Showing 87001 words to 90000 words out of 149705 words

Chapter 30 - Jalilah Book One Complete Hausa.doc

Ayusher   

28 Oct 2025

641

abin zan miki ba."
Shiru tai ta kwanta, janye rigarta yai yana neman kaita wajen kirjinta, da sauri tasa hannu ta rike sannan ta kalleshi.
Kallanta yai idanunsa na kanta ya sa hannu ya zare mata hannunta, shiru tai tana kallansa.
Sai dayakai rigar saman cikinta sannan ya tattareta a gun.
Hannu ya saka a bayanta yana mata tausa da hannayensa suka biyun.
Idanunta ta rufe gaba daya jikinta yai sanye, Hassan kam tausa yake mata sai dai daurewa kawai yakeyi.
Kallanta yai yace " kinajin sauki? Naga haka suka rubuta haka akeyi."
Ta daga kai idanunta a rufe dan bazata iya kallansa ba.
Hassan ya cigaba da yi mata, tun tanajin abin har bacci yai gaba da ita.
Ganin alamar bacci takeyi yasa ya kalleta, kusa da ita ya matso ya sa hannu akan gefen fuskarta yadan shafa kadan, meyasa kike sani yin abubuwan da ban taba tunani ba?Ganin motsin idanunta sun canza da alama nauyin baccin nata ya fara raguwa, komawa yai ya sa hannu ya cigaba da yimata.
Sai can ya tsaya ya kalleta tana bacci hankalinta a kwance, murmushi yai wanda shikansa bai sani ba.
Sannan ya mike ya cire kayansa ya daura towel ya shiga wanka.
Bai dade ba dan yana tunanin karta tashi, a hankali ya bude kofar ya fito ya zo zaisa kaya.
Wayarta ce tai kara da sauri ya matso ya dauka, number Ummy ce ya daga a hankali yace "Ummy."
Cikin mamaki tace "Hassan?"
Sageer dake kusa da ita ya kalleta, Ummy tace "Hassan kaine? Ina Jalilan?"
Yace "bacci takeyi bata danjin dadi ne."
Da sauri tace "lafiya? Me ya sameta?"
Yace "ba wani abun bane Ummy sako ne?"
Samun kanta tai da wani murmushi tace "a'a bakomai kace kartai abinci ta kwanta ta huta."
Yace to ya kashe wayar.
Da kallo yabi wayar sannan ya kalleta, me nakeyi hakan?
Ajiye wayar yai ya zo ya saka doguwar riga ta jallabiya sannan ya zauna akan kujera ga dau littafi wanda ya kasa karanta ko layi daya.
Sai kallanta da yakeyi, duk motsin datai a kansa.
Can ya daure ya koma ya maida kansa kan littafin, motsinta yaji, ya mike ya zauna a bayanta ya dan fara yi mata tausa a gun.
A hankali ta bude idanunta kallansa tai, yace "kin tashi?"
Da sauri ta kalleshi tace "yaya, bansan nayi bacci ba wlh yahkuri."
Mikewa yai tsaye yace "ya jikin?"
Tace da sauki sosai, yace "ki tashi ki sake wanka amma yanzu kiyi da ruwa mai zafi, sannan kisha ruwan tea black ne."
Tace "to."
Juyawa yai da sauri ta riko rigar jallabiyarsa.
Juyowa yai ya kalleta, yace "menene?"
Tace "yaya nagode, sannan kayi hakuri."
Shiru yai yana kallanta, yace "kin gode dame?"
Tace "taimakon dakamin."
Yace "karkiyi tunanin wani dalili ne yasa na taimakeki, I really hate naga wani bashida lafiya, ko wanene na gani cikin wani hali ko ba ke bace zan taimaka mai."
Kallansa tai jiki a sayaye sannan ta sakar mai rigarsa, ai dama batace dan ita special bace, me yasa wai yaya baya magana da sanyi?
