Showing 15001 words to 18000 words out of 158722 words
Chapter 6 - Tantiriya A Gidan Yari Book1 Hausa Novel Complete
ji,Naila ta karaso bakin kofar tana murmushi tasan dama tunda taji ya kwantar da Kai to da dalili,tace haka kawai na bude ka zaneni aradu bani budewa,yace na fasa na huce,tace anya Yaya to rantse, yace wallah kinji na rantse haba My sweet sis, budewa tayi, ya waro idanu ganin yanda ta canjawa furniture din dakin wajen zama ta gyara bed ta dame shi yayi masifar kyau,yace ai ko Dan wannan gyaran bazan zaneki ba.
Ina kika samu tsintsiya da mopper? Naila tace naga matarka kazama a daki ta barsu sabo da kazanta da ganda tayi aiki da safe ta barsu a daki,kaga a toilet na ebo ruwa a famfo na zuba Omo duk a toilet na gani Kalli yanda yayi kyau ko uwarta Abu me man kuli baza ta iya irin aikin nan nawa ba,bakinta ya bige taji zafi,yace bana son rashin iya maganarki ki dinga zagin mutane kina ambatar sunan iyayenta kina zagi,Bai dace ba matar yayanki ce yanda zaki min biyayya haka zaki mata to nima ba biyayyar kike min ba bare ita,ki daina kinji ko ba tarbiyya bace wannan sannan wannan shigar da kike shi yasa ake ce miki Yar kauye bana Jin dadi in ana miki haka,nace muje na kaiki Saloon a gyara miki gashin kinki yarda,Umma tace ki tsaya ta taje miki kinki kowa yace ki bari a gyara miki kinki ji sai dai ki wanke shi a cukurkude babu sharcewa ba komai da ya bushe a haka zaki tufke abinki, Naila tace zafi Yaya ni bazan yarda ba wallahi akan a taje min gashina gwara a maidani kauye,ai sai da nace baza ku iya rike ni ba ka wani je ka dakko ni a dole ni wlh bana son birnin nan,gwara Ina kauye da yanzu nayi ashar tafi million amma anan ba dama sai da dalili ake ashar haba rayuwa tayi tsanani ba freedom ba kolabo,ni wallahi na gaji,sau daya ne aka taba cinye ni a caca badan na tafi da wasu kayan ba da zigidir za a min sabo da suturar da take jikina na saka a caca.
Mohsin Allah birni ba dadi ba kolabo iskancin banza suke yi na karya suke yi iskancin,Allah wallahi saura kadan Yaya na sa budurcina a caca,Mohsin ya saki salati da sallalami yace ke wai da gaske kike? Ni Ina wasa ne wlh da gaske nake yi Maka a dajinmu mata da Maza caca suke yi har matan aure, ranar da nace na sa budurcina a caca ranar kazo ka dakkoni,samari sunyi ca kowa ya shiga cacar ko zai dace harda dattijai sun shiga cacar kawai kuka zo daukana shi yasa samarin kauyen suka ce duk ranar daka koma wallahi sai kasha ruwan sanduna tunda ka cuce su,Kai ka sanni kuwa kowa respecting Dina yake a garin babu kamata,ga iya wankan gayu,ga kyau gani chass Umma ta haifi yarinya,babu me taurin kaina duk garin shi yasa aka sa min tantiriya amma ni ba yar iska bace fa,banyi komai ba kalau nake Yaya fess nake ba abinda ya faru da budurcina.
