Showing 57001 words to 60000 words out of 150681 words
balain da masifar ya sakata tashi a firgice cikin baccin da bai dauketaba sbd gadin jiran dawowan Jannah sai asubar me nauyi ya dauketa.
Tana bude idanuwanta a rikice taga mutane tsaye tsakiyar dakin Jannah na qanqamesa da karfi idanuwanta cikeda hawaye tana rokonsa kada ya fita a lokacin shikuwa Kansa Yama kasa daukan uban waye yake ihun kwarto a cikin gidansa sannan ita ta sakasa daki ta boye?
Fatma datake a rikice da ihun su Madam Sisi kurma sabon ihun tayi sbd da duhu a dakin ba haske tana miqewa da tsananin gudun gaske itama ba Kayan arziki a jikinta ta banka kofa da gudun gaske ta fito tana taya su Nicky ihun.
Rintse idanuwansa d sukai ja sbd tsananin bacin rai yayi zai yi magana jannah tayi saurin saka hannunta dake rawa bakinsa tana rungumesa cikeda tsoro da kunyar da zata iya kasheta idan ya fita.
Nicky na ganin tsananin tashin hankali da firgicin da Fatma ke ciki bata tsaya wata wata ba ta nufi dakin ta fada tana tsananta ihunta sbd ta tabbata Ammar da Jannah suna ciki.
Tana sako kai cikin duhun dakin tana ihun AZIZ da yagama kai maqura a bacin ransa hannu ya daga ya zabga mata wani mahaukacin marin daya sakata zubewa baya tana fadowa Madam Sisi data biyota suka zube qasa take jikin madam Sisi ya dauki muguwar rawa cikin tsananin mugun tsoro ta ture Nicky da karfin gaske tana miqewa ta bar gurin da gudu tana cewa
"Wlh yana dakin,
Gashinan a ciki"
Mama n jiyo hakan ta dawo da gudu duk a rikice,
Su Maheer ma dasu Sayd zagayowa da gudu dukansu sukai gabaki daya gidan suka taru a kofar dakin,
Zaadens da sukasan zinariyarsu n ciki take suka qarasa haukacewa suna tinkarar dakin da karfin gaske.
Falaq dataji Jannah na ciki hakama kwarton kasa riqe kanta tayi da gudun da babu wanda ya ankara ta wuce kowa ta isa kofar dakin jikinta n Tsananin rawa ta tura kofar dakin daidai Jannah zata rufe dakin d key.
Da karfin gaske Falaq ta fada jikin Jannah din tana qanqameta jikinta na rawa har lokacin ta fasa kuka tana sake kankameta kaman zata shige jikinta.
Gari ya fara haske dan haka Sayd yayi saurin cewa kowa ya dakata da makaminsa sbd Falaq data tare kofar..
Kuka takeyi sosai tana sake qanqame Jannah,
Jannah dake rikice cikin tsananin tashin hankali kasa motsawa tayi tana kokarin janye Falaq din Falaq ta bude idanuwanta ahankali kaman a mafarki idonta ya sauka akan Daddynta dayake tsaye dukkanin bacin rai da fushinsa a fili amma ya kasa take rokon Jannah din ya fito yaci uban duk wani mahaukacin dayake gidansa.
Da tsananin mamaki me karfi ta saki Jannah ahankali tana kallansa kafin ta dawo da kallanta kan Jannah Wadda kunya ta sakata qasa da kai.
Juyowa Falaq tayi da sauri taga yanda kowa yayi cirko cirko tsuru tsuru suna jiran ta fadi abinda ta gani sbd sun tabbatarda duk abinda yake bayan Jannah cikin dakin ta gani.
Cikin ihu Fatma tace wlh naga mutum a cikin dakinmu,
Madam Sisi da tin dazu take zuba rantsuwar taga kwartaye da idonta karbe zancen tayi tana maimaitawa.
Nicky da tini jinta ya dauke sbd Marin datasha hakama ganinta rawa yake a hakan ta saka aka kawo mata wayarta ta kunna recording dn kofar dakin sbd tanason nunawa AZIZ lokacinda aka kamasu suna fitowa dakin.
Juyowa Falaq tayi ta sake tare kofar ita kuma Jannah ta sake kama hannunsa ta jasa bayan kofa tana sake riqe hannunsa cikin nata idanuwanta duk sunyi ja kuka takeson yi sbd abinda take ji na wannan mugun yanayin da suka samu kansu.
