Showing 21001 words to 24000 words out of 150681 words
din suka nufo motar ganin Jannah itama sai alokacin take isowa sbd tsayawa yiwa Ummah addua datai sbd haka kawai taketa hawaye ba kakkautawa.
Uban akwatina ne nasu masu shegiyar tsada designers na LV dasu Versace dasu Fendi set set,
Jan kayan suka fara Jannah da Fatma da Amina suna kaiwa cikin gida a first sitting room da babu kowa sai madam Sisi datake kokarin fara hada dining kafin su sugama shigowa da kayan sbd masu gidan sun riga sunyi ciki.
Sun dade suna shigowa da kayan kafin suka gama shigowa dasu tas
Kafin daga palo suka sake daukansu daya bayan daya suna kaiwa bedrooms nasu Wanda kowannensu Yana toilet babu wanda suka tarar a daki,
Suna gama kaiwa suka sauko suna barin palon zuwa kitchen dake palon suka cigaba da hada dining da warming wasu abubuwan da duk aka dafa musu.
Suna gama shirya dining din suka wuce sbd madam Sisi ce keda hurumin serving nasu.
Dakunansu suka koma sukai abinda zasuyi suka kwanta.
Washe gari tinda safe suka tashi tinda yanzu masu gidan sun dawo aikin daban yake dana baya dan haka kai tsaye wanke Jannah tafara yi ta kafin Fatma suka shirya tsaf a natse suka nufi cikin gida.
Jannah ce me aikin sitting rooms dan haka ta fara wucewa sama tafara aikinta a natse.
Fes ta gyare koina ta kunna AC da qamshi ta sauko tafara na palon kasa shima ba jimawa ta gama koina ya sake daukan kyau da qamshi me nutsuwa da dadi tareda tsit sbd babu wanda ya tashi bacci.
Kitchen ta nufa Wanda Fatma da Amina sunyi nisa a aiki dan haka ta saka hannu suna dan fira sama sama Banda ita bata wani cika saka baki ba hakama firar bame hayaniya ba sbd kada a tada masu gidan.
Sbd abincin kusan kowa da Wanda yakeci a menu da aka basu dan haka basu gama aikinba sai kusan 10 dan haka suka jere dining tsaf ita kuma ta fara gyara kitchen din da wanke kayan da akai amfani dashi.
10:30 masu gidan suka fara fitowa ciki hadda fiddausi Wanda ta dade da zama limba itama kawai dai sbd sabo ne wani abin idan ba ita tayiba sai su Falaq din basa jin dadinsa.
Zaunawa sukai dukkaninsu a dining suka fara cin abinci madam Sisi da Fatma ne sukai serving nasu Jannah da Amina na kitchen na fama da sauran aikin.
Sosai suka samu nutsuwa da komai na breakfast din dan haka duk complain din Mama da Falaq basu ce komaiba har aka gama saima Nicky dake kokarin nunawa Mama maids din gidan ba laifi.
Suna gamawa suka bar dining din suka haye sama dukkaninsu babu Wanda ya sake jins dan haka masu aiki suka hau aikinsu a natse.
Jannah ce ta gyare dining din ta sake gyare koina,
Fatma kuma sai lokacin taje sama ta gyaro bedrooms dinsu duka ta sauko.
Lokacin sallah nayi sukaje sukayo sallah bangarensu suka taho suka Dora abincin rana Wanda shima bame hayaniya sukeso ba dan haka Jannah ce yawanci datasan kan abincin mutan turai suke barwa gurkin suna ji da sauran ayyukan walahar.
Hidima suka wuni sunayi sai magrib suka baro bangaren,
Jannah ce ma tafara wucewa tana gama girkin ta zuba a warmers da sauran abubuwan
Su kuwa sai bayan sun gama shirya dining tsaf da tsaftace kitchen din kamar baayi aiki a cikinsa ba suna kokarin ficewa fiddausi ta shigo tana sakewa dasu harda Jan su dan surutu ta dafawa Mama Arabian shayi ta kai dining suka sake gyare gurin suka fice zuwa bangarensu sbd fiddausi ce zatai serving nasu tace.
Jannah na isa dakinsu wanka tayi Tai sallah ta nufi gurin shan iskansu itada familynta ko data isa suna kan qatuwar dadduma Ammar na sallah da bai samu a jam'i ba sbd shegen yawon da Nicky ta fita dashi wai siyan facesheet dinta daya qare.
Maheer da Dad na zaune suna magana Ummah na gefen Dad din Yana bare mata lemun bawo da qaramar wuqa Garba kuwa ruwa ne yaje kitchen din girkin masu aiki ya dauko musu.
