Showing 66001 words to 69000 words out of 158722 words
Chapter 23 - Tantiriya A Gidan Yari Book1 Hausa Novel Complete
Jamilu?
Naila hankali kwance ta juyo ta bankaro mata kirji tace Kalli kirjina me kika gani? Beauty tace nono,tace mashaallah to Allah ya albarkace ni da su gasu Nan mashaallah,Kinga kina da su kema,bani bra na saka ma,Beauty tace dama Kai mace ne Jamilu? Naila tace wlh haka Allah ya nufa ko na cire wando ki gani? Beauty da mamaki tace ya akayi kika zauna a gidan Maza.
Ni mamakin ma da nake da ka iya kallo na ba kunya ba komai kace macece,wai baki ji nauyi na ba? tsakani da Allah daukanki nayi da har zanji wani nauyinki,Beauty murmushi tayi tana kallon Jamilu mace kyakyawa tace wai yanzu yaudarata da kayi baki ji komai ba irin kunya? mene haka da suna Kunya? Menene ma'anarta, Beauty a ranta tace wannan ta fini iya iskanci,a fili tace amma kinci amanata,Kinga ki kawo min bra da abincin kawai,Beauty ta ajiye tire ta fice ranta na suya ta dakko bra ta dawo sannan ta kawo abincin Naila ta kwashi girki sannan ta cire rigarta ta saka bra ta Maida kayanta, ta shiga bawa Beauty tarihin rayuwarta da shiga gidan yari har fitowarta yau,Beauty ta tausaya tace kin bani tausayi Kuma na miki uzuri a abinda kike yi,yanzu ita Mummy din ya za ayi da ita? Naila tace wata zan samu na turata a matsayin Yar aiki gidan asalin wacce ta haifi Ashraf ni ta kansa zan fara,so nake shima ayi Masa sharrin kisa a kaishi prison,tare zamu je Abujar ni Kuma gidan ogar zanje Mummy,wannan Dan nata sai na sumar Masa da Hallare dinsa ta daina amfani zai ci ubansa,Beauty ta sheke da dariya harda shewa tace baki San ma me zaki Masa ba,Naila tace abin ne yayi min yawa sai dai naje Abuja tukun sai naji tarihinsu sai nasan ta Ina zan fara ramawa,Beauty tace to a kira Chikar gayu mana kuje tare,fitsararriya ce bata tsoron uban kowa, Naila tace nima shegiyar kaina ce fitsarriyarce,ke bani da mutunci,ni kadai ma na ishi kowannensu amma duk da haka a kira Chikar Gayun Nan da kwana biyu mu wuce idan zata yarda,amma ke zaki bamu tallafin kudi,Beauty tace babanmu Yana da gida acan da masu aiki da masu gadi kawai ku zauna a nan ba mace a ciki a banza ake gyara shi,kawai dai a samu kudi ayi miki dinki na manyan yara,sannan ya kamata ki koyi mota a can akwai na Daddy na ki dinga ara idan ta kama,Naila tace godiya nake sabo da ni kaina ban san me zanyi ba ma sai na je tukun,na fara Jin tsoron kaina Beauty Ashraf bazai ga da kyau ba,to kije musu a me kudi,Kinga baza su taba ganeki a shigar mata ba,sannan kina daukan wanka kinga kin canja salo kenan da an sanki a namiji yanzu a mace zaki fito Kuma ki boye kanki kar a gane kece,Naila tace tab ai Murya zan makale wlh ko Spark sai yayi da gaske zai gane ni,yanzu ni Kuma ya za ayi dani yaudarar da kika min? Har kuka nayi a kanka Jamilu wlh Ina hangoka a namiji me damatsa da faddan kirji, Kuma yanzu Daddy ya bani 2weeks cikin masoyana na fito da wani,Naila tace to ba sai ki zaba ba,ai Banda Wanda nake so,kiyi hakuri ki jira Kiga zabin Daddy idan bai miki ba ki fada min master planner ce ni sai an rushe auren.