Ta dan saukar da idanunta tace "nasani, duk da hakan nagode, sannan kayi hakuri da laifin da bansani ba."
Ya sake kallanta yace "nagane tashi kiyi abinda nace, kina mace amma bakisan menene zai taimaki lafiyarki ba, na rasa me yasa gaba daya baki damu da kanki ba."
Jalila ta kalleshi tadan canza fuska zuwa shagwaba tace "to ni ya zanyi?"
Yace "ba ni zaki tambaya ba."
Ya juya ya zauna.
Mikewa tai tana mamakin yanda taji sauki, dan ta saba in har ta fara da safe to fa sai dare, in kuma da daddare ta fara sai safiya.
Dan ma tayi sa'a tanajin yanayin nan ta sanar ma Ameera ita kuma ta bata pads, ta boye a cikin basket na laundry din dake cikin toilet din.
Ruwa mai zafi tasa ta gasa jikinta ji tai jikinta ya sake warewa ta tsaya a toilet din, sanye da toilet, taya zata fita? Shiyasa fa daga ta tashi takeyin wanka in kuma batai da wuri ba sai ta bari ya fita takeyi, tunowa tai jiya daya ganta tana sa bra.
Shiru tai tana tunani, ta kalli kayan data cire wanda tasa a ciki basket din laundry.
Ganin ba yanda zatai ne yasa tadan bude kofar kadan ta leko kanta.
Shikuma yana jin alamun bude kofarta ya kalli gun.
Suna hada ido ta komar da kanta.
Mikewa yai dan ya fahimceta.
Agoggo ya kalla, yaga azahar tayi ya mike ya tada sallah.
Ita kuma tana komawa ciki ta jingina da kofar toilet din, massage din daya mata dazu ta tuno, da sauri ta girgiza kai.
Sake lekowa tai taga yana sallah, a hankali ta fito tazo jikin wardrobe ta bude ta zura hijab.
A cikin hijab din tasa bra sannan ta zura skirt ta sa riga sannan ta cire hijab din ta matso jikin madubi ta shafa mai sannan ta fesa body spray da turare.
Kallansa tai yana zaune akan sallaya ta lalaba tai waje.
Tana sauka ta hada tea kamar yanda ya sata tasha, sannan ta koma kitchen ta bude fridge ta dauko nama zata sa tafashe.
Bayan ta fita ne yai tunanin yanzufa sai ta tafi sa abinci ko?
Mikewa yai ya sauko kasa, kitchen ya nufa, ya taka ciki ya shiga.
Raban da Hassan ya shiga cikin kitchen shikansa ya manta, ko magana zaiyi sai dai ya tsaya daga falo, ko kofa.
Juyowa tai jin motsin shigowa, kallansa tai cikin mamaki tace "yaya!"
Me zance? Abinda zuciyarsa ta tambayeshi kenan.
Hade rai yai yace "ruwa zaki bani."
Tace "ruwan sama har ya kare?"
Yace "a'a ba sanyi ne."
Cikin mamaki ta mikomai robar ruwa tana cewa ko na kashe fridge din?
Mikamai ruwan tai yasa hannu zai amsa, kan hannunta hannayensa suka taba, kallansa tai shima ya kalleta.
A hankali ta zare hannunta ta dan juya.
Ya amshi ruwan kafin yace "me kike? Ke da ba lafiya ba?"
Tace "abinci zanyi kaga ba kowa a gidan."
Yace "dan ba kowa sai akace mara lafiya yai abinci?"
Ta juyo tace "ba haka nake nufi ba, kaga sanda zasu dawo ne a gajiye zasu dawo."
Yace "in ance bakya kula da lafiyar ki kice ba haka ba, to Ummy ce tace karkiyi."
Ya juya ya bar kitchen din.
Da kallo ta bishi, tadan yi ajiyar zuciya tace "oh ni, yanzu ma laifi na sakeyi?"
Maida namantai cikin fridge din sannan ta fito.
A falo ta sameshi tace "Yaya!"
