Showing 45001 words to 48000 words out of 168255 words
canja.
A cikin wannan lokacin zan nemo miki inda mahaifinki da yan uwanki suke. Da gaske ne mahaifiyarki ta rasu a kan idona, ba zan taba mantawa ba. Ba zan ce miki komai a kai ba, ki jira Mammah ta gaya miki kamar yadda ta yi alkawari. Idan na yi miki hakan ina ga na gama cika burikanki ko? Sai ni ma ki cika min nawa burin wanda ba shi da wahala, abu ne mai sauki Hafsah, shi ne ki amince in lokacin da na dibar wa Muazatu na aurenta ya cika za mu rabu, wato ZAN SAKE KI. Mu hadu mu bai wa Mammah uzuri da cewa halinmu bai daidaita ba, ko kuma haka kaddara ta tanadar mana. Mun rabu ne ba don ba ma son juna ba, sai don kowannenmu ya kasa jure halin dan uwansa.
A wannan lokacin na san ba su da wani zabi sai su barni in auri Muazatu, ke ma ki auri wanda ki ke so. Ga mahaifinki da yan uwanki a gefe da kuma karatunki, ina fatan kin fahimce ni?
Ta yi shiru na tsawon lokaci, idanunta na hango mata ranar da za ta kammala karatunta ga mahaifinta da danginsa a gefe, dasu Mammah kamar yadda aka yi wa Abdulazeez a (Law school). Hakika ranar za ta zamo ranar madaukakin farin ciki a gare ta wadda babu irinta...
Me ki ka ce Hafsah?
Ta tsinkayi muryar Abdulazeez mara amo kuma mai taushi a can tsakar kanta. Ta dawo da ita daga duniyar tunanin da ta tafi mai nisan zango. Ta yi ajiyar zuciya, sannan ta daga kanta a hankali ba tareda wani dogon tsinkaye ba ta ce,
Na amince.
Ya gyada kansa shi ma, Haka nake son ji, idan da amincewarki to komai zai tafi daidai babu tangarda har zuwa lokacin da (contract) din zai kare. Mammah ba za ta yi irin fushin da ki ke tunani da mu ba, za ta fahimce mu, in har ki ka gaya mata da amincewarki aka yi komai, kika nuna mata ke ki ka zabi sakin don ba za ki iya da halina ba. Ni ma na fada mata na kasa jure halinki ne.
Sai dai ina so wannan ya zama babban sirri a tsakaninmu Hafsah. Sirrin da babu wanda za ki fada wa mun yi shi duk duniyar nan.
Sannan bayan rabuwarmu insha Allahu zan zamo mai taimaka miki ta kowacce fuska a rayuwarki, na yi wannan alkawarin, I promised.
Sai da ta daga kanta alamun ta fahimce shi, sannan ya mike yana sanya wayoyinshi a aljihu.
Ina ga iyaka abin da za mu tattauna din kenan, dare ya yi. Ki je ki kwanta.
Ya mike ya nufi kofar fita daga dakin karatun kai tsaye without giving her a second look(ba tareda ya kara kallontaba).
Yaa Azeez!
Ya ji ta kira shi a hankali.
Sai ya ja birki ya tsaya a inda yake dab da kofar, hannunshi na kan handle din kofar. Cike da mamakin kiran sunansa da ta yi. Ba ta taba yin hakan ba ko da wasa a kafatanin rayuwarsu. Duk da cewa ta kira sunan ne kamar yadda sauran kannenshi ke fada amma a kunnenshi sai ya ji kamar wani abu daban ta fada ba sunan nasa ba. Ya juyo ya fuskanceta daga inda yake tsaye ba tare da ya dawo ba.
Ba ta ko motsa daga inda ya barta ba, har zuwa lokacin kuma tana ta cakuda kyawawan yatsunta cikin junansu. Kanta a sunkuye.
Na gode!.
Ta furta tana mai dago kai ta kalle shi.
