Showing 126001 words to 129000 words out of 150681 words
yasake kashesu shi dai kawu jibo kallan garban kawai yakeyi yakasa dauke idanuwansa akansa yana Jin tsananin dadin 'dansa ne ya koma hakan,take yaji shi birni to tagama yi Masa komai ko ahakan sbd 'dansa ya zama me nasarar datafi ta kowa yaxo birni ya zaman Masa abin alfahari ba kaman sauran da suke lalacewaba idan sunxo su koma su zamarwa mutane abin kunya.
Motar suka shiga take wani sanyi da kamshi ya fara ratsasu suka fara Jin kaman dadi tin anan zai fara kashesu Dan haka suka hau tambayansa Shima yana tambayan mutanen gida da innarsa wadda yake jimawa baiyi waya da itaba sbd yanayin kauyen nasu.
Fira sukeyi sosai suna kokarin tambayansa adadin kudin da Zaadens sukai a yanzu sbd su San abinda zaa basu tin yanzu.
Murmushi kawai yayi yana Dan juyowa ya kllesu yanda suka zuba Masa idanuwa dukkaninsu suna jiran amsarsa yace
"Modibbo babu ta yanda kowa zai San yawa ko adadin arzikin da suke dashi amma dai muna cikin arzikin sosai Kuma ku sani bawai maganar kudin da zaa baku bane ziyara kuka xo Kuma zaku samu lada me yawan datafi abinda kuke tinanin samu Dan haka Dan Allah modibbo kada kuyi maganar a Baku kudi ni kaina zan Baku ko nawa kukeso."
Shiru sukai dukkaninsu suna nazarin zancensa sbd shi kawu jibo a iya ganin da yayiwa garban nasa ma shi ko baa basa komaiba zai koma a Hakan sbd yasan dai 'dansa Shima yayi arzikin kansa.
Suna isa anguwan tin kafin su isa gidan su kawu ke kallan gidajen da suke sakasu rudani da lissafi sbd basu saba zuwa birni kaman modibbo ba dayake yawan zuwa Abuja.
Gate securities suka bude Masa yashigo yayi parking yana fitowa ya bude musu suka fito ya dauko jakar kayansu da tsaraban da sukayo ta kauye yayi ciki dasu suna biye dashi.
Akwai lafiyayyan Palo da Daki ta bayan nasa dakin Dan haka acan ya kaisu sbd bama kowa a gida duka suna asibiti duk da kowa yasan da zuwansu din shiyasa akace shi yaje ya daukosu.
Fatma daman kafin isowansu ta saka me aiki ta sake gyare dakin Dan haka suna shiga Nan ma kamshi da sanyin AC take yafara sanyayasu suka ringa Jin kasala suka zauna yana sake musu sannu da hanya.
Fita yayi masu aiki suka shigo da ruwa da drinks harma da abinci lafiyayyu aka fara jere musu suna gaidasu tareda musu barka da zuwa.
Muhammad dinne ya dawo yakai musu kayansu har bedroom ya Kuma kirasu ya nuna musu yanda zasuyi amfani da komai harma da toilet kafin ya nuna musu gabas ya fice Dan basu daman hutawa suci abinci suyi salloli.
Yana fita toilet suka fara shiga daya bayan daya sukai abubuwan da zasuyi suka zo sukai sallolin dake kansu suna gamawa suka fara bude abincin suna ganin yanda aka salwantar da rayukan kaji masu girma da tsoka kaman ba kaji ba take suka fara cin abincin duk da suna ganin plates din da aka kawo na cin abincin sun musu qananu sosai Dan haka kusan so uku uku suna ci kafin suka koshi suka cinye kajin tas suka cinye abincin Shima tas suka Sha ruwan sanyi da lemu masu sanyi take baccin gajiya ya daukesu ba jimawa ga AC dayake sake kashe musu jiki da kasala.
Muhammad asibiti yakoma ya sanar dasu isowan su modibbon suna gida suna hutawa.
Fatma ce ta koma gida sbd su modibbon da Kuma hada abincin da zaa kawo asibitin da Kanta.
Doctors sun samu dakatar da jinin dayakewa Jannah din zuba bayan tasha tsananin azaba tayi laushi sosai daqyar aka samu tsayar mata da babynta Wanda dukkanin zaadens babu Wanda hankalinsa baiyi mummunan tashi ba akan rasa babyn Wanda rashinsa zai tana Jannah hakama suma kasancewan babyn Jannah ne yasa suke tsananin kaunarsa a yanzu bama sa duba waye ubansa su a gani da tinaninsu babyn zaadens ne.
