Showing 99001 words to 102000 words out of 149705 words

Chapter 34 - Jalilah Book One Complete Hausa.doc

Ayusher   

28 Oct 2025

625

hankalinta na falo, jin alamun mutum yasa ta kalli bakin kofa.
Hassan na ganin ta juyo ya shigo kitchen din da sauri kamar ma wai baisan tana ciki ba.
Kallansa tai da sauri ta matso cikin zumudi tace "yaya ya kukai? Sun tafi?"
Yace "ke meya hanaki zuwa?"
Tace "kawai, banasan ganinsu."
Yace "kin tabbatar ba tsoro ne ya hanaki ba?"
Tace "ba wani tsoro ni kawai........"
Kai ya shiga jijigawa wai alamar ya fahimta irin na wulakancin nan.
Tadan kalleshi fuskarta a hade tace "kaifa? Abu ka shigo yi?"
Ya kalleta yace "me? Kina tunanin gunki nazo?"
Tace "bance ba." Tai maganar cikin sanyin jiki.
Yace "ah to gwara dai ki fuskanci reality."
Baki ta dan turo ta juya ta cigaba da suya, Hassan ya kalleta hankalinsa ya kwanta ya dauka ganinsu ya sata cikin wani hali.
Fridge ya bude yadan sha ruwa kadan dan karta gane, yanayi yana kallanta amma yaga ko kallansa bata sakeyi ba.
Da karfi ya buga murfin fridge din, juyota tai ta kalleshi.
Yace "wani irin fridge ne wannan? Daga sakeshi sai ya tafi?"
Tace "anya kuwa ba kai ka buga shi ba, naga ne baya haka."
Hassan ya kalleta yace " akan me zan nemi hucewa akan fridge? Laifi akamin?"
Tace "ina na sani?"
Juyawa yai ya fita yana cewa "ke dai da kike tsoro sai ki karashi zama a ciki."
Tana neman magana ya fita, haushi ne ya kamata ta kashe gas din ta biyoshi.
Yana shiga falon itama tana shiga, da Sageer suka fara hada ido, tai saurin daukewa sannan ta karaso.
Hassan na zama yaga shigowarta, murmushi yai a ransa ta shiga ta zauna a kasa daga gefe, ta gaida Inna da Mumy.
Inna cikin sanyin murya tace "Jalila ki yafemana abinda muka aikata miki."
Mumy ma tace "kiyi hakuri Jalila, bamu kyauta ba."
Kallan Hassan tadan yi taga ko kallanta ma bayayi tace " ya wuce."
Kallanta yai, itama ta kalleshi, ta maida kanta kasa, ganin zaman nasu ba so ake ba yasa sukaitama Jalila dasu Abba godiya, dan Abba yace zaibar kudin zuwa wani lokaci.
Haka suka fito suka shiga motarsu suka tafiAbba na shirin barin falon Hassan yace "Abba!"
Abba ya kalleshi yace "Hassan da magana ne?"
Hassan ya daga kai yace "dukanku, magana zamuyi."
Ummy cikin mamaki ta kalleshi, shima Abba kallansa yai.
Jalila ta juya zata fita, da sauri yace "Jalilah."
Cak ta tsaya saboda yanda ya kira sunanta, ya kata alama data dawo falon.
Komowa tai ta zauna, bayaji zai iya jawabin nan ba tare datana kusa ba.
Falon yadanyi shiru, Sageer na zaune shima, Hassan ya fara da cewa "Abba kayi hakuri ka yafemin, duk wani hukunci da zakamin zan dauka ko menene shi kuwa, sai dai ina neman yafiyarka a gareni."
Jikin Abba ne yai sanyi yace "rabuwa kakesanyi da matarka?"
Hassan ya kalleshi yace "Abba Husain...."
Ummy ce ta kalleshi da sauri tace "Hassan."
Kallan Ummy yai ya saki wani sansanyan murmushi yace "Ummy nine sanadiyar mutuwarsu."
Ummy da Abba a tare sukace bangane ba???
Jalila kam Hassan kawai take kallo sai idanunta da suka ciciko da kwalla.......
Hassan yace " a ranar sunan Ameera............"