Ji ya yi kamar zuciyarsa ta yi tsalle ta fice daga kirjinsa ta dawo, da gaske ne (shes so innocent) in ba haka ba me ya yi da har zaa gode masa? Shi a nasa tunanin ma in zaa dubi lamarin da idon basira ai babban laifi zai aikata a gare ta (saki a wajen diya mace). A gefe guda ga kuma tsallake maganar mahaifiyarsa da zai yi, ai kuwa bai cancanci godiya ba ta kowanne bangare. Sai dai ko ta wajen Muazatu wadda zai tsallake umarnin iyayensa a kanta saboda farin cikinsu shi da ita.
Bai san me zai ce mata ba, saboda haka kawai ya daga kai sannan ya juya ya fita daga dakin karatun.
Ya koma dakinsa idonsa cike da bacci da gajiya. Ko da Muazatu ta kira shi don su yi hirar daren da suka saba (midnight call) cewa ya yi da ita, ta yi hakuri bacci yake ji. Kuma ya yi magana mai yawa saboda ita a daren nan. Ya yi alwala ya yi nafila rakaa biyu, ya roki Allah ya rufe bakin Hafsah kar ta tona masa asiri a wajen Mammah komai runtsi.
Duk da dai ya lura yadda ta ke son cika burikanta, zai iya danne komai, wanda haka yake har zuciyar Suhaanan.
SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870
*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*
*****
Kwana ta yi tana juya maganganun da suka yi na karatunta da nemo mahaifinta a zuciya da kwakwalwarta. Su kadai ta ke tunani a matsayin matsalolinta yanzu a rayuwa, ga shi ta samu wanda ya yi alkawarin dauke mata su. A kan me kuwa ba za ta yi masa yadda yake so ba ita ma? Auren ko kadan ba ya kanta dama, bata da wani hopea kansa ko experience kan abin da ya kunsa sosai balle har ta sa shi a lissafinta. Ta amince ne dama saboda Mammah don ta amince wa ranta babu abin da Mammah za ta nema a wajenta ta kasa yi mata, amma sam ba ya gabanta.
Sai ga shi a yanzu ya juye ya zama sanadin alkhairi a gare ta, sanadin da zai kai ga cikar burikan rayuwarta (karatu da mahaifinta). Ta faranta wa Mammah, sannan ita ma ta samu farin cikinta. Har ila yau, shi ma ya samu nasa cikar burin. A iyaka dan kankanintunaninta, me ya fi wannan kwangilar sauki da riba kuwa???????
*****
Gadan-gadan Tsohon ambasada Hamza Atiku da maidakinsa Hajiya Maryam suke shirye-shiryen auren yayansu, auren da suke so ya bar tarihi a dangi don haka ba karamin shiri suke masa ba.
Soyayyar Abdulazeez da Muazatu sai abin da ya karu, kullum suna tare a waya, ko ta biyo shi office ko shi in ya tashi ya je can inda ta sauka gidan Antinta har ta koma gida Lagos ba abin da ya sauya.
Ba ya yi mata zancen komai game da aurensa, ita ma ba ta tambaya, ba ta taba neman sanin yarinyar da za a aura masa din ba, shi ma bai taba yin wannan gwanintar ba. Zai iya cewa daga ranar da suka yi magana ta farko shi da Suhaana ko a hanya ba su kara haduwa ba, duk da cewa gida daya suke kwana. Yana riga kowa fita a gidan, sannan ba ya dawowa da wuri. Mammah ma ba ta kara damuwa da su kebe din ba don su kara fahimtar juna, shirye-shiryen biki kawai ta ke, hankalinta kwance, don ta lura yar damuwar da Suhaana ta ke ciki bayan ta yi mata zancen auren tun daga ranar da suka yi magana ita da Abdulazeez ta rabu da ita, ta saki ranta tana ba ta hadin kai a kan komai.
