Showing 3001 words to 6000 words out of 150681 words
da Ummah na aiki ya dakatar dasu daga komai yace su ringa zaman banza yafi masa kwanciyar hankali da nutsuwa.
Zuwansu Maheer binni kai tsaye lokoja suka fara fafutukar neman aiki bayan sun sauka a wani gidan haya me dakuna da yawa suka biya na wata daya,
Sabon tashin hankali da firgici Ammar da Maheer suka shiga a gidan sbd ganin wata sabuwar rayuwar da basusan ana yin irinta,
Idan Ammar zai shiga bandakin gidan se Maheer ya rakasa ya tsaya masa hakama shima Maheer din se Ammar ya tsaya masa sbd tsoron mutanen gidan ma sukeyi dan kowa a gidan kamar qasurguman yan dashi da makami babu ke kyan gani a fuskarsa ga fada da a take yake barkewa a gidan a ringa ciro makaman dake kusan sakasu zarewa da tsoro.
Shi Kansa modibbo daurewa kawai yakeyi yana danne tsoronsa sbd ya nunawa su Ammar jan wuya ne shima dan kada su cucesu idan an samu aikin.
#MAMUH
#JANNAH ZAD LIMBA
#AZIZ AY LIMBA
#ZAADENS
#LIMBAS
#NEW LIFE
#BEST LOVE
#BEST ROMANCE
#NEW TWIST
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
Mamuhgee
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo
ADUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee
Book 2
Chapter 3
Ranar da suka fara fita aiki wuni sukai suna yawo se yamma sosai suka dawo da ledar bread da kosai se ruwan pure water dasu Ammar din sukejinsu kamar ruwan zam zam,
Haka suka kwana washe gari ma suka sake fita modibbo yakaisu gurare kafin ya tafi nasa wasu yan harkokin ya barsu suna sake yawon bincikawa cikin azabar rana da rashin isashen abinci ruwa kawai suke zubawa cikinsu,
A ranar ma haka suka gama yawo suka dawo gida a gajiye suka samu kosai da dankalin hausa sukaci suka hau baccin gajiya da azaba.
Rana a uku wani kamfanin gine gine suka nufa inda wani mutumin modibbo yayi musu hanya suka isa cikeda burin su samu abinda suke so.
Zaman jira suka fara zaune a bakin office din Wanda sukaxo ganin lokaci me tsayi batareda an nemesu ba.
Dago kai Maheer yayi yana kallan koina yana karantar yanayin gurin,
Tsari da yanayin gurin dama mutanen gurin ya saka Maheer da Ammar sauke ajiyan zuciya a Karo na babu adadi sbd Banda rayuwa da sauyin kaddara basuma San akwai kananun kamfani irin wainnnan ba da mutum ma zaiyi tinanin samun albashin da zai riqe kansa harma da wani.
Wani turanci director din gurin ya wuce Yana yi Wanda ya saka Maheer da Ammar kallan juna jiki a mace sbd wannan ko securities dake aiki kamfani ko gadin gidansu sunfi wannan ilimi da lafiyayyan turanci amma wannan ace shine director din da zasuyi aiki a qarqashinsa.
Ammar ne ya bude baki cikin damuwa da takaici yace
"A hakan sunyi degree da Masters zasuce ko?
Numfashi Maheer ya sake saukewa Yana cewa
"Koma basu taba shiga aji ba is their problem mudai mu samu aikin kawai musamu mu dawo field din yanda zamu fara sake gina Zaadens"
Modibbo dayake gefe sosai tsaye sbd baa bari ya shigoba shi tinda bada shine zaa bawa aikinba.
Se bayan sallar laasar suka samu akace su shiga bayan me gidan ya dawo sallah kenan.
Miqewa sukai suna dan sake nutsuwa suka shiga cikin nutsuwa.
Dagowa yayi Yana daga zaune kan kujera ya kallesu Yana amsa sallama da gaisuwansu Yana tinanin kamar yasan fuskokin nasu.
Ganin irin kallan dayake musu ya sakasu sauke kawunansu a tare cikeda jin damuwa na rufesu sbd sunsan tabbas kila ya sansu din koda a jarida da labarai ne tinda sunyi lokacinda babu ranar da a labarai baa fadar irin tarin nasarorinsu da arzikinsu hakama kusan kowa daya sansu yasan labarin kaddarar data samesu,
Wasu sun tausaya musu wasu kuma sunyi Allah wadai dasu,wasu kuma sunyi Allah ya qara musu azaba da kunci dan haka a cikin mutane yanzu basusan da wace fuska kowa ke kallansuba.
