Showing 105001 words to 108000 words out of 149705 words

Chapter 36 - Jalilah Book One Complete Hausa.doc

Ayusher   

28 Oct 2025

618

rayuwa, mutum bacin ran yini d'aya yashiga ya yake tsintar kansa, bare tsawon shekaru irin haka"

"Gaskiyane, mucigaba damasa addu'a, inaji ajikina zaki sauya komai insha Allah, nima kicigaba damin addu'a Allah yabani wadda zata tallafeni irin haka."

Tausayi yabama Jalila, dan haka takuma k'asa dakanta, karka damu Ya Sageer dan Allah kaima ka dawo yanda kake da mai walwala, dan Ummy ta bani labarin bahaka kakeba abaya, duk da bazata nunama ba na tabbatar abin na damunta."

Murmushi yai yana k'ok'arin barin wajen, "karki damu, zan canja insha Allahu."

"ALLAH yasa" itama tafad'a tana fara tafiya domin duba Hassan.

Da sauri Hassan yakoma baya dan karta hangoshi, tun farkon maganar tasu yana tsaye, amma basu ganshiba, saboda sun juya masa baya, yaje yana kokarin shiga falon yaji suna zancenshi, fuskarsa dauke da murmushi ya tsaya a bayan bango yana jikinsu, a hankali kunnensa ya dinga juyo mai hirarsu.

Yana zaune bakin gado Jalilah tashigo cikin d'akin da sallama.

Bai kalletaba amma ya amsa, da 'yar fara'arta takaraso inda yake tace "Laa Yaya ashe katashi? nifa wai hawowa nai na tasheka."

"Na tashi!"

Haka kawai yace ba tare da ya kalleta ba, kallon data masane yagane shima maganar tasa tafita da tsauri, amma saiya dake.

Jalilah batayi zuciya ba tace "Yaya mai zai hana yau kazo kaci abinci tareda Ummy da Abbah, kodan kakuma saka zukatansu cikin nutsuwa?"

Yanzu kam bashida zabi. daya wuce kallonta da kyau, yarasa wane irin mahaukacin so zuciyarsa takema Jalilah, baikamata yaji zafin maganganunsu da Sageer ba, musamman idan yai dubi da sadaukarwar dasukayi suduka agareshi, yadad'e yana mamakin yanda kokad'an Jalila bata sakewa da sageer dan Sageer mutum ne mai faran faran yasan sageer da saurin sabo da yawan barkwanci.

Ashe akwai abinda ke tsakaninsu, ya akayi haka ta faru? tayaya iyayensa suka aura masa budurwar k'aninsa? shin basu sani bane? Da wani ido zai kalli Sageer? Ace shi da yake babba bai barma kaninsa abu na sai shine kanin nasa zai barmai? kai amma yasan babu yanda za'ayi Abbah ya aura masa wadda yasan Sageer na nema amatsayin matar aure kuma, to meke faruwa.......?"

Girgiza hannunsa da jalilah tayine yakatse masa tunanin nashi.
Tace "Yaya lafiya kuwa?"

Baice komaiba, amma yamik'e tsaye, gani tai yanufi hanyar fita, sai da ya bud'e k'ofar sannan yajuyo ya kalleta yace "kona koma na zauna ne?"

Da Sauri tamik'e tana murmushi tace "a'a Yayah ina fa."
Karasowa tai kusa dashi a hankali tace "Nagode."

"Da akayi me fa?"

Yai maganar yana karasa fita daga dakin.

Ta biyoshi tace "daka amince."

"Hmm" kawai yace, yacigaba da tafiyarsa.

Suna sakkowa kuwa saiga Abba da Ummy suma sun fito.
Hassan ya karasa kusa dasu ya gaishesu, duk cikin fara'a suka amsa masa, Sageer ma dake zaune a falo yataso, gaishe da su Abba yafarayi, kafin ya gaida Hassan shima.