Ya kalleta yace " kin warke ko na kaiki asibiti?"
Tace "Allah na warke har mamaki nakeyi."
Ya juya ya hau sama.
Shiru tai tare da binsa da kallo.
*******
Ummy kuwa tana kashe waya ta saki wani murmushi, Sageer ya kalleta yace "Ummy wani abun ne?"
Tace "a'a bakomai, kawai dai abin ne kemin dadi, dan na tabbatar yanzu Hassan ya fara san matarsa."
Sageer ya kalleta wani abu ya ratsomai, ya daure yai murmushi yace "ai Ummy ki daina damuwa na tabbatar Yaya zaiso Jalila yanda bakya zato, tanada halayen da zaija ra'ayinsa."
Ummy ta jinjina kai cikin jin dadi tace "sosai ma, na yarda dakai Sageer."
A tare sukai murmushi Ummy tace "ya kukai da Goggo dazu?"
Sageer yace "ai bakiga kukan datake ba nidai har na taho tana kuka akan itakam da munbarta ta koma kauye ina ita ina wannan gida haka?"
Ummy tai murmushi tace "Sageer in na tuno abinda mutanen nan sukayima Jalila da mahaifiyarta sai naji kamar bai kamata mu kyalesu ba."
Yace "hakane Ummy koni abin na damuwa, bansan haka tai rayuwa ba."
Ummy tace "nikaina, sai dai mu barma Allah komai."
A ransa yace "bansani ba Jalila, bansan haka kikasha wahala a rayuwa ba, i am really sorry......."
*******
Suna saukowa Dady ha kalli Mumy yace "mumyn Yasmeen me kikeyi hakan?"
Rungumeshi tai tace "ba sai ka shiga maganar nan ba, wannan shikadai ne hanyar da zaisa Inna tadinga ganin girmanka."
Dady ya dago ya kalli sama, inna ya gani a tsaye tana kallansu, murmushi ya mata sannan ya kankame Mumy tare da sa kansa a wuyanta.
Inna ta dunkule hannunta sannan ta juya, snake yanzu kake nunamin abinda ke boye a kasan zuciyarka, u really try na yanda ka boye fuskarka a cikin mask ba wanda ya fahimci abinda ke tattare da ita.
Tace sai dai ka makaro dan kana tafin hannuna wlh.
(Nace damuwarki=??)
#OneLuv=ؕ?
[12/7, 9:53 PM] El-hajj: *JALILAH* =???
Written By : *AYUSHER MUHD*
'?ote me on Wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_=ء?)
*49*
Goggo tana zaune tana kara bin gidan da kallo, hawayenta yaki tsayawa, ashe alheri ne a dukulle a tattare da sharrin da aka jefesu dashi.
Ba wani katon gida bane, falo daya ne babba sai 2bedrooms a cikin falon da toilet daya.
Sai tsakar gida kato wanda za'a iya ajiye motoci kananan guda biyu.
Ameera da Lantana dake sa labule ta kalla tama rasa ta ina zata fara, ashe a rayuwa akwai rana irin wannan? Shiyasa mutane ke cewa Allah yasa muci darajar 'ya'yan mu, a da bata fahimtar abinda ake nufi da hakan amma yanzu ta gane dalilin fadan hakan, in kai a rayuwa bakai sa'ar abokin zama ko iyaye ba sai ka nemi sa'a akan 'ya'yanka.
Hawayenta ta share, ko mahaifiyarta da mahaifinta nada rai?
Haka su kai ta aiki, itama tana tayasu, sai yamma su Ummy suka dawo, sun siyo abin kitchen, tv set, toilet, abinci da sauransu, dama zuwan farko aka siyo kujeru, gado da labulaye.
Haka suka taho musu da gashashiyar hanta da juice suka ci suka sha, Ummy ta nunama Goggo kawai komai ta samu tayi. Hamdalla bawai taita kuka ba, hakan yasa ta saki jiki sukaci abinci tanata godiya.