Falaq bude hannuwanta tayi ta sake tare kofar ta bude baki tana kallan Sayd tace
"Ba kowa a ciki Jan ce kadai"
Mama da duk ta haukace tace
"To ta fito mana me takeyi a dakin kowa ya fito dan wanke Kansa"
Sayd Falaq ta kafawa ido Wanda yake kokarin fahimtar me take son fda masa tace
"Papa ina Daddyna? Sai yazo zan matsa jikin kofar Nan"
Sayd na jin hakan ya kalli kofar dakin da sauri Ya juya ya kalli fiddausi wadda itama take ta shiga shock ta kallesa tana soke kai.
A rikice Sayd din ya fito yana cewa securities su koma bakin aikinsu,
Kallan kowa yayi zaiyi magana Ammar cikin tsananin zafi ya katsesa da cewa
"Karma hauka ta debeka kace mubar gurin Nan sbd wlh duk abinda yake dakin Matata saina shiga na dubosa idanma mutum ne ya Sani yau kwanansa ya qare,
Waye ya isa ya shigarmun gon...
Kaman saukan tsawar aradu suka ji wani mahaukacin ihun tsawarsa yana bayyana gabansu idanuwansa jajir kaman zasu kama da wuta ya bude baki gabaki daya gidan Yana daukan sautinsa yace
"Securities,ku bude motarku duk Wanda yayi ihun kwarto da duk Wanda ya dauki makami a cikin gidana ko waye da waye ku kwashesu gabaki daya ku kai office ku rufemun"
Jannah dake bayan kofa silalewa qasa tayi tana cusa kanta cikin kafafunta kuka me karfin gaske na zuwar mata.
Mama kuwa jiri ne ya debeta taji kaman rabin jikinta na neman shenyewa idanuwanta na kasa gasgata AZIZ da kansa a dakin masu aiki.
Nicky wayar hannunta ce ta kubuce daga hannunta ta fadi qasa hannuwanta na kakkarwa sbd kasa gasgata abinda idanuwanta suka ganar mata AZIZ LIMBA dinta bangaren masu aiki kuma a cikin daki.
Su Dad kuwa tsananin tashin hankali da shock din da suka shiga ya saka su kasa motsawa Banda Maheer daya Yar da makamin hannunsa Yana isa dakin da sauri ya shiga dan dubo Jannah.
Yana shiga ya isa gurinta da sauri Yana dagota ta rungumesa tana fasa kuka me karfi tana cewa
"Maheer babu abinda yazo yi ba girina yazo ba babu ruwana dashi ba abinda yake tsakanina dashi"
Ynada take maganar tana kuka sosai ya saka jikinsa sanyi hakama Dad da Ammar Wanda yayi mutuwar tsaye sanyi sukaji jikinsu yayi sbd sun tabbatarda Jannah bazata taba komawa AZIZ ba tagama dashi har abada hakama bazata taba musu karya akansaba.
Securities da sukafi kowa hauka akan umarnin uban gidansu da ayau suka tabbatarda a zafafe yake tini suka taho da mota doguwa a rife koina aka bude bayanta aka fara gargada kowa idonsu a rife basaji basa gani dan bama asalin securities na gidan bane bare kaga sauki ko damar nuna matsayinka.
Kowa makaminsa aka sakasa sake dauka aka dinga turasu mota hadda Sayd sbd kowa da kowa akace dan haka babu ruwansu ko Mama rufe ido sukai suka bude mata motar.
Madam Sisi da Fiddausi tace ita ta fara ihun talla mata mari daya daga cikinsu yay Yana cewa
"Zakaci uban bakinka"
Fiddausi da Falaq da Jannah se Amina kadai aka bari sai me gidan kansa da tinda ya bada umarnin yabar gurin Yana samansa kishin Jannah zai kashesa sbd zuciyarsa dake jin zai iya illata Ammar har abada akan kalmarsa ga matarsa.
Falaq ce ta dakatar dasu daga tafiyar sbd tasan kwata kwata daddynta baya hayyacinsa ya bada umarnin dan haka idan ya dawo hayyacinsa zai tsani kansa har abada akan hakan ace shine ya bada umarnin aka rufe hadda mahaifiyarsa da mahaifin jannarsa dan haka bazata bari ya dandani wannan dacin ba.
Samansa taje tayi tayi tagansa Amma shiru bama ya palon yana bedroom dinsa Wanda ta tabbatarda ba lafiya ba.
Tsoro ne ya kamata dan haka ta sauko da sauri taje gurin Jannah da batama San an tafi da kowama ta sanar mata.