Cikin danne abinda ya tokare mak'oshinsa ya amsa, harda mik'ama Sageer d'in hannu tareda daga kafadarsa, a tare suka mike suka nufi cikin falon.

Ummy da Abba suka bisy da kalli cikin jin dadi, haka suka k'arasa kan dining suka zauna, Jalila ta shiga ajiye musu plate, kowa ka kalla fuskarsa a sake take.

Abba da Ummy kuwa cikin mamaki suke da kallon Hassan daya ja kujerar dining ya zauna, alamar yau taredasu zaiyi breakfast.

Cikeda jin dad'i Sageer yace "Yaya yau zakaci abinci damune?"

Kansa ya jinjinama Sageer din.

Gaba d'ayansu farincikin ya bayyana a fuskokinsu, Ummy harta kasa boyewa ta furta " Alhamdulillahi ala kulli halin".

Abba ma abinda yafad'a a zuciyarsa kenan.
Sageer kam harda d'an rungume Hassan saboda jin dad'i, Ummy tace "inama Auta tana gida yau taga abinda take buri a rayuwa?"

Jalila ai murmushi tace "Ameera yar makaranta."

Hassan ya juya yana kallon Jalilah da itama jin dad'in yasakata taketa murmushi, ganin yanda dukkansu suke farinciki, sai itama takema nata dangin irin wannan fatan wataran.

Kamar zaiyi magana saikuma yayi shiru.

Abba ne yalura da hakan, yace "Jalila taho mana ki zauna."

A kunyace ta matso zata ja kujerar kusa da Ummy, Ummy tace "Malama Jalila zauna kusa da mijinki, nima bakiga a kusa da nawa nake ba?"

Da saurin tai kasa da kanta saboda kunya, Ummy ta kalli Sageer tace "wanda yasan gauro ne sai yai sauri ya kawo tashi matar."

Sageer ya kalleta sannan ya kalli Abba cikin shagwaba yace "Abba kaji Ummy ko?"

Abba yace "gaskiya kar a sake cema d'ana gauro inba haka ba kuma yanzu nai zuciya namai aure."

Kallansa Sageer yai yace "aure?" Ya matsa daga gun Abba da sauri.

Tuntsirewa da dariya sukai yanda ya matsa din, Hassan ya kalleshi cikin wani yanayi da shikansa baisan wani iri bane.

Yaukam cikin far in ciki sukayi break d'in nan, dukda Hassan baya magana, kuma koda komai yafito fili dama har yanzu bawai yana yawan magana baneba, baikuma saki jiki dasuba gaba daya, amma abinda yazama dole yayi magana akansa yanayi.

Bayan sun gama Abbah yafita aiki cikin tsantsar farim ciki.

Suko duk a falo suka zauna suna hira, harda Hassan, dukda shikam ko k'ala bai ceba a zaman nashi, amma yana saurarensu, gaba daya hankalinsa nakan abinda yaji, kodai zuciyarsa ce take kara mai? Kodai ba wani abu tsakaninsu? Kallansu yai yana nazarin su, soyake yagano abinda ke faruwa? suna son juna har zuwa yanzu kokuwa? Su kuwa basusan dawan garinba, damage itama jalilan bawani baki take sakawa a hirarba, k'arfin hirar Sageer da Ummy ne, dan Sageer ya iya barkwanci, sai dai daga anyi abin dariya zata sa dariya.

Wajen karfe 12 Hassan ya mike ya hau sama, Ummy ta bishi da kalli cikin jin dadi.
Jalila ma bata dadeba ta mike tahau sama, a kwance taga shi kamar mai bacci.

Toilet ta shiga ta fito sannan ta kara kallansa, kamar bacci yake kamar kuma ba bacci yake ba, kamar tai magana sai kuma ta jona wayarta a charge kawai ta fito.

Sunkai tsawon lokaci suna hirar, har karfe biyu tai Ameera ta shigo.