Samun nasarar tsayar da babyn yasaka zuciyoyinsu samun sukuni da nutsuwa suka samu kwanciyan hankali da farin ciki.
Dakin hutawa aka Maida Jannah din can sama wani private daki Wanda dukkaninsu suke zaune a sofas suna sake samun nutsuwa ita Kuma har lokacin bacci takeyi.
Saida aka tabbatarda komai yakoma daidai tukuna Dad da Ammar suka wuce gida Maheer m ya fice zuwa wani gurin aiki Mai mahimmancin da aka riga aka samu delay sbd tashin hankalin Jannah din.
Saleem da ummah aka bari Shima bai jima sosai ba ya tafi gida ya dawo.
Fatma data fara isowa gidan driver me ya kawota Dan haka kai tsaye gurin su modibbo ta nufa tana isa ta buga kofar Shiru Shiru sai tabude Kai tsaye taga bacci sukeyi ta fice tabarsu su huta tukuna sbd sun debo gajiyan gaske ta sani tinda tafiyan Mota ce.
Sama ta nufa dakinta ta fara yin wanka ta cire Dan warin asibitin data debo tai sallan magrib da akai ta sauko sanye da riga da skirt na atampa masu kyau da suka zauna jikin daidai Dan anyi musu dinkuna masu yawa da haryanzu basu ma saka wasu ba,
Kitchen ta nufa ta fara duba abincin da akeyi baa qarasa ba Nan ta saka hannu ta qara da dafa farfesun kifi da potato porridge.
Ganin kowa ya dawo gida sai ta saka aka jera komai a dining bayan tayiwa Ummah nata lafiyayyan basket din sai Kuma nasu modibbo daban da suma a daki zaa kaimusu.
Fitowa kitchen din tayi bayan ta wanke hannuwanta ta gogesu da towel ta nufi sama tayi sallah ta sauko tana nufar gurinsu modibbo.
Da sallama ta shiga sbd Jin magana Ashe basu kadai bane Maheer da Muhammad da Ammar harma da Dad duka suna dakin Dan haka cikin farin cikin ganinsu kyakkyawan fuskanta dauke da murmushi me Kyau ta fara gaidasu tana zaunawa gefen modibbo daya kasa rufe baki yana kallanta.
Kawu isiya Kuwa baisan lokacinda ya fasa kuka ba yana cewa
"Yanzu Fatma Dina ce wannan?
Fatma kece kika zama sarauniyar mata haka?
Fatma anya zan iya bawa shehu aurenki yana can yana jiran dawowanki"
Dariya Ammar yayi Mai qaramin sauti yana cewa
"Kaji Kuma wai wani shehu yake magana yanzu ana Zaune kalau"
Dad ma murmushi yayi yana cewa
"Fatma ai karatun zata fara yanzu kuma ai ba maganar aure tukuna saita gama ko nisa"
Muhammad da zancen ya basa dariya dariyar yakeyi sosai sbd yasan tin dama can Fatman bata son shehu.
Maheer ma maganar Dad ya maimaita da cewa
"Ai gwara ta gama karatun kwata kwata tukuna ma ayi maganar auren dan anayin auren zata iya watsar da karatun bare kuma idan shehun ne ai ba maganar qarasa karatu" ya qarasa zancen yana kallanta ta sake marairaice fuska tana kasa cewa komai sbd tanada Jin nauyi da sosai a gaban manyanta.
Cigaba da santin ganin yayansu kaman turawa su kawu sukai suna yiwa Allah godiya tareda zaadens din da suka riqesu da amanar gaske.
Modibbo ma sake yiwa Dad godiya yayi sosai akan Hakan kafin suka shiga firar duniya inda su Dad is sake tabbatarda maganar Saleem su Jannah da Fatma dai basu tafi kauye ba yawon shakatawa suka tafi da AZIZ LIMBA Wanda ya cucesu wlh da hakan.
Sai guraren 8 da rabi suka fito dukkaninsu Dan sake zuwa asibiti.
Hadda su modibbo aka fito a motar Muhammad ya daukesu da Fatma sbd su sake samun damar sakewa da yayansu.
Dad da Maheer da saleem da Ammar ma mota daya suka shiga zuwa asibitin.
Suna isa Jannah din ta farka amma Bata iya magna da kowa idanuwan nata ne kawai a bude tana binsu da Kallo ta qare musu Kallo tsaf babu Wanda tayi tinanin tana bude Ido tafara cin karo dashi.
