Showing 15001 words to 18000 words out of 150681 words
schedules din.
Palon gidan suka shigo Wanda yake tsit babu kowa sai wani qamshi me sanyi da nutsuwa ke tashi hakama masu aikin dake aiki suna ganinsa saurin sauke kai sukai cikeda girmamawa suka gaidasa sbd yanada wuya masu aiki su gansa idan ba irin hakan ba daya fita da sassafe ya fito suna aiki.
Kai tsaye hanyar bangggarensa ya nufa Yana kashe wayoyinsa ya haye sama kai tsaye.
Yana isa kai tsaye bedroom dinsa ya wuce yana zare rigar jikinsa da fresh skin dinsa fari tas ya bayyana yana daukan idon wani irin hutu dayake bayyane a koinansa.
Ya sake budewa ya zama wani irin murdadden namiji lafiyaye da geamin ya budesa sosai.
Closet ya nufa ya zare koman jikinsa ya zaro towel a cikin jerin towels din dasuke jere guri daya fiyeda dozen biyu ya daura a kugunsa ya fada toilet ya sakarwa kansa ruwa Yana rufe idanuwansa ahankali.
Yana fitowa shirin kaya marasa nauyi yayi farare tas ya kashe hasken dakin ya kwanta bacci.
Karfe goma da sha daya mutanen gidan suka fara fitowa a natse cikin shiri na kwanciyar hankali dan lokacin ne lokacin breakfast dinsu.
Mama ce tafara fitowa kafin Falaq Wanda take sanye da doguwar riga me qaramin hannu mara nauyi ta kwanta jikinta ba hayaniya idan ka kalli rigar ma zaka dauka ta shan iska ne kawai sedai tsadar rigar kadai idan kaji kudinta zakai mamakin ace da hankalin mutum a jikinsa ya siyeta hakan.
Qamshi me sanyi da dadi take fitarwa na tsadaddiyar turaren original Fendi.
Fuskanta da skin dinta fresh na asalin Yar hutu da aka haifeta ta taso a cikinsa.
Fiddausi ce ta fito daga kitchen dauke da fresh fruits data hado tareda madara da zuma ta ajiye a dining tana kallan Mama tace
"Mama ina kwana narka da fitowa"
Amsawa mama tayi tana zama kan dining din,
Falaq ma gaida maman tayi a natse ba hayaniya sbd a yanzu falaq din ta banbanta data baya.
Zaunawan Falaq yayi daidai da fitowan AYSHA NICKI daga bedroom dinta sanye da maroon doguwar riga da itama take lafe a jikinta da dogon hannu me kyau fuskanta a fresh itama kyanta a bayyane.
Mama na ganinta ta sake fuskanta sosai cikeda wata irin kauna da kulawa
Itama AyshaNicki din da farin ciki da kaunar maman ta qaraso ta dan rungumeta ta baya tana cewa
"Good morning my mum"
Ajiyan zuciya Falaq Aziz ta sauke tana dauke idanuwanta daga kansu daidai qamshinsa daya doso gurin cikin sanyi yana ratsa hancinsu alamar Yana gap da shigowa gurin cin abincin.
#MAMUH
#AY LIMBA
#ZAADENS
#JANNAH ZAD
#AMMAR ZAD
#AYSHNICKI
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
Mamuhgee
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo
ADUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee
Book 2
Chapter 9
Nicky dince tafara juyawa ahankali ta zubawa inda zai fito idanuwanta da babu komai a cikinsu sai asalin tsananin azababben mahaukacin son datake masa Wanda ya gama rabata da duk wani tinanin komai na duniya da rayuwarta sbd akan son datake masa zata iya komai ba abinda ya dameta indai zata samesa a rayuwarta ta yadda ta rabu da komai da kowa.
Qamshinsa ne ya tsananta Yana sake gauraye sanyin gurin wanda ya tabbatarda ya iso,
Falaq ce ta dago ahankali itama ta zubawa inda zai fito din idanuwanta dake kama sak da nasa tanajin kaman ta miqe ta hanasa karasowa inda idanuwan Nicky zasu sauka akansa kada ta cinye mata shi.
Sako kai yayi a cikin wata irin nutsuwa da kamewa tareda wani irin annurin kwarjininsa fuskansa na sake bayyanarda wani irin sirrin kyau da Kamala kamar ko yaushe,
Milk Brioni's ne a jikinsa sosai agogon Cartier dake bayyanarda ba qananun kudine ke siyansaba.
Idanuwansa masu kashe Nicky ya dago ya kalli Mama Yana zama a natse ya bude baki yace
"Good morning Mama,
Mun tashi Lfy?
