Showing 102001 words to 105000 words out of 149705 words

Chapter 35 - Jalilah Book One Complete Hausa.doc

Ayusher   

28 Oct 2025

639

Innalillahi please Yaya katashi."
Gaba daya ya canza, abin ya tsorata ta, yau kam ciwon yamafi na kullum tsanani, dan jikinsa har rawa yakeyi, kansa tad'aga ta d'ora a cinyarta tana kuka da tofa masa abinda tasani, tun tana d'aukar lamarin k'arami sai taga yawuce tunaninta, da ciwon yayi kamar zai lafa saikuma jikinsa yafara rawa yakuma damk'e wuyansa yana jawo numfashi da k'yar.
Tanaso tatshi taje takira su Ummy amma takasa, bazata iya fita tabarshi shi kad'aiba, dabara ce tazo mata data hango wayarta, da k'yar tamik'a hannu ta d'auka, tashiga laluben number Ummy.
Jikin Ummy har rawa yakeyi wajen d'aukar wayar. Saboda ganin number Jalilah, Sageer nazaune gefenta, yayinda Abbah ke shirin fitowa daga d'aki.
Tana gama jin maganar Jalilah ta jefa wayar a kujera, bata tsaya sauraren tambayar da sageer kemataba, ganin haka shima Sageer yarufa mata baya zuwa sama, dan ya fahimci ba lafiya ba.
Gaban Abba ne yafad'i yabi saman da kallo cikin matuk'ar tashin hankali, badai jikin Hassan bane, da sassarfa yabi bayansu shima.
Sun tarada Jalila tanata kuka har yanzu, gata rik'eda Hassan tana kiran "Yaya katashi!".
Gaba d'ayansu suka rufu akansa kowa yana masa addu'a, Ummy kam tama kasa addu'ar, kuka kawai takeyi, hakama Jalila.
Ganin halin da Hassan ke ciki cikin kidima Abba yakira Doctor, a gaggauce yamasa bayani akan halinda Hassan d'in yake aciki, yana kashe wayar ya matso kusa dashi tare da riko hannunsa.
Babu dad'ewa saiga Dr, Abba na ganin kiransa ya fito da sauri, lokacin ciwon yafara lafawa, sai numfashi da yake fitarwa sama-sama, har yanzu kuma kansa nakan cinyar Jalilah dake share sauran hawayenta, da taimakon Abba da Sageer suka maidashi kan gado, doctor yafara aikinsa....
***********
Mumy ce ta kalli Dady tace "Dadyn yasmeen kayi shiru? ko kafasa zuwan"
Kallonta kawai yakeyi, amma yakasa cewa komai, yarasa miyasa suka damu da zuwansa gidan Taura itada inna, kodai wani k'ullin sukai masa ne? sukeso yaje ya afka.
Hannunsa Momy ta kamo ta kwantar da kanta akan kafadarsa, juyowa yai yana kallonta, kafin ya d'an saki iska a bakinsa.
"Wai shin menene dalilin da yasa kika damu da zuwana gidan taura ne haka?"Gaban Momy yad'an fad'i, ita kanta tarasa gane dalilin Inna nason Abakar sai yaje gidan Taura, duk da dai tamata bayani a dunk'ule, amma anya babu wata kullalliya a zuciyar Inna kuwa? Itakam sam Inna inta fadi abu akan Abakar hankalinta baya kwanciya, tasan Inna sarai hankalinta nakan company dinta.
"Ya akai? Naga kinyi shiru?
"Uhm ba shiru nayiba, amma nima ina ganin zuwan naka yanada muhimmanci, musamman idan kahad'a bayanan dana maka guri guda, akan abinda aka mana agidan, kuma nasan duk akan komawar Gwaggon tane, a ganina kawai kace kanason gwaggo tadawo nan gidan dazama kawai, ni wlhy nama amince tadawo d'akin Safeenah yanzun, kaga sai a gyara kafin ta iso, idan kuma za a canja mata kayan d'akinme to, duk fa wannan takamar da mukeyi dan munada company namu na kanmu mukeyi ni sam idanun mijin Jalila yanda yake kallanmu hankalina bai kwanta dashi ba, na tabbatar Innama hakan ne yasata fadar cewa kaje din, ai daga Jalila har Goggon naka ne."
Zuwa yanzun kam zuciyarsa tagama yarda akwai wata akasa, wato sai yanzu akasan da Jalila tasa ce?