Beauty tace na yarda da ke wlh tunda kika shiga gidan Maza kika fito lafiya ba kamarar Tantiriya bace ke,Naila tace ta can ciki ma kuwa,Chikar gayu suka kira nan take ta dauka,Beauty tace aiki ya samu fa tawan,Chikar gayu tace kice na bar Kaduna na taho Beauty tace ai nace zan zo,a'a tsakani da Allah dama na gaji kin san ni dama ba wani mafadi ne dani ba zanzo kawai gobe turo min kudin mota,Beauty tace to angama,Naila tace Shegiya me kudi gashi sai gudanar da abubuwa kike da kanki,kema ai zaki kudin idan kika auri Spark,Naila tace wlh ai da na fara baje Masa ai shike nan Kuma sai arziki dama tsohon tuzuru ne kadan yake jira Dan banzan da wani blue blue eye ai yaron nan na gana Masa azaba a gidan Dan kande ,na dinga jona Masa chaji sai kiga ya dauka Yana signa,Beauty ta sheke da dariya tace saurayin da kike so ma kenan kina zaginsa,Naila tace ai Ina aurensa bakina kanin kafata,oh ashe Spark soyayya kuka kulla,Naila tace bai fa ce Yana so na ba nima ban fada ba,Very soon zaku furtawa juna ne,Allah yasa number dinsa nake so na Nemo wlh,ya gama yarda shi zai fitar Dani giyar so na kwankwanda wannan fitowar da kika ga nayi ta ba a hayyacina na fito na,ai duk cikin Mayen giyar so ne yasa nayi zuciya na fito.
Nan suka lalace suna Hira har dare sallah ce da cin abinci ke tashinsu,ana idar da Sallah Naila tace anjima zaki kaini wani aiki wajen budurwar Abbanmu ita zan cikawa aiki na kafin na bar Kano,Karfe nawa?10pm mu dawo 2am, Beauty ta zaro ido tace kawai ki shirya karki tsorata, ni sai dazu ma na tuna gidan su Batoola Ashe gidansu kusa da gidan Yaya Mohsin ne,anyway ma dai yau zan gama da auren Nan.
Beauty tace anya kuwa ba shedanu ne suka shiga jikinki ba duk ke kadai zaki wannan aikin? ga gidan yari kin fito yanzu Abuja zaki je neman fansa,ga Budurwar Abbanku gashi kince kina gamawa zaki dawo wajen matar Yayanki,Naila tace ki zuba Ido ki gani,yanzu Jallabiyya zaki samo min fara,sai dai ta babanmu,dakko min aronta Beauty ta dakko Jallabiyar Daddy dinsu,tace saura farin Chalk,a daren nan suka Nemo abinsu komai da komai,Naila tace muje ki kaini yanzu zuwa 2am idan na fito na ganki a kofar gidan kina jirana da mota,Beauty tace an gama.
Naila kayanta ta cire ta saka Jallabiyar Daddy, ta dauki garin chalk dinta a leda da cumb,da wata color kamar jini tace muje,Beauty ta shiga mota ta ja suka tafi abinsu sai ungunwar su Mohsin,suna zuwa Naila Hijab ta Kifa a kanta sannan ta fita,gidan su Batoola a bude dama daga ita sai dattijuwar babarta a gidan sai wani tsoho tukuf babanta Wanda baya gani ma sosai.
Naila kamar abin arziki ta shige gidan,Tsohuwar da tsohon suna daki,Batoola an tafi gidan suna Naila ta shige dakin Batoola da yake a bude ta turo kofar kadan.
Wani ruwan color kamar jini ta yarfa a Jikin mudubin dakin Batoola kamar jini yayi tsartuwa,ta samu dakin ta hargitsa kayan ciki tayi kaca kaca da kayan dakin Batoola,sai 10pm taji Sallamar Batoola tana cewa Hajiya na dawo ni Kam na gaji sai da safe bacci zanyi,Naila da sauri ta samu tarin kayan wanki ta shige ciki ta rufe kanta ruf,Batoola tana shugowa tana wakarta.
Ta hau cire Kaya Naila ta leko da kanta kadan tana kallon Batoola,ita dai Batoola da hasken waya ta haska dakinta ta tube har bra dinta,Naila tace ji nonon shegiya sai kace kwababbiyar flour da za ayi meat pie irin an gama tabileta a inji,a haka take so Abba yazo ya jawo mana asarar kudi,Abba idan zaka lallaba na Umma ka hakuri da shi to,ni na kasa ganewa Maza kana da mace da yaranka kana wahala wajen ci da su da kyar ake Sha amma wai ka tafi neman wata macen,nifa na kasa gane muku Maza tsakani da Allah ahhh cewar Naila a ranta,tace shegiya ji cikinta duk da gani ta zazzagar da yara duk yayi spring yayi wani dabbara dabbara ayi fatar cikin bawa ta wani cuccure ba excesise ko wacce sai dai taci ta koshi ta kwanta,Dan motsa jiki irin na ciki da akeyi Yana damewa ya danyi kyau matanmu mu basa yi.