Sai wajen Magrib suka kammala komai, Ummy tace su tafi, sai asa ranar tarewarta.
Goggo tai shiru tana tunani, Ummy ta matso tace "lafiya? Ko kina tunanin zama ne gaba daya?"
Goggo tace " indai haka??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????n zai samu nafisan hakan, dan maganar gaskiya kunyar gidan nakeyi.
Ummy tace "shikenan ai ba wani abu bane, in har hakan yafi kwanta miki a rai, sai dai kamar ba'a gama jan wutar gidan ba, sannan bamu siyo generator ba."
Goggo da sauri tace "hakan ma ya isa, ba sai anja wutar ba dan acan gidan ma bamu samu wannan darajar ba ni har na rasa ta inda zan soma yi muku godiya."
Ummy tace "dan Allah ki bari, yanzu bari mu barku anan, sai nasa yanzu Sageer ya samo katuwar fitila kafin a gyara wutar gidan, kayanki kuma gobe in Jalila zata zo sai na bada a kawo miki."
Goggo ta kamo hannun Ummy cikin wani irin yanayi na farinciki tace " nagode nagode, sai dai dan Allah ina da alfarma daya dazan nema."
Ummu tace "menene?"
Goggo tace "Jalila tana bala'in san makarantar addini ta islamiyya, bansani ba ko da yanda zakuyi ku taimaka mata."
Ummy tace "basu sata a makaranta ba?"
Tace "basu sata ba, karatun da nake dashi kadan shi na koya mata."
Ummy tai shiru tana tunanin wannan muguntar kafin tace "shikenan zan sanar ma mijinta, hafizi ne na karatu dan da wuri ya sauke alqur'ani zan ji shawarar da zai yanke."
Goggo tace "nagode sosai."
Haka suka fito sukabar Goggo da Lantana a gidan, sai da suka sai katuwar fitila suka kai musu sannan suka fito.
Ummy a hanya ta kalli Sageer tace "Sageer akwai iyayenda in basuyi wasa ba alhakin 'ya'yansu shine dalilin da zaisa su shiga wuta."
Sageer yace "Ummy nikam haryanzu kwakwalwata na mamakin irin wannan mahaifin, wanda san kansa yamai yawa da har baya damuwa da halin da 'ya'yansa suke ciki."
Ameera ta kalli Ummy tace "Ummy nikam dan Allah kumin bayani, wai ya akai Goggo ta zama mahaifiyar Jalila, Mumy fa? Nifa gaba daya na rasa meke faruwa tun jiya nakesan yin tambaya."
Ummy tasa yatsa ta ta tura goshita tace "gulmar me kike sanji? Magana daya dai wannan ce mahaifiyarta me kike nemanji bayan wannan?"
Sageer ya sa dariya yace "Ummy in Ameera batai gulma ba ai ba Ameeran bace."Cikin shagwaba tace "Yaya Sageer haka zakace? Harda wani in banyi gulma ba?"
Ya kara sa dariya yace "To yahkuri ba gulma ba."
Ummy ta kalleta tace "ba wani tayi hakuri, ai dama uwar gulma ce da san jin komai."
Ameera ta kara shagwabewa tace "Ummy Allah ni abubuwan da nakeso in tambaya dayawa fa amma tun yanzu kunsa na kasa."
Ummy tace "sai ki hadiye gulmarki inkin samu Abbanki sai ki tambayeshi."
Tace "shikenan ai nasan Abbana bazai min haka ba..."
Haka sukai ta zolayarta suna dariya cikin farinciki har suka isa gida.
********
A can gida kuwa Hassan tunda ya shiga daki ya zauna a bakin gado yai shiru yana tunani, tabbas gaba daya rayuwarsa ta canza a 'yan kwanakin nan, gaba daya yarinyar nan taki barin zuciyarsa.
Abu daya ne ya fara zuwa mai badai santa kake ba?