#MAMUH
#LIMBAS
#ZAADENS
#4&4
#PSCHS
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee
Book 2
Chapter 33
*_SHOP WITH ME BY RANO_*
08030811300
Kina neman in da zaki samun kayan yara classy kaya na yan gayu at a very affordable price? Ko kina son fara kasuwancin kayan yara amma baki da jarin da zaki saro kayan? Nesa ta zo kusa, kiyi joining community din nan muna saka kaya masu kyau available da inganci a farashi me sauki da zaki dauka ki tallata har ki samu naki kema.
Burinmu shine kowacce mace ta samu sanaar da zata dogara da kanta.
**************
Daqyar ta iya zuwa inda yake din sbd ita kanta tasan zai tsani kansa sosai daga baya idan ya gane abinda yayi sbd tsananin son dayake wa mahaifiyarsa da kuma yanda itama yasan tana tsananin son mahaifinta.
Numfashi ta ajiye tareda ajiyan zuciya ta miqa hannu akan kofar bedroom dinsa ta bude Falaq na komawa palon qasa dan jira.
Duhu ne a dakin dan haka ta isa gurin haske ta kunna ahankali tana juyo da idanuwanta ga dakin.
Kwance yake a tiles can bayan sofa ya qanqame jikinsa jikinsa na rawa sosai Yana yaqi da zuciyarsa dake illata tinaninsa,
Qarasawa tayi ahankali tareda durkusawa gefensa ahankali ta miqa hannuwanta duka biyun ta rugumosa tana kwantawa jikinsa ta lumshe idanuwanta hawayen cikinsu na sauka akan fatar wuyanta.
Qanqameta yayi kaman zai ballata ta rinse ido tana shanye azabar hakan sbd ta saba tin ba yanxu din ba sbd tasan lafiyansa sai ta koyi hadiyewa.
Qanqameta yake sakeyi da karfin da azabar take mata yawa Amma bata iya kwacewaba ko magana sbd tasan relief din dayake samu da hakan.
Shiru sukai a jikin juna tsawon minta ya samu sassaucin zuciya da jiki.
Ahankali ta bude baki tace
"Zasu tafi dasu Dad da Mama ka dakatar dasu pls"
Shiru yayi idanuwansa a rufe har lokacin,
Wayarsa ta tashi ta dauko masa tareda zaunawa ta kamo hannunsa ta saka masa a ciki tana kallansa cikeda tsananin abinda takeji a zuciya bakinta yana kasa furtawa.
Shiru tsawon lokaci kafin ya daga wayar Yana miqewa tsaye yabar gurin Yana nufar balcony dinsa ya tsaya.
Jannah ma miqewa tayi ta fice daga dakin ta sauko a sanyaye,
Falaq na ganinta ta taso tareda riqe hannunta tana kallanta kaman zata cinyeta sbd kauna tace
"Is my daddy ok?
Numfashi Jannah ta sauke ahankali tana dagowa ta zubawa Falaq din idanuwanta tsananin kaunar Falaq din na taso mata.
Falaq ma ganin hakan sake riqe hannun Jannah din tayi tana cewa
"My Jan,
My Dad's Jan"
Rungumeta Jannah tayi tana cewa
"I love you my baby"
Shigowan Sayd palon ce Kansa a qasa ya saka Jannah sakin Falaq tana kallan kofar alaman an sake kowa.
Qarasa sakin Falaq tayi tana barin palon ta kofar AZIZ tana isa harabar gidan inda bata tarar da kowa ba.
Bangarensu ta nufa da sauri tana jin jikinta na sake sanyi.
Da garba ta fara cin Karo Yana ganinta ya tsareta da ido Yana ransa inda komai ma na rayuwarsu data mutan gidan ta dosa.
Maheer da Dad ta sama suna kokarin shigewa da sauri ta iso gurinsu tana Kiran sunan Dad bata tsaya komaiba ta fada jikinsa tana fasa kukan kunyar dake neman kasheta ta hau bayanin babu abinda ya hadata da AZIZ din kawai ganinsa tayi ita kuma tsoron ihun da ake ya sakata jansa ta boye ciki sbd ta dauka Ammar ne kada ayi masa sharri.
Ammar dake tsaye zuciya na son kashesa jin Ashe shi taje karewa take zuciyarsa tayi sanyi Yana sake jin sonta na cike koinansa.
Dad ma da Maheer da dukkaninsu koyaushe kaunarta ke rufe idonsu akan komai na rayuwa ydda sukai da zancenta suna tsake tsanar AZIZ din akan basusan niyarsa ta zuwa kofar dakin su Jannah din da dareba dan haka gabaki daya jin sukai sun sake tsanarsa da tsanar zama a 4&4 din akan a taba mutuncin Jannah sun zabi yafe Sanin inda Saleem yake zasu bar mansion din kota halin yaya ne.
