Showing 48001 words to 51000 words out of 168255 words

Chapter 17 - Auren Kwangila Book 4 Hausa Novel Complete

Takori   

12 Dec 2024

304

zo gabar da ta ke so don haka ta sassauta kukan.Abdul na dade ina yi maka tanadin kaina, ina tattala maka budurcina, ban taba wasa da shi ba. Ban taba shaawar bada shi ga waninka ba, kullum burina ya zamo kai ne za ka karbe shi cikin girma da daraja. A yau wata ta riga ni samunka, da ka kusance ta ta gama janye min kai, komai rashin son da ka ke mata. Wallahi in ka kusance ta na hakura da kai har abada ko kai ne autan maza. Zan roki Allah ya cire min sonka ko ya zama ajali na a kan in yi sharingdinka da wata, ni wannan ne kawai damuwa ta.
Shiru ya yi kamar ruwa ya cinye shi. Shi kansa bai san me ya sa ya yi shirun ba. Muazatu ta baro zance wanda shi kansa ya girmi kwakwalwarsa. A ganinsa bai kamata ta shiga wannan hurumin ba duk da akan-kansa bai taba kawo yiwuwar hakan cikin rayuwar auren kwangilar da zai yi da Hafsat ba, amma ai matarsa ce, koda yace da Hafsat kayyadadden zama zasu yi iyayensuda suka daura auren da tsarkakakkiyar niyya suka daura shi kamar yadda addinin muslunci yayi umarni, ba su san da wani abu bayan wannan ba, don haka ko ta ina aka je aka dawo sunan Hafsat matarsa, an taba gindaya wa miji hukuncin kada ya kusanci matarsa?
Koda yake son Muazatu shi fa ba sakarai ba ne da zai zauna mace ta gindaya masa abin da ta ke so ta ce dole sai ya bi ba. Don haka ransa ya baci sosai da maganar Muazatu kawai sai ji ta yi ya kashe wayar.
Matsanancin tsoro da mamaki suka taru suka lullube Muazatu. Ta ciro wayar daga kunnenta ta duba sosai, ya kashe. Tunda suke tare bai taba kashe mata waya ba, me hakan ke nufi??





SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870

*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama
*****
Yan kawo amarya sun ajiye ta sun juya, Mammah kuwa da dabara ta samu ta fice. Aka barta daga ita sai Harira yar Baba Azumi a dakin da aka tanada don mai aiki a gidan. Harira matar aure ce da yaya hudu, lokacin da Baba Azumi ta gayyato su biki daga Sokoto Mammah ta yaba da hankalinta da kazar-kazar dinta don su suka yi ta tsaftace gidan lokacin biki da rabon abinci, ta roki Baba Azumi ta barta ta zauna da Adda ta debe mata kewa zuwa sati biyu kacal. Kafin lokacin ta saba da sabuwar rayuwarta ta saki ranta. Baba Azumi ta amince don haka aka bar Harira a gidan tare da Hafsat.
Tunda Harira ta shige dakinta ta rufe kofa ba ta sake fitowa ba. Hafsat-Suhaana ta ci kukanta ta gaji har ta gode Allah, hawayen suka tsaya don kansu. Kanta ya sara, ya soma ciwo ta kwanta lamo! A kan filo ta rufe jikinta da mayafinta, ta takure a can gefen gadon ta soma ajiyar zuciya.
Ko da ya kashe wayar da suke yi da Muazatu komawa ya yi ya jingina bayansa da kofar dakin nasa. Ya lumshe ido zuwa dan lokaci ya bude ya zura wayarsa a aljihunsa. Lokacin ya tuna su Abdallah suna kofar gida suna jiransa su raka shi gidansa. Toilet ya shiga ya yi wanka ya canja kayan jikinsa da wani sassalkan ya din filtex (milk colour) ya taje sumar kansa, ya sanya hular da ta dace da kayan nasa, ya daura agogon (swatch) a damtsen hannunsa ya fesa turare har kala uku. Ya janyo manyan jakunkunan da ya hada kayansa na dakin nasa ya sanya takalmi sabo dal! Ya fito da jakunkunan sannan ya janyo kofar dakin nasa ya fita.