Biki ya rage saura sati uku tuni an bugo I.V an fara rabo cikin dangi. A yadda Mammah ta tsara za su taho Kano ne, a nan za a yi komai, liyafar cin abincin dare (dinner) kawai za a yi a Abuja washegarin daurin aure. Kullum za ka ganta tana waya da mutanen Dakata ana ta shirye-shirye. Ta fannin Daddy kokari yake ya kammala ginin da yake yi wa Abdulazeez a Estate din (Sun-City). Wani kyakkyawan Mansion mai hawa daya da ya dauki shekaru yana gininsa yana dakatawa tun yana Ambasada, yanzu ya maida hankali yana so a kammala komai cikin lokaci.
Mammah zaune a kayataccen falonta cikin kwalliya ta kece raini kamar kullum. Waya ta ke yi da aminiyarta ta cikin Abuja, Hajiya Halima matar Controller, magana suke yi a kan babarbariya mai gyaran jiki da Hajiya Haliman za ta turo ta fara gyara amarya daga yau har ranar da za a kai ta dakinta. Wannan shi ne gudunmawarta.
Sosai Mammah ta yi godiya, ta daga murya ta kira Hafsa wadda ke dakinta tana gyaran kayanta da aka kawo daga wanki da guga. Ta ajiye rigar hannunta ta fito ta tadda Mammah a falo, tun kafin ta zauna Mammah ta ce.
Ki yi shiri gobe za mu wuce Kano, kuma Hajiya Halima ta turo mai gyaran jiki za ta zo ta fara miki daga yau, tare da ita za mu tafi kano.
Suhaana ta ce, Mommah me jikina ya yi da za a gyara shi? Na yi dauda ne?
Dariya Hajiya Maryam ta yi, ta rike hannunta cikin nata.
Kullum Adda ta tsaf ta ke, kal-kal kamar tarwada saboda wanka. Shi gyaran aure daban yake, ba irin wanda ki ka saba yi ba.
Hafsat har tausayin Mammah ta ke ji a ranta in ta yi duba da yadda ta dora ranta a kai ta ke kuma zumudin auren nasu. Ba ta taba ganin abin da Mammah ke farin ciki da shi a duniya irin auren nan nasu ba. Ya ya za ta ji a ranta idan ta gaya mata na wucin gadi ne ba mai dorewa ba ne, ta kyale wata mai gyaran jiki? Ai ko Ya Azeex bai ce ta boye ba, ita a karan-kanta ba za ta iya fada ba.
Karfe shida na yammacin washegari suka isa birnin Kano, ta Dabo ci gari, jallabiyya babbar hausa, yaro ko da me ka zo an fi ka, mai Dala da gwauron Dutse, Kano tumbin Giwa, ta sarki Ado Allah ya yi maka rahma.
Abdulazeez bai taho tare da su ba, yana Abuja sai ana saura kwana daya daurin aure zai taho tare da tawagar lauyoyin chambarsu. Mai gyaran jiki mai suna Fannah ta shiga aikinta a kan Suhaana. Eh, lallai, ta yarda da abin da Mammah ta ce, shi gyaran auren daban yake, kuma wannan da ake mata ba karami ba ne. Ganin yadda cikin kwana uku fatar jikinta ke wani irin salki da sheki. Ga Addar babu kawaye sai yayan dangi ne suka zama kawayen nata su Halima yar Anty Luba, Saima da Khalisa yayan Anti Mariya da Anty Furairah duk da ta dan girme su don cikinsu ba wadda tayi candy. Gayya sosai Hajiya Maryam da kannenta suka yi. Ta bangaren maza ma ba karamar gayya Dr. Hamza ya yi ba shi da sauran yan uwansa. Baa maganar Minister Abdulkareem Dakata ya yo babbar gayyata ta manya zuwa daurin auren jikan nasa.
An yi kamu ranar alhamis, jumaa aka yi wunin biki a nan mainhouse nasu. A yammacin ranar wato ana I gobe daurin aure Abdulazeez da abokan aikinsa suka iso. Tsohon Minista Abdulkareem Dakata mai masaukin baki ya yi musu masauki a gidan saukar baki na Tahir Guest Palace.