Kallansa Mama tayi dakyau tana sake jin wani irin ciwo a ranta ta yanda 'danta ya sauya batareda shi Kansa ya San da hakan ba Amma akwai wani irin sauyi tareda shi wanda ita kanta a tsawon lokacin nan ta kasa tantancewa.
Cikeda kulawa da sakewa ta amsa tana cewa
"Barka da fitowa"
Gyada kai yayi Yana maida idanuwansa cikeda kauna me tsananin karfin da har koyaushe take qaruwa ya kalli Falaq wadda itama shi din take kalla tana narke fuska.
Hannunsa ya miqa mata a natse Yana cewa
"Hey my baby"
Kama hannunsa tayi tana qanqamewa cikin nata ta bude baki tace
"Good morning DADDY"
A yanzu duniyarsa gabaki daya itace ke ganin murmushinsa kai tsaye sai abokan aikinsa musu mahimmaci sai kuma fira idan anayi dashi a gidajen tv wanda ba asalin murmushin daya fito daga zuciyarsa ne suke gani ba,
Ita kadai ce take samun murmushinsa dayake fitowa daga qasan zuciyarsa sai kuma personal person nasa dan Amanarsa Sayd Limba.
Sakar mata wani lafiyayyan murmushi me nutsuwa yayi Yana kissing hannunta a natse yace
"Yau zaki samu enough time da Bestynki i promise you that my lady"
Murmushin farin ciki ke son fito mata amma tana kokarin dannewa sbd Wainda ke gurin.
Sayd ne daya iso ya saka hannu akan fuskanta yaja gefen kumatunta Yana cewa
"Yi murnanki anan waye zaki jawa aji tinda munsan lokacinda yarinya take kuka tana bin Daddynta da takarmi daya a hannu akan zata bisa duk inda zasu so just chill Ms Aziz"
Saurin kallan Daddynta tayi tana toshe bakinta batason dariya tace
"Did you hear that Daddy?"
Murmushi ya sake yi yana cewa
"Kyalesa yanason ya taba Miki steeze ne kawai"
Dariya Sayd yayi ganin tana kallansa tana juya masa ido alamar yayi trying next time yanzu baiyi nasara ba tana masa dariyar dayake jinta har cikin ransa sbd kwata kwata yanzu bata cika dariya ko dogon farin ciki ba kamar baya ba dan haka koyaushe yake kokarin tsokanarta sbd tayi dariya da farin ciki.
Nicky da tinda AZIZ LIMBA ya zauna a dining din bata sake motsin komaiba kallansa takeyi zuciyarta na wata irin narkewa,
Murmushin daya kewa Falaq ne yake sukar zuciyarta tana jin radadinsa har cikin kowane digon jinin dayake yawo a jikinta sbd irin son datake masa har yarsa Falaq jin takeyi tana tsananin kishin irin so da kaunar dayake mata har cikin ranta,
Sonsa takeyi kuma ita kadai WA kanta,
Ita kadai takeson yaso a rayuwarsa
Koda bazai sota ba ya bari to ita kadai taso sa,
Yanda take jin kishin Falaq badan 'yarsa ce ba jininsa da tini ta cireta a rayuwarsa kwata kwata duk da batasan gaba ko xata iya jure ganin irin wannan son dayakewa Falaq din ba,
Duk ranar da AZIZ LIMBA yaso wata macen irin yanda yake kaunar Falaq batasan iya mutanen da zata iya rabawa da duniya ba sbd kaf danginsu zata karar ko sunyi yawan me..
Sayd ne ya gaida Mama Yana zaunawa kafin ya dan kalli Nicky din yace
"Good morning Aysh"
Tana dan dauke idanuwanta daga kan AZIZ Wanda baima kalli inda take ba ta gaida Sayd din itama tana dawo da kallanta kan AZIZ ta bude baki tace
"Good morning Mine"
Saida ya dauki lokaci Batareda ya kalletaba ya amsa a taqaice yana daukan fork ya fara cin Italian breakfast din da fiddausi tagama jerawa a dining.
Shiru gurin yayi kowa na breakfast da masu tinani.
Bai iya gama cin abincin ba yaji ya ishesa ya rasa appetite dinsa gaba daya dan haka ya dauki tissue ya goge bakinsa ya miqe batareda ya kalli kowaba sai Falaq daya ranqwafo yayi pecking goshinta yana cewa mama
"Mu wuni lafiya" ya fice Sayd ma miqewa yayi ya bar gurin Yana manta files dinsa dayazo dining din dasu.