Gidan babu kowa a falo, duk sun dawo daga kai amarya sun gaji sun kwanta, gobe kowa zai kama gabansa.
Har ya fice bai hadu da kowa ba, ya tadda abokansa a waje zaune kan fararen kujerun da ke harabar gidan suna hira. Yana fitowa suka mike suka karbe shi jakunkunan suka shiga motocinsu suka wuce (Sun-city).
Kofar gidan akwai maigadi wani Danfulani da Daddy ya samar musu, ya bude musu (gate) suka shigo da motocinsu, suka yi parking suka firfito. Dukkaninsu Lauyoyi ne na gwamnati da masu zaman kansu. Shi ya bude kofar falon suka shiga, kowa ya nemi inda ya yi masa ya zauna a lafiyayyen (European parlor) da Mammah ta shirya, in ka wuce shi za ka tadda (African parlor) wanda bai kai shi girma ba, wanda ya ji shimfidun gargajiya da adon carpet din fata na jikin bango da su tum-tum abin gwanin ban shaawa kai kace sun hada jini da sarauta ne. A cikin wannan (African parlour) kofofi ne guda biyu wadanda suka kunshi dakunan barci biyu, daya nasa, daya na matar gidan. Daddy ya kawo shi ya ga gidan tun sanda ake gininsa don haka ya san kansa. A kowanne dakin barci akwai makewayi, kicin (madafi) yana gab da shiga kofar falon farko, wato ba a cikin falon aka yi shi ba.
Akwai yar doguwar baranda a kofar shigowa falon, wadda aka aje fararen tukwanen fulawoyi masu kyawun gani da fararen kujerun roba. Harabar gidan za ta iya cin motoci uku ba tare da kowacce ta gogi yar uwarta ba. Dakin maigadi na jikin gate, dakin mai aiki yana daga bayan ginin falon, wato sai an fito daga main building din an zagaya ta baya za a tadda dakin mai aiki.
Yadda su ESQ Abdallah suka nemi wuri suka zauna cikin tausasan kujerun falon haka shi ma ya nema ya zauna. Barrister Taufeeq shi ne karshen shigowa yana janye da jakunkunansa yana daga tsaye ya ce, Dare fa ya yi, ka shigar da kayan Malam ka fito mana da amarya mu saya maka bakinta, mu yi muku addua mu koma namu gidajen.
Harararsa ya yi ya mike ya karbi jakunkunan ya yi ciki. A ransa ya ce, wai su saya min bakinta, to in yi me da shi?
Tsakanin dakunan biyu zai yi rantsuwa bai san wanne aka ba ta ba, wato ba zai iya cewa ga nasa ga nata ba.
Tsayawa ya yi yana kallon kofofin guda biyu da kallo mai kama da harara. Ba wata amarya da ya yi niyyar kai musu su yi abin da za su yi, kawai su tafi. Ya ce ta zo cikin abokansa ma ai sai ta raina shi. Ya yi kundunbala ya murda handle din kofar dama ya tura jakunkunansa. Cikin ikon Allah shi ne nasa, ya jefar da jakunkunan ya fito ya tadda su.
Yaya ina amarya ka fito kai kadai? Taufeeq ya tambaya, sauran kuma suka bi shi da ido kamar sa cinyeshi.
Ta yi barci.
Ya samu bakinsa da fadin hakan ba tare da ya shirya ba. Duk suka mike, To sai mu wuce, randa muka zo idonta biyu mun yi muku adduar dare ya yi.
Ni na yafe adduar taku in ba za ku yi min ni kadai ba.
Dariya suka yi, Taufeeq na fadin, Ka fadi gaskiya Malam.
Suka wuce Ahmad na fadin, Da gaskiyarsa fa, wannan aladar babu kyau ko kadan. Mai kishin iyalinsa ba zai yarda da ita ba.
Baki ya kama yana kallon Ahmad cikin takaici, Kishi? Ya ambata cikin sigar tambaya da nauyin baki.