Batoola kayan bacci ta saka ta fada Saman katifarta,Naila tace ashshaa dole Allah ya bani sa'a a kanki shi yasa na samu damar shugowa Bata azkhar sai wake wake katifar ma baza a karkade ba ko da shedanu a Kai kawai an fada Kai,ai kuwa zaki ga shedanu yau,Batoola dai Bata San da kowa ba,wutar nepa aka kawo ta mike zata kashe kwai kawai taga jini a Jikin mudubi sai lokacin ta kula da yanda aka hargitsa mata dakin,tace menene haka jini,tsoro ne ya kamata tayi Maza ta kashe wutar ta kwanta ta lulluba da bargo jikinta na rawa,ta tashi ma ta fice ta kasa sabo da tsoro,tana haka bacci ya kwasheta wurin 2am lokacin gari yayi tsuuuu kowa yayi bacci an kulle kofar gida da Naila a ciki,a hankali Naila ta fito daga Inda take boye,ta lallaba ta zare key din dakin Batoola ta bude kofa ta fito Sadaf Sadaf taje ta bude kofar gidan da aka kulle ta barshi a bude ta dawo garin chalk dinta ta shafe fuskarta da shi ta cire Hijab dinta ta jefo shi tsakar gida da chalk din da wannan kalar Jinin.
Bulalar data shugo da ita ta daga ta tsulawa Batoola,a firgice Batoola ta bude idonta taga dodo sak Aljani gashi gashin Naila ta tashe sama kamar kayar bushiya,ta canja Muryar aljanu......tana zaro harshe kamar mayya tace bamuuuu... yardaaaaa.... kiyiiiiii....aureeee...baaaaa.....ko....zakiiiii ...aure.....to.oooooo......ki.....auri wani.....mun....lamunce.....ta sake zabga mata bulalar taci gaba da magana......amma.....Banda.....Hashimu Dolo .......bazai....iyaaaaa....ciyar....daaaaa ke.....ba...muuuuuu...Kuma....muna...kaunarki.....tunda aka haifi kakanki na talatin.....muke.....tareee....dakuuu....bama....son...abinda....zai ..tabaaaaaa.....mana ke....idan...Kuma...kinki ji....zamu...bawa.....sarki jininki....ya....shanye....Naila ta nuna Jikin mudubi da yatsa...ta sake zaro harshe waje kamar karya tace....waccen....Jinin...tsohon mijinki ne.....sabo ..da ya Saba mana umarni muka aika shi lahira....sarki ..ya shanye jininsa......ki....tabbatar kin fadawa.....Hashimu Dolo....kin fasa aurensa....Kuma....kiyi gaggawar......fitar da miji cikin sati daya...kiyi wani auren.....karki bari ni....na dawo ..na samu... Baki auri wani ba amma Banda Hashimu Dolo ... yanzu zan tafi kasar Ethiopia mu asalinmu a can muke.....Hallaren Hashimu baza tayi miki ba ....sai dai tsofaffi.....Naila tayi wata dariya tace....karki bari na dawo baki da aure.....sai ta canja harshe ta koma fulatanci tafi minti talatin tana fulatanci a kan Batoola,karshe cikin tsawa tace kwanta ki lulluba ta sake tsula mata bulalar tace lulluba da bargo....wannan bulalar da muke miki.... ta karban dubu goman Hashimu Dolo ce.....da kika ce zaki anko......Bama son karya.
Batoola ta hada zufa sharkaf jikinta Yana uban bari ko wacce addua tazo bakinta karantawa take tace bazan aure shi ba wlh dama Ina da wani Usman nafi sonsa ma,Naila tayi haushin kare wan... wan ...mun sani... ba sai kin... bamu labari ba ...sannan tayi fulatanci tace zan... koma suffata ta aljanu..... Wacce Allah ya halicceni da ita kina kallona zaki mutu.....zaki mutu...