Wasu hawaye masu dumi dumi ne suka gangaro mata ta lumshe idanuwanta tana amsa gaisuwa da sannun da kowa ke mata da Kai cikin sanyi.
Har dare sosai suna asibitin Saleem nata Kiran AZIZ baya samu hakama sayd wayansa Bata shiga Dan haka dole haka suka tafi dukda kusan kowa yasan rashin zuwan waye yake sake taba zuciyar Jannah din amma basuda yanda zasuyi sai fatar yazo din da kansa sbd ta Dan sake ta samu lafiyarta.
Fatma aka bari tareda ita suka koma gabaki dayansu harda Ummah wadda tana isa wanka tayi tai Shirin bacci ta kwanta kawai sbd already taci abinci.
******Sai karfe goma Sha biyun dare LIMBAS suka samu nutsuwarsu ta fara dawowa jikinsu sbd koda suka sauka Lagos jikin Nicky ya rikice sosai Wanda ya sakata har wani fixga takeyi take hankalin kowa ya sake tashi Dan haka kai tsaye daga airport ambulance ce ma ta dauketa zuwa asibiti gabaki dayansu can suka fara sauka suka fara addua da fatan samun lafiyanta sbd babu Wanda tausayinta bai gama sanyaya jikinsa ba a familyn.
Anyi nasarar itama tsayar mata da nata babyn daqyar sedai ita sbd wuyan datasha Bata farfado ba har lokacin.
Sai a lokacin duka familyn suka tafi gida,
Suna isa gida kowa wankan gajiya yayi sunyi sallolinsu already Dan haka abincin ma sama sama kowa yaci ya nufi daki ya kwanta sai baccin gajiya.
Wanka yayi ya shirya ya fito cikin brown sweatsets sbd Dan sanyin da akeyi ya fito sai a lokacin jammy ta kawo Masa milk tea me zafi sosai yasha ahankali tareda sponge cake.
Bai nema wayarsa ba bare ya kunna duk da dare yai babu me kira a lokacin amman bayason damuwa ko kadan Dan haka Sayd ne ya kira saleem Wanda ya turo Masa komai na inda taken Dan haka da kansa ya dauki key shi kadai yaja mota ya fice lokacin kowama yafara nisa a baccin gajiya.
Kai tsaye asibitin ya nufa yana isa Kai tsaye dakin datake din ya wuce yana sanye da hular Burberry data rufe har kunnuwansa kaman wani sabon matashin saurayi.
#MAMUH
07019691719*_KALBIM_*
Mamuhgee
Book 2
Chapter 73
Yana isowa dakin a natse ya miqa hannunsa zaiyi knocking kaman Fatma ta san ya iso ta bude dakin a natse sbd Saleem daya Kirata ya sanar da ita AZIZ LIMBA na isowa asibitin kowane lokaci.
Cikeda girmamawa Fatma ta gaidasa tana janyewa daga kofar zuwa gefe.
Amsawa yayi a taqaice yana shigowa qamshinsa me sanyi da ratsa zuciya na gauraye dakin da sanyin AC ya gama cikewa da kame koina.
Ficewa fatma tayi daga dakin tana zaunawa a doguwan kujeran dake kofar dakin tana kalle kalle a wayarta Samsung da aka sauya mata tini.
A natse ya tako ahankali cikin yanayi na samun nutsuwansa daya rasa tsawon lokaci tana dawowa Masa a Sannu tana shigarsa ya zuba mata idanuwansa masu haske yana sauke wata sanyayyan ajiyan xuciya data sauka cikin kunnuwanta
cikin baccinta taji kamshin datake tsananin kewa yana shiga hancinta a natse da sanyi,
Motsawa tayi ahankali batareda ta farka ba amma still shigarta kamshin yakeyi Dan haka ta bude idanuwanta ahankali sanyaye.
Akansa idanuwanta suka sauka yana tsaye akanta ya zubawa cikinta daya fito idanuwansa yana Jin wani irin feelings masu karfi na sake shigarsa akan cikin dayake nasa ne,'dansa ko yarsa ne a ciki da zasu fito duniya suyi bearing sunansa,jininsa gudan tsatsonsa.
Kafesa da idanuwanta da sukai laushi sosai tai suna Dan cikowa da hawayen tsananin kewansa da damuwan halinda ya sakata,
Maido da kallansa kan fuskanta yayi sbd Jin idanuwanta akansa ya Kafeta da nasa idanuwan yana mata kallan tsaf na mintina kafin ya janye idanuwansa yana zaunawa a sofa a hankali cikin nutsuwa ya kalleta yace
"Yaya jikin?