Yace, "ita inna tayarda da hakan?" Yai maganar cikin zargi.
Da sauri tace "sosaima, itamace tabada shawarar hakan, aganina tahanyar goge laifinmu ne kawai zai hana Taura karbe kud'insa koda kuwa dansa yaso yin hakan, dan wannan dan nasa ni yafi bani tsoro, dafa zai tambayi kana ina cewa yayi wai Inashi mutumin?"
Dady ya cije lebansa, daya tuna ma rainin hankalin da Hassan yamasa randa sukaje asibiti, wai ka fito da kudi kuwa? Ya tuna sanda ya miko mai 1000, kamar shi??
Momy takatse tunaninsa da fad'in "kagani zuwan naka yanada muhimmanci kaji Darling? koba komai zaka lallaba Jalilah, ai komin lalacewa naka naka ne, mu fa kosamun damar kebancewa da ita bamuyiba."
Dady yai shiru kafin can yace "Shikenan, babu damuwa, zanje din, amma kafin natafi zan shiga wajen Inna inji miya kamata nafad'ama Jalilah idan naje, kinsan yarinyar tana jarabar son uwarta, sam bata damu da ni dana haifeta ba.
Mumy ta kalleshi, jawota yai jikinsa ya rungume ta a ransa yace wato yanzu dalilin 'yata shine na samu 'yancin roko? Da ai komai sai dai a yanke min hukunci, danasan mijinta kafin aurenn lalai dana dade da canza shika.......
*********
Alhmdllh komai ya dai-daita, Hassan yadawo dai-dai, amma kallo d'aya zaka masa kahango idanunsa da sukai ciki, har wata yar karamar rama yayi.
Tun d'azun idonsa nakan Abba, kallonsa yakeyi ko kiftawa bayayi. ita kanta Ummy ganin kallon da Hassan kema Abban nasu yasata maida kallonta kansa, tasan soyake yace wani Abu, amma Abba sam bashida alama.
Hannun Abba Hassan yakamo, yarik'e sosai acikin nasa, wannan yasaka Abba maido gaba d'aya hankalinsa kan Hassan, ya zubamai ido cikin wani yanayi da shikadai ya san me yake nufi.
Wasu hawaye masu matuk'ar zafi suka ziraro daga gefen idonunsa.
"Abba nasan ban cancanci a yafe min ba, ni kaina nakasa yafema kaina wannan laifin, nasha addu'a inama tun sanda nayi jinya nima nabi bayan su Husain, na roki Allah akan inhar mutuwata shine mafi alkairi ya daukeni, sai dai da alama ba yanzu ba......"
Ya kara kallan Abba da idanunsa da suka canza yace "Abba kamin dukkan hukuncin dakaga yadace dani kaida Ummy, duk hukuncin da kukamin bazan taba ganin tsaurinsa ba, Ummy! Abba dan ALLAH Ku hukuntani ko nima zuciyata xata samu sukuni.
Kasa karasawa yai saboda gaba daya zuciyarsa ta yi rauni, hannu yakai yarik'e wuyansa yana k'ok'arin janyo numfashi.
Lokaci d'aya Abba da Ummy sukai kansa, Jalilah kam fita tayi daga d'akin tana kuka, shi kansa sageer yakasa jarumta dan tuni shima kwalla tacika masa idonsa har suna neman zubowa.Addu'oi Ummy da Abba kemasa, ahankali numfashin yafara dai-daita, Sageer yamik'o gorar ruwan daya d'akko, Abba ya taimakama Hassan yatashi zaune ya jingina da fuskar gadon, bayan yasaka masa fillo.
Ummy tabashi ruwan yasha sosai, kafin ya janye bakinsa.
Idonsa yayi jajur, kalle-kalle yafara yanason ganin Jalilah amma bata d'akin.
Ummy Ce talura da hakan, ta juyo tana fad'in "Sageer! Jalilah fa?".
Shima waige-waige yafara, kafin yace, "inagafa tafita".
Abba yace, "Sageer jeka kirata".
Yace "To Abba"
Afalo ya isketa tacusa kanta a cinya tana rusar kuka, tausayi tabashi ya kura mata ido, murya a sanyaye yace "Jalila"
Shiru kamar bata jishiba.
Ya sake cewa "Jalilah!"
Batare data kalleshiba tace "Naam." Cikin muryar kuka ta amsa.
"Kizo inji Ummy."
Abinda yafad'a kenan yajuya yakoma cikin d'akin. saida ta goge hawayenta sannan tamik'e tabi bayansa.