Da sauri ya girgiza kai yace "so? Ni? Yarinyar nan?"
Kai ya sake girgizawa alamar ba haka ba yace "tausayine."
Tausayi akan me? Ka tabbatar shi kadai ne? Damuwar da kakeyi fa in abu ya sameta?
Tambayar dake tamai yawo a zuciya kenan, shiyasa ma gaba daya daga ta shigo sai yai gamar yana bacci, ko ya dau littafi wai a dole karatu hakeyi ko ya dau wayarsa....
Ita kuwa daga baya ta sauka falon kasa ta zauna.
Bayan tayi sallar isha'i ne Abba ya dawo, ta gaisheshi ya amsa fuska a sake bai dade da dawowa ba su Ummy suka dawo.
Tanajin dawowarsu ta tashi da sauri tazo taryarsu.
Ummy ta kalleta cikin kulawa tace "Jalila jikin ne?"
Tace "na warke Ummy gashi banyi abinci ba."
Tace "nina hana kiyi, bakida lafiya wake ta abinci?"
Sunkuyar da kanta tai, Ummy ta amshi ledar hannun Sageer tace "ga shi kije kuci da Hassan muma munyo namu tsarabar."
Jalila ta amsa tace "angode."
Ta fada sannan ta leka bayan Ummy, Ummy tace "tana can."
Jalila ta sunkuyar da kai tace "tam."
Ameera ta matso tace "ya jikin?"
Jalila tace da sauki.
Ummu tai gaba Ameera ma tabita, ta kalli Sageer tace "Sannu da zuwa."
Kallanta yai yace "ya jiki?"
Tace "na ware ba wani serious bane dama."
Ya kalleta cikin kulawa yace "Sannu Allah ya kara sauki."
Tace Ameen ta juya, da kallo ya bita.
Kowa daki ya shiga da ledarsa dan duk sun gaji.
Jalila ta wuce sama.
Tana shiga ta sameshi a zaune, yana ganinta ya dau littafi wai karatu yake.
A ranta tace ko gajiya bayayi.
Ta matso dan dama ta dauko plate daga kasa, ta bude tace "yaya sauko Ummy ta kawo mana abin dadi."
Kallanta yai yace "menene abin dadin?"
Ta bude kedar ta ciro ledar juice sannan ta ciro foil paper ta bude, kaza ce da kuma daurin kundu wanda yasha hadi na musamman.
Juyowa tai ta kalleshi, kallanta yai sannan ya sauko fuska ya zauna, dandai yunwa yakeji amma da cewa zaiyi bazaici ba.
Kallansa tai batasan yanda zata raba musu ba gashi plate daya ta dauko, kallansa tai shima kallanta yai tace bari na dauko wani plate din.
Ta fada tana kokarin mikewa, hannu yasa akan hannunta data dafa kasa zata tashi, kallansa tai, yace "muci tare."
Tace "naam?"
Yace "me? Dama ba haka kikeso ba?"
Tace "nakeso kamar ya kenan?"
Yace "duba ki gani, kinsan mu biyu ne a dakin nan kika dauko plate daya, yimin bayani meyasa kikai hakan to?"Jalila ta kalleshi kamar zatai magana kawai sai tasa dariya tace "lalai Yaya, yanzu nace zan dauko plate ka hanani sannan kace nice nakeso."
Yace "to ba hakan bane?"
Tace "wlh ba haka bane, ni na....."
Yanda ya mata da fuskarsa ne yasata ta kasa magana alamar bayarda zaiyi da duk abinda ta ce ba.
Bismilla tai tasa hannu tana cewa "shikenan tunda an dakeni an hanani kuka."
Bai tanka mata ba yasa hannunsa, a tare suka fara ci, itadai kunya take, shikam wani irin sanyi yakeji a ransa, yana kallanta yasa hannu cikin plate din, a kann hannunta yasa hannunsa.
Dagowa tai ta kalleshi, kallanta yai sannan ya kalli hannunsa, yace "yanzu nine nasa hannuna ko kece?"