Kasa amsawa tayi sbd babu shauqi ko daya a cikin sautin muryansa Dan haka ta zuba Masa ido hawayenta na gangarowa ahankali.
Sake maimaita tambayarsa yayi cikin nutsuwa wadda ta sakata fasa kuka me sauti tana miqewa zaune ahankali tareda ziro kafafunta kasa zata miqe ya tashi tsaye yana riqeta da sauri idanuwansa da suka fara sauyawa sbd kukanta dayake shigarsa suna sauka akanta yace
"Kinsan me kike yi Kuwa?
Kukan ta sake fasawa tana fadawa jikinsa tareda qanqamesa tana cewa
"Kayi hakuri nidai bazan sake ba Dan Allah ka dena fushin haka wlh bazan iya dauka ba xuciyana ciwo takeyi I can't take it anymore please"
Yanda cikinta ya tokalesa ya sakasa kasa cewa komai sbd a Karan farko yaji tudun babynsa a jikinsa Wanda ya kashe duka jikinsa da zuciyarsa datake tsananin kaunarsu Dan haka Shiru yayi batareda yace komaiba yana Jin dumi da tudun cikinta na shigarsa cikeda wata irin kauna mara sirki.
Sake shigewa jikinsa takeyi tana kuka batareda yace komaiba har sai dayaga kukan yayi yawa zai iya sata ciwon Kai ya daga hannuwansa ahankali yana rungumeta cikin nutsuwa ya bude Baki yana cewa
"Ya isa kafin kukan ya saki wani ciwon"
Kamata yayi suna zaunawa ya zaunar da ita kan kafafunsa yana sake kallan cikinta yana mamakinsa ya dago ya kalleta Kanta a qasa ya zuba mata ido yanajin tausayinta duk da yana fushi da ita babu ranar da tausayinta baya cikesa da damunsa sbd Allah ya sani yana mata wani irin so ne Dan baisan Yaya zaiyi dashi ba Dan Kuwa yayi Masa yawan da shine yake fushin amman shine a cikin azabar sbd quncin dayake cikeda kirjinsa na rashinta da rashin jinta.
Lafewa tayi a jininsa sai a lokacin cikin muryan datake cikeda tsananin kauna da shauqinsu yace
"Yaya jikin naki?
Yaya baby limba?
Ya kikeji yanzu?
Akwai inda kike Jin sauran damuwa ne?
Dagowa tayi ahankali cikin sanyi ta kallesa sai Kuma taji tana Jin haushinsa akan fushin da yai da ita Dan haka ta miqe daga jikinsa ahankali tana komawa bakin gadonta ta zauna tana Dan hade fuskanta cikin Jin bacin Rai da gaske.
Karantar yanayinta yayi ya zuba mata ido take ya saki wani malalacin murmushi yana miqewa ya nufi inda take din cikin nutsuwa sedai ko isa beyiba ta miqe tana barin gurin zata nufi toilet ta shige ya riqota yana rungumeta ta baya yana Dora hannunsa akan cikinta ya shafa ahankali yana sauke ajiyan xuciya me sanyi ya bude Baki yace
"Fushin na menene Kuma? I tot mun gama fushi fushin Nan ko?
Zare hannunsa tayi daga kan cikinta tana kokarin sake tafiyarta ya sake riqota yana cewa
"Ok I'm sorry too"
Jin tayi ranta ya sake baci ta fasa Masa kuka tana cewa ya tafi basa sonsa itada baby limba din Kuma babynta baby Zad ne.
Wata murmushin mamaki ya sake yana cewa
"Meye baby Zad Kuma?
Da sauri ta kallesa tana turesa cikin fushi zatai magana yakai lips dinsa ya bawa nata lips din kiss ahankali me sanyi Wanda ya sakata Bata fuska tana turesa tace
"Banaso ka tafiyanka ma kawai"
Ganin da gaske takeyi sai kawai yafara rarrashinta yana kwantar mata da hankali ta gama kukan da fadar bacin ranta da fushinta ta lafe a jikinsa suka shirya abinsu.
Abincin da akai akai taci taqi ci shine ya Bata da kansa taci sosai Tasha ruwa ya zauna hannunsa na cikin nata sarqe da juna a cikin rifarta yana magana a ita cikin kulawa da sanyi harta fara Jin bacci.
Se datai bacci yabar asibitin ya tafi gida.