Mama ce ta zubawa files din idanuwanta ta tsayar da idanuwanta akan sunan sabon kamfanin 4&4 din uLIMBAS zuciyarta na tafaso mata wani irin nauyi da damuwa tareda rashin nutsuwa da sukuni ko kadan sbd komai na rayuwar AZIZ LIMBA yana tafiya akan maana da tsari dan haka koma tayaya aka bayyanarda wannan kamfanin akwai babban mahimmaci da girman dayake tattare dashi gashi kamar yanda bai taba fadawa duniya maanar uLIMBAS ba sai bayan shekaru da komai ya fito duniya tasan maanarsa Wanda ita datake uwarsa ma bata saniba sai daga baya hakama wannan din haryanxu babu Wanda yasan maanarsa bakuma Wanda zai taba sani ta Sani sai bayan shekaru kila Amma dai koma menene wannan Karan hankalinta kwata kwata bai kwanta ba Musamman da maganar komawansu Nigeria ta bullo gabaki daya zuciyarta qunci da zafi takeyi sbd har abada bata kaunar AZIZ ya sake kusantar inda ma zasu iya samun labari ko ganin Wanda ma yasan ko labarin ZAADENS dan har abada bazata taba barin Jannah dawowa rayuwar AZIZ LIMBA da Falaq ba sbd babu alkhairi a rayuwar Zaadens da duk Wanda zasu ra6a dan haka zata tsaya komai zatayi zataisa dan hana ko tarihin Zaadens dawowa rayuwarsu dan hakanne ma ta tsani komawa kwata kwata Amma Falaq ta tsaya ita kuma Nigeria takeso hakanne ya saka ya yanke komawar,
Wannan dalilin ne ya saka kusanci da karfin kaunar dake tsakanin Mama da Falaq ragewa sbd a rayuwar Falaq babu inda take so take kuma son komawa tayi rayuwa irin Nigeria Wanda ko daddynta ya tambayi dalilin hakan Amma Sam babu dalilin datake basu Nigeria din kawai takeso.
A bangaren Mama itace ta bada umarnin auren AyshNicky ga AZIZ LIMBA Wanda haryanxu bai bata cikakkiyar amsa akan hakan ba duk da bai taba tsallake umarninta ba dan haka ya bar mata komai a hannunta Amma kwata kwata ba maganar auren a kusa sbd rashin bada fuskansa ga Nicky da kuma rashin bada fuskan sake zancen.
Maganar tafiyansu Nigeria ya saka Mama qin yadda da tafiyar kwata kwata sai anyi auren sbd tanason ko zai sauka Nigeria ya sauka da aurensa akansa ta yanda har abada ba gurin shigowan kowace irin mace sbd AZIZ LIMBA mijin mace daya ne babu tsari ko kadan na auren mace biyu a rayuwarsa kuma itama ta yadda da hakan.
Sayd ne ya dawo da sauri ya miqa hannu ya dauki files din ya juya ya sake ficewa Yana daga wayarsa dake ringing.
Mama da Nicky ne suka bi bayansa da kallo sbd idan har AZIZ LIMBA zai iya yiwa kaunar Ummitah kishiya ta hanyar bude sabbin companies da abubuwa da dama da sunan 4&4 to tabbas 4&4 din nata mahimmancin dake gogayya da kauna tareda girman Ummitah a rayuwarsa tinda bai taba bude komai da sunan Falaq ba ko wani abu daya shafetaba to tanason sanin maanar 4&4 komai tsanani sbd itama zuciyarta girgiza takeyi da koma menene bai kwanta mata a zuciya ba.
Falaq ma miqewa tayi daga dining din ta fice tana kwala sunan fiddausi tanason su fita kafin lokacin zuwanta da Daddynta asibiti yayi.
Binta Nicky tayi da idanuwa tanajin inama itace Ummitah ya haifi Falaq data samu dukkanin soyayya da kaunar AZIZ LIMBA yanda bata buqtaan komai a duniya hakan ma ya isheta.
Bayan ficewan Falaq ajiyan zuciya Mama ta sauke tana jin ciwo da radadin yanda kusancin Falaq ya rage daga gareta duk da suna tsananin kaunar juna na zamtowansu kaka da jika.
Daki Falaq ta isa ta dauki wayarta da mini bag ta chanel ta janyo jacket din Dior black ta saka akan kayanta ta fito fiddausi ma a shirye ta fito sanyeda doguwar rigar Egypt ta sanar da Mama.