Numfashi ya sauke yana nuna musu gurin zama a hankali tareda karban folders din hannuwansu Yana cewa
"Kun dade kuna jira ko? Baqin ne da yawa hakama ayyukan"
A natse Maheer yace
"Ba damuwa ai munsan yanayin ayyukan"
Bude takardun yayi Yana dubawa ahankali
Akan sunayensu ya tsayar da idanuwansa tsawon mintina kafin ya dago ya kallesu a natse tukuna ya sake maida idanuwansa akan takardun Yana dubawa.
Abinda ya ganine a ciki game da irin girman ilimi da tsagwaron karatu da experience da suke dashi ya sakasa jin ganganci ma ne a gurinsa daukansu aiki a gurinsa sbd ba bata lokaci yake ganin zasu dokesa su zarcesa sedai ya koma kallo.
Dan haka ajiyar zuciya ya sauke yana rufe takardun ya kallesu da dukkanin nutsuwarsa yace
"Well gaskia a yanzu ba kowace irin damar dauka aiki tako ina
Mun riga mun cike slots namu Wanda ko zaa samu wata damar ba yanxu kusa kusa ba so ina me baku hakuri sbd Kunyo tafiya me tsayi"
Numfashi me dumi suka sauke ahankali idanuwan Ammar na sauyawa ahankali zuwa ja sbd baqin ciki da damuwa da wani irin sanyin jiki
Maheer ma cikin karfin hali da juriya tareda hadiye damuwarsa ya bude baki yace
"Ba damuwa,thank you so much"
Miqewa sukai suka nufi kofa Ya bisu da kallan tausayi kafin ya bude baki yace
"Kunga ku dawo na fada muku wata damar idan kunaso"
Dakatawa sukai a tare tareda juyowa a natse suka sake zauna suna jiran bayaninsa.
Ajiyan zuciya ya sake saukewa Yana fuskewa kai tsaye yace
"Akwai securities na gate da masu aikin cikin gida da masu aiki da ake nema a wani kamfani Zaa kai gidan wani baturen Alh da baa qasar nan yake ba,
Masu aiki da securities da ake nema wainda sukeda ilimi me zurfin gaske akeso sbd yanayin familynsa da turancin suka fi ji,
So a taqaice dai masu ilimi irinku ake nema idan zaku iya
Slots din na nan amma sai anyi muku interview so if zaku iya yayi muku zan iya gabatar daku a kamfanin da ake neman"
Zuba masa idanuwa Maheer da Ammar sukai idanuwan na jajir sbd wani irin baqin ciki da qunci daya cike kirjinsu da zuciyarsu da maganganunsa wai securities masu gadi fa kenan kuma har sai an musu interview a gidan wani Wanda bayama kasar gadin gidansa zasuyi abanxa kafin ya dawo din.
Ganin yanda idanuwansu sukai jajir na Ammar hadda wasu zafafan hawayen qunci da dacin zuciya ne suka cikasu
Bude baki yayi sbd ya sake fahimtar dasu yace
"Karku damu aikin ba wani aikine me wahala ko yawa ba
Zakuji dadinsa na tabbatar sbd a bayanin gidan mansion ne sabo da aka kammala a watan nan hakama kwata kwata fa basa qasar,
Matarsa da zai aura ce baturiya shiyasa dole se masu zurfin ilimin irin naku,
Hakama a cikin mansion din akwai bangaren masu aiki da da zaku zauna acikin kwanciyar hankali da wadata tareda jin dadin gaske,
And idan kunada mata ko kanne mata kuma sunada ilimi irin naku duka sauku cike slots din sbd ku samu zaunawa dukanku a cikin mansion din bangarenku na masu aiki sbd samun nutsuwa
Daga karshe kuma albishirin da zanmuku albashin nada tsananin tsoka da girman gaske Wanda duk aikin da zaku samu na kamfani bazaku samu albashi me Kyansa ba"
Ammar kasa cewa komai yayi ya miqe hawayen idanuwansa na gangarowa yafice kirjinsa na masa wani irin nauyi,
Hannuwansa yasaka Yana share hawayensa da suka gangaro Yana jin zancen na sake yankar zuciyar ta yanda bama akansu zancen ya tsaya ba ace wai idan sunada kanne ko mata suzo suyi aikatau dasu,
Tayaya zai iya kallan Jannah a matsayin maid tana aikin aikatau a karkashin wata macen?