Batoola magana ma ta kasa ta rufe kanta cikin bargo jiki na bari karrrrr karrrrr, Naila fit ta fice ta kwashe Hijab dinta da tarkacenta da tazo da su har bulalar ta tafi da ita ta fice da gudun gaske lokacin Kuma yaran Dan Indo suka sake zuwa bincike suma cikin dare Neman Jamilu suna fara buga gidan Naila ta fito daga gidan su Batoola da uban gudu kamar zata tashi sama ga fuskarta duk chalk fari tas ga gashinta buuuuu.....ga farin kaya,ai suma yaran Dan Indo sai gudu suka rasa ta Inda ma zasu shiga motar tasu, jiki na bari suka bude kamar zasu ballata suka shige,Driver hannu na mazari ya kasa saka key dinma Yana hakki Yana karkarwa Yana cewa wlh bazan sake zuwa unguwar nan ba ko me Dan Indo zaiyi sai dai yayi,wani aciki yace ka ja mota dalla Aljanu ne suke wasan buya buya yau a..,driver ya fisgi mota suka fita a million,sai da suka yi nisa wani a ciki yace tunda nake ban taba ganin aljani Ido da Ido ba sai yau,Kai kaga wani gudu wannan gudun ya wuce na mutum.
Bangaren Naila tana bi ta lungun da tace Beauty tazo ai kuwa tana zuwa Beauty tana jiranta a mota,Naila ta bude kofar gaba ta fada tace muje na gama da wannan case din, Beauty sai dariya take Naila ta yayyafa ruwa a hijab din ta goge chalk din tare da yafa mayafu, Beauty tana sharara gudu sai ga yaran Dan Indo suma a kwalta kamar zasu tashi sama sun wuce a million wani yuuuuut.....Beauty itama ta Kara take gudun motarta tace ko barayi ne suka biyo su wannan gwara muyi ta kanmu,Naila tace naga wasu fa kamar suna dukan kofar gidan Mohsin dina ko su ne oho dake a hargitse nake shi yasa,suna komawa gida sai bacci kawai.
Batoola kuwa sai da Naila ta Dade da barin gidan sannan ta mike a hankali ta fice fit daga dakin ta fada dakin su Tsohuwa tana cewa aljanu aljanu...zasu kasheni....Dattijon suka tashi suka dinga zazzagawa Batoola fada suna cewa ai kece Azkhar yayi miki karanci ke dai wake wake kawai,ance ki gyara halinki kinki ai gashi nan,ke dai sai waka babu Azkhar da addua sallah ma sai anyi yaki Dake kullum kece hada sallolin hudu a lokaci daya,ai gashi nan,Tsohon ya shiga tofawa Batoola Ayatulkhursiyyu Yana cewa bakya karanta Ayatulkhursiyyu shi yasa,Batoola tace wlh da na ga Aljan din na karanta yafi sau dubu amma ko gezau,wai fada min suke fa kar na sake na auri Hashimu Dolo,wallahi na fasa zan auri Usman din yafi min na hakura da son sai na juya miji,ga dubu gomansa ta anko da dansa ya kawo a Maida Masa abarsa,babu ni ba Hashimu Dolo har abada,aljanuna basa kaunarsa Sam sunce ina aurensa zasu kashe ni wai sune suka kashe tsohon mijina,Dattijon yace wanne irin rashin tsoron Allah ne Batoola ai aljanu ma Allah ne ya halicce su idan Allah ya kaddara sun isa su Hana ne, Batoola da sauri tace nidai nice me auren Kuma ni zan zauna sabo da haka wlh na fasa,ga bulala Aljanin ya dinga zuba min kamar da karfe yake dukana na hakura indai Hashimu dolo ne,sunce kar na wuce 1weeks banyi aure ba,ai Usman ma mutumin kirki ne Kuma Yana da aikin yi duk da matansa biyu ace ya turo,zan fada Masa in ya shirya nan da sati sati,Dattijon yace ai dama na fada miki Hashimu ya miki tsufa kika ce ke Wanda zaki juya kike nema ai gashi Nan,sai ki fadawa Usman din ya turo,ranar Batoola tare da iyayenta ta kwana daki daya.