Tana isowa zaunawa tayi gefen Maheer tana miqa masa hannu a gajiye tace
"Nima zansha oranges din,am just so tired"
Kallanta Sukai dukkaninsu suna ce mata sannu.
Miqawa Ummah nata Dad yayi cikin kulawa Yana cewa
"Gashi kisha Amma karki sha da 'yayan ki zubar shima idan yayi Miki tsami karki sha a yanka Miki wani kinji"
Gyara masa kai tayi tana rabawa biyu ta basa tace
"Kasha kaima"
Karba yayi yakai bakinsa yasha Yana jin baida tsami yace
"To nasha Kisha kema zan yanda Miki wani"
Fara Sha tayi shikuma ya fara yankawa Jannah Maheer kuwa kafafunta data miqe yafara dan Danna mata sbd jikinta ya rage gajiya yanajin kaman ya cire gajiyar da duk takeji ya dawo da ita jikinsa.
Ammar na gama sallah juyowa yayi yana yanka mata lemun harda cire mata yayan yana bata Yana basu labarin tsinannan yawon da matar gidan ta jasa shikuma Dad yaci gaba da yankawa Ummah suna firarsu hankali kwance.
Fatma na isowa bayan taje itama tayi wanka da sallah suka fara cin abinci duk da baa kwano daya bane sun saba tare suke ci suna firarsu wadda take cikeda kulawan da sukewa juna da yanda suke tsananin kaunar juna.
Ummah da Dad a plate daya sukeci Wanda duk rabi ita yake bawa saita koshi kafin yaci,
Maheer da Jannah da Ammar kuwa suma a plate daya suke ci wata ran kuma Ammar da Jannah din zasu tare Maheer yaci shi kadai.
Fatma da Garba da suke uwa daya uba daya kwata kwata babu sabo ko shakuwa ko tsananin kaunar juna a tsakaninsu a baya Amma zama cikinsu Zaadens din a yanzu kauna da shakuwa ce me girma a tsakaninsu sbd suma a ko yaushe yanzu tare suke ci dan haka suke samun nutsuwa da kwanciyar hankali sbd duk wunin da kowa zaiyi Yana aiki da anyi magrib suna tare har dare sosai sungama shan iska da fira kafin kowa ya shige.
Gari na sake wayewa hkaa kowa ya sake kama aikinsa kamar koyaushe Jannah na gamo gyran sama tana kitchen tana aikinta Wanda tana gamawa zata koma bangarensu kawai dai abu dayane take fuskanta yanda Nicky haryanxu bata son aikin kowa sai nata din Wanda zatai so goma tace bai mata ba ahaka zatai rabin wuni tana wahala a dakin Nicky din.
Tana gano quntata mata da cin zarafinta Nicky din takeson yi sai bata taba nuna damuwa ko gazawa ba akan duka wahalar datake bata ba sbd kada ta nuna gazawa familynta tsaf zasu aje aikin sbd ita su tafiyarsu su hakura da duk abinda zasu samu ita kuma tinda basuda wani xabi gashi ko gurin zama basu dashi batason ta zamo sanadiyar sake jefasu wani hali sai kawai tana shanye duk wata quntatawa da wahalar datake fuskanta.
Tinda masu gidan suka dawo koyaushe suna sama basa saukowa idan ba abinci zasu ci ba dan haka kaf masu aikin gidan bayan Madam Sisi da Fatma data taba ganinsu kokuma ace datake ganinsu sbd lokacin datake zuwa gyaran dakunansu sun tashi suna gurin cin abinci ztaje ta gyaro ta sauko.
Babu wani me aiki dayake da ikon ganinsu sai da babban dalilin dan hakanne ma da sun gama ayyukansu suke ficewa zuwa bangarensu fiddausi ce me aikin serving nasu da sauran ayyukansu dan haka basu damu da masu aiki ba kaman yanda masu aiki basu taba samun dama ko hurumin tinanin ganinsu ba.
Basa yawo koina sai Nicky datake yawon fita aiki da kuma yawonta na banza koyaushe a cikin kashe kudi a banza a wofi take dan haka ne ma koyaushe tana gurin yawo tana dawowa zataita saka aikin rashin dalili sbd Mama ta tsaya mata kaf masu aikin gidan babu Wanda yasan cewa bawai asalin matar me gidan bace da babu aure a tsakaninsu shiyasa ake tsakanin girmamata da bin dukkanin umarninta.