Washegari asabar karfe goma daidai na safe daruruwan jamaa suka shaida daurin auren Abdulazeez da Hafsat a kan sadaki naira dubu hamsin lakadan, wanda ya fito daga aljihun Abdulkarim Dakata. Aka yi adduoi masu yawa aka shafa. Daga nan maza suka wuce liyafar cin abinci acan Tahir wadda Dr. Hamza ya shirya, mata kuma suna shirin tafiya Mothers Nighta daren ranar a (FABS EVENT CENTRE) wanda Hajiya Maryam ta shirya.
Rana ta farko da fuskar Hafsat-Suhaana ta soma daukan make-upna zamani a rayuwarta. Ta koma tamkar wata sabuwar kyakkyawar halitta ta daban wadda aka baro daga cikin kwai don kyau da ban shaawa. Hatta Anty Zuwaira da ke adawa da auren a zuciyarta sakin baki ta yi tana kallon Hafsat, ta kuma yarda har ranta yarinyar kyakkyawa ce tun asali, kawai ta raina asalinta ne har gobe tana ganin wautar Hajiya Maryam na hada wannan auren, yaro irin Abdulazeez yarinya yar asali, yar gata, yar babban gida ta dace da shi ba yar mai aiki ba. A raayinta fa. Amma tunda ita ta haifi abinta wa ya isa ya yi magana? Ta yi tsaki ta dauke kanta daga kallon yarinyar.
Wadda Hajiya Maryam ta shirya cikin wani rantsattsen leshi baki mai ratsin silver, goggoron kanta silver, dankunne da sarka, takalmi da purse duka silver. Duk wanda ya daga kai ya dube ta sai ya ce, Masha Allah.
Hannunta cikin na Mammah wadda ita ma ta sha nata adon cikin koreni tattausan leshi, kawayenta su Anty Halima na take mata baya cikin tasu shigar ta alfarma suka shiga motoci zuwa (Fabs Event Centre).
Taron na mata ne zalla, don haka babu bukatar zuwan ango da abokansa. Sai dinnerta gobe da za a yi a Abuja ne zasu halarta, washegari lahadi za a yi ta (by- couple), wato kowa da mijinta. Iyakar (programmes) din da suka tsara kenan, kuma alhamdu lillah komai ya kayatar. An ci an sha, an yi hotuna da vedio don tarihi aka watse.
Suna fitowa daga mota za su shiga gida Abdulazeez da wasu abokansa biyu, Barrister Abdallah da Barrister Adebayo na tsaye a dakalin kofar gidan suna magana. Yana cikin farar shadda kal (hilton) da babbar rigar rataye a kafadunsa. Hasken fitilar kofar gidan ya haske masa yaran yammatan dake fitowa daga mota, fuskar Hafsat tarwai a tsakiyar yammatan. Ya gyara tsayuwa yana kallonsu suna shige shi daya bayan daya zuwa cikin gida. A ransa ya ce, ina ruwan (sweet sixteens), gaba daya kawayen ma wadanda duk ya sansu a dangi yara ne kamarta. Abin ya ba shi dariya sosai, sai da ya yi murmushi.
Adebayo ya ce Wow! Abdulazeez you have a beautiful wife, looking gourgeous.
Abdulazeez ya galla masa harara, ita ma ya juya ya galla mata tata, ya dauke kai suka ci gaba da maganarsu da Abdallah.
Ta ga hararar da ya yi mata sosai, don wajen akwai wadatar haske duk da dare ne. Jikinta ya yi sanyi da ma a sanyayen yake. Tun lokacin da aka tabbatar mata an daura mata aure jikinta ya mutu, bakinta ya mutu. Mammah ta lura da hakan, amma ba ta ce mata komai ba. Is normal ai, mace ta canza sanda aka daura mata aure. Nauyi ne babba ya hau kanta, ta zama karkashin mulkin wani, ta zama UWA, ai kuwa nauyin ba karami ba ne.
Washegari da safe kowa na gidan ya tashi ne da shirin wucewa Abuja. Karfe tara daidai motocinsu suka tashi zuwa Abuja dauke da amarya shi ma angon da tashi tawagar sun kama hanya, zuwa azhar suna cikin Asokoro gidan tsohon Ambasada Hamza Atiku. Nan kowa ya ci abinci aka huta. Su Anty Halima suka wuce gidan amarya don kara gyaggyara komai, wato jeren da suka tsaya maaikatan kamfanoni suka yi.