Mohsin sai da ya gama sauraronta sabo da idan ko yaro ne yazo da shirme ka saurara maybe akwai abin dauka ko na gyara sai a dauki mataki,yace ai bamu San haka kika lalace ba Naila,Naila tace ai na wuce haka ma,mu da muke zama a cinyar Maza watarana ma Affa ne ya min duka yace idan na sake sai ya yanka ni,shine ban Kuma ba,Mohsin ya saki salati yace Allah ya hadaki da mijin da zaici ubanki yayi maganinki Naila,dariya ta sheke da shi tace sai dai naci nasa uban Yaya,idan ba duk Wanda ya aureni ya auri masifa da kudinsa ba Allah ya konani,Mohsin yace Baki hadu da Wanda ya fiki bane,dole kizo ki buwaye mu ashe kin lalace da yawa
Naila tace ba karamar lalacewa ba Yaya Dan Allah yasa ma na tsaida Sallah wata daya da suka wuce,Mohsin ya sake bude Baki yace dama bakya sallah duk shekarunki har Sha Tara 19yrs to 20yrs? Naila tace wallahi sai bana Allah ya nufa,ai azumi ma sai shekarar Nan data wuce na tsayar da shi amma duk na karya nake yi sai na buya na Sha ruwa da Koko,watarana Kuma idan naje kiwo sai mu kafa baki a nonon saniya direct musha mu koshi.
Dan Allah full stop zo ki tafi gida goma tayi,a kauye ma sai na Kai 12 na dare a waje muna wasa bare Nan birni fitila ko Ina gari kamar rana,to naji ke duk turancin da kika iya a Ina kika koya? Makaranta mana,na yarda ai kina da brain,bature ne yazo dajinmu yawon bude Ido Ina zuwa makaranta,sai watarana zan baka labari,yanzu ka kaini gida Yaya,bacci nake ji na fada miki ki shiga napep,to kuwa sai dai na kwana,tsaki yaja yace jeki Palo bari nayi wanka nazo,Palo ta dawo ta zauna tana kallo har yayi wanka ya fito cikin 3qurt fari da t-shirt brown,yace muje mana kina ta kallona kamar baki sanni ba.
Naila tace, kayi kyau Yaya Ina ma ba Umma ce ta haifeka ba,gaskiya Umma Bata kyauta ba ta cuceni data haifo ka Kuma ta haifo ni ai sai ta tsaya idan ta haifeka ma ba laifi sai ta bari ni a haifeni a wani gidan can sai mu hadu sai muyi aurenmu ko ya kace,ai haihuwa ta mana illa kawai yanzu sabo da Allah sai a haife mu a gida daya the same father and mother haba haba,ai da ba gida daya bane ni nasan ma da Kai zan hadu dole in aureka, da anga 'Ya'ya wai wai zuky, dariya ce ta kwacewa Mohsin sabo da suna masifar kama da Naila duk gidan sunfi kama kowa ya gansu basai ance Yan uwa na jini bane.
Dariya ya dinga yi sosai tana kallonsa tana murmushi Yana dariya yace taso mu tafi ya riko hannunta, ta mike ta dauki sandarta da bata mantawa da ita,shi ya manta ma da shegiyar sandar yasan wannan sandar baza ta kwatu ba,ya bata rai yace ajiye sandar nan,haushi taji tace idan baza ka kaini ba ni zan tafi a kafa,ba yanda ya iya haka ya fitar da machine dinsa lifan.
Tace ban iya hawa machine ta gaba ba mu zaman dare muke a kaikaice muke Hawa, Yaya sai an dorani,ko Affa dorani yake yi,tayi tayi ta kasa hawa sai faman juye juye takeyi da kyar dai ta hau ta juya Masa baya maimakon ta Kalli gaba sai ta Kalli baya ma'ana sun hada baya da baya,ga sanda sakale a wuyansa, Mohsin yace wallahi idan kika fado ba ruwana Dan iskanci kinyi kusan wata guda a birni kina kallo yanda ake Hawa machine sai ki juya baya zaki fado kinji na rantse"
Naila tace to Yaya kaifa yayana nane na jini yanzu idan na juyo Enndu(Boobs) Dina suka taba jikin ka fa,mu mun iya hawa machine a haka,yace ke kika san Enndu shashasha, yaja machine dinsa suka Kara gaba ana ta kallo ta zauna daram amma dole ta rike machine din ta Dafe da hannaye biyu sanda Kuma ta tsakiyarsu a kwance.