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
Mamuhgee
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo
ADUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee
Book 2
Chapter 13
Kusan watansu fiyeda daya da dawowa babu Wanda ta taba fita a tsakanin Mama ko su Falaq koyaushe suna sama hutu da rayuwar hutu kawai.
Suna cika wata biyu da dawowa Mama ta shirya tayi tafiya zuwa kauye dan haka aiki ya dan rage musu sbd an rage yawa sbd tareda fiddausi ta tafi daga Falaq sai Nicky ne.
Ahankali ahankali kawai Nicky taji batama kaunar Jannah kawai sbd har yau ta kasa ganin gazawarta hakama a yanda tai mata tambayoyi taji makarantikan da qasashen datai yawo take taji ta qyamaceta sbd har abada batason Wanda ya fita sbd idan aka fita jin takeyi zata iya hallaka ka ko illataka sbd ka koma nakasu akanta,
Akan marks na school tasha tura yara da yawa a staircase na school tin tana yarinya har zuwa gama karantunta Tasha taka mutane da mota ta ayi case din a gama sbd bata yadda da zuwa bayan wani ba a komai na rayuwarta dan hakanne ma takejin batada nutsuwa har abada koda ta samu AZIZ LIMBA saita San inda matarsa ta farko take idan tana raye ta kawar da ita daga duniyar gabaki daya hankalinta zai kwanta shiyasa ta dagewa zuwa Nigeria sbd tasan tabbas a Nigeria take Amma babbar matsalar datake tokare da zuciyarta shine kaf familyn har Mama babu Wanda ya taba fada mata komai na rayuwarsu na baya bata Sani ba waye matar?
meya rabasa da ita?
Tana raye ko mace?
Rabuwa sukai ko rasuwa tai?
Matarsa ce ta haifi Falaq kokuwa Ummitah?
Duka wannan abubuwan babu Wanda ya taba fada mata su ta kuma rasa tayaya zata Sani sbd AZIZ LIMBA sai Abinda yaso a Sani akansa ko familynsa ake Sani dan rayuwarsa a tsari da wani irin tsaro da privacy yake yinta.
Yayanta Dr Nico har haukarta tashi tayi akan ya fada mata Amma yaqi fada sbd sirrin dake tsakaninsa da LIMBA da yawa sedai idan sun mutu Amma akwai Amana me karfin gaske a tsakaninsu dan haka bangarenta daban bangaren LIMBA daban a rayuwarsa.
Wannan dalilin ne ya saka batada cikakken bayani komai akan tsohuwar matar LIMBA Amma tayi alkawarin bazata taba samun nutsuwa da kwanciyar hankali ba idan bata nemo ta ba.
Sosai taji ta tsani Jannah a gidan dan haka kai tsaye tace a nemo replacement dinta batasonta a mansion din kwata kwata.
Hakan ya saka Madam Sisi ba tareda tinanin komaiba ta dauki tsana itama ta dorawa Jannah din sbd sake samun gindin zama a gurin Nicky wadda manyan kudi ta direwa Madam Sisi tace tanason kota halin yaya ta nemo mata komai gameda matar LIMBA tshohuwa.
Indai ga kudi babu abinda Madam Sisi bazata iya yiwa Nicky ba dan haka itama goal dinta ya zama daya shine koda zata bata saita nemo labarin tsohuwar matarsa duk da tini Mama ta saki kudi masu yawan gaske aka goge labarai da komai daya shafi auren AZIZ LIMBA da JANNAH ZAD.
***Satin Mama biyu ta dawo d yamma motarsu ta shigo harabar gidan wanda Maheer dake gefe taya Ammar goge mota jin horn da sauri ya nufi gate din
Dad ma dayake baya da sauri ya fito jin horn ya nufo gate din shikuwa Ammar juyowa yayi Yana kallan motar dake shigowan su Dad da Maheer suka bude gate din a tare suna fitowa a tare daga bayan gate din wanda yayi daidai da dagowan Mama dake waya da AZIZ LIMBA ta kalli gabanta bakinta na rawa ahankali cikin wani irin sauti bugawan zuciya na shirin kamata tace "ZAADENS"
Shiru AZIZ yayi sbd yanda sunan ya sauka cikin kunnuwansa ahankali ya isa kirjinsa Yana yanka wani budadden ciwon dake dabaibaiye da kowane irin lungu na zuciyarsa,
Ahankali ya kashe wayarsa batareda ya iya furta kowace kalma ba sbd sanin koma menene Maman bata hayyacinta tinda bakinta ya furta kalman da itace tace bata yafe kowa a ahalinta ya fada ba.