Jannah data samu sassaucin nauyin kirjinta ganin sun amince da zancenta numfashi da ajiyan zuciya ta sauke ta dago ahankali tace
"Ina Ummah??
Gabaki dayansu daki suka kalla
Dad ya sauke numfashi me sanyi cikin nutsuwa da Yar damuwa yace
"Batajin dadi sosai sai asubar ma ta samu yin bacci bayan Tasha magani shiyasa inaga bata farka ba haryanxu abarta ta samu hutu yanda ya kamata.
Ammar ne ya bude baki yace
"Ko zaa kaita asibiti ne Dad sbd Ummah fa bata baccin safe har haka"
Girgiza kai Dad yayi yana qin kallan ko wannensu ya juya Yana cewa
"Zata farka Lfy kalau inshallah"
Jannah ma kaman munafuka ta juya dakinsu ta shige tana shiga ta zube qasa tana jero ajiyan zuciya da numfashi tana dafe kirjinta da bugawarsa ayau ta kusa tada ciwon data jima bataiba.
Fatma datai sallah take tsaye tsuru tsuru tana jiran Jannan sbd tasan ta kwafsa Amma kuma batai tinanin su bane tinda ko a mafarki bata taba tinanin AZIZ LIMBA a bangaren masu aiki ba bare dakinsu.
Jannah bta iya cewa fatma din komaiba toilet ta wuce ta sakarwa kanta ruwa tayo wanka ta fito zauna tareda kallan Fatma da zatai magana ta katseta da cewa
"Fatma pls kada kice komai nima haryanxu ban gama dawowa daidaiba abar abinda ya wuce kawai banason Tina wannan masifar ta yau"
Shiru fatma tayi tana sake jin kunya na rufeta itama na yau din.
*********Da taimakon fiddausi Mama ta isa dakinta ta zube qasa tana son fasa ihun kuka amma girmanta ya wuce hakan hakama radadi da wutar dake cin zuciyarta ya hanata komai bare iya cewa komai,
AZIZ dinta ne ayau a bangaren masu aiki a cikin dakin Jannah?
AZIZ dinta ne idonsa ya rufe akan mace ya hadata da Zaadens ya zuba a motar karfe?
Idan AZIZ zai mata haka akan wata macen mezai faru idan yaga Fatima?
Menene kuma bazai iyayiba akan fatima?
Wlh tallahi wannan ba AZIZUN ta bane dan har abada AZIZ bazai taba take doka da umarninta ba bare tattarasu a zuba a mota kamar wainda aka kamo gidan gala,
Wlh da sake dan kuwa tana buqtaan tashi da tsayen gaske dan kwato danta daga hannun kowa da kuma hanasa shiga hannun kowa koda zata zama zarrriya ne.
Miqewa tayi daqyar takai kanta bathroom tayo alwalar asubar da basuyiba suka ari hauka suka tada anguwa.
Nicky kuwa tana shiga dakinta wani mahaukacin ihun ta fasa tana fasa kayan dakin da karfi cikin tsananin hauka da wata masifar wuta dake ci a kirjinta tana tafarfasa jininta.
Hannuwanta da wasu sassan jikinta jini sukeyi sbd yanda take fasa komai da hannuwanta ga glasses tana kukan baqin ciki batareda ya damu da jinin ba.
Dayake kowa yasan yanayin nata babu Wanda yayi yunqurin zuwa dakin shiru sukai Banda Falaq datake jin zuciyarta fes batajin sauran baqin ciki ko damuwar komai sbd Jan dinta data samu.
Duk sautin haukarta Bata isa bangarensa dan haka baisan mema Yan gidan suke ciki ba.
Dan kanta ta gama tayi laushi ta zube qasa tana kuka kaman ranta zai fita tanajin babu Wanda takeson rabawa da duniya irin Jannah da duka ahalinta ma.
Fatma da Amina ne sukai aikin abincin gidan wunin ranar sbd Jannah kasa fitowa tayi dakinta hakama madam Sisi da take a tsorace,
Su kuwa masu gidan kowa baqin cikin duniya ya hanasa fitowa cin abinci.
Fiddausi ce kadai ta sauko ta dauki abincinsu takai musu sama sukaci itada falaq hankali kwance.
Sayd ma ya fito dining yaci ya koshi ya koma dakinsa Yana ayyukansa.