Cikin kulawa mama tace
"Ki kula da ita sosai kinsan yanayinta kuma ki kula da hanya"
Gyada Kai fiddausi tayi tana cewa
"Inshallah amma dai Mama ya kamata ki shirya fa da mutuniyarki"
"Kyaleta bata ji ne haryanxu ta kasa sanin ta girma koyaushe shirme ne a tinaninta Wanda nasan inda aka samu matsalar lalacewan tarbiyanta dan haka kuje kawai"
Fiddausi tasan inda maganar Maman ta dosa da abinda take nufi dan haka bata sake cewa komaiba ta juya tabi bayan Falaq wadda maganar Maman ta sosa zuciyarta sbd Jannah da aka kira da wadda ta lalata tarbiyanta.
Suna ficewa itama Nicky ta zari mota tabar gidan sbd shirye shiryen tafiya datake dan a yanda takeso zata riga su LIMBAs din isa dan ta fara shigarda report dinta na aiki da zata fara acan ta gama komai sbd ta shirya bin LIMBA duk duniyar da zashi ko da aurensa akanta ko babu zata bisa har sai lokacin auren yayi.
Karfe 2 na rana motar Ferrari ta shigo LIMBAs din wadda take motar Falaq amma fiddausi ke ja har yanzu bata kai fara ja da kanta ba,
Suna parking motarsa daya fita da ita Porsche cayenne tana shigowa Sayd ke ja Yana gefensa sukai parking,
Atare suka shiga gidan hannunta na riqe dana Sayd tana masa wata gulma Yana murmushi sbd fadanta da Mama kwata kwata ya dena qarewa.
AZIZ kuwa waya yakeyi a natse dan haka kai tsaye wucewa yayi bangarensa Yana cigaba da wayar.
Karfe 4 bayan yayi sallar laasar ya fito a natse cikin black highneck Bally wears da fcap din Calvin Klein komai nasa clean a natse Yana fidda qamshinsa me sanyi da bayyanarda luxury life kawai.
Yayi lunch already dan haka Yana fitowa Falaq ma ta fito cikin black Louis Vuitton dinta masu kyau daidai jikinta suka fice tana gefensa.
Daga shi sai itane suka fita dan haka shine da kansa yake jan motar a natse Yana jin idanuwanta akansa dan haka ya juyo a natse ya kalleta kafin ya bude baki yayi magana ta rigasa da cewa
"Daddy kamun alkawarin idan na cire damuwan komai a raina na samu cikakkiyar lafiyata zaka barni na koma Nigeria dan Allah Daddy pls inason komawa"
Shiru yayi batareda ya juyo ya kalletaba yaci gaba da driving a natse.
Idanuwa ta zuba Masa tana jiran amsarsa sbd baa taba iya gane yanayin Daddyn nata dan haka batasan a wane yanayin ya sake karban zancen nata ba sbd wannan shine Karo na uku tana masa maganar komawansu Nigeria.
"Yaushe kikeson ayi tafiyan?" Shine abinda taji a bazata dan haka cikin rudewa a farin ciki tace
"Ko next week Daddy"
Juyowa yayi ahankali ya kalleta da fararen idanuwansa yayi shiru tsawon seconds kafin ya bude baki yace
"Next week familyn LIMBA zasu koma Nigeria Falaq Aziz nayi Miki wannan alkawarin inshallah"
#MAMUH
#BEST LOVE
#BEST ROMANCE
#JANNAH ZAD
#AZIZ LIMBA
#FALAQ AZIZ
#AYSH NICKY
#AMMAR ZAD
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
Mamuhgee
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo
ADUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee
Book 2
Chapter 10
Wasu hawayen samun abinda zuciya ke tsananin so ne suka gangaro mata tana kasa dauke idanuwanta akan Daddyn nata kawai iya bude baki tayi ta furta "thank you Daddy"
Bai juyo ya kalletaba sbd babu wata magana da zasu iya yi akan duk abinda ya shafi Nigeria da Yan cikinta bayan wannan sbd rantsuwa me karfin gaske da alkawarin dayake kansu na Maman akan babu Wanda a ahalinta zai taba sake maganar zamansu a Nigeria baya bare abinda ya faru acikinta dan hakan ne kwata kwata a LIMBAs aka shafe wannan tarihin a fili da baki.
Shiru ne kawai ya ratsa motar sbd babu me abin fada kuma har suka isa asibiti.
Dayake likitanta ne kai tsaye Wanda shine da Dr Nico tsaye a komai kanta har aikinta da akai da donor da aka ciro aka saka mata dan haka kai tsaye ciki suka wuce dan daman shi din su yake jira.