Ajiye wayarsa yayi gefensa Yana dago idanuwansa da suka sauya take ya kalli baqin da Sayd ya shigo dasu Yana miqewa dan basu hannu su gaisa a natse cikin steeze dinsa dayake boye kowane irin yanayinsa.
Kallo daya Sayd yayiwa idanuwansa ya sauke kai Yana juyawa ya fice dan dauko takardun daya baro office dinsa Wainda dasu zasu zaman da baqin.
***Mama da bugun zuciyarta ke tsananta numfashinta na neman sarkewa ko tsayawa motar bata gama yi ba ta Dora hannuwanta dake wata irin rawa akan murfin motar zata bude sai kuma ta fasa da sauri ta janye hannunta tana zubawa fuskar Dad idanuwanta dake qanqancewa tsabar shock da masifaffen tashin hankali.
Fiddausi ma dake gaban motar zaune akan fuskar Ammar Zad idanuwanta suka fara sauka take numfashinta ya tsaya cak a rikice ta juyo da sauri ta kalli Mama dake baya taga numfashinta na neman daukewa idanuwanta kafe akan fuskar Dad.
Da sauri fiddausi ta juya inda Maman ke kalla itama nata idanuwan suka sauka fes akan fuskar Dzad kafin ta riqe numfashinta dake futa da karfin gaske Maheer ma ya bayyana a bayan Dzad din dukkaninsu sanye da shirts masu dauke da sunan 4&4 mansion Wanda babu tantama hakan na nuni da a cikin maaikatan gidan suke,
Shin sun San a inda suke kuma suka zauna suna aiki kokuwa basu Sani ba??
Shin wace sabuwar masifar ce zata afko ayanzu da katsam Allah ya bayyanardasu a cikin gidan bayan rantsuwa da alkawarin da duka ahalin gidan suke daure a cikinsa na Mama.
Kokarin dawo da kanta daidai Mama tayi cikin karfin hali da hadiye duk wata tafasan zuciya da baqin cikin daya taso tayi ta sauke ajiyan zuciya kafin ta dawo da idanuwanta ahankali akan fiddausi da har jikinta rawa yake dan yi.
Numfashi me zafi Maman ta sake sakewa kafin ta iya bude bakinta tana kame fuskanta sosai ba sakewa ko kadan tace
"Ko a cikin mayen hauka karki yadda ki fadi abinda kika gani,
Baki ga kowa ba,
Bakima San kowa ba idan wannan maganar ta shiga kunnen Falaq ko Sayd da zai iya kai zancen kunnen 'dana ki Sani zamanki da Falaq a limbas ba ma ya qare kwata kwata har abada,
Ina fatan kin fahimta kin kuma San abinda kikeyi?
Jajir idanuwan fiddausi sukai take sbd girman magana da abinda Maman take shirin aikatawa na hana kowa sanin Zaadens na mansion din duk da tasan zaiyi wuya gobe a wayi gari dasu a mansion din batareda ta tabbatarda sun bata ba.
Tayaya zata boyewa Falaq Zaadens na tareda su a mansion daya Wanda ta tabbatarda Jannah bata nesa tana kusa idanma bata cikin mansion din sbd zaiyi wuya Zaadens su iya tafiya koina batareda jannarsu ba?
Tayaya tana kallo Falaq na kuncin rashin Jannah suna guri daya Amma ta kasa gaya mata har sai Mama ta korasu inda bazata taba samunsu a kusa ba kila?
Amma kuma hukuncin Mama yayi mata tsaurin da batada xabi saina binsa dan haka ta sauke idanuwanta ahankali jikinta a tsananin mace tace
"Inshallah Mama"
Ajiyan zuciya Maman ta sauke kafin ta dauke kai daga kallan fiddausin ta cewa driver yakaisu ta gurin hanyar shigar Mai gidan idan yana gari.
Daman bai kashe motan ba ya jata zuwa gaba sosai har bakin inda motan me gidan take ta kofa ta Musamman yayi parking.
Su Dad bayan motar suka bi da kallo da mamakin kodai Mai gidan ne a ciki y dawo tinda akai can ciki sosai da ita.
Basu wani damu ba suka koma bakin aikinsu a natse hankali kwance.
Ita kuwa mama bude mata motar driver yayi ta fito ta shige ciki har lokacin zafin zuciyarta bai sauka ba.
Fiddausi jiki a sanyaye ta fito ta shige ciki da kayansu itama zuciyarta gabaki daya a sanyaye da kuma fargaba.
