Showing 162001 words to 165000 words out of 168255 words

Chapter 55 - Auren Kwangila Book 4 Hausa Novel Complete

Takori   

12 Dec 2024

334

ta makanta ki.
Ta ja baya tana kumburi dafe dda bakinta, bata kara magana ba don lebenta ya yi mata nauyi sai ga Adda Hafsatu ta shigo kawo mata gasasshen nama sai tiriri yake ya ji albasa da yajin daddawa, ta mika mata, Cinye maza kafin a kwashe tuwon.
Ta kalli jaririn da yake ta tsotson baki da hannu, ta ce. Shin yaushe rabonki da ba shi abinci?
Zumburo kumburarren bakinta ta yi, Adda wallahi da zafi, da karfi yake zukowa sai na yi hawaye.
Adda ta dube shi sai juya yaron yake a hannunsa yana kare masa kallo kamar bazai daina ba. Kai bata shi ta ba shi abincinsa, tun azahar rabon da ta shayar da shi, yaro mai hakuri amma sai kin kure hakurinsa, yau kwana shidda ana abu daya, haka za ki daure nan da kwana goma zai daina zafin.
Kallon Adda ya yi cikin mamaki. Nonon ne sai an roke ta take bayarwa?
Addah Hafsatu ta ce Wallahi haka ake fama da ita kullum.
Idanuwa ya watso mata.
Mugunta ki ka koma?
Ta kawar da kai nan ya yi nasarar ganin yadda bakinta ya kumbura daga dalli daya. Dariya ta kama shi amma ya dake, Adda kin ga matso ki rike min yaron nan, danneta zan yi wallahi sai ya sha ya koshi.
Adda kuwa ta karbi yaro ganin ya mike ya nufo ta da karfi ta ce.
Adda kawo shi!.
Ta yi dariya ta dora mata shi a cinya, juya masa baya ta yi ta janyo katon hijabi suka shige ciki ita da jaririn, ta bayanta ya leka, Adda za ta toshe masa hanci fa?
Adda ta harare shi, ta ce, Abin da ka yi wa Mariya za ka yi min ni ma? To ta toshe din, ko ka taya ta nakudarsa?
Da sauri ya tare ta tun kafin ta kai ga rufe baki. Amma ba don ni ba ai da ba a samu cikinsa ba...
Salati Hafsat ta saki daga cikin hijabinta, Addah ta tattara kwanuka ta bar dakin kunya kamar ta nitse. Mariya ba karya ta ke ba, Abdulazeez haihuwa ta sa ya zama fitsararre.
Tana fita ya sassauta murya.
Don Allah, don Annabi ki cire hijabin nan in ganku, Hafsat don Allah. Itssomething Im always dreaming oftundawowarki.
Kamar za ta yi kuka ta ce Idan ka takura ni yin haka a gidan nan ka shiga hakkina Yaya Azeez.
To shi ke nan na hakura, amma in mun koma gidanmu ba za ki dinga rufewa ba ko?
Shiru ta yi ta kyale shi, inda Allah ya cece ta shi ne isowar mutanen Jimeta da aka zo aka fada wadanda suka wuni a hanya, dole ya tashi ya bar dakin ba don ransa ya so ba don sun soma tuttudowa dakin.
An yi suna na gani na fada a washegari a gidan marigayi Malam Abdullahi Dakata. Fulanin Jimeta sun hade da kanawan Dabo. Tafe suke da motocin gara mai ban mamaki ta aure daban, ta haihuwa daban har da manyan bajimai da ransu guda biyar a motar shanu. Aka dinga saukewa a tsakar gidan don dakin da Inna Hafsatu ta ce a zuba ya cika. Gidan suna sai ya koma gidan wani gagarumin biki don su kam kamar yanzu suke ji sun zo auren Hafsat. Baffa Atiku fada ya hau yi a kan garar nan a cewarsa an riga an wuce gurin kuma su Hafsat ba surukarsu ba ce yarsu ce. Daada ta ce sun san da hakan su ma ba su ce yarsu ba ce, abin da alada ta gadar ne suke son a yi musu alfarma su yi ko yaya ne. Shi kansa Abdulazeez ya sha bandiran shaddoji manya-manya, hatta Daddy da Mammah nasu daban, jariri akwati biyu fal da kayan sawa masu kyau da tsada, haka mai jego akwati guda na turamen zannuwa da lesuka. Kakanni ma ba a barsu a baya ba.
An ce wai ko kogi ba ya kin yayyafi wannan gaara ta yi wa iyalin Dakata dadi duk da ba su taba kawo hakan a ransu ba. Na Baffa Atiku daban, na Adda Hafsatu daban. Aunty Zuwaira ta zo suna don Uncle Abdulkarim ya bude mata wuta wannan karon kuma a kan idonta aka yi komai. Tana zaune a gefen gadon da Hafsat ta ke lokacin da Ibrahima autan su Mammah ya shigo ya ce mahaifin Hafsat zai shigo ganin jariri, sosai ta muskuta ta baza ido a kofa.
Prof. Bashar Mai-Jamaa Numan ya daga labulen dakin da sallama, zaratan matasan yayansa uku na biye da shi. Kwarjini da kamala da tantagaryar boko ya dallare idanunta. Ita da kanta ta dauki jaririn ta kai masa a kujerar da ya zauna daga can farkon dakin. Hafsat baki ya ki rufo, ga kunya tana ji wai ita ce ta haihu Abba ya dau jika. Imaamu na ta tsokanarta wai ta zama Maama, Abdurrahman ya ce jariri bai dauko su ba da ya fi haka kyau. Aunty Zuwaira yau har da cewa da Abdurrahman.
A gabana? Ai kuwa Abdulazeez ya fi Addah kyau, fari kawai ta fi shi.