Sai shirin tafiya dinner wadda za a yi a (A-class). Ana yi mata kwalliya, amma gabanta faduwa yake yi jin ana fadin har da angon da abokansa za a yi dinar, idan ta tuno da muguwar hararar da ya zabga mata a Kano ba laifin tsaye babu na zaune. Amma sai Abdulazeez ya bada mamaki, har aka yi dinnar aka kare bai ba da wata matsala ba. Ko nuna wata kafa da zaa gane baya maraba da auren Hafsat. Da aka tashi ne dai ya bi abokansa bai tsaya bi ta kanta ba ko motar da ta kawo su tare, sai ita kadai aka dauko a motar aka dawo da ita gida.
Sai shirin tafiya kai amarya. Nan fa ake yinta. Yau zaa raba Suhaana da Mommah, Suhaana da Baba Azumi. Kuka ta ke kamar na fitar rai, ko Mammah ta ji tausayinta ta barta su ci gaba da rayuwarsu tare. Ita kanta Hajiya Maryam dauriya kawai ta ke yi, amma zuciyarta ta gama karyewa. Baba Azumi dai sai kewaye ta shige ta kulle, sannan aka iya fitar da Hafsat zuwa falon Daddy. Albarka kawai ya sa mata ya ce su je da ita, zai biyo ta gidanta ya yi mata fadan. Kawai sai aka ga Mammah ta dauko mayafi ta yafa ta kama hannun Hafsat zuwa mota ta ce da ita zaa je. Su Hajiya Halima na tsokanarta wai surukar sabon qarni. Murmushi kawai tayi tana shanye hawayenta. Sannan ne Hafsat ta rage kukan motoci suka kama hanyar Sun-city.
A daidai wannan lokacin Abdulazeez yana dakinsa na gidansu. Ya kulle kansa yana waya da Muazatu, kuka ta ke yi masa sosai cikin matsanancin tashin hankali. Gani ta ke ta rasa Abdulazeez ta gama, yau zai shiga dakin amaryarsa shi ke nan fa! Shi kuma lallashinta yake yana kara tabbatar mata da alkawarinsu. Amma ina! Muazatu jinsa kawai ta ke, ta kasa yarda duk da ta san har zuciyarsa yake nufin alkawarin, amma tunda ta ga hotunan bikin da yarinyar da yake cewa ba ya so din a wayoyin abokansa hankalinta ya yi mugun tashi. Ta dauka wata bakauya aka aura masa da farko, ko wata wadda ba ta amsa sunan mace ba, amma idonta ya gane mata Hafsat-Suhaana kwance a kafadun mahaifiyarsa, ta kuma gansu tare a hotunan sun sha anko sun durkako (A-class) inda aka yi dinar kamar don su aka halicci juna. Tuni ta daina yarda da kalaman bakinsa duk da cewa duk cikin hotunan da aka nuna mata din babu inda ta ga ya kama Hafsat ko ya mannu da ita don nuna soyayya.
Da ya gaji da lallashinta, amma ta ki daina kukan, sai ya yi shiru. Amma bai kashe wayar ba, bai san kuma da kalaman da zai yi amfani da su Muazatu ta yarda da shi ba. A ganinsa duk wasu kalamai da yake da su sun kare. Ta sanshi ai, ta san halinsa, ta san babu karya cikin halayensa. Ya yarda ya auri Hafsat ne don ya samu hanyar aurenta, kuma babu soyayyarta ko kankani cikin zuciyarsa. Me ya sa ba za ta yarda ba? Shirun nasa sai ya kara tunzura ta, ta ci gaba da gursheken kuka. Zuciyarsa ta dinga bugawa fat-fat-fat, tsigar jikinsa ta dinga tashi.
Enough, is enough Muazatu, ki gaya min yanzu me ki ke so na yi?
An