarwa me tsoro ya shaqo wuyanta da karfin gaske Yana hadata da bango da karfin gaske.

Ihun azabar da bata taba ji ba a rayuwa taso fasawa Amma tinawa da halinda suke ciki ya sakata hadiye ihun tana wuni gurnanin azaba ido a waje,
Baki takeson budewa ta nema ceton su Dad Amma ba damar hakan sbd shaqar rabata da duniya Ammar yayi mata dan haka hannu ta ringa dagawa dakyau tana kokarin cetan kanta.

Dad da Maheer ne suka miqe suna banbare Ammar din daga gareta Amma gabaki daya baya hayyacinsa ya koma kaman wata halittar daban ma.

Da karfin gaske suka ringa kokawa dashi suka cirosa da kyar Maheer na qanqamesa da karfin gaske Yana rufe masa baki da karfi sbd wani irin numfashi Mai hade da ihu dayake kokarin sakewa.

Kallan Maman dake neman hanyar fita a rikice dad yayi yace

"Ki dauki kudinki ki tafi zamu tafi a cikin Daren Nan bazaa tashi damu ba
Nema kuma idan kin matsu kinsan Yan uwan Fatiman ki sanar musu su nememu kokuma ke ki kawosu gurinmu"

Yana fadar hakan ya juya itama bata tsaya daukan kudin ba ta fice tana cewa

"Ku tabbatarda Kun bar nan kafin safe"

Hanyar komawa ta kama tana hada hanya da numfashi koina jikinta na rawa.

Ko data Isa dakinta qasa ta zube tana son fasa kuka amma yaqi xuwa sbd wannan ne Karo nabiyu tana shan dukan mahaukata a cikin gidan nan.

Bata iya bacci ba sbd fargaba da yanayin datake ciki na tsoron daya kasa sakinta na shaqar Ammar da kuma gadin window taga ficewansu.

Akan idonta karfe biyu saura suka fito dukkaninsu ba Sanin kowa suka fito suka fice gate na biyu.

Ajiyan zuciya ta sauke tana zubewa bakin gadonta cikin samun wani abu me nauyi da tsoro da suka danne kirjinta.

Sai alokacin taji wani irin zazzabi ma Yana sauko Mata daqyar ta kwanta wuyanta na tsananin ciwo.


Suna isa babban gate kai tsaye aka dawo dasu tareda sanar dasu taku daya wlh idan dayansu yayi zuwa qarasowa gate zasu fasa qashin kafar mutum da bullet.

Babu annuri ko sauki ko kadan a duka fuskokin securities na gidan Wanda kuma har wani dogon Imani basu dashi dan haka zasu aikata abinda sukace dole suka dawo suka koma dakunansu suka kwanta.



******Washe gari sai qarfe 9 na safe AZIZ ya farka daga alluran da Sayd yayi masa a cikin Daren.

Kansa yayi nauyi dan haka kan yake a toshe baya iya tinanin komai saiya dawo daidai.

Toilet ya nufa ya sakarwa Kansa ruwa.

Ya jima sosai Yana duk abinda y saba kafin ya fito sanyeda bathrobe fara.

Sallah yayi wadda ta zame ta latti sosai haka sbd lalura shiyasa baya son yayi loosing control sosai ta yanda sai anmasa wannan allurar dake kaman sumar dashi kaman sakasa bacci na awanni.

Yana gamawa ya dade Yana istighfar da adhzkar kafin ya miqe.


Mama ma tayi Lattin tashi sbd zazzbin data kwana dashi Amma kuma tinawa da matsalarta ta kau sai ta tashi zuciyarta fes ba damuwan komai dan haka karfe 9 da rabi dukkaninsu suka fara fitowa breakfast daya bayan daya.

Suna zaunawa Shima ya iso a natse a kame Yana fidda kwarjinsa da haibarsa Yana daukan idanuwan duk Wanda yake kallansa.

Nicky da yanayinsa na jiyan yake dawo mata wasu mayun yawu ta hadiye tana masa kallan maita.

Gaida Mama yayi a kame hakama a Kamen ya amsa gaisuwan kowa Yana zaunawa.

Fara breakfast din sukai wanda Yana daukan cup din gabansa yakai bakinsa Fiddausi da Jannah suka sako kai a palon...

Jannah ce baya cikin nutsuwarta da a kame fuskanta bata kowace halitta a cikinsu ba ta qaraso gurin Nicky dauke da qaton plate din chicken potato.

Sayd daya dago a lokacin tea din dayake bakinsa ne ya dawo masa da karfin gaske haryana biyo ta hancinsa sbd mummunan firgicin da ba zato.

Mama m kusan abincin bakinta dinne ya dawo mata ta sarke da karfin gaske tana neman agajin ruwa da gaggawa sbd qwai da yayi mata cikin kai.

AZIZ LIMBA cup din hannunsa ya dire da karfi a kan dining din wanda ya saka gaban kowa faduwa tareda dagowa ya sauke idanuwansa da tin jiya basu koma daidai ba akanta.