Hafsat na kallonta a ranta tana mamakinta. Tunda ta taso ta san Aunty Zuwaira, ba ta taba yi mata kallon arziki ba, kalma mai dadi bata taba shiga tsakaninsu ba. Iyakaci ta gaisheta ta amsa a wulakance. Yau ita ce da yin wasa da dariya da yan uwanta don ta ga idon mahaifi. (Ya Allah ka barmu da iyayenmu ba don halinmu ba, ka kara musu tsawon rai da lafiya. Wadanda nasu suka rigaye mu Allah Ka sabunta rahma a gare su, ka jikansu ka yi musu gafara kama Rabbayaany saghirah).
Dr. Bashar ya dago ido ya dubi yarsa Hafsah cike da kauna.
Kina ina ki ka bari Abdulazeez ya kwashe komai shikadai bai sammana ko kadan ba?
Dariya ta yi ta rufe fuska, ya karanto adduoi ya tofawa baby. A bakinsa ne ma ta ji sunan yaro Abubakar-Sadiq (Khalipha) sunan da mahaifinsa ya zaba masa kenan.
Suna da kwana biyu yan Jimeta suka koma, yan Abuja suka soma nasu shirin. Adda Hafsatu ta yi tsalle ta dire ta ce nan za a bar mata masu jego ba za a lalata mata aiki ba. Mammah ta je tana mata wanka da ruwan (gass-cooker). Su tafi in ta yi arbain su zo su dauka. Mammah ba ta yi musu ba don ba ta jayayya da mahaifiyarta a kan komai, kuma ta yarda sai sun fi samun kulawa a nan fiye da wajenta.
Abdulazeez dama kwana uku zai yi ya koma U.S sai nan da watanni biyu zai dawo gabadaya.
A daren da su Mammah ke shirin komawa Abuja a washegari, shi ma a daren yake nasa shirin komawar. Jirgin da zai bi na asubah ne daga Kano, zai yi transit a Ethiopia. A dakin Uncle Idris na da yake kwana a soron gidan na farko. Wanda shi yanzu gidansa yana nan cikin gidajen likitoci na asibitin Malam, iyalinsa da su aka yi sunan Khalipha.
Mammah da kannenta mata hudu Luba, Mariya, Furairah, Murja da Hafsat dake can saman gado tana shayar da jaririnta. Sun saka mahaifiyarsu a tsakiya ana hirar bankwana kasancewar gobe ita Mammah za ta koma Abuja ita da Jummai mai aikinta, Abdulkarim da iyalinsa sun koma tun jiya. A cikin hirar ne Mammah ta sako zancen da ya dade yana cinta a zuci, ya kuma fi karfin a yi shi a waya sai yau da Allah ya hada su ido da ido. Ta dubi mahaifiyarsu ta ce.
Addah!
Ta ce, Naam.
Ki tambayi Mariya da Luba shin ko Saima da Halima sun tsayar da mazajen aure ne?
Addah ta ce, Ai da kunnuwansu, kuma sun ji ki.
Mariya ta ce. Halima sarkin ruwan ido? Tana nan tana ruwan idon nata wai mijinta ma ba a haife shi ba. Ni abin da ya sa ban damu ba ganin bana ne ta kammala secondary tana da sauran lokaci a gaba, amma Babanta ya fi so ya yi mata aure.
Luba ta ce, Saima dai akwai wani yaro da ta ke so, sai dai bana jin auren nan zai yiwu?
Mammah ta ce. Saboda me?
Yo, Yaya Maryamu tsiransu a haihuwa shekara uku, yanzu ne yake shekararsa ta farko a jamia ita kuma tana ajin karshe a secondary, sannan iyayensa sun ce ba za su yi masa aure ba sai ya gama degree ya yi hidimar kasa ya samu aikin da zai iya rike iyali. A matsayin Saima na mace yaushe za ta tsaya jiran wannan mijin?
Wata ajiyar zuciya Mammah ta yi cikin jin dadi, ta maida akalar zancen ga mahaifiyarsu. Adda ki roka min Mariya da Luba, su baiwa yayansu Usman da Haleem auren Halima da Saima, shi Ismael ya zabo wadda ta yi masa tuni, su kuma sun bani zabi da yake sun fi shi son kwanciyar hankalina. Ni kuma na hanga na ga gida ba ta koshi ba baa kai dawa ba. Yayan nan ina da su yammata har ukku, ban da Ismael ya kawo wata Wasila da sai a hada har Khalisa (yar Furera).
Hajiya maryam sai gani ta yi kannen nata sun fashe da kuka. Da fari ta tsorata kafin Mariya ta soma bayani.
Yaya Maryama anya akwai sauran mutane irinki a duniya? Yadda zumuncin zamani ya koma mutum ko ciki daya ku ka fito in shi ba shi da shi kai kana da shi ba ka jawo shi jikinka, neman yadda za ka nesanta kanka da shi ka ke, amma ke yayanmu za ki aura wa yayanki yan gata irin haka?
Ta ci gaba da kuka. Aunty Furera ta ce, Tunda Ismael ya kawo wadda yake so kada ki kara zancen Khalisa, da Saima da Halima da Khalisa duka daya ne. Yaya Maryama mu da yayanmu naki ne ba sai kin roke mu ba. Iyakaci mu gaya wa iyayensu maza saboda hakkin haihuwa. Allah ya tabbatar mana da wannan abin alkhairin. Ya sa zumuncinki shi ne silar shigarki aljannah.
Adda ma albarka ta yi ta sa mata, ta ce, Maryam har gobe ina alfahari da haihuwarki, daya tamkar da goma. Allah ya albarkaci gabanki da bayanki.
Sun tsayar za a fara yin bikin Ismael da Wasila, Usman da Haleema in sun kammala hidimar kasar da suke yi. Zaa jinkirta na Haleem da Saima sai ya gama karatunsa nan da shekara biyu lokacin ita ma ta gama secondary watakila har ta fara tertiary. Hafsat na gefe tana jinsu tana shayar da danta Khalipha ita ma abin ya gamsar da ita. A ranta ta ce Fitinanne ya je ya nemo yar Abuja haka za ta zo ta fitine su kamar yadda ya fitine su.