Nan ya kwashe komai ya sanar dasu, gaba daya falon hankalinsu ya tashi najin abinda ke faruwa, sai dai Hassan nakaiwa karshe bai jira amsar wani daga cikinsu ba ya tashi da sauri ya hau sama, Ummy na kiransa ko juyowa baiyi ba.
Jalila ta mike da sauri tahau sama, yana shiga itama ta shiga.
A bakin gado ta ganshi yana neman zama, hannunsa ta riko da sauri tace "Yaya"
Da sauri ya jawota jikinsa ya rungume tsam, zuciyarsa na wani irin bugawa, yanda ya kankameta ne yasa tai shiru, cikin wata irin murya yace "Wani hali Abba zai shiga? Yaji d?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? ansa ne yai sanadiyar......"
Kasa karasawa yai saboda raunin da zuciyarsa ke neman yi, Jalila tace "Yaya wanda bai sanka ba inya ganka zaiyi tunanin zuciyarka rike take gam, ba tausayi a cikinta, sai dai wanda ya zauna dakai a hankali zai fahimci zuciyarka cike take fam da tausayi."
Yace "ke tausayi hakan yai miki kama?"
Tace "sosai zuciyarka saboda tsananin tausayinta ne yasa take zargin kanta da aikata laifin da ba ita ta aikata ba."
Hassan yace "ya isa haka nan Jalila, na san kina fadar hakan ne dan hankalina ya kwanta, please keep quiet."
Shiru tai sai dai haryanzu bai saketa ba, Sageer wanda hankalinsa ya tashi ya taso da sauri ya gansu a haka a cikin dakin, juyowa yai jiki a sanyaye fuskarsa na dauke da murmushi a ransa.
Yana saukowa Ummy tace "Sageer ina Hassan din?"
Yasan yanda Ummy ke tsananin san Hassan, yace "karki damu Ummy matarsa na gunsa."
Komawa tai ta zauna ta kalleshi, yace "Abba fa?"
Tace "ya shiga daki."
Sageer ya zauna a kusa da ita yace "Ummy kinsani ko kema sai yanzu?"
Ta share kwallarta tace "bantaba sani ba, Sageer Hassan haka yai shekara sama da 15 cikin zargin kansa?"
Sageer cikin tausayawa yace " Ummy ni nama rasa me zance."
Shiru sukai suma........
Hassan kam ya dade manne da ita kafin daga baya ya saketa, kallanta yai sannan yace "na matseki ko?"
Tai murmushi tace " to ni yanzu yaya wace amsa kakeso na baka?"
Zama yai a kan gado sai kuma ya kwanta baice komai ba, harta juya zata sauka saboda girkin da ta kashe taji yace " Jalilah!"
Juyowa tai ta kalleshi sai dai sanyin jiki yasa ta kasa amsawa, yace " kina tunanin hankalin Abba zai kwanta?"
Tace "shima Abba zai fahimci ba laifinka bane ba."
Yace "nagode."
Kallansa tai sannan ta fito.
********
Dady ne ya kalli Mumy yace "ya kukai?"
Tace "ni wlh gaba daya na kasa fahimtar takamaimai abinda ya faru a gidan."
Dady haushi ya kamashi, amma ya murmusa yace " amma kina tunanin sunji haushina?"
Tace " ai dukanmu ma ko kamanta Goggo na gunsu? Na tabbatar sunsan komai."
Dady yai dan tsaki a ransa yace dolene ya je ya lalaba Jalila ai dama ba mai shiga tsakanin jini? Yana zuwa zaisan yanda zaiyi ta yafemai......
#OneLuv=ؕ?
[12/7, 9:55 PM] El-hajj: *_=???JALILAH!!=???_*
Written By : *AYUSHER MUHD*
'ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_=ء?)
*Gaisuwa gareki BillynAbdul akoda yaushe ina miki fatan alkairi arayuwarki......*
*56*
Damuwa da rashin sukuni suka saka hassan gaba, gakuma jalilah tafice tabarsa shikad'ai a d'akin, jiki a sanyaye yasakko daga gadon, yad'auki wayarsa da key yafice.
****
Su Ummy nazaune haryanzu a parlor itada Sageer, bai kalli inda sukeba yafice da sauri, dan kunyar had'a ido yakeyi da Ummy.