Tana ganin me tsire Yana yawon dashi a Kai a bude tace Mohsin tsaya na siyi tsire,da karfi tayiwa me tsire magana Kai me tsire da zafinsa? Mohsin yace wannan abin ya gama Shan iska duk kwayoyin cuta sun hau Kai,tace mu haka muke siya a can kauye idan munje kasuwa,ta sake cewa da me tsire kaga ya hanani siya Kuma Ina so,kowa Yana jinta duk na gefen titi tana cewa ya hanani siyen tsire Kuma Ina so, sai dariya ake musu ga hanyar gefen tasha ne,Mohsin Yana ji yace nan ba haka bane to ba a wannan shirmen, sai da ya karasa waje me kyau Wanda nasu a cikin glass yake yace na nawa zaki siya? Tace na dari biyu
Uban wa zai baki nama a dari biyu,sauka tayi shima ya sauka ya siya mata na dubu daya,ya siyi na dubu biyu yace gashi nan ba yawa wannan nasu Umma ne da yaran,tace to mun gode ta sake juyawa zata hau machine irin dazu,Mohsin yace wallahi kika hau da baya sai dai na barki a nan,dole ta juya gaba ta shako wuyansa sannan ta hau ta rirrike shi Kam a haka ya kaita har gida,yace to shiga Kinga ma basu rufe gida ba da alama ke ake jira ta sauka
Tace Yaya? Ya amsa da Naam,tace ka dinga yiwa Umma fada ta tsaneni su Hidaya take so kullum suyi tace min Yar kauye jahila,Wani furucin da Umma take yi wallahi tambade yaranta take bata sani ba,kanaji wai naje Abuja na samu masu kudi na dinga cin kudinsu ai wannan jefa yarinya ne a hanyar banza,ni da nayi haka ai gwara na bada kaina a caca, nace sana'a zanyi taki yarda yanzu sabo da Allah wa na sani a Abuja da za ace nabi wata Hajiya Tagwadas,Kai daga Jin sunan kasan ba na kirki bane wai Tagwadas,Kuma idan nace bazan je ba ta dinga zage zage da lafazi marasa dadi,gaskiya kayi mata magana ato ana shiga hakkina a gidan nan,gashi nan sai ramewa nakeyi kullum,Mohsin yaga yanda take uwar kiba da kyau amma tace ramewa take.
Mohsin murmushi yayi yace ashe dai kina da hankali Kanwata,Ina da shi mana amma Kai kadai nake nunawa hankalina a wajen kowa ni bani da hankali ato Kuma bance ka fadawa kowa ni Ina da hankali ba,abin sirri ne,dariya Mohsin yayi ya mika mata hannu yace give me five, ta mika Masa hannu suka tafa,yace idan ta takura kije kawai amma ki nutsu ai tace rako zaki yi just 2weeks zaku dawo ko ai ba matsala idan ta takura kije, shike nan ta furta tace sai da safe,idan ka koma kar ka kula Yar banzar matar Nan taka ko kaji sha'awarta ka makale kafada kace a'a,idan yaki hakura ka fada min zan baka magani shike nan sai kayi wata baka ji kana son mace ba, Baki Mohsin ya tabe,tace ka daina rainawa da gaske nake nazo dasu ni nake da sirrin,lakani ne Dani I can fix you, gwasaleta yayi yace oummm ke dalla rufe min baki,jeki good night ta shiga ciki ta rufe gidan gaba daya .