Suna haka suka ji sallamar Abdulazeez, dare ya yi sosai don sun soma jin barci ma. Aunty Murja ce ta amsa masa Mariya sai harara. Kai kuma lafiya da tsohon daren nan? Kai da ke da tafiya a gabanka da asubahi ya kamata a ce yanzu ka kwanta.
Hafsat na ganin shigowarsa ta yi maza ta cire yaron ta gyara rigarta. Ya dubi Aunty Mariya cikin lallashi.
Wai don kawai na ce bai isa goyo ba ki ka dauki gaba da ni haka?
Ta ce, Au, wato haka ka ce ko? Wallahi sai in fallasa abinda idona ya gane min....
Da sauri ya ce, Mammah ki bata hakuri, kuma ni ba da wani nufi na ce Khalipha bai isa goyo ba, don kada ya samu gocewar kashi ne kasancewar kashinsa bai yi kwari ba.
Mariya ta ce. Ita Addar har a bakwaininta mun goya ta a Saudiyyah, nata kashin ya goce? Balle wannan shekararre a ciki?
Wani irin bata fuska ya yi. Ni Dana bai shekara a ciki ba.
Mammah ta kalle shi, sai da ya ji kunyar da yake jin ba shi da ita yanzu. Ya hau shafa kai ya ce. Wai sallama na zo muku.
Mariya ta ce. Ka zo mana ko ka zo musu?
Dukkanku.
Ta ce To, mun karbi tamu. Allah ya kiyaye hanya. Ke Addah ku je daga falo ku yi sallamar mu muna magana.
Ya kuwa juya ya fita yana ce da Anty Mariya. Dadina da ke zuma ce, ga zaki ga harbi.
Ta ce, Ka ce min kunama ma duk daidai da kai ne.
Ci gaba suka yi da maganganunsu, Murja ta lura Hafsat ba ta da niyyar tashi ta dube ta ta ce Addah ba jiranki yake yi ba ne?
Anty Mariya ta ce, Bar munafuka jira ta ke sai an maimaita don a ce mata saliha, ni yau a tafin hannuna suke.
Da sauri Hafsat ta zura hijab ta sauko daga gadon ta doshi kofa saura kadan su yi dariya amma ban da Mammah, magana suke ita da Adda Hafsatu.
A falo ta tadda shi a zaune da alama a kagare yake da zaman jiran da ta sa shi. Yana ganinta ita daya ta ce. Koma ki dauko shi.
Kamar za ta yi kuka ta ce Ni wallahi ba zan iya dauko shi a gabansu ba.
Mikewa ya yi ya koma dakin, sai ga shi ya dawo da yaron a hannunsa ya zauna yana ta aikin kallonsa. Can ya lura har yanzu a tsaye ta ke kamar a ce Kyat ta arta a na kare. Ya ce, Kin min kerere a ka!.
Ta dosana can nesa da shi ta zaune a dofane. Wani haushi ya kama shi ya zube shanyayyun idanunshi a kanta.
Is that the kind of farewell you choose for Us(wannan ce irin bankwanar da ki ka zabar mana)?
Ya yi maganar ne cikin kwantaccen sauti yana danne bacin ransa.
To wace iri za mu yi? Ita ma ta tambaya cikin irin yanayin da ya yi tasa tambayar.
Au tambaya ta ma ki ke yi?
Ta mirgina kai, Yaya Azeez we are not alone. Muna tsakiyar iyayenmu ne, please ka tuna wannan.
Su suka ce ba za mu yi sallama ba saboda suna nan?
Ba su ce ba,we are to make use of our senses, mu yi abinda ba zaa ga rashin kawaicinmu ba.
Muryarsa a sanyaye ya ce.
Madame! Yanzu ni me na yi na rashin kawaici? Ko dakin da nake ban ce ki je ba, ko soro ban ce ki je ba. Im going thausand miles away, amma ko kusa da ni ba za ki zauna ba. Ba za ki zo mu kalli Khalipha tare ba. Ba za ki gaya min abin da zan ji dadi ba in dinga tuna shi yana debe min kewarku ba. Guduna ki ke yi kamar zan sace ki, in wannan ita ce kunya, toh Allah wadaranta! Wuce ki ba ni waje, Allah ya hada fuskokinmu da alkhairi.
Kasa tafiyar ta yi duk da kafin a yi hakan ita ce abin da ta fi so ta yi, sai hawaye da ta soma sharewa. Bai kara bi ta kanta ba ya ci gaba da kallon Dansa yana sumbatarsa. Daga karshe ya mike ya shiga da shi ciki ya kwantar ya zo ya wuce ta ya fice.
Ji ta ke kamar ta bi bayansa ta bashi hakuri, amma ta san ba za ta iya ba. Hawayenta ta share da gefen hijabinta, sannan ta shiga dakin. Daga ita sai Mammah suka kwana a dakin, tana daga kasa kan carpet. Dukkansu a daya bedroom din suka kwana, Addah Hafsatu da ma (kwana sallah) ce kaman Dadanta.
Washegari gida ya watse kowa ya koma inda ya fito. An nemi wayarta kafin a gano Abuja aka baro ta, Mammah ta ce za ta bayar a kawo mata ko za ta sayi sabuwa? Ta ce a barta, yanzu kam ba ta da bukatarta, in za ta yi kira za ta yi amfani da ta Adda. In za a kira ta a kira Addan ta ba ta.
Ta fadi hakan ne sanin halin kayanta, in ya yi fushi da ita punishment dinta a yi barring dinta zuwa sanda aka ga dama.