Tana shigowa ta baje a falo wai ta gaji, Ummy tace tashi malama ki wuce kitchen.
har agogo yanuna 2, Ummy tace, "Ameera tashi kishiga kitchen, yau kece zakiyi abincin rana, kullum sai dai kici ki kwanta."

''Wayyo Ummy, nikad'ai zanyi?yanzu fa na dawo daga makaranta."

Ummy tace "to kedawa zakiyi? Tunma kafin rana tamiki kitashi kije ki d'ora, dan abbanku da wuri zai dawo yau, inya dawo baki gama ba kinga sai ki bashi amsa."

Ameera ta shagwabe tare da kwanciya akan kujera tace "Ummy wlh....."
Kallan da Ummy ta mata ne yasa tai shiru ta mike tsaye kamar zatai kuka.
"Karki damu, tashi muje natayaki kinji Ameera". Jalilah tayi maganar tana dafa hannun Ameera.

Cikin murna tace "yauwa matar yayana"

Hararta Ummy tayi "Jalila kiyi zamanki, taje tayi ita kad'ai, zauna ki huta".

Jalila tace "Ummy bangajiba aii, bara na tayata yanzun nan sai kiga mun gama."

Bata bari Ummy tasake maganaba taja hannun Ameera suka tafi kitchen da sauri.
Ummy tabisu da kallon sha'awa da tsantsar k'auna.

********

Tunda Abba yafito daga gida Zaliha kebin motarsa abaya abin da zai baka mamaki a ina tasan gidansa?tun jiya da yamma tashigo garin, a hotel ta kwana, yau kam da farar safiya tazo unguwar tasu take jiransa, guri tasamu tayi parking tana dakon fitowar Abba daga gida. tana hango an bud'e gate tafara addu'ar ALLAH yasa shine, ganinsa kuwa tasaki wata ajiyar zuciyar dan dad'i, haka taita binsu abaya har zuwa office.

Yana zama a kujera yayinda Secretary d'insa kemasa bayani akan wasu bak'i, dakuma wasu abubuwan da suka faru a jiya sukaji ana knocking d'in k'ofar.

Atare suka kalli k'ofar Abba yace, "munada bak'ine?".

Yace "a'a gaskiya Alhaji, amma bansaniba ko shigowarmu nan suka zo"

"OK, jeka gani to".

Yana bud'e mata, batajira komaiba taturo kai cikin office d'in tana yauk'i, sanye take cikin wani shegen leshi, daya gama had'uwa, ga d'inkin yayi mata k'yau sosai tamkar zata fashe saboda matsetan dayayi, takawo siririn gyale ta d'ora a kafad'a, bak'amar fad'uwar gaba Abbah yajiba azuciyarsa, saida ya had'a da addu'ar " Hasbinallahu wa ni'imal wakil".

Ganin haka Secretary din yafita, dan hannu zaliha tad'aga masa alamar yafita.

Yanda kasan gunki haka Abba ke zaune yana bin Zaliha da kallo, harta k'araso inda yake.

Mai makon ta zauna akan kujerar dake gaban desks din, saita zauna a saman desk d'in kawai tana juya idanu "haba myT! babu fad'a miya kawo gaba kuma?".

Yanda tayi maganar cikin matuk'ar salo, dole Abba ya tsirama labbanta dasukasha janbaki ido, bai iya cewa komaiba sai ajiyar zuciya ya sauke, jiyake kamar yajawota jikinsa, amma ya daure yana ambatar dukkan addu'ar datazo bakinsa, yana neman d'aukin ubangiji yafiddashi akan wannan masifa daya tsinci kansa aciki.

***********

#OneLuv=ؕ?
*_=???JALILAH!!=???_*

Written By : *AYUSHER MUHD*
'ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*

*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_=ء?)
Day

*59*

Ummy tabi Sageer da kallo, yanda ya ajiye waya da sauri yamik'e bayan yagama ansa kiran da'aka masa, sama yahau da sauri, Hassan na kwance ya shiga bai ko jira ya amsa sallamarsa ba, yasan Jalila na kasa.