Da sauri Ummy ta yunk'ura zata bishi amma Sageer ya rik'e hannunta da sauri, juyowa tayi ta kalli sageer d'in, idonta harya fara tara kwallah, Sageer ya girgiza mata kansa,
"A'a Ummy kibarshi"
Ummy ta kalli hanyar daya fita tace "Yaza kace Na barshi Sageer? bakaga a yanayin daya fita bane?".
Sageer ya kalleta yace "Nagani Ummy hakan ne ma yasa nace ki barshi, addu'a kawai zamu mai."
Shiru Ummy tayi takasa magana.
Fad'uwar Abu dasuka jiyo a kitchen ya sakasu juyawa su duka suna kallon kofar kitchen d'in, sai kuma suka tafi kitchen d'in a tare.
Shigowar su tasaka jalilah dake tsuggune tana kwashe fasashshen kofin daya silmiyo daga hannunta wanda ya fashe haryasa su Ummy sukajiyo yasata d'ogowa tana kallonsu.
Da sauri Ummy ta k'araso gareta tana fad'in "bakiji ciwoba ko jalilah!?".
Kai jalilah ta girgiza mata alamar a'a sannan tace
" a'a Ummy, banji ciwoba".
Ganin haka sai Sageer yajuya yafita.
Jalila tad'an bishi da kallo, kafin tadawo da kallonta kan Ummy dake mata magana.
"Jalilah mijinki fa?".
K'asa tayi da kanta cikin kunya tace " Ummy yana d'aki".
"Baya d'aki gaskiya, dan yanzu yafita nama zata kema kina d'akin aii? Sam ban kula da saukowarki ba."
Cikin d'an zaro ido waje na alamun tsorata Jalilah tace, "Ummy yanzufa nafito, nabarshi a d'akin a kwance, naga kuna magana ne da ya Sageer, shiyyasa na taho nan banyi magana ba".
K'aramar ajiyar zuciya Ummy ta sauke, sannan tace,
"Amma a wanne hali kika barshi? Ni na kasa ganewa."
Jingina sosai Jalila tad'an karayi da fridge din dake bayanta, tareda murza tafin hannunta na dama.
"Ummy ki kwantar da hankalinki, babu wata damuwa wallahi, wannan fitarma k'ilan akwai zaman cikin ne ya isheshi".
Ajiyar zuciya mai k'arfi Ummy ta sauke, sannan tak'arasa inda Jalila take tsaye, hannunta datake murzawa ta kamo, dan zatonta ko Jalila taji ciwone da kofin data fasa".
"Ummy babu komai fa, ba ciwo najiba".
Murmushi Ummy tayi, "ai nazata ciwone kike boyemin, bara nataya ki mu k'arasa girkin".
Da sauri tace "Ummy kibarshi na k'arasa dan Allah kije kawai ki huta".
"A'a, muk'arasa kawai, kafin mijinki yadawo".Shiru jalilah tayi saboda kunya, a tsanake suka gama komai, Ummu dai tausayin Hassan duk ya dameta, sai da taga sun kusa gamawa sannan tafito Jalila ta k'arasa.
Babu kowa a falon, Sageer ma ya shige d'akinsa. Ganin haka sai Ummy tanufi wajen Abbah, dan duba halin dayake ciki.
Bayan jalilah ta kammala komai ta d'auki abincin su ta haye sama.
Ajiye tiren tayi, sannan ta d'an gyara gadon dasuka bata d'azun, gefen zuciyarta na tunanin ina Yaya yaje? itadai tasan lafiya lau tafita tabarsa, to miya fasu ne?.
Haka taita 'yan tunane tunanenta harta kammala, tashiga toilet tayo wanka, a gaggauce tafito ta shirya, dan batason Yaya yashigo ya ganta ba kaya kamar rannan.
Babu maganar kwalliya a tsarin jalilah, tasaka doguwar riga ta material, d'as takama jikinta, ta d'aura d'an kwalinta simple, harta bar jikin mirror sai kuma tadawo, ta d'auki turare tana fesawa, abisa tsautsayi kuwa ta fesowa fuskarta, sai cikin idonta Na haggu.