******
Alhamdulillah! Yau Abubakar (Khalipha) ya cika kwana arbain a duniya. Sun yada wanka. A washegarin ranar gidajen yan uwa suka wuni. Uncle Ibrahim ya kakkaisu har AKTH gidan Dr. Idris Dakata. Mammah ta ce da Adda Hafsatu Hafsat ta shirya ta wuce Jimeta daga Kano ta yi sati daya sannan ta koma Abuja.
Ibrahim autan Addah shi ya kai su filin jirgi ya yankar musu tickets ita da Zulai mai sa mata ruwan wanka wadda tsohuwar mai aikin gidan Malam Abdullahi Dakata ce. Ita Adda ta sa ta rakata Jimeta don ta taimaka mata da hidimar Khalipha. Sun samu Imamu na jiran saukarsu ya dauke su zuwa Demsawo.
Dangi sun ga Khalipha sun more. Haka ake kwantar da shi a gefen buzun Mallam a kan yar katifarsa mai laushi wai ya je taya shi hira. Su ne har Numan, daga karshe a gidan Abbanta ta kwana biyu. Suka dawo babban gida Daada ta soma yi musu shirin komawa. Gyaran haihuwa ta ke mata bana wasa ba irin na fulanin usli da nono da madara da tukudi da hakukuwansu na gado. Ta kuma yo mata guzurinsu. Ranar Lahdi Abba da kansa ya kai su filin jirgi shida su Modibbo. Aka sa Zulai a jirgin Kano, Hafsat da danta a jirgin AZMAN mai zuwa Abuja.