Tayaya zasu bari Ummah tayi aikatau a qarqashin wata bayan yanayin lafiyarta ma dasuke lallabawa dan su samu su farfado su nema mata lafiya da duk abinda zasu tara.
Maheer ma dago idanuwansa da sukai jajir yayi ya kalli mutuman ya bude baki ahankali yace
"Mun gode bama buqtaan hakan zamu ci gaba da neman aikin a wani gurin"
Miqewa yayi shima ya fice yana danne radadin da zuciyarsa ke masa.
Modibbo na ganinsu hankalinsa ya tashi jikinsa yayi sanyi sedai kafin ya juya ya bisu secretary din office din yazo yace ana kiransa.
Modibbo na shiga office din ya zube qasa yana gaidasa cikeda girmamawa.
Amsawa yayi kafin ya sake korowa modibbo zancen dallah dallah da irin tarin kudin da zasu ringa samu a aikin kafin ya ciro katinsa ya bawa modibbon yace
"Ga numbern wayata nan idan kunje gida sun sake shawara akan zasuyi saiku nemeni"
Karba modibbo yayi da sauri yana rudewa akan jin kudi da alkhairin da zaa iya samu a aikin idan sunyi.
Kudi ya ciro dubu goma ya bawa modibbon yace
"Gashi ku hau mota sai naji daga gareku,idan kuma kunja lokaci zasu iya rasa damar sbd aikine da duk me wayo ya samu zaiyi gaggawan karba"
Godiya modibbo ya hau yi Yana rawan jiki kafin ya fito yana jin idan badan masu zurfin ilimi da akace ana nemaba da babu abinda zai hanasa tattaro su Garba dasu isiya suzo su karba aikin amma ko su Ammar din wlh ba barinsu zaiyiba sai sun karbi aikin nan koda asiri ne.
Yana fita tini su Maheer sun fice daga kamfanin zuciyoyinsu cikeda daci da radadi me zafi.
Acaba suka tara su uku sukai overload suka wuce masaukinsu kowa zuciyarsa cikeda tinani me nauyi Musamman modibbo daya matsu daya koma ya fayyacewa su isiya wannan samu da rashin dasu Maheer ke kokarin janyo musu dan rashin tinaninsu,
To wlh tsaf zai gama zugasu da takurasu saiya tabbatarda sun karba aikin dukansu har Jannah tinda itama tanada ilimin da akeson gwara suje suyi aikin ai yafi zaman banza.
#MAMUH
#BEST LOVE
#STEEZ
#ROMANCE
#LIMBAS
#ZAADENS
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
Mamuhgee
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo
ADUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Book 2
Chapter 4
Suna isa gida Maheer jin yayi gabaki daya garin ya fita ransa kauye ma kawai yake son komawa sbd zuciyarsa ta huce daga radadin datake masa,
Ammar ma jin yayi kamar ya hakura da neman aikin gwara su fara wata sanaar su fara Gino kansu daga nan sbd baa taba cin fuska da mutuncinsu kamar yau din ba da zaa kalli girman takardunsu da babu inda ko a ido zaa samu ganin irinsu ba ace wai zaa basu aikin securities a matsayin masu gadi Jannah da suke gwagwarmayar neman komai dan inganta rayuwarta data Ummah ace suma a matsayin masu aiki,wace irin cin mutunci da tozartawa ce wannan?
Modibbo ganin yanayin da suka shiga ya saka ya dakata daga musu magana ya bari sai sun koma gida tukuna amma kam wannan aikin shi a gurinsa kamar anyi an gama ne Banda rashin godiyan Allah irin nasu tayaya zaka samu aiki irin wannan ka tsaya wani duba darajar kai da duba girman iliminka,
Banda sun samesu masu zuciyar tausayi da duba zumunci uban me zai saka su karbesu su basu gurin zama Harma da abubuwa da yawa harda gurin nema da basu damar sanaa tinda su a lokacin da suke cikin daularsu basu taba tinawa ma da akwai dangin kakarsu kakarsu a kauye ba saida suka hadu da qwallon shegen da baya barwa Allah ya fisu zama dan ta'adda ya ruguxasu tukuna suka nemesu.
Har dare babu me walwala a cikinsu sunyi sanyi sosai haka suka kwana bama tareda sun nema wani abincin kirki sunciba.
Washe gari suka so komawa amma Maheer ya daure ya dangana suka sake fita neman aikin Wanda kamar hadin baki babu inda suka samu komai sai wulaqancin dayafi na farkon dan akwai inda aka daukesu amma wai shi Maheer din driver shi kuma Ammar security a kamfani.
