Showing 144001 words to 147000 words out of 149705 words

Chapter 49 - Jalilah Book One Complete Hausa.doc

Ayusher   

28 Oct 2025

622

Hassan ya cigaba da kallansa, Dady ya riko hannunsa yace "Hassan ka taimakeni, wallahi yanzu inda zansa hakarkari na ma bani dashi, Hassan kai mijin 'yatane kantaimaka ka bani ko gida ne inda zan zauna."

Hassan ya bishi da kallo yace "in baka gida? Nidin cema akai gidajen rabarwa gareni?"

Dady yace "nasan na batama dayawa nayima abubuwa kala kala nasan ma gaba daya rayuwata bana kyautawa, sai dai na tuba ka duba ka taimakeni."

Hassan ya zare hannunsa daga nashi yace " da kai a tunaninka hakkin mutanen daka take ka gakesu ne a banza? Ko ka dauka duk abinda kai Allah bazai hukuntaka ba?"

Dady baki na rawa yace "nasan ban kyauta ba."

Hassan yace "zanshiga bacci nakeji dan inada abinyi gobe, harya juya sai kuma ya juyo yasa hannu a aljihu ya zaro wallet dinsa dubu biyar ne a ciki, ya zara ya mikamai, Dady ya amsa satoto yana kallansa, kafin ya tattara abin fada har Hassan ya shige ciki.

? Daki ya shiga, ya kwanta kusa da Jalila tare da sa hannu akan fuskarta a hankali yace "am sry Jalila, sai dai ina tunanin barin duniya ta dan gara mahaifinki shine zaisa yasan rayuwa yasan kuma abinda ya aikata bamai kyau bane, kiyi hakuri zan daukeki ba tare da kinsan halin da yake ciki ba, duk lokacin da kika sani zan nemi yafiyarki akan kin taimaka masa danai."

A hankali ya sumbaci bakinta sannan ya kwanta yana kallanta.


********

Dady kam kasa motsawa yai daga kofar gidan, yana tsaye satoto ruke da kudi a hannu, sai dayaji sanyi na busashi sosai sannan ya koma mota ya ja yai gaba gaba daya kansa ya kulle.

Sukam su Jalila washegari suka shirya tsaf, Ummy ta biya itada Abba, Mamman na jansu suka je suka dauko Goggo suka tafi airport.

Sageer kuma da Ameera a gaba Hassan da Jalila a baya, Hassan nata tsokanar Sageer akan budurwarsa, Hassan yace "in bikin yazo ma zo muyi sati daya."

Sageer yace "indai sati ne banaso."

Hassan yana dariya yace "to kwana 10."

Jalila tace "a'a sati biyu dai ya kamata."

Sageer yace "yauwa matar yaya kaga inda ake min kara."

Ameera tasa dariya tace "Gaskiya yaya sati biyu dai."

Ya kalleta yace "wai ni ina Aina'u ne? Sam ta buya"

Ameera tace "Yaya kaida ka gujeta?"

Yace "ba gujeta kamar ya?"

Ta juyo tace "badai yaya bakasani na?"

Jalila ya kalla wacce itama kallansa take, da sauri yasa hannu ya buge kan Ameera yace "to yanzu waya kawo wannan zancen daga tambayarta?"

Ameera tasa dariya tace "Ai naji haushi me makin yaya Sageer ya dan yi mata hucce shine shima ya nemo a waje."

Sageer yace "wa? Ni?"

Haka sukaita zolaya har suka isa airport.

Jalila kam abin kamar mafarki haka take ganninshi wai yau itace zata hau jirgi zuwa wata kasar, abinda takeji a labari.

Goggo ma tayi shiru tana tunanin rayuwa, suna tsaye ne sai ga wani yazo ta gaban Abba, Abba ya kalleshi sannan ya mika mai hannu tare da sakin fuska. Yace "Ghali?"

Wanda ya kira da Ghali ta washe baki yace "kasan tundaga nesa nake kallanka ina zargin ko ba kai bane."

Ghali ya kalli Ummy yace "Hajiya shekaru masu yawa."

Ta kalli Abba tace "wai Dr Ghali naka?"

Yace "nine Hajiya."

Ya kalli Hassan da Sagir yace "'yan biyun ne?"

Ummy tace "eh, ikon Allah."

Ta kalli Hassan tace "kaga wanda yai treating din Yaya (mahaifiyar Hassan) kafin ta rasu."

Hassan ya gaisheshi, su sageer suma suka gaisheshi, Goggo ce ta gaisheshi itama, ya kalleta yace "ka kara aureni?"