Da sassafe Batoola ta fito ta nufi gidan Mohsin da dubu gomansa a hannu tayi sallama,Hanan ta danji sauki tana kwance a Palo amma da kyar take gani,Batoola ta shiga ta samu Mohsin Yana hada tea,yace ah Aunty Batoola sannu da zuwa,gaisawa suka yi ta mika Masa 10k din tace gashi ka mayarwa Abbanku ka fada Masa na fitar da miji yayi hakuri na fasa ni dai bazan aure shi ba,Mohsin yace a ransa ko dai Naila ta cika aikin ne,sai ya hau dariya a ransa yace Alhmdllh haka kawai zan sake dakkowa kaina masifa ai sai Naila Allah ya tsare min ke,a fili kuwa yace ba damuwa zan fada Masa amma ki rike kudin an bar miki,Batoola da sauri tana karkada Kai tace a'a la a'a ku rike abinku ta ajiye a Saman kujera ta fice,Hanan ta tabe baki a ranta tace Umma an shiga malamai,ai baza su taba yarda a aureta ba,naji haushi wlh hmmm har naje mun gama hada baki da Batoola yanda za a ganawa Umma azaba a gidan miji ta zama ita da hoto daya amma jarabar shegiyar ta fada malamai zata haukata Batoola Allah yasa Abba ya gano wata,Mohsin ne ya katse mata tunaninta yace kina ganin Batoola har ta tafi ko gaisawa bakuyi ba Kuma naga kwana nan Kun zama kawaye,Hanan a ranta tace dama kawancen namu na yanda za gallazawa uwarku ne idan ta kama ma a saketa kamar yanda nima tasa aka sakeni ashe ta tafi kauye wajen Ubanta ya hada asiri ansa Batoola ta dole ta fasa ba komai bari a samo wata,Mohsin Yana kallonta kamar tana magana a ranta bai dai ce komai ba ya kwashe 10k ya zuba a aljihunsa.
Naila ce ta kira shi ya tashi tsam ya fice daga gidan ya koma kofar gida sabo da Hanan kar taji sirrinsu, kashewa yayi ya kirata back,tace Yaya my love ,yace Na'am ya a Ina kike ne? Naila tace wajen Baby Beauty ta gane gaskiya yanzu tasan ni Macece mun zama kawaye Ina gidansu,Mohsin yace Abu yayi kyau,tace ai na gama aiki jiya a kan Batoola,Mohsin yayi dariya son ransa yace har 10k din ta dawo da ita dazu wai ta tsaida wani ba dai Abba ba,Naila ta sheke da dariya ta dinga bawa Mohsin Labari yanda ta aikata komai,yace in kina Abu kamar ba Yar gidan Hashimu Dolo ba,Naila tace Dolo ya haifi me basira ai Alhmdllh,suna ta hira tace saura Abuja kafin na dawo kanka nayi waje da Hanan,matar tawa ni ban saketa ba ki sakar min mata,Naila tace Kai Yaya baka da zuciya wlh akan Jin dadin Hallare sai ka zauna ana Maka anyhow,wlh bazan yarda ba sai na dauki mataki ni,yace to ai zan gani ya kashe wayarsa.
Ranar Kuma Beauty ta fara koyawa Naila mota,Naila da naci ance an gama na yau ta taho amma ta rike mota tace jeki ni zan kawo motar gida,Beauty tace tab kika fasa min mota Daddy sai yaci ubana idan ya dawo,tun safe suna filin har dare sannan Naila ta bari aka dawo gida,suna zuwa Chikar gayu tace sai nan da sati zata zo an hanata fitowa yanzu.
Naila tana gidan su Beauty ga Daddy baya Nan a nan take cin karenta babu babbaka tana aikin koyon mota ba ji ba gani,Kuma Beauty ta zuba karya ta karbi kudi wajen Daddy dubu dari da hamsim aka samu Dan kaya masu kyau aka siyawa Naila kala biyar,Leshi,biyu,shadda biyu da atamfa,sai takalma da jaka kala uku,harda su agogo da glass na sawa a fuska na Yan gayu, Naila tace akwai tsiya a Abuja,Sati daya Chikar gayu tayi karya a gida tace aiki ta samu a Abuja zata je ta a mata screening,ana ta murna a gidansu sabo da suna