ESQ Ahmad bai ba shi amsa ba, ya daga masa gira ya yi murmushi, ya ba shi hannu. Amma Abdulazeez ya noke ya hana shi nasa.
Ka yi min sharri, sannan ka ba ni hannu? Wuce ka tafi. Na gode zan rama.
Suka yi tafiyarsu kowannensu da irin dariyar da yake yi masa.
Da wannan haushin ya dawo ciki. Ya rasa abin da zai yi. Har ga Allah bai yi niyyar shiga inda ta ke a daren nan ba, sai kawai ya shige dakinsa ya rufo, ya dauki (remote) ya kunna naurar sanyaya daki ya hau shirya kayansa, daga jakunkuna zuwa sif din jikin bango.
Sai karfe biyu na dare ya gama, ya yi sallar nafila ya kashe wuta ya kwanta. Wayarshi da ya bari a kunne a gefen kansa ita ta tashe shi da kiran Muazatu da assalatun fari. Kansa ya yi masa gingirin sabida bacci da gajiya ba zai iya magana ba don haka ya matsar da ita gefe ya koma ya ci gaba da barcinsa. Wannan ya kara daga hankalin Muazatu wadda yadda ta ga rana haka ta ga dare, cikin matsanancin tashin hankali.
Sai karfe biyar da rabi alarm din da ya saita ya tashe shi, ya dauro alwala ya gabatar da (rakaatainil fajr), sannan ya bada farali. Haka kawai ya ji ya kamata ya tashe ta ta yi sallah in ba ta tashi ba, ko ransa na so ko ba ya so.
Dan karamin tsaki ya yi, sannan ya mike daga inda ya yi sallah. Haka kawai an dora masa nauyin mutum yana zaman-zaman sa.
Har zuwa lokacin wayarsa na ci gaba da ruri, jinjinawa naci irin na Muazatu ya yi, in ya tuno yadda suka yi sai haushinta ya sake kama shi, ya kasa amsa wayar. Da ya ga ba ta da niyyar daina kiran sai ya kashe wayar gabadaya ya mike ya nufi dakin Hafsat.
Kwankwasawa ya yi sau biyu ya saurara babu amsa, ya sake (knocking) har yanzu babu motsinta, sai kawai ya murda kofar ya shiga a sike, ba tare da tunanin komai ba.
Tana lullube cikin bargo bakidayanta, zazzabi, masassara da ciwon kai sun taru sun rufe ta tun daren jiya. Allah kadai ya san yadda ta yi ta kawo yanzu.
Gabadaya ta rufu ko don yatsanta babu a waje, sai karkarwa ta ke. Shi kansa bargon da filon da ta ke kai karkarwa suke. Ya lura da hakan, ya dan yamutsa fuska.
Ba ki da lafiya ne?
Daga cikin bargon ta daga kai, bai san ta yi ba, haushi ya soma kama shi, ba ya son shiga shirginta ko kankani, kuma ba ya son yana magana a kyale shi. To kuma ta dukunkune cikin bargo bai san halin da ta ke ciki ba, tana ta faman karkarwa wanda ke nuna bata da lafiya. What could he do? He actually dont know.
Yana wannan sake-saken ya jiyo motsin mutum a falo. Da sauri ya juya ya fito. Da farko har ya so ya tsorata don bai yi zaton akwai wani mahaluki a gidan bayan su ba, kawai sai ya ga mace a tsakiyar falo da tsintsiya a hannu. Gari ya dan soma haske wanda ya ratso daga fararen curtains din falon ya haska masa matar sosai.
Da mamaki ya ce.
Daga ina?
Harira ta zube tana gaishe shi da sakkwatancinta. Da sauri ya amsa, so yake ya ji daga ina ta billo.
Sunana Harira, yar Baba Azumi ce.
Ya yi ajiyar zuciya, a take ya ji kamar an yi masa rahama. Ya wuce dakinsa yana mata magana ciki-ciki.
Ki shiga ki duba ta, nake jin ba ta da lafiya idan akwai bukatar taimako na zan fito anjima ki sanar da ni.