Yace "a'a mahaifiyar matar dana ce."

Yace Allah sarki, sun danyi hira kafin sudan ware gefe suna kara tattaunawa, Su Hassan da Jalila kuma suka shiga ciki inda zasu kai kayansu.

Ghali ya kalli inda Goggo take yace "Diabetes's n da ita?"

Abba yace "wa? Ya fada yana kallan gun, ganin Goggo yasa yace "eh wallahi."

Ghali yace "ayya da hawan jini kuma kenan?"

Abba yace "gaskiya ne likita."

Dariya yai kafin Dady yace "ya matarka? Da yaranka?"

Yace "mai dakina Allah ya mata rasuwa shekara biyu da suka wuce yarana kuma sunata karatu, yanzu ma babban ne zai koma makaranta a saudia yakeyi."



Abba yace "Wayyo Allah ya jikanta banji ba ai."

Sannan ya cigaba "Allah ya taimaka kace shi acan yake?

Yace wallahi.
Abba yace "....Ah to ko zaka kula da patient?"

Ghali yasa dariya dan ya gane sannan yace "batada aurene?"

Abba yace "tanadashi kuma batadashi."

Cikin mamaki yace "kamar ya?"

Abba yace zan baka labari inmunje gida, dan su Hassan na tafiya gidana zaka musha hira, itama can zata kaga sai ka kara ganinta dakyau."

Ghali yai dariya.

Idanun Jalila gaba daya sun canza, ganin sun fito yin sallama zasu shiga ciki, tana zuwa ta rungume Ummy kawai tasa kuka, Ummy ma idanunta duk suka ciciko, ta shiga shafa bayanta alamar lalashi, Jalila ta dago ta dawo gun Goggo ta rungumeta taba kuka, Goggo kam sai da hawaye suka zubo mata, ta sharesu tare da yi mata addu'a, shikam Hassan yana tsaye gun Abba da Sageer suna magana, kafin Goggo ta dagota tace
"Jalila akara hakuri, karkice akoda yaushe dan mijinki nasanki zan dinga miki duk abinda kikeso, karkizama mai takura masa akan sankanki, sannan ki dinga jin maganar sa, yanzu shine uba, aboki sannan mijinki, kiyi kokafi kyautata masa akoda yaushe."

Jalila ta daga kai tana hawaye, Goggo ta kalli Hassan wanda kentsaye yana jinsu tace "Hassan ga Jalila nan, kawai abinda zance kenan."

Ya kalleta tare da yin murmushi yace "nagane Goggo insha Allah bazan sata kuka mai yawa ba."

Ummy ta makamai harara tace "zaka sata kenan kake cewa?"

Yai dariya yace "eh amma kadan dan haka..." ya fada yana nuna dan karamin yatsansa.

Goggo tai dariya tace "nayarda Hassan."

Jalila ta kalleta sannan ta kalli Ummy tace "Ummy kinjisu?"


Ummy tace "karki damu yana samin ke kuka zanzo in daukeki."

Dariya sukai su dukansu, nan sukama Abba sallama, idanun Jalila ne suka fara neman kara cikowa.

Hassan ya kamo hannunta, da sauri ta kalleshi, yace "in bakyasan na rikike wallahi ki hadiye hawayen nan."

Da sauri ta zare hannunta tare da kokarin hadiye kukanta.

Ya guntse dariyarsa,nan suka karayin sallama da Abba suka wuce ciki.

(Nace a sauka lafiya=?J?)


***********

Ghali ne ya kalli Abba yace "inalilahi, ita kuma haka tata kaddarar take?lalai taga bakincikin rayuwa."

Abba yace "ai abin ba'a cewa komai."

Fuskarsa ya shafa sannan yace "amma wannan kwai dan iska, menene laifina dazai wulakantaa haka? Mace kamar ta haka?"

Abba yai shiru cikin takaici.

Yace "to ya shi ya saketa ne?"

Abba ya kalleshi yana dariya yace "kana so ne?"

Yace "naga kai kace in kula da patient ya kake neman canza shawara?"

Abba yai dariya yace "kabar komai a hanuna ni kaina babban burinane maga matarnan na cikin farinciki."

Haka sukai ta hirar Goggo har dare yaja, Ghali yace zai wuce gida.

*********


? Zaune yake a kofar gidan sanyi sai ratsashi yakeyi, yanata kiran number Jalila bata shiga, sanyi sai kara kadashi yakeyi ga azabar yunwa dake damunsa, tun safiyar jiya har yau bai ci abinci ba, hasken daya dalleshi ne yasa ya rufe fuskarsa, tsayar da motar yai maimakon ya shiga gidan, ya fito sannan ya kunna fitilar wayarsa yana? haska shi.