Nicky ganin hakan da sauri tareda son nuna kokarin datai tace

"Mine na saka ayi maka wani abinda zakaci bayan tea sbd nasan bazaka ci breakfast me nauyiba"

Kallan Jannah tayi tace

"Ki ajiye a gabansa ki tafi"

Mama datake tari har lokacin cikin tsananin baqin ciki tace

"Waye ya bawa me aiki izinin shigowa muna breakfast"

Da sauri Nicky tace

"Nice na sakata ta kawowa Mine abu ne"

Zuciya Mama kejin kaman zata hadiya sbd baqin ciki ta bude baki zatai magana Nicky ta katseta da cewa

"Mama shatin meye a wuyanki?
Rataye kanki kina tashi yi ne sbd abinda ya faru jiya ko me?
Kodai mahaukciya Maman Jannah ne ta sake Miki wani abin kaman wancan Karan?
Mama kin hana a koresu last time gashinan tana neman sake illaki
Mama ki......

Wani irin baqin cikin daya taso ya rufe mama akan Nicky da babu alkhairi ko daya a duk lokacinda zata aikata abu dan haka bazata kashe ita kadai da ciwon zuciya ba sedai su mutu tare dan haka batasan lokacinda tace

"sbd JANNAH ZAD ce matar AZIZ shiyasa"

Daidai lokacin da maganar Maman ta fita daidai AZIZ din na kama hannun Jannah data juya zata bar dining din ya juyo da ita gaba dayanta.

Ita kuwa Nicky dip ta dauke wuta zaune a gurin maganar Mama tayiwa qwaqwalwanta saukar bomb din soji.

Shi kuwa budan bakinsa kalman daya furta itace

"Mimi na raye????

Sayd kuwa bakinsa a rikice yace "4&4"
#MAMUH
#ZAADENS

07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee

Book 2
Chapter 25

*SHOP WITH ME BY RANO*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.


************
Qarasa sarkewa mama tayi da jin abinda AZIZ yace ruwan datasha suna qarasa biyowa ta hanci da yi cikin kanta,

Ita kuwa Nicky maganar Maman da 4&4 din da Sayd ya ambata Yana kallan Jannah suka saka jini fara fitowa kawai ta hancinta habo me karfi na balle mata.

Fiddausi a rikice take bawa Mama ruwa tana kuma daukan tissue da sauri tana dorawa Nicky a hanci da hannunta daya..

Jannah da maganganun Nicky itama suka gama tinzira zuciyarta akan Ummanta Fizge hannunta tayi daga cikin nasa tana juyawa zata fice Nicky tayi wani irin yunquri tana daukan ruwan tea masu tsananin zafi ta watsa mata setin fuskanta Wanda kafin saukansu AZIZ din ya miqe tsaye da sauri Yana rufe fuskan jannah da tafin hannuwansa biyu yana bada bayansa ga ruwan zafin.

Falaq da sauri cikin tsananin tsoro ta miqe tana daukan tissue tafara goge bayansa hnkali tashe tana cewa

"Daddy ruwan zafi ne f sosai?
Daddy ka cire rigan da sauri"

Ko abinda Falaq din ke fada baya ji hannun Jannah din ya sake komawa ya jata kai tsaye suka bar dining din yana janta zuwa palonsa sedai ko taku hudu basuyiba ta qwace hannunta da karfi tana dakatawa tareda dagowa ta kallesa da idanuwanta da sukai ja suna bayyanarda tsanar datakewa duk Wanda yake gidan tace

"Idan umarni ne dakai ka fadamun ba buqtaan zuwa koina,
And Ni me aiki ce inada haqqina na Yar Adam kuma musulma dan haka tabani keta haddin Allah da kuma na addini na ne"

Wani irin zafi da radadin gaske zuciyarsa ke yi ya kalleta da idanuwansa da sukai jajir ya bude baki yace

"Meya samu tinani da hankalinki?
Aiki kike magana?
Ke me aiki a cikin gidana?
Are you mad or just stupid?
Wane son of a bitch dinne ya baki matsayin me aiki a gidan nan?,
Duka Zaadens suna aiki a gidana a matsayin me aiki waye da waye suka San da hakan a gidan nan?

Cikin izgilin maganar da yayi mata ba tsoro ko shakkar kowa ta juya ta kalli Mama da idanuwanta tana bude baki tace

"Wannan maganar ahali ce Ni dai a matsayina na me aiki idan har aka sake wucen iyakata ta hanyar tabani ko sake ambatar Ummana da wani sunan da ba itace ta dace dashiba masu gidan ne to tabbas zamu tafi kaman yanda ake bin dare ana biyanmu dan hakan"


Juyowa yayi ya kalli Maman Wadda gabaki daya ta qarasa rikicewa tana debewa Jannah da Nicky albarka cikin ranta...

Baki ya bude zaiyi magana Nicky ta kalli Mama cikin wani irin tsananin baqin cikin da zarewan kai har lokacin hancinta na jini tace

"Meyasa tin farko kika boyeta kina kallo bayan alkawarin da kikai har abada bazata dawo rayuwarmu ba,
Amma shine Mama kina kallo kika hana a koresu bayan dukan da mahaukaciyar mahaifiyarta tai Miki?
Menene yasa kika hana su tafiya Mama?