Me gidan babu Wanda ya gansa har washe gari tukuna kowa ya samu danne abinda yake ransa suka hadu gabaki dayansu a dining hadda shi daya sauko a kame kyakkyawar fuskansa ba sakewa cikinta ko kadan.
Gaida Mama yayi a taqaice yana zaunawa,
Gaidasa kowa yyai ya amsa a taqaice daga Nan babu Wanda ya sake magana har aka gama ya miqe daga dining din ya fice Sayd na miqewa yabi bayansa.
Bayansa dukansu sukabi da kallo Banda Falaq data miqe tabi bayansa tana riqe hannunsa tana masa magana.
Mama da dankalin datake ci ya tsaya mata cak a maqoshi ya tokare jin tayi kaman ta Dora hannu akai tayita zunduma ihu tana tsinewa asalin Wanda ya haifo zuriar Zaadens a duniya.
Nicky kuwa jin tayi idan bata cika kudiranta akan Jannah da Ammar ba bazata iya rayuwa a duniya ba hakama idan bata mallaki AZIZ ba tafi son ta bankawa 4&4 wuta kowama ya mutu har ita har AZIZ din shikenan a rufe tarihin kowama ya huta dan haka bawai faduwa a karon farko zai sakata hakura ba idan na farko beyiba na biyu zeyi ta tabbatarda wannan.
Tashi sukai kowa yakoma dakinsa dan kulla sabon shiri.
Wuni guda babu Wanda ya fito hakama gidan tsit har dare,
Washe gari ma haka dan haka Jannah ta fito ta koma bakin aikinta sbd ganin komai ya lafa.
Madam Sisi ma ta fito ta koma bakin aiki sbd jin shiru maigidan yaqi cewa kowa komai.
Kwana biyu kowa ya nutsu babu tashin hankalin komai hakama ita kanta Jannah din kwata kwata bai sake nemanta ba sbd kaman hadda ita a laifin.
Ummah tayi jinyar kwana biyu kafin ta warke ta koma daidai ta dena kwnaa dakinsu Jannah kwata kwata kuma.
Ranar da akai sati da lamarin Nicky ita kadai ta fita batareda Ammar ba tana dawowa Garba ne ya bude mata gate ta shigo tayi parking ta fito motar.
Garba ta kira ya taso ya iso gurinta a natse Yana sake mata barka da dawowa.
Kallansa tayi tareda bude Jakarta ta ciro apple a leda Guda biyu ta miqa masa batareda ta masa kallan arziki ba ta miqa masa tace
"Give it to Ammar kace abokinsa drivern Office Dina yace a basa"
Gyada Kai Garba yayi Yana cewa "ok ma'am"
Juyawa yayi da sauri ya nufi Ammar dake wankin kayan Jannah a baya nufesa.
Da Sauri tabi bayan garban dan ganewa idonta.
Tana isa ta leqa sai kuwa taga Ammar na cin abu a bakinsa kuma a hannun garban ma tana dubawa daya ta Gani a hannun.
Wani irin tsananin sanyi da nutsuwa taji tana samu ta juya tabar gurin tana jin dukkanin ciwon ransu ayau inshallah zai wanke.
Garba juyawa yayi zai tafi Ammar dayake cin carrots kallan garban yayi yace
"Ka dauki dayan ka hada duka banaci daman ummah da zan bawa dayan Amma kuma zan siyo mata da kaina dan ban yadda da Nicky dinnan kwata kwta ba.
Garba bai tsaya musu ba ya dauka dayan ya hada biyu ya wuce yana fasa daya Yana fara ci.
Yana fitowa daga baya Fatma na ganinsa ta karbe dayan tana cewa lallai ya Garba hr apple kakeci da yamman Nan,
Dariya sukai a tare cikeda jin dadin apple din yace
"Ke duniya fa ta samu gwara muji dadi"
Dariya tayi tana wucewa kitchen sauri takeyi itama.
Tana isa aiki ta saka hannu a ciki tana ajiye apple din saita gama ta koma daki.
Jannah dake tattara gurin bata wani San na waye ba ta dauka ta saka a Fridge cikin Sauran apples din tana rufewa.
Har dare suna aiki suna gamawa Fatma ta bude Fridge ta dauki apple dinta daya suka fice bayan sun kashe komai.
Da daddare fiddausi ce ta kawo ruwa da juice a dining a lokacinda zasu abinci tareda fruits hadda su apple ta jere a dining din.
AZIZ da Sayd har lokacin basu dawo ba dan haka daga Nicky se Mama da Falaq da