Modibbo ganin hakan yasa suka aje maganar aiki suka bisa sabgar kasuwancinsa data kawosa suka koma yawon kasuwannin hatsi da dabbobi a haka suka cike kwanakinsu suka tattaro suka dawo.
Dan abinda ya rage musu na canjin da suka samu a kasuwa tareda modibbo suka siyowa Jannah da Ummah sabin takarmi da dogayen riguna masu dan kyau da turare da sabulun wanka me kyau da toothbrush da sabon brushes na dukkaninsu su biyar sbd iya kokarinsu basa son Jannah ta rasa kyan sigarta ko yayane bazasu iya bari ta koma abar tausayi ba tinda sun fito zasu nema komai su kuma qarar da koman akanta da Ummah.
Jannah ce ta fara samun labarin isowansu a bakin yaran gidan daketa ihun modibbo ya dawo dan haka ta wanke hannunta ahankali daga gama gyara daure dogon gashinta da fatma ta gama mata kitso me kyau.
Kofar shigowa bangarensu ta kalla daidai lokacinda Ammar ya fara sako kai da sallama ta sake murmushi me kyau da nutsuwa na farin cikin ganinsu zuciyarta na sanyi me dadi ta karbi babbar jakar hannunsa tana cewa
"Welcome Ammar Zad"
Sanyi daya mamaye zuciyarsa ne na saukan muryanta kunnensa da yanda haryanxu take kiransa yake kashesa akanta take quncinsa ya narke yabar kirjinsa murmushinsa me kyau shima ya bayyana yana qarasawa ya zauna a kujeran data tashi Yana cewa
"Thank you Jan,
Yaya kauyen nan?
Ina Ummah ne ta shiga?
Hannu ta miqawa Maheer suka gaisa Ya jata zuwa shimfida suna kokarin zama Ummah ta fito dgaa daki tareda Dad da zai fita suna ganinsu Ummah ta sake fuska sosai tana kallan Ammar da shima ita yake kalla Yana nuna mata gefensa taxo ta zauna ya fidda Apple Guda biyu daya siyo mata ya miqa mata Yana cewa
"Ci wannan kiji yafi wancan mangwaron nasu garba me shegen tsami da saka ciwon ciki"
Cikin farin ciki me tsanani Umman tace
"Da gaske kake?
Wannan yafi wancan dadi kace??
Gyada kai yayi yana dariya
Juyawa tayi ta kalli dad ddaa farin ciki sosai a fuskanta alamar hakane
Yana dariya cikeda kulawa da wani irin sanyin kaunarta dake cikeda zuciyar Dad din ya gyada mata kai yace
"Yes kici zakiji"
Maheer ta maida kallanta akansa har lokacin farin cikinta a bayyane yake
Dariya shima yayi Yana gyada mata kai alamar eh
Zata kalli Jannah
Jannah din Tai saurin karbewa tana cewa
"Bara na wanke muji ko Ummahna"
Da sauri Umman ta miqa mata dayan tana cewa
"Wanke duka mu cinye"
Maheer dake kusa da ruwa ne ya miqo musu Yana cewa
"Ba kudine ai da ansiyo da yawa tinda nasan Ummah zata so shi sosai dan nima bana son suna shan mangwaron nan kwata kwata"
Jannah cikin kulawa ta bawa Ummah tana cewa taci.
Dad ne ya kalli Maheer Wanda shima shi din ya kalla kafin suka kalli Ammar suka miqe dukkaninsu suka fice zuwa waje.
Suna fita Jannah ta bisu da kallo sbd tin shigowansu taga damuwa boye a tattare dasu.
Suna fita masallaci suka fara nufa sukayo sallar laasar kafin suka dawo a hanya Maheer yakewa Dad bayanin abinda ya faru.
Shiru Dad yayi zuciyarsa na sanyi da damuwa kafin yace
"To Allah yasa hakan shine mafi alkhairin ya kuma kawo mana wata mafitar"
Amin" suka amsa dashi suna qarasawa gida.
Abinci suka ci da daddaren kafin suka fidda siyayyr da sukayo musu,
Fira suka hau yi hankalinsu kwance cikeda kulawa da juna har dare sosai kafin kowa ya shige.
Da sassafe Garba ya shigo bangaren yayi sallama ya sanarda Dad su Modibbo na son magana dashi.
Fitowa Dad din yayi daga daki Yana saka hular sanyi a Kansa sbd akwai sanyi ya fice Maheer na bayansa Ammar be tashi ba hakama Jannah da Ummah.