Cikin wata irin tsawan data saka kowannensu sake shiga mummunan tashin ya katse Nicky da cewa

"Kina shan weed ne?
Mahaifiyan Jan kike ambatarwa hauka ko me?
Daga lokacinda bakinki ya qara furta mata irin wannan kalman zakisan matsayinki bai gama cikaba a gidan nan......

"AZIZ" Mama ta kirasa da idanuwanta jajir na azabar da bata gama futa ba ta sarkewa zuciyarta na wani irin tiririn fara kare mahaifiyar Jannah da yayi maimakon ita tace

"AZIZ jin nayi kaman Kana daga matsayin Zaadens akan taka Uwar??
Menene matsalanka da duk sunan da zaa kirasu?
Inace Jannah din tsohuwar matarka ce da babu aure a tsakaninku idanma akwai wlh ban yafe yau auren ya kwana ba batareda ka saketa ba"

Dago jajayen idanuwansa yayi y sauke akan Maman yana hadiye maganar da yayi niyar fada sbd idan akwai wnda yake girmamawa da jin nauyi a duniyarsa yanzu d baida mahaifiyar data haifesa to Mama ce,

Fada mata magana a cikin ido ba dabia ko halinsa bane Amma kuma akwai abinda ko bai fadaba mutuwa ce kadai takai can.

Nicky da hawaye ke bin fuskanta jikinta koina na wata irin rawa fita tayi da gudu bta ko ganin gabanta tayi kitchen wanda ba shiri dukkaninsu suka bi bayanta Banda AZIZ din daya qi motsawa ko taku daya sbd yasan dai haukarta ko rabin tasa bataiba ita qananun likitoci take gani shikuwa manyan likitan kwakwalwa yake gani.

Mama datasan bangaren masu aiki Nickyn tayi kuma kowama zuwa zeyi dan haka ganin Fatima ayau din kila ya tabbata dan haka da gudu take bin bayan Nicky din tana kiranta tareda yimata tsinuwar da duk taxo bakinta sbd tana taba Jannah Allah ne kadai me hana AZIZ zuwa bangaren.

Cikin daga sauti Mama ke cewa

"Sisi ki tareta duk tsanani kada ki bari ta qasa bangaren Nan"

Sisi na jin hakan suka fito itada Yan aikin gidan gabaki daya.

Nicky a haukace take bata ji bata gani abu daya takeso ta kashe Jannah idan yaso ko bata auri AZIZ ba tasan dai bazai taba auren kowa ba.

Ammar ne a tsaye Yana goge motar Nicky din y hango Nicky tafe a haukace da kwalban glass cup a hannu.

Jannah dake kokarin fitowa daga bangarensu ta tinkara gadan gadan dan haka da gudun gaske ya tinkari Jannah din

Kafin ya isa Nicky ta daga kwalban da karfi zata bugawa Jannah a kirji Jannah ta kauce sedai cikin tsautsayi kwalban ya yankata sedai ba sosai ba sbd ta kauce.

Cikin mummunan tashin hankali Ammar da idanuwansa suka rufe ya zabgawa Nicky wani mahaukacin marin daya saka Mama tsallakewa da wani irin tsallen gudun gaske sbd tasan shima haukar ta motsa kenan bige bige zaayi.

Madam Sisi da daman a tsorace take itama wani mugun tsallen ta daka tana neman hanyar guduwa kafin uwar Yan haukar itama ta fito jin ihun 'yarta Wanda tasan duka gidan haukacewa zeyi tinda mahaukatan ciki sunfi masu lafiya.

Sayd da gabaki daya hankalinsa ya tashi da wannan tashin hankalin da rikicewa da gidan yayi da sauri ya nufi Ammar shi da Maheer sbd ganin yanata kifaw Nicky Mari ba kakkautawa.

Mama gabaki daya hankalinta ya rabu kashi biyu ga tsoron haukar gaske tuburan datke gani ga tashin hankalin kada Ummah ta fito.

Riqe Ammar akai har lokacin itama Nicky bataji bata gani Jannah take son illatawa..

Ammar hannuwansa na wata irin rawa ya dawo gurin Jannah dake tsaye idanuwanta jajir tana kallansa cikeda tsananin kauna da tausayin halinda yake shiga akanta ya zubawa kirjinta dake jini ta cikin doguwar rigar jikinta.

Qara ja idanuwansa ke yi ya miqa hannunsa kai tsaye zai bude rigarta ta wuya ya duba gurin
Hannunsa na isa kafin ya sauka jikinta aka riqe hannunsa cak.

Wata irin rawa hannunsa keyi Wadda ba tasa rawar hannun ce ba ta hannun daya riqe nasa hannun ne...

Gabaki dayansu tsit sukai tareda tsayawa cak sbd yanayin AZIZ din yayi munin da tsoronsu ya qaru.

Falaq kuka takeyi tin dazu tana jikin fiddausi a qanqame.

Mama kuwa rawa kafafunta suka dauka ganin AZIZ din da bata taba ganiba tin yana yaronsa kuwa.

Alluran

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login