Ashe Abbansu Yana waje bai shugo ba,
Naila tana shiga ta same su masu Assignment duk suna ta yi wasu suna kallo,Umma zaginta tayi tace Dan iskanci sai ki tafi waje ki Dade haka har dare ki zauna baza ki dawo ba,sabo da ni ban isa ba ubanku dolo ne,ni Kun rainani banza bagidajiya,Naila tace amma ai na fada miki na tafi gidan Yaya,shine zaki Kai dare haka sabo da hauka irin taku ta Yan kauye, Naila baki bude take kallon Umman tasu, ledarsu ta mika musu tace gashi inji Yaya,da sauri Umma ta fisge ledar tace miko min waccen ta hannunki
Ai nawa ne wannan shi ya siya min daban,to Baki isa kinci ke kadai ba,Naila ga taurin Kai tace wlh bazan baki ba ai nawa ne ai ga naku na baku,kune bakin nama ni a can ci muke mu koshi sai ya ishe mu kullum,Naila kika sake fada min magana baza ki samu albarkata ba,da sauri Naila ta bude baki,tace wai ku me kuke yi haka ne komai akayi sai ku dinga furta munanan kalamai akan yaranku wani abinda da iyaye basa ganewa duk Baki ne,amma ni kikewa su Hidaya me yasa ba a musu wai? Ko sabo da ba a nan na girma ba,karku bari nayi fushi wlh Ina da taurin Kai duk duniya babu me sakko Dani,ai samun lafiyarki Naila kiyi aure ko ki bi Hajiya Tagwadas Abuja kiyi kwana biyu kiyi samari ki dawo masu kudi nake so yawwa.
Naila tace ai bance miki bazan je ba amma ni ana matsa min zan fasa Kuma babu me sani,ai kuwa da na tsine miki,Su Hidaya suna jinsu, Hidaya irin mugayen nan ne da basa magana sai bakar zuciya da hassadar tsiya,amma a haka sai ka rantse tafi kowa hali me kyau,tunda taga Naila ta fita kyau da komai shike nan take Dan Jin haushi amma ba sosai ba.
Naila tana cin Dan tsirenta Umma tasa hannu ta kwashe guda hudu ta karawa Hidaya biyu ta bawa Zara daya sai Aslam ta bashi shima suna ci,Naila zuciya tayi ta tura musu tsirenta tace ku hada ku cinye na koshi,suka dauke kuwa.
Sai lokacin ta lura ba Abbansu ta shiga nemansa tace Umma wai Abba fa? Shi yasan Inda yake cewar Umma ta share zancen,
Naila ta mike zata bude kofa tace idan kika bude wallahi sai ranki ya baci,Umma a waje zai kwana fa,ya kwana a bola ma mece matsalarki uwar shishigi cewar Umma.
Tsabar dolonci irin na Abban su Naila da yazo yaga an rufe gida bai iya kiran kowa a waya ba,har yayi niyyar bubbuga musu kofa ya Kai hannu kenan sai ya fasa yace bazan tashe ku ba haka kawai,uhm uhm Ina Sam sai ya juya ya koma masallaci ya kwanta a ciki,a Nan yayi bacci idan ya farka ya tashi yayi Ibada ya koma bacci a haka ya kwana,bayan anyi Sallar asuba ma bacci ya koma a masallacin,yace bazan shiga hakkin su ba suyi baccinku, sai 10am ya fito ya nufi gidan.
Lokacin su Hidaya duk sun tafi makaranta sai Naila sai Umma,Naila ta tasa kokonta a gaba da ta Saba da dashi kullum ita bata Shan shayi kullum sai ta siyo Koko da kosai, Bata ga Abba ya dawo gida ba sai ta kasa Sha ta zauna tayi tagumi,Umma kuwa ko a jikinta wanke wanke take yi a Jikin pampo tana faman zubar da yawu, 10:11am Abba ya shugo gidan dauke da Sallama,Naila tace ahhh.... Alhmdllh Abba Sannu da zuwa Ina ka tafi ne?
Ita kuwa Kubra Umman tasu ko kulashi Bata yi ba sabo da bashi da kudi gashi baya iya komai,shi ba a fada da shi,yace Naila a masallaci na kwana nazo naga Kun rufe kofa kar na tashe ku Kuna bacci shi yasa na kwana masallaci,Yanzu ma nasan Kun tashi shi yasa nazo gidan,Tausayin Abbanta ya kama Naila matuka
Tace Abba kana zuwa ka dinga bugawa komai dare Kai da gidanka,tsaki Kubra ta ja tace gidan Mohsin dai ai shi ya siyi filin ya gina mana da ai a wani wulakantaccen gida muke ,wannan me zai iya tsinanawa kansa bare wani ta ja tsaki taci gaba da wanke wankenta karshe ma ta gaji tace na gaji ka gama kazo ka karasa wanke wanken,da sauri Abba yace to,Naila ta fara hawayen Tausayin Abbansu tace haba Umma haba Umma ni zanyi a madadinsa,Abba bai iya cewa komai ba,.