Karamar kara tasaki, tareda saurin rufe idon da hannu daya, dayan hannun kuma tana yarfawa tare da kiran "wayyo Goggona".
A haka Hassan yashigo dakin ya sameta.
Kallo yabita dashi, ganin yadda take tsalle-tsalle taki tsayawa waje daya saita bashi dariya, amma bai yiba ya zauna bakin gadon tareda ajiye key da wayarsa agefe.
Jalilah batasan dashiba, dan kokad'an bataji shigowar saba, sai tsalle-tsallen ta takeyi tana shiiiiii da baki, har yanzu hannunta dafe da idon, d'ayan kuma tana yayyarfashi, lokaci-lokaci takance "wayyo Gwaggona, Goggo kizo na makance".
Tausayi tafara bashi, yabita da kallo daga sama har k'asa, sai yanzu yalura da gwangwanin turaren dake k'asa a yashe, da alama shine tasama idonta.
Da sauri ya mike ya matso kusa da ita, sannan yakai hannu yariko hannunta datake yayyarfawa.
Tsorata tayi, tace, " Wayyo Allah na, wanene?".
Bai bata amsaba, suka je kusa da gado ya zauna, jawota yayi ta fad'o jikinsa saman cinyarsa.
Jiyayi wani mugun shock ya shigesa, har sai da yad'an rintse idonsa. Itakam jalilah k'amshin turarensa yasa tagane shine, dan haka saita nutsu, tabar mutsu-mutsun datakeyi.
Hannunta data rufe idon yajanye, ya kwanto da kanta saman k'irjinsa, yasaka hannunsa d'aya ya bud'e idon da k'yau, d'ayan kuma ya tallafo kanta sosai, sannan yafara hure mata a hankali, idon yayi jawur kuwa.
Yanda yake matanne yasakata yin luf ajikin sa, gakuma k'amshin turarensa mai dadi tana shaka.
Ya dad'e yana hura mata idon, sai da ya tabbatar ya huce sannan ya daina hurawar, amma yaki sakinta.
Bud'e idon tayi ahankali ta saukesu akansa, ganin ita yake kallo saita d'anyi k'asa da idanunta, a hankali ta furta "Na gode yaya".
" Uhhm".
Kawai yace mata, sai kuma ya k'ara hura mata iska a fuska.
Ta bud'e idon sosai tana kallonsa.
Da ido ya nuna kanta dake kwance a k'irjinsa, sai kuma yace, "A nan zaki kwana?".
Baki ta d'an turo gaba, ta yunk'ura zata tashi, amma saita kasa, saboda har yanzu yana rik'e da ita.
A shagwabe tace, "to taya zan tashi? bayan kamin d'aurin goro".
Firicin nata yasakashi sakin guntun murmushi, ya janye hannunsa batareda ya tanka ba.
Kanta kawai ta cire daga k'irjinsa, amma bata tashi a cinyarsa ba tace "Yaya wai ina kaje?""idan kin gama more cinyar itama saiki d'aga, idan kuma zaki biyane to?."
Baki takuma turowa, ta yunk'ura zata tashi tana k'unkuni
Harta mik'e yarik'o hannunta ya dawo da ita.
"Ah ah, mikuma nai?"
Hannunsa duk biyu yasaka ya zagayeta dasu, yakawo bakinsa kusada kunnenta.
"kina son sanine?".
Juyowa tayi ta kallesa da sauri, amma batace komaiba, saboda gabanta dake faduwa.
Ya huramata iskar bakinsa a fuska, yana kallon idonta dayay ja yak'ara d'an girma.
Yace "kin tabbatar ba saboda ki zauna kika sa turare a idan naki ba?"
Kallansa tai ta hade fuska tace "Yaya wai......."
Kauda kanta tayi, zuciyarta tana mamakinsa....
Barakai k'arshen tunanin taba taji yasaka hannun damarsa yadawo da fuskarta saitinshi.
Kafin tasamu damar magana taji bakinsa kan labanta.
Waro idanunta tayi saboda mamaki, shima ya waro nasa sosai kamar yanda tayi, sannan yahad'e bakin nasu sosai.
***********
Ummy kuwa koda tashiga d'aki sai ta tadda Abba zaune yana duba wasu takardu, shiru tayi nad'an wani lokaci tana nazarinsa, kafin tayi sallama. ya d'ago idanu yad'an kallrta ya amsa sallamar tata.