? Dady ya mike da sauri yana neman yin gaba.

Abakar? Abinda ya fada kenan, gaban Dady ya fadi dan yanzu ya gane Abba ne, kasa juyowa yai saboda tsananin kunyar yanda kayan jikinsa da yanda duk ya canza yake.

Abba da sauri ya karaso ya jawoshi, Dady ya juyo tare da yake baki yace "Taura!"

Abba cikin tsananin mamaki yake kallansa yace "menene hakan?"
Ya fada yana kallan jikinsa, Dady ya dan zare hannunsa yace "bakomai."

Abba yace "daga ina kake haka?"

"Daga ina ma zance? Dama zuwa nai ko zanga Jalila inata kiranta bansameta ba."

Abba yace "Jalila ai bata kasar ita da mijinta."
? Da sauri Dady ya kalleshi yace "batanan?"

"Suna Kuwait, amma kai meya faru naganka haka? Kwanaki inata nemanka har gidanka naje akacr kum tashi."

Yai shiru yana kallan Abba, Abba yace "Abakar?"

Dady ya kalleshi, idanunsa suka canza yace "dama inasan ganin Jalila ne ta bani dan wasu kudi wanda zan koma kauyen mu dan na gaji da kwana a masallaci ko karkashin gada."

Abba cikin mamaki yace "bangane ba?"

Nan Dady ya sanar dashi abinda ke faruwa, Abba yai shiru yana kallansa kafin yace "Abakar kaga yanda rayuwa take ko? Shiyasa akesan mutum yayi dakyau, yanzu gashinan bakada wani wanda zaka nemi taimako agunsa, bakada wanda zai ji tausayinka, kanada 'ya'ya amma ka banzatar dasu, y????? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? ? 
anzu meka mora a duniyar nan?"

Dady cikin raunaniyar murya yace "nikam ai banga wani abun dana mora ba...." hawaye suka zobo masa yai saurin gogewa.

Abba ya kalleshi yace "menene matsayin mahaifiyar Jalila a gurinka?"

Kallan Abba yai yace " nikaina ban sani ba."

Abba yamai wani kallo yace "kai kana tunanin da hakkin ta kadai ma zai barka? Ka saketa ne ko me?"

Dady yace "nikaina bansan halin kaina ba, amma ni tun farko ban dauketa a matsayin mata ba."

Abba ya runtsr ido cikin wani irin kunar rai yace "yanzu ba aurenta kenan a kanka?"

Dady da sauri ya kalli Abba, yace "ko akwai?"
Dady yace "bangane nufinka bane."

Abba yace "in ba auranka akanta ka bata takardarta ta nemi miji ta aura, saboda wannan abinda kake yi ba karamar tauye mata hakkin rayuwa kakeyi ba, ayanzu ma danaji baka dauketa a matsayin mata ba, in na sanar da ita auranku ya rabu sai dai nafisan ka rubuta saboda abinda zai iya faruwa nan gaba."

? Dady yace "amma ni.:......."

Abba ya katseshi "akwai sauran cin zarafi ne dakake kokarin yi mata?"

Dady yai shiru yana tuno irin wulakancin dayama Goggo, Abba yace "akwai mai santa inhar kanaso wani ya gyara abinda ka bata sai ka rubuta min yanzu ka bani."

Dady ya kara goge kwallar data zubomai sannan yace "to zan rubuta yanzu, dan na tabbatarban camcanci zama mijinta ba."

Abba ya wuce mota Dady ya biyoshi, paper ya dauko da biro ya mikamai, Dady ya rubuta saki daya yaba Abba.

Gaba daya sai ya kara ba Abba tausayi, Abba ya koma cikin mota yana tunanin ya taimaka mai ne? Sai dai in ya tuno abubuwa marasa kyau da Dady ya aikata sai yaji inaa bazai iya ba gwara ya kara sanin duniya ta garashi tukunna, wallet dinsa ya dauko ya duba ciki, dubu takwas ne a ciki, yasa hannu a aljihunsa yaji dubu biyu ya mikamai yace "gashi kai kudin mota sannan ka nemi na abinci."

Dady ya fara godiya, Abba ya shige ciki da sauri.

Yana parking ya fito jiki a sanyaye..........


#OneLove=ؕ?[1/11, 10:17 PM] El-hajj: =??? *JALILAH* =???


Written By : *AYUSHER MUHD*
Wattpad: *Ayusher Muhd*

>?p?>?p?