SUMAYYA ABDULQADIR TAKORI
07030137870

*Littafi na farko shine kawai free. 234 na sayarwa ne. Idan ka fidda 234 ba sai na hada ka da Allah ba zai isar min insha Allahu. Ku biya Ku karanta a nitse cikin farin ciki yafi maka kayan zunubi ranar gobe kiyama*
*****
Hafsat ta iso Abuja lafiya ta tadda dalleliyar kankanuwar motarta tana jiranta. Tafiyayya tun daga General Motors din Amurka, sakon Baban Khalipha matsayin gift dinsa na haifa masa Abubakar Sadik. Usman ne mai wannan bayanin ganin ta tsaya tana shafa motar tana tambaya ko Daddy ya yi sabuwar mota ne?
Maimakon ta yi murna, kunya ta yi ta ji ba ta kara zancen motar ba. Ismael ya ce, in ba ta so ta ba shi ya samu ta kai Wasila shopping. Harara ta dalla masa, Mammah na bada baya ta sassauta murya ta ce da shi.
Ashe ba sonta ka ke ba, tunda ba za ka iya saya mata mota ba.
Tafi ya yi har sau uku. Cikin ransa yace haihuwa ta bude idon Addar su. A fili kuma a yace Sannu matar so! Ki bari in samu aiki ki sha kallo, Wasila ta fi karfin mota wallahi, private jet zan gwangwaje ta da shi in ta haihu. Ki ma daina murna wai SO ne ya sa aka siya miki, wallahi arzikin Sadik ki ka ci, da can me ya hana a saya miki aka bar mu muna jigilar kai ki makaranta da dauko ki?.
Ismaeel ya kunnata yadda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login