Naila tace sai kiyi ta cewa Abba bai iya komai ba bayan gashi ya haife mu ai kuwa ya tsinana miki,tunda gashi ma yanzu wani cikin ne Dake na Abba ai kuwa shike tsinana abubuwa, Naila ta mike ta riko hannun Abba ta kaishi Palo ya zauna a kujera tace Abba kaima Dan birni ne shayin? Yace ae Ina da ulcer bana Shan Koko,Naila ta mike ta shige kitchen ta hado Masa tea ta fito,Umma ta mike tana harararta tace dan ubanki mu gani
Ta sa cokali ta juya shayin tace madarar da kika gambaza Masa a ciki shi yake siya mana ko kece? Ai Yaya Mohsin ke siya dansa ne Kuma ai kuwa kayansa ne cewar Naila
Ae to naji bread din da kika dakko na ubanki ne? Ko kina sana'a ne Umma naga dai Mohsin shi ke bada kudin sabo da haka Abba Yana da Iko da shi,kwafa Umma ta ja haka Naila ta kaiwa Abba,shi Kuma ba zuciya ya fara Shan abinsa, Naila juck din kokonta daga kwat kwat kwat sai da kusa shanyewa ta huta ta sake yin kwat kwat kwat, sanye take cikin dan gajeren wandonta buje da shi ba kyan kama da vest a jikinta wai kayan baccinta ne tun a dajinsu, gashinta buzu buzu a cukurkude
A haka Mohsin ya isketa ya Sha wankan shadda fara ya zuba kyau Yana ta kamshi ya shugo,Umma ya fara gaisarwa har kasa,kamar wani sarki ne yazo haka Umma take murna sabo da shike daukan nauyinsu komai da komai, Cikin Palon ya shiga Naila ta kalle shi sama da kasa ta juya ta Kalli Abbansu ta tabe Baki ta zurawa Abban ido.
Abba yace lafiya Naila? Naila tace me yasa kuka haifo wannan a Nan gidan ne muka zama Yaya da kani,ai kunyi hadama sai ku barshi a haife shi a wani gidan mu hadu can muyi aure,har Umma dake waje sai da tayi dariya,tace wannan kwai sakara, Mohsin Yana dariya yace sannu Naila,hannu ta mika Masa suka gaisa harda dunkule hannu ta mika Masa shima ya dunkule nasa ya mika suka hade yanda gayu suke gaisawa.
Naila tace kayi kyau Yaya.
Abuja birnin tarayya Zaune yake a katafaren palonsa Saman kujera ta alfarma da files a gabansa Yana ta rubuce rubuce ga laptop a gefe Yana dubawa,babu Sallama Asmau ta fado palon tare da furta hey Baby,ko kallonta baiyi ba bai ma San iskar data ajiyeta ba,kamar ba mutum take yiwa magana ba,gefensa tazo ta zauna, wata uwar tsawa ya buga mata wacce ba shiri ta mike tsaye zumbur, ba tare da ya kalleta ba yace waye yace ki shigo min gida har Palo ba sallama ba komai, zata yi magana kenan cikin tsawa yace get out.
Asmau ta Sha Abaya me tsada tayi kyau itama kyakyawa ce wankan tarwada taci make up,tace karfa ka manta Spark an mana baiko aure zamuyi,kwana nan zamu zama miji da mata,tunda Mummy ni ta zaba Maka a matsayin mata amma sai ka dinga wulakanta ni,ko da yake ai kowa ma Kai wulakantashi kake yi, Mima ma baka kyaleta ba bare