Suka d'anyi shiru zuwa 2minutes. Abba yakatse shirun da fad'in "Hassan fa?".
Sanyi Ummy taji aranta kafin tace, " yana lafiya. dama zan sanarma lokacin salla yayi".
Kansa ya jinjina mata, ya ajiye takardun hannunsa yamik'e zuwa bathroom. ita kuma zama tayi abakin gadon tana binsa da kallo, takasa tantance yanayin dayake ciki gaba d'aya. babu dad'ewa yafito, baiko kalleta ba yace, "naje masallaci".
"Adawo lafiya".
Ummy tafad'a tana mik'ewa tashiga toilet d'in domin d'auro alwala itama.
**********
Tunda suka dawo inna takasa zaune takasa tsaye, maganar family d'in Taura kawai take juyawa a zuciyarta, gakuma dadyn jalilah a gefe daya zame mata k'ayar kifi a mak'oshi, Tarawa wace hanya zatabi 'yarta ta fahimci manufarsa.
K'aramin tsaki taja, kafin ta zauna tareda d'aukar wayarta tana dannawa alamar akwai abinda take nema.
" humm" tafad'a tarefa ajiye wayar tana mik'ewa, sai kuma tace, " dukanku nasan hanyar dazanbi nai maganinku aii"
Ni dai nace, "humm".
************
Sun kai adadin wasu mintuna Hassan na baje kolinsa, kafin yacire bakinsa yana guntun murmushi.
Jalila kam kunya tasakata sinne kanta a jikinsa, sai kuma ta zame ta sauka daga cinyarsa takoma kan gado, bai ce komaiba shima yamik'e bayan yakai dubansa ga agogon dake d'akin.
Kallonta yad'anyi ya kauda kai, yanayinsa ne ya canza ya kalleta yace "Jalilah! Har yanzu Abba baice komai ba, kinganshi ne?
Shiru tayi tana kallonsa, shikuma yacigaba da tafiya.
Saida yakama k'ofar toilet d'insu zai bud'e sannan yajiyo muryarta tana cewa "amma Yaya kaimafa nakula matsoraci ne, a haka kamar....."
Kallan daya mata ne yasa tai dif tana sinne kai, fuska ya hade ya nuna kansa da d'an yatsa "ni ne matsoracin?"
Dariya tayi kawai, amma batace komaiba.
Ya jinjina kansa sannan ya ida bud'e k'ofar yana fad'in "lokaci zai nuna a gane wanene matsoraci tsakanin ni da ke yarinya"
Bataji miyaceba sosai, Dan acikin toilet ya k'arasa sauran maganar, babu dad'ewa yafito yana gyara hannun rigarsa alamar yayo alwala, itama alwalar ta tashi tai, dan dazu tai wanka, ita dama bata dadewa intana period.
Lokacin data fito shi harya fara salla, itama saita shinfid'a abin sallah abayansa ta fara tata.
Bayan sun idar ta kalleshi yana zaune inda yai sallar, yayi shiru alamar yatafi duniyar tunani, a wani halin Abbansa yake ciki?
Daurewa tai cikin k'arfin hali tace "Yaya nakawo abinci"
Kansa ya jinjina mata batareda ya kalleta ba ta mik'e tana cire hijjabin jikinta, kafin ta d'akko tiren ta dire a gabansa, yauma bayan tagama zuba masa, harta janyo wani plate d'in zata zubama kanta yarik'e hannun, daga ita harshi suka kalli junansu a tare, sai kuma yasaki ya ture plate d'in gefe, ya d'auki d'ayan spoon d'in yasaka a inda tazuba abincin.
Sai da yafara ci sannan itama tafara cin, babu mai magana acikinsu, har sukai rabin abincin.
Sai can jalilah tace, "Yaya mizai hana ka fara gwada shiga masallaci cikin mutane yin jam'i?"
Ido yad'ago yad'an kalleta, baice komaiba har suka kammala, har ta d'auka bazai ce komai ba. tana tattare kwanikan taji yace "Kina tunanin zan iya?"