Tin daga nesa Maheer ganin irin kallan dasu kawu ke jeho musu da irin yanda suka zauna babu me faraa a fuska ya san akwai inda aka samu matsala.
Dad a natse ya qaraso yai musu sallama ya nema guri ya zauna suna gaisawa.
Maheer ma gaidasu yayi cikeda girmamawa kafin ya zauna dga gefe kan dutse.
Shiru gurin yayi tsit kafin Kawu Jibo ya bude baki yace
"Dzad kasan da labarin su Mahe sun samu aiki me kyau da asirinka da nasu harma da namu zai rufu sunqi karba sbd girman kai da ganin sunfi karfin hakan?
Kai tsaye Dad yace
"Wane aikin ne wannan??
Modibbo ya karbe da cewa
"Aikin securities me kyau da albashi me tsokar gaske"
Numfashi Dad ya sauke yace
"Ni bana takura yarana akan abinda basaso ko basuyi niya ba sbd kawai ina cikin talauci,
Idan har tin acan since bazasu iyaba to shikenan din bazasu iyaba"
Wani kallo kawu isiya yayiwa Dad din cikeda mamaki da siqewa tareda takaici yace
"Kenan dai sun fada maka kuma ka goya musu baya?
Harkar samu?
Harkar ci gaba sbd kada mu lasa arziki shine kuka taru kuka yanke shawarar bazasuyiba"
Kawu Jibo daya gama cika shima da baqin ciki kai tsaye yace
"To Ni kawai aban kudina dana bayar bazan iya wannan kayan baqin cikin ba tin yanzu anfara kafin ayi nisa,
Dubu sittin cif a miqomin abuna yanxun nan inada abin yi dasu"
Kawu isiya ma cewa yayi
"Eh gaskia indai bazaa karba aikin da aka gani a kasa ba nima aban kudina bazan iya jira ba dan ba ranar samun wani aikin gwara aban na fara wata sanaar dasu kawai"
Modibbo daya rasa abin fada kallan dad yayi ya gyara zama Yana tattaro nutsuwarsa yace
"Dzad ka nutsu ka duba lamarin rayuwar dake gudana a yanzu,
Kai din baya ba kai bane a yanzu
Hakama yayan naka da sunan da mutuncin da matsayin duka basu bane a yanzu,
A baya idan akace Zaadens magana ake ta masu qasa da wajen qasar ma amma ka duba a yanzu a ina kake?
A ina rayuwa ta dawo da kai.
Maheer ya kalla yace
"Kai Mahe inace cewa kukai zaku sake farowa daga farko ku sake gino Zaadens da guminku da gwagwarmayar da duk ya kamata,
Idan da gaske hakan ne to banga dalilin qin karban aiki kowane irri bane indai bana haram bane ko sabon Allah,
Aikin nan fa bana dindindin bane ku karba ayi na dan lokaci ana samun abin Gina kai saiku ajiye ku fara duk kasuwanci ko aikin da kukeso,
Dan haka xabi dai anan biyu ne kodai ku karba aikin nan ku samu damar fara kafa kanku kokuma ku tabbata anan kauye cikin wannan rayuwar da bakwason ku mutu a cikinta,
Hakama dukanmu idan lamarin bazai yiyuba muna buqtaan kudinmu a cif cif ba bata lokaci"
Shiru Dad da Maheer sukai jikinsu a mace zuciyoyinsu a jagule da maganganun su Kawun.
Ajiyan zuciya Dad ya sauke kafin ya kalli su Kawun yace
"Ba damuwa inshallah zamuyi shawara muga abinda zai yiyu gameda biyan kudin"
"Ah ah bawai shawara ba muji shiru,
Aikin nan dai modibbo yace kada a wuce dan lokaci Idan ba hakan ba zaa rasa dan haka ayi me yiyuwa asan nayi"
Kawu Jibo ya fada hakan Yana sake matse fuska.
"Inshallah zaa kokarta kafin lokacin" Dad yace Yana miqewa yabar gurin Maheer na bin bayansa.
Suna isa ciki babu Wanda yayi magana saima shiri da sukai suka fice bayan sun karya da madara da zafi da waina
Se yamma sosai suka dawo,
Dare nayi suka ci abinci gabaki dayansu a tare kafin Dad da Maheer suka sanar da Ammar abinda yake faruwa da kuma tafiyar da zasuyi goben hadda Dad su sake bazama neman aiki koda bana office