Tunda tashigo Hassan ya kura mata ido, a hankali ya lumshe idanunsa, garin yaya ya bari yarinyarnan ta gama kama zuciyarsa? Ummy tajawo hannunta ta zaunar kusada ita tana lallashi.
Bayan wasu 'yan mintuna Abba yai gyaran murya, har yanzu hannunsa nacikin naHassan.
Cikin kakkausar murya yace "Hassan!"
Abba yakira sunansa cikin muryar damuwa.
Kallonsa kawai Hassan yayi amma bai amsaba.
Abba ya kalli Sageer yace "Sageer zauna anan."
Gefensa kadan ya nunamai, Sageer ya zauna kusa dashi.
Abba ya kalli Hassan yace " me kake san ji Hassan? Me kakeso kaji daga bakina?"
Hassan ya kalleshi yace "Abba!"
Yanda ya kira sunansa sai da Ummy ta juya kai saboda kwalla, Abba ya sa hannunsa akan kafadarsa yace "kasan me yafi damuna akan abinda ya faru?"
Hassan ya kalleshi, Abba yace "gani nake duk nine mai laifi ba kai ba, alamace ta ban nuna ma kulawa ba, ban nunama duk kaddarar data samemu mu dogara da Allah ba, sannan ban nunama duk wani abu daya faru ka sanar dani ba, ban nunama ko me ya faru bazai zama laifine ba."
Hassan kallansa kawai yakeyi kafin ya juya kansa gefe, tare da runtse idanunsa, Abba yace " baka taba tunanin ko baka fita waje ba su sai sun fita kuma sai ajalinsu ya kama a gun? Hassan ina karatunka? Har ka bari zuciyarka ta damaimaiye da zargi? Ta hanaka walwala? Ta hanaka sukuni? Ta maidakai gaba daya wani mutum wanda baza'ai magana dashi ba? Ta maida ma baccinka nightmare?"
Hassan ya kalleshi yace "Abba ni na jaa su....."
Abba ma idanunsa ma gaba daya sun canza kala ya sa hannu ya jawoshi ya rungumeshi yace "Ko kaine hakan ta faru dakai, ace misali dukanku ne ajalin ya kama akanku alokacin, ace bare ne wanda yasaku kuka hau titin, bazanso ya zargi kansa ba har tsawan wannan lokacin bare kai dana, Hassan babban abinda yafi damuna shekarun daka diba kana zargin kanka."
Sageer ya riko hannun Hassan rungume juna sukai a tare suka saki kuka, Abba ya kallesu sannan ya kalli Ummy.
Murmushi tamai tare da jinjina kanta alamar hakan yayi.
Jalila kam na kwance a cinyarta tana share kwalla, a yaushe Hassan ya zama haka a rayuwarta????
**********
"Wai zaliha wacce irin rayuwa kika saka kankine? nifa nace ki kwantar da hankalinki, sai Taura yadawo hannunki, kima bar damuwa darashin d'aga wayarki dayakeyi. nifa nama fara zargin kodai wayar tasace tafad'i? Dan nasan aikinmu ba k'aramin aiki bane dazai bar jikinsa dawuri haka""To amma Anty idan kince wayarsa fad'uwa tayi miyasa har yanzu bai sake zuwaba? tunfa daga d'aga wayar wannan d'annan nasa shikenan ba labarinsa, Dan ALLAH kibarni naje gidan nasa kamar yanda nafad'a miki tun farko"
"amma dai Zaliha bakida hankali ko? shin kin manta sharad'in aikin nan ne? Sannan da kankifa kika sanarmin bak'ak'en maganganun da d'ansa yamiki awaya, ko an fad'a miki Na daina sonkine dazan bari a illata minke abanza? kodai sake shawara amma ba wannanba".
"To Anty yazanyi?"
Lakwai abinda zamuyi kuwa, kibani nanda kwana uku, zanyi tunanin mafita"
"Shikenan Antyna, shiyyasa nake matuk'ar k'aunarki wlhy" ta kwanta akan cinyarta.
Murmushi Anty tayi, batace komaiba ta shafa kanta, Dan halinsu d'aya babu wani banbanci.
***********
Tun bayan fitarsu Abba Jalila ta duk'ar dakai tana murmushin jin dad'in kalaman Abba, ga fuskar Yaya tanuna shima yasamu nutsuwa yanzun.
Kad'an tad'ago idonta tasaci kallonsa, saitaga Ashe shima d'in ita yake kallo, murmushi takumayi tareda kauda kanta gefe.