Suna shiga cikin girmamawa Yana tsaye yana waya ya kashe yana qarasowa gurin LIMBA din ya miqa masa hannu Yana masa barka da zuwa kafin ya kalli Falaq cikeda kulawa yace
"Hi Ms Falaq Aziz barka da zuwa"
Murmushi tayi tana cewa
"Thank you Doc"
Zama sukai Yana Kiran wasu nurses Guda biyu sbd Dr Nico baya nan.
Abubuwan daya kamata ayi mata na duba cikakkiyar lafiyan zuciyar dake kirjinta da bugawanta da duk sauran abubuwa kuma komai ya fito lafiya kalau babu komai a ayanzu shikenan bata buqatan sake zuwa sai taji wasu complications din.
Ajiyan zuciya cikin samun nutsuwa AZIZ ya kalli Dr Sam din yayi masa godia yana miqa masa hannu kafin suka miqe
Itama Falaq din godia Tai masa kafin suka fito ya rakosu har mota yana sake yiwa AZIZ bayanin komai akan masu ciwon.
Mota suka shiga suka bar asibitin Yana shiga tinanin ciwon da yanda yake a yanxu a zuciyarda ta shiga qunci da damuwa.
Numfashi ya sauke a boye Yana dan juyowa ya kalli Falaq dake cikin yanayi na samun nutsuwa kafin ya dauke kansa yanaci gaba da driving kirjinsa na nauyinda Yana buqtaan nasa maganin dayake kai tsawon shekara kusan biyu a yanzu.
Suna isa gida kai tsaye wucewa yayi bangarensa Yana buqtaan kebewa kawai.
Falaq tasan hakan sbd babu ranar da zasu asibiti bai shiga irin wannan halin na baya buqtaan kowa ba sbd ciwon da ake sake maimaita illolinsa ko bayan transplant indai ka shiga kunci me girma ko tashin hankali kan tashin hankali.
Ajiyan zuciya Falaq ta sauke tana bin hanyar palonsa da kallo idanuwanta na cikowa da hawaye sbd zuwa yanzu tasan Daddynta nada matsanancin ciwon depression daya kusan taba kwakwalwansa shima sedai batada yanda zata iya masa sbd a lokuta tashin ciwonsa ba hurumin shigarta bane tin ranar data ga halinda yake shiga idan ciwon ya tashi,ta shiga mafi girman shock da tashin hankali da qunci a rayuwarta sbd a iya shekaru bata taba sanin Daddynta na cikin wannan masifar ba da batada kyan gani,
Tayi kuka,tayi kuka ta kusa zarewa akan hakan har saida Papanta Sayd ya samu ya kwantar mata hankali daqyar ya kuma sanar mata komai akan shekarun rashin Ummitah a rayuwarsa da haihuwarta sune tsawon shekarun dayake cikin wannan mummunan halin batareda kowa ya Sani ba a duniya bayan shi da likitansa sai kuma JANNAH ZAD.
dago jajayen idanuwanta tayi ta kalli papan a lokacin sbd jin sunan Jannah dinta a Karo na farko a bakin wani tin bayan tsawon lokaci kuma Jannah ta San ciwon Daddynta ta zauna dashi ahakan ta tayasu rufewa batareda ko familynta ta fadawaba su da suke neman abinda zasu bata sunansa alokacin koman kankantarsa.
Kusan depression din itama ta kusa shiga sbd damuwa da baqin cikin halinda Daddynta yake rayuwa koyaushe kamar me ciwon hauka Amma ya boye musu sbd kada su shiga damuwa Amma shine Mama zata sakasa a rantsuwa da alkawarin daya qarasa lalata lafiyarsa da Sayd yayi shekaru Yana nema sbd a yanzu ciwonsa yafi baya tsananta a yanda papan ya fada shiyasa tayi alkawarin nemawa mahaifinta lafiya kota halin yaya.
Numfashi ta sauke me tsananin zafi da ciwo a alokacinda take tsaye har lokacin tana kallan kofar palonsa tana gurin tsaye P dinta yazo ya wuce ciki kai tsaye da sauri yana rufe kofar daga ciki
Wasu hawaye masu tsananin zafi suka gangaro mata ta kasa wucewa ta nufi kujeran dake saiti da kofar palonsa ta zauna ahankali tana share hawayenta ahankali ta zubawa kofan ido dukkanin jikinta na sanyi.
Tsawon lokaci me tsayin gaske kafin Sayd ya fito yabar palon batareda ya iya kallan Falaq dinba.
Ajiyan zuciya