Hassan na kwance yana tunanin abinda ke faruwa tsakanin Sageer da Jalila yaji shigowar mutum.

Sageer ya matso ya masa bayani, ai bai bi takan Sageer ba naga ya sauko da sauri ya dau key din mota ya fita "Ummy ina zuwa" abinda ya fada mata kenan a sanda ya ganta a zaune.

Kafin ta amsa masa yafice, tad'anji zanyi aranta, tunda yau ga Hassan zai fita harda fad'in yana zuwa, tamance shrkarun daya d'auka bai Sanar mata zai fitaba.

Sageer na saukowa yaga har ya ja motarsa ya fita, motarsa shima ya shiga yana tunani, ya bishi ne?

Can kawai yaja motar sa shima ya fita.

***********

"Alhajina kayi shiru, kobakayi murna da ganina baneba?".

Abba ya had'iyi yawu da k'yar, kafin yace, " bahaka baneba zaliha, kawai nayi mamaki. ganinkine, musamman idan anyi la'akari da safiyane, dolene kayi mamakin ganin Wanda yake Abuja a Kano a irin wannan lokacin".

Cikin salonta Na yaudara tace, "Alhajina kamanta da maganarnan ta Malam ba haushe dayace garin masoyi baya nisa........

.......baya nisa kam, balle idan kaci karo da ballagazar mace, wadda batasan muhimmancin dunk'ulalliyar zuri'a ba, narasa wane rukuni zan sakaki acikin jinsin d'an adam....."

Daga Abba har Zaliha a rikice suka juyo suna kallonsa.

Bakowa baneba face Hassan.

Yauce rana tafarko daya taba shigowa company d'in Abba ballema office d'insa, dukda yasan inda company d'in yake, amma yanzuma bisa jagorancin Sectary d'in Abba yazo, yanaji ajikinsa dama wataran sai zaliha tabiyo sawun Abba tunda batasamu yanda take soba.
Sai gashi kuwa, tunkafin ayi nisa saigata tazo d'in, hasashensa yazama gaskiya.

Bak'aramin tashin hankali Abba yashigaba, hakama Zaliha dake zaune, dan sarai tagane Hassan d'in, shine taga hotonsa a wayar Taura shida k'aninsa, tun ama hoton ta shaida wannan guy d'in bazaiyi mutunciba, balle tundaga waya dashi Taura ya dauke mata kafa.

Hassan yakatse mata tunani da fad'in "Bakiji gargad'in dana miki bane ko kuwa wanda na miki ne ya miki kadan?

Zaliha ta kalleshi idanunta suka firfito, a hankali ya fara takowa har inda take yace "zaki sauko daga inda kike zaune ko inzo in saukeki?"

Da sauri ta cire hannunta daga jikin Taura ta sauko daga kan desk din, wani kazamin kallo ya mata yace " fita fa? Zaki iyayi ko sai na jaki daga nan har waje?"

Kallan Taura tai tace "MyT?"

Taura ya kalleta ya dake yace "ke karki kara cemin wani urT agidan uban wa na zama naki?"

Juyowa tai jiki a sanyaye ta fara takowa, kusa dashi tazo ta tsaya tana kallansa, tare da dan girgiza kirjinta.

Tsaki yai yana kallanta yace "kina tunani wai kin cika mace a hakan?"

Tace "mene?"

Bai bata amsa ba yace "kinsan wani suna ake kiran mata irinku?"

Tace "mene?"

Nan ma bai bata amsa ba yace "kinsan a wani jere nake sa mata irinku?"

Haushi ya kamata tace "mene?"
Yace "Trash! Get out."

Idanunta ne suka firfito fuskarta ta nuna tsananin bacin rai ta kalleshi tace "mene?"

Yace "bakyajin turanci?"

Kallansa ta sakeyi cikin wani yanayi na tsananin bacin rai, cikin mumunan bacin rai ta fito.