Muryarsa can k'asa yace taji yace "Jalilah!"
Kasa d'agowa tayi ta kalleshi, amma ta amsa da "na'am".
Shirune yaratsa d'akin Jalilah tana wasa da yatsun hannunta, shikam Hassan idonsa k'yam akanta, ko k'yaftawa bayayi, jinsa yake tamkar wani sabon mutum, bayanin Abba yasaka zuciyarsa ta k'ara bud'ewa, dan Abba ya dade da shi bayan su Ummy sun fita yana kara nusar dashi da nunamai ba laifinsa bane, zuciyarsa ta kuma rage nauyi sosai, wata nutsuwa ta musamman ke ratsa dukkan sassan jikinsa, harma yana tuhumar kansa miyasa bai fad'ama su Abba gaskiya ba a duk tsawon shekarunan? miyasa yasaka ummynsa mai sonsa da da k'aunarsa aciki k'uncin damuwa har wannan shekarun, tabbas ya yarda *JALILAH!* alkairice a rayuwarsa, Dan itace ta bashi k'arfin gwiwar canja komai, yafirzo k'aramar iska daga hancinsa...
Jin yayi shiru sai Jalilah takuma d'ago idonta, karaf suka kalli juna itadashi, tafin hannunta tasa tarufe fusakar tana k'aramar dariya.
Shikuma ya lumshe idanunsa yana gyara zama.
Tashi tayi zata barmasa d'akin yai saurin rik'o hannunta dukda jikinsa babu k'arfi sosai.
Gabamta yad'an fad'i tana jira taji ya janyota amma sai taji shiru.
"Dawo ki zauna to, magana zamuyi".
Rintse ido tayi, kusan 1minute sannan tadawo ta zauna, shima zamansa yagyara sosai yadawo kusada ita....
Jalilah!
Kallansa tai yanda yake kallanta yasa tai saurin sauke idanunta, gani tai kawai ya koma ya kwanta akan cinyarta, ya juyo da fuskarta saitinta.
Kallansa tai tare da zaro ido, yace " dazu ba haka kika min ba? Na tabbatar dana bude idona a haka na gani." Ya fada tare da sa hannunta akansa.
Kallansa tai tare dayin murmushi tace "tunda ka gani menene na sake gwadawa?"
Yace "abinda kika fada nakesan ki maimaita."
Ta dan juya kai tace "ni namanta ma me nace."
Murmushi taga yayi, ta zubamai ido batasan a fili ta fada ba sai jitai yace " haba? Kinasan kiga ina murmushi?"
Da sauri ta kalleshi ashe datace murmushi na masa kyau a fili ta fada.
Kallanta yai yace "badai kina kara sona bane inkika ga ina murmushi?"
Da sauri ta kalleshi tace "naam?"
Yace "me? Bakya sona?"
Bakinta na rawa tace "ni bance ba."
Ya kara gyara kwanciyarsa yace "basai kin fada ba kukan da kikai ya bayyana min."
Kallansa tai da sauri, da gaske? Abinda zuciyarta ke tambayarta kenan......
***********
"Ya kukayi da mijin naki?".
Innace mai maganar tana tattara wasu takardu waje d'aya.
Momy tace, " ya amince inna, k'ilama zuwa gobe yaje ya dawo da ita".
"Humm, Ku azatonku zata dawo cikin sauk'i? kokuwa ita Jalilan kuna tunanin zata amince cikin sauri?".
"To amma inna kinsan da hakan miyasa kikace yaje d'in?".
"Kallonta inna tayi da k'yau, kafin tasaki guntun murmushi "Shi dai yaro yarone, aii sometimes bana banbance tunaninki dana Safeenah dama kisamin ido kiga inda na dosa, tunda ke kullum naki hasashen daban, ke ba komai a gabanki sai wannan mijin naki da ba abinda zai tsinana miki."
Tabe fuska Momy tayi, "to nidai Dan ALLAH koma miye dai kika shirya banason yataba mutuncin Abakar, dan nikam bazan dauka ba."
Sosai inna ta kalleta kafin tace, "bazai ta6aba, tashi kije 'yar gatan miji".
Kuma had'e fuska Momy tayi, kafin tatashi, tasan bak'ar maganace inna ta fad'a mata, itakam koma miza'ayi saidai ayi, bazata bari a wulak'anta mata mijiba ehe.
[12/7, 10:10 PM] El-hajj: *_=???JALILAH!!=???_*