*80*


*************

Bayan wata takwas.

Jalila ce ta turo kofar falon, tana shigowa ta zube a kasan carpet din falon ta kwanta.

Hassan na kitchen yana jinta ya fito falo yana cewa "Hajiya an dawo?"

Harararsa tai tace "wallahi daga yanzu na daina yarda da wannan wayan ace wai ni kadai xan dinga zuwa siyayya."

Kusa da inda take kwance yazo ya kwanta shima yace "kefa kikace ayi game, wanda ya zabi zuwa siyayya shizai dinga zuwa cefani."
Tace "amma ai wayau kamin, kasan wanda ka rubuta hakan, tunda kana dauka ka zabi abinda kake so."

Juyowa yai ya kalleta tare da jawota kafadarsa yace "baby ba wayau, ya zakiyi? Tunda kin zaba ai ba yanda zakiyi."

Ta turo baki tace "ni gaskiya a sake."

Yace "inaaa ban yarda ba."

Tace "Allah ga yunwa, na dawo daga makaranta ansani wucewa cefani."
Ya dan bubugata alamar lalashi yace "karki damu wannan ur Hubby ya shirya miki sai dai kawai kici."
Da sauri ta kalleshi tace "Allah?"

Ya mike yana daga mata gira alamar yes, da sauri ta bishi kitchen ta bude tukunya tana murna, hade ran datai ta juyo ta kalleshi ne yasashi yin dariya yace "Surprise!"

Kallan Indomien dake cikin tukunyar tai tace "Yaya Allah ni nagaji dacin indomie."

Yace "ah haba? Ta kalleshi tace "nisaidai kamin dan wake."

Dan wake? Tayaya akeyi? Badani ba."

Tace "Allah yau inbanci ba banaji zan iya bacci."

Yace"baban magana, sai ki dafa mana muci."

Nanta shigayindan wake, sai dai tana gamawa sunzo ci ta kasa, da sauri ta mike tai toilet ta shiga kela amai, Hassan cikin mamaki ya kalleta tare da dafa goshinga yace "Baby stress ne ya miki yawa? "

Ta kalleshi tace "bakai bane ka sani?"

Mikar da ita yai yace "muje gari ki duba wani abin kichi."

Ta kalleshi kamar zatai magana sannan sai yaga kuma ta tsaya, yace "ya akai?"

Kallansa tai tace "Yaya yaushe rabon nai period?"

Yace "period? Na manta, badai shi bane? Ahh nikam gaskiya....."

Yanda yaga tana irge da hannunta ne yasa ya kalleta yace "oh gaskiyarki fa kin dade bakiyi ba."

Ta kalleshi tare da saurin rikimai hannu tace "muna ta fama da skul ga murnar zani nigeria bikin Ya Sageer next month inaji shiyasa sam ban kula ba."

Yace "da matsala ne?"

Tace "a'a sai dai inaji......"
Sai kuma tai shiru, yace "me?"
Ta kalleshi ta nunamai yatsa guda biyu, yace "baby?"

Tace "maybe."

Da sauri ya sureta sama yana wani irin farinciki, Jalila ta hade rai tace "yaya murna ma kakeyi? Karatu na fa?"

Ya sauketa yace "menene aciki? Sai muje mu taho da ko Amira tunda ta gama secondary tazo ta zauna mana."

Ta kalleshi cikin gamsuwa tace "amma saifa munje anyi test karka sa rai dayawa."

Hannunta ya rike kawai yanata tsalle kamar wani yaro, dariya kawai ya shiga bata.....


************

Yanda aketa shirye shirye a gidan ne zai kayatar dakai, Goggo da Ummy na kitchen suna ta shirya abinci kala kala, Ameera da Aina'u suna gefe suna aiki suma, Goggo ta kalli Ummy tace "Oh na tabbatar jiya Jalila batai bacci ba."

Ummy tai dariya tace "inafa zatai zata zo taga na gida, malam Hassan dai na tabbatar ya shari baccinsa."

Goggo tai dariya, Ummy ta kalleta tace "Dr dai yau zai bar mana ke ki kwana ko?"

Goggo tai dariya tace " bazan bar Nabila da Muftahu ba a gidan, shima cemin yai in kwanab amma nikam badani za'ai wannan abin kunyar ba, anjiman nan zan koma, suna zuwa zamu tafi."

Ummy tai dariya tace "ya labarin su Mumy kuwa?"

Goggo tace "suna nan, ai kun gama musu komai, tunda kukace su dawo gidan danake ciki inyaso su sa dayan haya."