A waje taga Sageer a tsaye a jikin kofa, kallansa tai yai dariya har tayi gaba yace "ke Trash kin manta jakarki."

Yafada tare da kallan jakarta dake kan desk.

Dawowa tai ko kunya ta dauka ta fita da sauri.

Sageer ya bita da kallon mugunta, ya kalli Hassan yace "kai Yaya baka zafafa ba?"

Hassan yace "kaima ka zafaffa ai wai ke Trash...."

Abba ne ya hade fuska yana kallansu yace " wato dai kune masu kula dani ko? Sai a fadamin wanene ma ya samar daku?"

Hassan ya kalli Sageer, da sauri Sageer ya juya kai yace "Abba na manta inada appointment" dariya suka saka a tare hardashi Abban, Abba yace "amma yanzu ai bazata sake dawowa ba ko? Sageer yace "inta dawoma tana da mai maganinta....

Suka kara yin dariya.....

Abba yace kuyi alwala muje masallaci sallar la'asar tare.

Hassan ya kalleshi, Abba yace "let us try kaji?"

Ya daga kai alamar to.

Haka suka yi alwala suka zauna a office din Abba macema Sageer ya daure ya fara aiki anan, Hassan na taya Abba har la'asar ta karasa, Abba ya kalli Hassan yace "muje?"

Atare suka fito su uku abin sha'awa, basuga motar Zaliha ba agun da alama ta bar gun.

Masallacin suka nufa, tsayawa yai yana kallan yanda mutane ke ta shiga ciki, ya kalli Abba.

Abba yasa hannu ya riko hannunsa sannan ya riko hannun Sageer yace "gamunan mu uku, ka cire komai a ranka kawai kasa a ranka gun bautawa Allah zaka, sannan gamu a kusa dakai."

Hassan yai murmushi suka nufi masallacin, daurewa kawai yake dan zuciyarsa sai bugawa take da sauri da sauri.

A bakin kofar suka tsaya sukai addu'a sannan suka shiga.

Haka suka shiga, suna shiga ciki suka hau jam'i a tsakiya suka sakashi, liman yaja sallah.

Suna idarwa Abba ya kalleshi, wasu zafaffan kwalla ne suka shiga neman zubomai a lokacin daya daga hannu yana rokon Allah, yaushe rabo? Addu'a ya shiga yi har bai san sanda hawaye ya zubo mai ba.

Sageer ma sai daya zubo da kwalla saboda tsananin tausayi.

Ya dade yanata addu'oi kafin su fito, dan sukan shi suka tsaya jira, dukansu sai tausayinsa yakeyi.

^**********

Dady ne ya kalli kofar gidan, kwanansa biyu kenan yana zuwa yana komawa dan shifa gaskiya ya kasa sa kafa cikin gidan, ko dai wayau zaiyi ya fara zuwa gidan da Goggo take? Ita yasan mai sauki ce inyaso sai tazo nan da kanta ta basu hakuri.....

Juyawa yai da motar kamar zai koma sai ga motarsu Abba.

Kallansu yai sun shiga ciki, sun hada ido da Hassan amma sai ya dauke kai, da kallan takaici ya bishi yace "wannan dan iskan yaran....."

Suna shiga shima ya shiga da motarsa.

Su Abba na fitowa shima ya fito da sauri yace "Ranka ya dade!"

Abba ya juyo ya kalleshi, murmushi yai yace "Ah Alhaji kai ne?"

Dady ya matso yana kallan Sageer da Hassan da sukai kamar basu ganshi ba.

Hassan ya kalleshi bayan ya karaso yace "Ina wuni?"

Dady ya washe baki yace "Hassan an wuni lafiya?"

Hassan yace "lafiya."

Ya wuce ciki, Sageer ma yace "Ina Wuni?"

Nan ma yace "malam Sageer ko?"

Sageer yace "eh."

Ciki yai Abba yace "bismillah!"