Written By : *AYUSHER MUHD*
'ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_=ء?)
2pages

*58*

Alhamdulillah zuwa yanzu nutsuwa tazoma hassan, dan a kwanakin nan ko kad'an ciwonsa baya tashi.

Abba da Ummy sunma rasa wani irin farin ciki zasuyi, ga wata k'aunar jalilah dasukeji har cikin jininsu, yarinyar tazamarma zuri'arsu alkairi.

Ummy ta kalli Abbah dake zaune yana kallon labarai, fuskarta d'aukeda murmushi tace, "wlhy bansan wane irin alkairi zamu yima yarinyar nanba mu nuna mata jin dad'inmu akan sauyin rayuwa data kawo a duniyar Hassan".

Kallonta Abba yayi shima yana d'an murmushin, kafin ya maida kansa ga TV "gaskiyane, yarinyar ta cancanci kowanne irin alkairi, Dan ko'a mafarkina bantaba kawo zamu sami wani cigaba ba akan ciwon Hassan, dubi dai irin shekarun damuka d'auka muna famar bin likitoci na kasar nan da kuma na ketare, sosai nake jin dadi da alfahari da auran yarinyar nan."

"Ta cancanci a k'aunaceta kam....."

Maganar Ummy ta katse saboda jin wayarta na ringing .., daga ita har Abba wayar suka kalla, cikin damuwa Abba yace "ina ganin kawai acire layinnan, idan takira taji baya aiki ai dole ta hak'ura ko?"

"Ba cirewa nak'iba, muhimman mutane dake da number d'inne damuwa ta kuma kaga aii suna kira ai, amma kai yakakeji yanzu gameda ita? dan Allah zuciyarka kadai zaka duba karka damu dani ko su Hassan."

Shiru yai yana kallanta kafin yai mata murmushi ya kamo hannunta yace "Hummm....Alhmdulillah, dan kaso mafi yawa yaragu, yanzu sai lokaci-lokaci ma nake tunota, sabanin da danakejinta har raina, lalai ba shakka na tabbatar yanzu wani abun sukamin, sai dai Allah ya rabamu da sharrin mutane ni........

Ummy ta kalleshi tare dayin yar dariya kadan tace
"miye nak'in k'arasawar to?"

Shima Abba yar dariyar yayi "Ummyn Hassan, yanzu da Hassan zai yajini ai sai an samu wata yar karamar matsala, shi da bai had'a damuwar ummynsa data kowaba."

Ummy tai murmushi tace "Kaima kasan Hassan tun yana yaro haka yake, zan iya ajiye Husain nadan shiga ko toilet amma shi yana tsaye a kofa yana jirana, ko ina zani yana biye dani, sannan kaima kasan yanda Hassan ke tsananin kaunarka, na tabbatar abinda yake zargin ya aikata shine dalilin dayasa yake neman janyeka daga jikinsa saboda in kasani kar abin ya wahalar dakai."