Washe gari ko data tashi gabaki daya su Dad sunyi mamakin ganin samun sauyinta sbd ta tashi da karfin jikinta da yar sakewa wadda ta saka farin cikinsu dawowa,
Ammar yana shigowa dakin yasan AZIZ LIMBA ya taho sbd kamshinsa da hancinsa ya shakar Masa Dan haka take ya fahimci dalilin warwarewan Jannah din baice komaiba ya kama kansa sbd ba huruminsa bane.
Suma acan LIMBAS washe garin Nicky ta farfado sedai kwata kwata babu kuzari ko wata lafiya me karfi a tattare da ita Dan haka fiddausi ce me kulawa da ita sosai cikin kulawa da tattali sbd kowa yanzu kokarin gyara kuskuren da sukai na shareta ta zama kamar Bata cikinsu yakeyi.
Batada kuzari ko lafiyan doguwan magana dan haka da ido take bin kowannensu da Kallo tana Jin inama ace tanada familyn da zata samu kulawa sosai a gurinsu irin Hakan da yanzu Bata samu Kanta a wannan rayuwan datake ciki ba.
Ciki dai gashinan ya bayyana a idon kowa ansan da tana dauke dashi amma babu Wanda yace mata komai akansa tukuna.
Tin daga AZIZ har Mama da kowa a familyn kulawa yake nuna mata da kauna batareda fara tinanin maganar cikin ba tukuna,
AZIZ bai fadawa Dr Nico halinda ake cikiba tukuna sbd yanason Nicky din tafara dawowa daidanta tukuna,
Kulawan da suke Bata da janta a jiki ya saka lafiyarta take samuwa sosai Dan daman kadaici da rashin kowa ne yake sake lalata lafiyan tata.
Kullum yana zuwa gurin Jannah asibiti itama yana dubata kowane dare acan yake kaiwa Asuba kafin ya fice batareda ya taba haduwa da kowane zaadens ba Saleem kawai yasan yana zuwan Kuma yana gari da familynsa gabaki daya Shima.
An sallami Jannah Takoma gida Dan haka tinda Takoma Bata sake ganinsa ba hankalinsa ya koma ka matsalar Nicky data warware sosai itama.
Ta bangarensu Mama dasu Fi da falaq yanda suke kulawa da ita da nuna son babyn cikinta ya sakata Jin tafara son cikin nata itama musamman idan yana motsawa Jin takeyi kaunar abinta yana ratsata sbd shine kadai familyn datake dashi idan yazo duniya sai yayanta Wanda ta yanke shawarar rashin komawa rayuwansa sbd ta basa damar zaunawa da macen dayake so ya aura tinda tana komawa zata iya sake zama sanadin rabuwarsa da ita.
Babynta shine ahalin datake dashi na jini Dan haka zata so abinta tinda Allah ya riga y kaddara mata Hakan Kuma ta runguma kaddarar tinda dai ta fahimci kowa daya zubar da tashin hankali ya rungumi zaman lafiya gashinan duka sun samu nutsuwa Dan haka itama sbd bawa babynta rayuwa nutsuwa da kwanciyan hankali ta saki komai akansa ta yadda ta shiryu.
********Kwanansu kusan Biyar basu hadu ba sai yau din da aka sallami Nicky itama ta warware tas ankoma gida da ita Kuma har cikin ransa sai yanzu yakejin yana kulawa da amanar da Dr ya basa sbd gashinan ta sake a cikin mutane tana sauyawa ahankali ahankali tana zama macen daya kamata ta zama Dan haka yanzu zaman Jin inda cikin jikinta ya samu ya rage yayi da ita Wanda ya bari ne yau ta huta daga dawowa asibiti zuwa gobe.
Karfe 8 na dare motarsa ta isa Zads Kai tsaye babu shakkar kowa Kai tsaye securities na ganin Lamborghini dinsa suka San Shine suka taso dukkaninsu suna Masa barka da zuwa tareda bude Masa gate din gabaki daya ya shige yana parking.
Saleem ne da Muhammad da suka dawo gidan daidai lokacin suma suka qaraso gurinsa Muhammad na bude Masa mota ya fito yana gaisawa da saleem kwarjinsa na sake cike idanuwansu sbd wani sirrin Kyau daya qara fuskansa fresh kaman koyaushe hutu ne bayyane tako ina.
Kai tsaye Palon gidan Saleem ya nufa dashi suna shiga Dad dasu Maheer dake zaune Palo da qamshinsa suka