Suna shiga suka haye sama fiddausi takai kayan Mama har bedroom dinta tukuna ta fito ta nufi nata dakin tkaia kayanta ta kasa fitowa taje dakin Falaq sbd yanda takejin kaman bazata iya fuskantarta ba.
Da daddare a waya Mama ta kira Madam Sisi har bedroom dinta abinda bai taba faruwa ba.
Zaune Maman take kan sofa bayan gama sallar ishai dinta sanye da damuwar riga me laushi da qaton mayafi a jikinta ta fito dattijuwan datake cikin hutu da daula.
A natse Maman ta kalli Madam Sisi ta bude baki batareda ta amsa gaisuwanta ba ta jefa mata tambayar data sakata mamaki kai tsaye
"Su waye securities na second gate Dana gani?
Meye sunayensu?
Tsawon yaushe suke aiki a mansion din nan?
Su kadai ne ko akwai budurwa a tareda su???
Shiru Madam Sisi tayi kafin ta dago ta bude baki ta fara da amsa tambaya ta karshe da cewa
"Mata biyu ne a tareda su da budurwa da kuma mahaifiyarta me tabin hankali"
#MAMUH
#ZAADENS
#LIMBAS
#HOT LOVE
#HOT ROMANCE
#TWIST
ZAFAFA BIYAR
KALBIM 500
Mamuhgee
KIRJIN ME HANKALI 500
Miss Xoxo
ADUNIYATA 500
Huguma
AJIYA A DUHU 500
Billyn Abdul
09033181070
09032345899*_KALBIM_*
Mamuhgee
Book 2
Chapter 14
*_ZUZEAM VENTURES_*
08144015291
Best Aphrodisiac/kayan mata
ASLM barkanmu da wannan lokaci
Ina Mai farin cikin sanar daku cewa Zuzeam ventures takawo maku ingantattun magunguna masu inganci cikin Aminci Muna da kaya kamar haka
Mallaka Maganin sanyi
Maganin cire tumbiMaganin farin jini
Maganin matsiMaganin mata
Maganin sa ni’ima da dandano
Dulka Amare Set na gyran jiki
Set na amarya
Tabaje tsumin Gomba
Xuma kiba ta hips and Brest
Magungunan gyran Brest
Magungunan Karin hips
Maganin sliming
Turaruka kala kala Na jiki da kaya da daki turarukan amare
Turaren kabbasa
Muna da kaya masu inganci cikin sauki da rahusa
Ina wadda keneman mallaka sahihiya quaranty wlh hajiya kixo ga zuzeam ventures xakiji ddin mallaka duk fadin ran ogah duk fadansa wlh sai yyi sanyi 08144015291
Idan maganin mata kikeso akwai
Idan gyran jiki kikeso gyran fata gyran Brest magungunan sa kiba da hips
DOMIN samunta Kai tsaye kira wannan no 08144015291 DOMIN mgn da ita whatapp 08144015291muna tura kayanmu ko ina cikin iKon allah 🥰👌🏻
Bononza Bononza Tsimin mallaka 2k Tsimin dabino 1k Gumba madara 1500 Gumba aya da nonon rakumi 1500 Garin kafi ciccibi 1k
Garin bata gaban kishiya 1k
Matsin mallaka tada zaune tsaye 2500
Turaren mallaka ba aba mai kishiya 2500 Total kayan 13k
Za a bakisu akan 5500
Kuma mutun goman farko nadakyautar Abun 2k
🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️🗣️ ASSALAMU ALAIKUM ALHAMDULILLAH YAN UWA NEW PROMO YA KAMMALA💃🏽💃🏽💃🏽😁😁😁 da 8k dinki ki kwashi kayan 16k hajiyata 💃🏽💃🏽💃🏽😃🙃Kazar gadali ta mallaka sashe 3500 Tsimin gam gam 1500 Ruwan kara zunzurutun dadı😋 1k Garin 7in1 2k Gumba 3 balai 1500 Gumba kwakwa da dabino 1500 Na Infection 1500 Garin zunzurutun dadi 1500Matsin ba a fira d wando 500 Matsin infection mai matse mace gam 500 18k All at 8k koda kudinki saida Rabonki.
******************
Dago idanuwa Mama tayi ahankali cikin tsananin mamaki da son sake jin abinda Madam Sisi din ta fada zuciyarta na wani irin zafi da quna me tsanani jin Jannah Zad na cikin mansion din itama,
Jannah Zad na cikin inda LIMBAs suke?
Jannah na guri daya da inda Falaq da