Kallansa tai jiki a sanyaye, yace "a koda yaushe inaga taron mutane sai naga kamar lokacin da mutane suka taru akan su Husain."
Shiru tai kafin tace "banyi tunanin hakan ba n......"
Yai saurin cewa "I won't stay like this forever, nagode da shawararki sallah cikin mutane tafi lada."
Kallansa tai cikin jin dadi tace "tam Yaya."
"Humm" ya fad'a yana mik'ewa, kayan jikinsa yafara k'ok'arin cirewa, dan haka Jalila tayi saurin d'aukar tiren tafice.
Binta yayi da kallo, ya d'an saki guntun murmushi, sai kuma ya lumshe idanunsa, ahankali ya furta " kin cancanta jalilah ".
Ni kam danake labe nad'an dara kad'an.=??
*************
Har washe gari Abbah baice komai gameda zancen da Hassan yay masaba, wannan ne yakuma saka Hassan cikin matuk'ar damuwa, amma kasancewar Jalila a gefensa zuciyarsa tana d'an rage nauyi.
Ita kanta Ummy shirun na Abba ya dameta, duk da bai canza fuska ba, amma yanda ya share maganar sai lamarin yake nuk'urk'usarta.
Sageer ma daya kasa daurewa sai da ya tambayeta mi Abban yace gameda maganar jiya.
"Sageer baice komai ba fa, nikaina abin ya dameni, gashi bansan wane hali Hassan yake cikiba, naga har yanzu matarsa bata fitoba".
Ya sageer ya ja ajiyar zuciya, sai kuma yace "insha ALLAHU babu abinda yafaru Ummy, bara muga zuwa 9 idan bata sakkoba sai a bincika"
Ta kalli Sageer cikin jin dadi tace to Sageer.
Ummy batace komai ba tacigaba da aikinta, amma zuciyarta sai sak'e-sak'e take mata akan Hassan da kuma shirun Abbah. tare sukayi komai da Sageer.
*************
Safeena ta kalli RAM tace "ina ne nan din?"
Yace shiga ki gani, tura kofar tai, yan mata ne da maza kowa yasha kaya na duniyanci suna ta cashewa.
Da sauri ta kalleshi tace "menene hakan?"
Yace "baki gane ba? Wannan shine rayuwa ai."
Ta kallesu sannan ta kalleshi da sauri ta juya da gudu tana girgiza kai, yanda taga mata na rungume maza ba kunya? Ina zata iya shiga tai abin nan?
Daki ta shiga ta fada kan gado tana kuka da kiran sunan Inna da Mumy da Dady..........
Nace hmmmmm
[12/7, 10:10 PM] El-hajj: *_=???JALILAH!!=???_*
Written By : *AYUSHER MUHD*
'ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*
*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_=ء?)
*57*
Har 9 tawuce babu jalilah babu labarinta. Su Ummy suka kammala aiki tsaf itada Sageer, ko ya Ummy taji motsi saita waiga, azatonta jalilah ce.
Shi kansa Sageer hankalinsa yafara tashi, yana daurewane kawai saboda karya k'ara tada hankalin Ummy.
A can kuwa bangaren su jalilah ciwon Hassan ne ya motsa, saboda damuwar daya kwanta dashi a zuciyarsa, akan shiru da Abba yai akan maganar su Husain, gani yake maganar tazama gaskiya shine silar barinsu duniya, shiyyasa Abba yake fushi dashi, dama Jalilah tana fad'an bahaka bane saboda kawai ta kwantar masa da hankali.
Cikin dare sau biyu ciwon natashi, shi yasa sam jiya basuyi wani barcin kirkiba, sunayin sallah da asuba kuma suka kuma kwantawa dansu rage barci.
Dama Hassan jiya a k'asa ya kwanta, duk yanda Jalilah taso yadawo saman gado bai dawo ba.
Bayan sunyi sallar asubahi ma a k'asa ya kwanta akan sallayar dayai sallah, can cikin barci Jalilah tadinga jiyo kakarinsa, a zabure ta mike cikin tsoro ta kalli inda ya kwanta.
A razane ta sakko kusa dashi ta tsugunna agabansa, hannuwansa daya rik'e wuyansa itama ta rik'e tana kiran "Yaya! Yaya!

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login