Murmushi ya mata shima sannan ya saki hannunta yace "na sani, sannan ko da wasa ni ban dauki abinda yakemin a matsayin haka ba, tunda ni nasan yanda ya damu dani, tsautsayine dai da kaddarar data afka mai, Allah ne kadai yasan yaro dan shekara goma sha ya yai rayuwarsa a wannan dakin...."

Ummy tai shiru cikin tausayi tace "sai nakeji duk laifin nawa ne, kamar nice ban kula dasu yand......"

Kallan daya mata ne yasa tai shiru.......

Yace "mu ma wadanda suka rasu addu'a mu kuma mu nemi cikawa da imani."

Tace "hakane Allah ya jikansu da rahama, amma zaka fadawa mahaifin Sudais ne?"
Yace "su da basa kasar? Sai dai insun dawo mayi maganar."

Nan ta jinjina kai tare da kara maidakai kan Tv din da yake kallo.

*********

Bayan sun kammala had'a breakfast Ummy tabar Jalila ta karasa sauran dan dama haka suka saba, tana cikin shirya abincin a dinning Sageer ya fito, sotake yau Hassan yafito ayi breakfast d'in dashi, shiyyasa bata d'iba musuba, ta shirya komai a kan dining.

Tsayawa yai yana kallanta yana jin dadin yanda ta canza musu gida, dan da a koda yaushe matsalar Hassan sai ta maida gidan kamar ba kowa, amma yanzu kam Alhamdulila.

Ji tai ance Jalila!"
Juyowa tai ta kalleshi tace "Un.... Ya Sageer ina kwana?"

Murmushi yai sannan yace "Jalila mungode, mungode sosai da farincikin dakika kawoma family dinnan wannan shine abinda naso ki fahimta a waccan ranar, Yaya shine yafi cancanta da samun irinki, amma dan ALLAH ki gafarceni, da. nakula har yanzu kinkasa sakin jiki dani a gidanan, bansan ko har yanzu kina fushi daniba, ni kanin Yaya ne haka kawai zakisa a ranki kinga........."

'Dagowa tai ta kallonshi, wannan yasakashi yin shiru batareda ya k'arasa maganar bakinsaba, ta gyara tsayuwarta tana kallonsa sosai, idon????      

                  ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ? ta ya fara tara hawaye tace "Yaya sageer nafad'a maka tuni komai ya wuce agareni, kuma zuwa yanzu na fahimceka, bani yakamata ka godemawaba, kaine ka cancanci a godema, domin ka sadaukar da farincikin ka saboda d'an uwanka, samun irinka a wannan rayuwar sai an tona, kazama mai rama alkairi da halacci, ta share kwallar data zubo mata akan kumatunta sannan tacigaba
"Ya Sageer ka cancanci kowanne irin godiya, amma kayi hak'uri da rashin sakin jikina agareka, nasan ahankali komai zai zama labari insha Allah, kaima Allah na tabbatar bai manta dakai ba zai baka mace tagari wacce tafini komai sannan mai sanka da k'aunarka".

Kallanta yai tare da sakin murmushi wanda har hakoransa suka fito yace "nagode Jalilah, sannan dan Allah ina rok'on wata alfarma agareki".

Kallansa ta sakeyi tace "ina jinka, Allah yasa bai fi karfina ba."

Sageer ya kalleta yace "Jalilah inason koda wasa kar dan Allah kar wanda yasan wata alak'a tataba shiga tsakaninmu, sannan dan Allah ki kuma nika kulawar dakikema Yaya akan tada, kullum burina yadawo normal mutum kamar kowa, inga yana farinciki, yana shiga jama'a, yana mu'amullah acikin mutane kamar kowa."

Kanta ta gyad'a a kunyace, tace "Allah ya bani iko Ya Sageer, zanyi iya k'ok'arina kai ma sai kai naka, har cikin rains ina tsananin tausayin halin da Yaya yake ciki nima, dan babu abinda yakai k'untatar zuciya a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login