Nan suka shiga ciki...........

Falonsa ya kaishi ya zauna sai wani washe baki yakeyi, yana cewa "wlh na dade inasan nazo."

Abba ya kalleshi baice komai ba.....

Shiru sukai dan Abba kam shikanshi haushinshi yakeji, ai koda laifin su Inna da Mumy to tabbas laifinsa yafi yawa, dan a matsayin sa na uba, miji abinda ya aikata shi kansa yayi alawadar dashi, tun ma daga auran mahaifiyar Jalila zuwa zaman da sukai......

Dady ya kalli Abba jiki a sanyaye yace "Ranka ya dade nace........"

Abba ya kalleshi, Dady yanda yaga ya kalleshi ya daure yadanyi shiru......

**********

Hassan na shiga ya kalli kitchen, Ameera ce ta fito rike da kofi tana shan abu, tana ganinshi ta matso tace "Yaya."

Kallanta yai yace "baki tafi islamiya ba?"

Tace "ai yau alhamis."

Yace "okay."
Ya wuce sama, da sauri ta koma kitchen ta taba Jalila tace "Aunty mai sanyin ya dawo...."

Jalila ta juyo ta taka kafarta, Ameera ta saki yar kara Jalila tace "bari na fadamai wai mai sanyi."

Ameera tace "wayyo Allah na ki rufamun asiri."

Jalila tana dariya ta fito, da sauri ta hau sama tana murmushi, ina yaje dazu?

Tana shiga ta taraddashi yana cire kaya, da sauri ta juya baya tana cewa "yaya ashe ka dawo."

Yana cire kayan amma kallanta yakeyi, yace "nemana kike?"

Juyowa tai ta manta sam da abinda yakeyi tace " naga......."

Ganin ya cire rigar tasa gaba daya tai sauri sake juyawa, murmushi yai yana kallanta, Jalila menene tsakaninki da Sageer? Me ya faru a baya? Anya ya dace nama Sageer haka?

Tambayoyin da yakeji kamar ya yimata kenan, ta juyo ita kuka da sauri tace "Yaya kasan me?"

Kallanta yai, ta kara kallan jikinsa da sauri ta sa hannu ta rufe fuskarta.

Murmushi yai sannan yace "ki hadiye maganarku tunda kunyata kikeyi, in kuma so kike in matso to."

Tace "ka matso ina?"

Takowa yai yazo inda take, idanu ta bude da sauri, ya sa hannu ya lankayo cikinta yace " haka kikeso?"

Idanu ta zaro tana kallansa tace "yaya wlh ni......."

Shiru yai yanayin fuskarsa ne ya dan canza, murmushi yai sannan ya saketa yace "Mahaifinki fa yazo."

Tace "yaushe?"

Yace " yanzu ya shigo, da alama yazo ganin yar sa ne."

Tace "hmm yadai zo abinda yazo yi, ko an turoshi."

Hassan ya kalleta kamar zaiyi magana sai ya fasa, cikin toilet ya shiga ya rifo kofar.

Da kallo ta bishi tare da yin ajiyar zuciya.....
Itakam batasan ya akai take tsananin san ganinta da Hassan haka ba, lalai yanzu ta fahimci kaunarshi ta fara yin nisa a ranta.

Dolene ta je gun Goggo ta fada mata dan itakam yanzu tanajin Hassan har ranta...........



#OneLuv=ؕ?
[12/7, 10:12 PM] El-hajj: *_=???JALILAH!!=???_*

Written By : *AYUSHER MUHD*
'ote me on wattpad : *Ayusher Mohd*


*HASKE WRITERS ASSOCIATION*
(_D home of expert and perfect writer's_=ء?)
Day

*59*



Ummy tabi Sageer da kallo, yanda ya ajiye waya da sauri yamik'e bayan yagama ansa kiran da'aka masa, sama yahau da sauri, Hassan na kwance ya shiga bai ko jira ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login