A cikin ransa in ban da godewa Mammah ba abinda yake yi da ta samar da third party a tsakaninsa da Hafsat, da ina zai sa ransa? Zuciyarsa ba za ta juri shiga harkarta ba, sannan zai je koina hankalinsa kwance ya dawo sanda yake so ba tare da tunanin ya ajiye wani ba. Kowa ya ci gashin kansa.
Harira ta shiga da sallama, amma Hafsat ta kasa amsawa, ta daure dai ta yi motsi daga cikin bargonta. Harira ta isa gaban gadon ta yaye bargon, sai Hafsat ta kara dunkule jikinta. Karkarwa ta ke sosai, wadda ta bai wa Harira tsoro. Abinda tayi zato ba shi ta gani ba. Tun kayan data zo dasu ne a jikinta har sarka da dan kunne suna nan a muhalli su. Ta hau gadon ta ciccibo ta, ta taimaka mata ta shiga bayi ta yi fitsari, ita ta yi mata alwala ta ce, ko a zaune ne ta yi sallah sai ta gaya wa maigida su je asibiti, ya ce inda matsalar rashin lafiya a sanar da shi.
Ta ba ta katon mayafi ta yafa, ta shimfida mata darduma. Daga zaune ta yi sallar. Harira ta taimaka mata tana daga zaune ta canza su zuwa doguwar riga yellow da mayafinta ta kamo ta suka fito falo, ta zaunar da ita a (three seater), tana dunkule jikinta cikin karkarwar jiki kanta cikin cinyoyinta.
Tun Harira tana kallon kofar dakinsa da tunanin zai fito, har ta hakura da kallon kofar tasa ta mayar kan baiwar Allah wadda ke cikin wani hali na neman taimako na masassara da zazzabi mai zafi da matsanancin ciwon kai. Ita ba abun ta je ta buga masa kofa ba tunda bai ba ta umarnin hakan ba. Haka ta zauna shiru, ta tallafo Hafsat jikinta.
A daidai lokacin ya murdo kofar dakin nasa ya fito, lokacin gari ya idasa wayewa sosai.
Kallo daya ya yi musu ya dauke kansa wayar da ke hannunsa ta fara ruri.
Ba ta da lafiya ne? Ya tambayi Harira.
Zazzabi ne ya rufe ta, ina ga gajiyar biki ne.
Ya wuce gaba yana amsa wayarsa, bayan ya ce da ita, Ku biyo ni mu je asibiti.
Harira ta kamata, ta taimaka mata suka bi bayansa.
Baya suka shiga duk su biyun. Ya tada motar a ransa yana fadin, Lallai direba ya samu. Ya ja dan karamin tsaki. Yarinyar ta faya langwai, shes not strong anymore kamar lagwanin risho. How could he be the husband of such a fragile and delicate woman? Hes bold and energetic,yana son jarumar mace kamarsa ba dangin ta-kitse-ta-narke ba.
Asibitin da file din gidansu yake ya kai ta wato DIFF. Nan da nan likitoci suka karbe ta, ashe tana ma da file da su bai sani ba. Yadda Mama ba ta sakaci da lafiyarta tun dawowarsu Abuja ta ke kawo ta check up lokaci zuwa lokaci na nimoniyarta. Kulawa ta musamman suka shiga ba ta a daki na musamman. Ya nuna wa Harira inda za ta zauna ya yi tafiyarsa gida, ya manta da su. Wanka ya yi, tare da yin shirin (office) don shi ba wani hutu da ya dauka don bai dauki kansa ango ko sabon aure ba. Yana nan a (single Abdulazeez) dinsa, he will never answer the namemarried sai ranar da Muazatu ta zamo matarsa.
A office ya tadda sabon case mai tsauri, don haka ya zama (occupied) bai kara tunawa da wata Suhaana ba. Aiki ya dukufa yi kain da nain kamar yadda ya saba a kullum.
Sai da Suhaana ta samu barci zazzabin da ciwon kan suka sauka, likitocin suka fito suka kyale ta. Suka ba wa Harira izinin shiga da umarnin kada ta yi wani kwakkwaran motsin da zai tashe ta, sai ta tashi don kanta.