Ummy tai murmushi tace "kinsan da ke naso a dinga ba ma rabin kudin hayar dazasu dinga samu, sai dai ke yanzu kinyi gaba, tunda Allah ya dagaki."
Goggo tai murmushi tare da cewa "Ummy Dr ba karamin kyautatamin yakeyi ba, 'ya'yansa ma basida hayaniya, sai godiyar Allah, duk abinda nakeso kafin ma in nema yamin, sannan kinga akwai gidansa na haya da ya barmin, mezan nema nikuwa yanzu a duniyarnan, inba kuma san zuciya nake neman bi ba?"
Ummy ta jinjina kai tace "Alhamdulila ala kulli hal, hakurinki me ya biya miki, Allah ya dubi zuciyarki ne."

Goggo tai dariya sannan tace "Ai duk haduwata da ku shine ya ja min haka, daga ni har Jalila,/ shiyasa akoda yaushe nake gode ma Allah daya hadanu daku."

A tare sukai murmushi.

Lantana ce ta shigo da kaya da sauri ta ajiye tamatso gun Goggo tace "Goggo gashi, kiranki akai."

Goggo ta amsa tare da fitowa daga kitchen din dan tasan Dr ne.


*************

? Juye yake akan gado yana ta zuba waya sam bai kula yazo karshen gadon ba, Maimuna tace "nikam kunya nake ji."

Yace "Kunya ko? Ki jira......."

Dim ya tiko daga kan gadon, Maimuna tasa dariya, yace "wayyo Allah na." Dan kam Sageer yaji zafin faduwar, budar kofar Ameera tai dauke da kayan guga, kallansa tai a kasa yana shoshe soshe, dariya ta saka ganin alamar waya yakeyi tace "Yaya anji jiki, ka fito za'a tafi airport."

Ta ajiye kayan ta fita.


******^^^*

Ya dage sosai yanata wanke dakin, sai daya gama tass ya fita sosai sannan ya maida katifar ya shifida ya zauna akai tare dasa kansa a cikin cinyoyinsa yana tunanin rayuwa, tunda ya dawo kauyen nasu mahaifinsa ke kwance ba lafiya, haka ya shiga jinyarsa, baya iya komai sannan komai a kwance yakeyi, haka yai ta kula dashi har Allah ya dau ransa a daren jiya.

? Gaba daya rayuwa tamai zafi, yai shiru yanzu shikam baisan ina zai nufa ba dan yan uwansa duk ba wanda yake sanshi, kowa kyararsa yakeyi, yau ya samu ma su barshi ya zauna a waje gun amsar gaisuwa sun hana sun koroshi ciki.

Jakarsa ya dauka dan baiga amfani zamansa ba, dan dama sun sanar dashi mai tarar mai fada wato mahaifinsu ya rasu ya tattara nasa ya nasa ya bar musu gida.

? Haka ya fito yana neman zama a tabirmar yayansa yasa kafa agun yace "malam kama gabanka."

Dady ya fito daga kauyen gaba daya abin duniya ya dameshi, balle waccen watan daya wuce yana garin Goggo tazo itada mijinta, haka tazo da kaya kala kala taita rabawa, yanaji zatazo gidansu yabar gidan, haka ta kawo kaya dayawa, haka ya tsaya ta bayan gari yana lekensu.

(Ranar kam ko ni sai da dady yaban tausayi.....lol)


? ***********


Gida ya cika sosai anata hira da dariya abin gwanin ban sha'awa kana ganinsu kaga mutanen dake cikin farinciki.

Jalila na kankame da Goggonta, Ummy ta kalli Hassan yace "nikam Hassan sai naga Jalila ta rame, ko Goggo?"

Goggo ta kalleta tace "bangani ba nikam."

Hassan yai dariya yace "wato Ummy so kike kice banaba 'yarki abinci ko?"

Ummy ta kalli Jalila tace "Jalila? Anya ana kila dake kuwa?"

Jalila tai dariya tana kallan Hassan, yana kallanta yace "da alama zuciya zatai kafin Sageer yai aure tana so ta maidani babba saboda kar a rainani."

? Ummy tace "babba? Oh Hassan kaikam dai......"

Sai kuma ta tsaya tare da kallansa da sauri tace "Jalila ciki ne da ita?"

Da sauri Jalila ta kalleshi tana mai alamar yai shoru.

Ya kalli Abba yace "Abba ya ka gani na kusa zama baba fa."

? Nan fa murna ta karu, Sageer yace "gaskiya ne yaya."

Hassan yai dariya yace "ya? A ina zaka zaunane?"

Yace kasan layin nan, muka samu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login