Tai dariya sannan ta kalli hannun nashi tace "to hannun waye a sama?"
Ya kalla yace "nawa ne sai dai me yasa nakeji a jikina kamar dauramin akai?"
Tace "me? Daurama?"
Dariya ta fara yi tana kallansa, samun kansa yak da shagala gun kallanta, wanda har bai san ganin yanda take dariya yasashi sakar murmushi ba.
Tsayawa tai da dariya tace "Yaya! Kasan kayi murmushi yanzu?"
Fuska ya hade tare da zare hannunsa da sauri yace " a ina nai murmushin?"
Tace "wallahi kayi yanzu, baka san kayi ba?"
Juya kansa gefe yai yace "u are mistaken."
Tai shiru tana kallansa kafin tace " mistake nai? Amma na tabbatar naga kayi murmushi."
Yace "are u sure ba hakan kike san gani ba?"
Tace"wannan karan bazan musa ba, dan ina san inga ka yi murmushi kullum fuskarka a daure take."
Ya kalleta tare da daukan cup din juice yasha.
Haka sukaci abinci tare sannan ta mike ta wanke hannu ta sauka kasa dan kai plate.
Tana fita ya saki ajiyar zuciya yace "Hassan?"
Gaban madubi ya koma ya kalli kansa, a hankali naga yanayin fuskarsa ya canza zuwa tashin hankali, yasa hannu ya bude drawer karshe ta jikin madubi.
Wani littafi ya dauko ya bude tsakiyar hoto be ya bayyana, kallan hoton yai cikin wani yanayi sannan yamaida hoton ya rufe ya runtse idanunsa, bancancanci farinciki ba, ban kuma cancanci inso ko a so ni ba.
Mikewa yai ya dafa kansa dake sarawa........
Gaba daya ranar bai sake magana ba har ta gaji ta kwanta dan ba alamar fuska.
Washegari ma da Ummy tace ya kaita gidan Goggo bai musa ba ya jira ta suka fita tare, yana kaita kofar gidan baijira me zatace ba yai gaba.
Da kallo tabi motar tana mamakin abinda ya faru, ko a mota duk yanda taso suyi magana kin yarda yai.
Shikuwa yana ajiyeta yaja mota yana tunani.
Jalila kam tana shiga gidan Goggo ta saki baki tana kallan iko Allah, ta shigar da kayan data taho dashi, nan suka zauna suka hau hira cikin farin ciki.
Lantana ma ta zauna sukaita hira.
Goggo cikin hira ne take tambayarta wanda ya kawota.
Jalila tace driver dinsu ne ya kawoni, Yaya ya fita ne.
Goggo tace "Allah sarki, na dauka shine ince bai shigo mun gaisa ba na mai godiya."
Jalila tace "zaizo shima."
Haka sukai ta hira suna tuno rayuwar baya da yanda sukasha wahala, Goggo tanata kara nuna mata ta kula da mutanen nan dan tabbas sun musu hallacin da basu taba tunani ba.
Jalila jefi jefi tana tuno abinda yaya ya mata yanzu da zata sauko, ta fito ta kalleshi tace "Yaya baza......"
Gano tai ya dauke kai yana neman wucewa.
Tsayawa tai dagalo tana kallan ikon Allah kafin ta shigo.
Meya sameshi?
Sai bayan magrib yaro ya turo ta fito, tana fitowa taga Mamman, jikinta ne yai sanyi ta bude bayan mota ta shiga tayima Lantana da Goggo sallama akan sai ta dawo.
Haka suka hau hanya, ta kasa daurewa tace "Mamman ina Yayan?"
Yace "wlh Hajiya bansani ba, waya yamin yace in daukoki."
Tace "okay."
Haka suka isa gida taitama Ummy godiya da Abba.
Kafin ta hau sama.
A daki ta sameshi yana karatu, sallamarta kawai ya amsa shima baiko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login