Tun Harira na kallon kofa tana tsammanin shigowar Abdulazeez har ta gaji ita ma barci ya yi awon gaba da ita a kan kujerar da ta ke zaun a gaban Hafsat. Ba ita ta farka ba sai ana kiran sallar azahar. Ta bude ido ta kalli Hafsat da ke barci ta ga ta tashi itama tana kwance ne kawai lamo a kan filo.
Ta ce, Hafsatu kin tashi?
Kai ta daga mata.
Nurse ta turo kofa ta shigo da keken magunguna, ta dubi Hafsat ta yi mata murmushi, Kin tashi?
Ita ma kai aka gyada mata.
Ta dubi Harira ta ce, Ki hada tea ki bata mai kauri, sannan in ba ta magungunanta.
Harira ta ware ido tana kallon dakin, babu komai na ci a dakin. Ta rausayar da kai ta ce da Nos din,
Don Allah ko za ki taimako da shayin? Maigidan nata bai dawo ba tunda ya kawo mu.
Nos din cikin mamaki ta ce, Ya zai kawo matarsa ba lafiya ya tafi bai ajiye muku komai ba?
Harira ta yi shiru, don ita ma abin ya ba ta mamaki. Amarya ce fa, amarya guda! Da aka kai masa jiya-jiya? Za ta iya tunawa ko sallama bai yi mata ba da zai tafi. Ta ce da Nos din, Wattakila uzziri yarrike shi, kiddai taimakko mata da shayin.
Nos din ta fita a harzuke, can ta dawo da shayin a kofin. A wajen wasu marasa lafiyan ta karbo. Harira za ta kama Hafsat ta tashi, ta dakatar da ita ta tashi da kanta. Nos ta ba ta shayin ta karba tana sha a hankali, kamar ba ta so.
Sai da ta shanye ta ba ta magungunan da ruwa, ta ce ta koma ta huta. Ta sa hannu a wuyanta da goshinta, zazzabin ya sauka sai zufa ta ke.
Ta ce, Good, ki kara hutawa zuwa yamma in Doctor ya zo ya kara ganinki za ku iya tafiya gida.
Ta amsa daga can kasan makoshinta, Toh.
Karfe shidda na yamma Abdulazeez ya tashi aiki. A matukar gajiye ga yunwa, coffee kawai ya sha tun safe. Ya harhada komatsansa da system zuwa black robe dinsa da wig ya zuba a kujerar gaban motarsa. A hankali yake tuki idanunsa na lumshe sabida gajiya, a kan hanyarsa ya gifta ta asibitin da ya zube su Hafsat. A take ta fado masa a rai, ya tuno da su.
Da hanzari ya yi reverseya shiga asibitin yana fadi a zuciyarsa. Haka kawai an dora wa mutum nauyi, yana fama da kansa. Ni kaina kulawar nake bukata. A yadda na kwaso gajiyar nan kulawar mace nake bukata, ba ni in yi ta fama da ita ba.
Sosai ya yi dogon tsaki, amma a take ya yi istigfari cikin zuciyarsa a lokacin da zuciyarsa ta tambaye shi, Wa ka ke wa tsakin?
Daga shi sai bakaken suit din jikinsa ya fito kansa babu hula. Cikin takunsa na nutsuwa ya nufi cikin asibitin. Ya murda kofar dakin ya shiga da sallamarsa can kasan makoshi. Doctor da Nos din nan ya tarar a dakin suna kan Hafsat. A fusace Nos Hindatu ta dago ta dube shi don ta kudure a zuciyarta sai ta kare wa mijin yarinyar nan Hafsat tanadi idan ya zo, don hatta abincin rana ita ta ba su. Amma me? Kwarjini da kamalar Abdulazeez Hamzah Dakata sai ya disashe ganinta ya kashe kuzarinta, ya warware mata duk wasu kalami da ta shirya na cin mutuncinsa.
Fuskarsa a daure ta ke tamau, ya ba wa likitan hannu suka yi musabiha. Likitan ya ce, za su iya tafiya gida ya rubuta musu sallama yanzun nan, don ta warware, stressne kawai wanda ba ta saba da shi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login