Showing 18001 words to 21000 words out of 158722 words
Chapter 7 - Tantiriya A Gidan Yari Book1 Hausa Novel Complete
wasu Kai kawai wacce ta raineka itace mutum a wajenka, ko wacce mace an kawo Maka kaki aurenta gashi Nan har ka Kai 31yrs baka yi aure ba ga kannenka nan su suke Shirin yin aure, anya kuwa kalau kake baka da wata cuta ko aljana ta aure ka,Kai duk wankan da mace zata yi bata birgeka duk kyawunta ko kallon mata baka yi,ai kuwa ni nasan Aljana ce ta aureka ma.
Waya ya dauka fuskarsa kyakyawa a murtuke ya kira securities suka shugo mutum biyu yace ku dauki wannan abin kuyi waje da shi karku sake na sake ganinta a gidana ,sorry sir suka furta suka dauki Asmau tana ihu da karaji tana tsine tsine suka jefo ta waje, dama bata shigo da motar ba haka ta shiga motarta sai gidan Mummy wacce ta raini Ashraf Spark.
Spark kuwa wata ajiyar zuciya ya sauke yace an maidani yaro,matar aure ma ace sai an zabar min a rayuwa ni bani da yanci,me yasa ni ake takura min ne,ba laifi na bane,nayi soyayya da yawa,nayi Yan mata daban daban baza su irgu ba at the end zan gano kudi na suke so ko kyawun da Allah ya min bani ba, sabo da haka soyayya ban Kara yi har abada aure na hakura bazan yi ba dama ban taba yinsa ba.
Kwanciya yayi a Saman 3str ya baje kafarsa daya tana kasa daya Kuma tana Saman kujera,kansa ya dafe yana kallon sama ya Lula tunanin duniya.
Babban Amininsa ne ya shugo Kuma cousin brother dinsa Kamal,Sallama yayi ba tare da ya kalle shi ba ya amsa Masa, Kamal ya kare Masa kallo sanye yake cikin jallabiya coffee color me tsadar gaske kawai shining take tana sheki, hannu Kamal ya mika Masa suka gaisa sannan Kamal ya tambaya Spark how far?
Ashraf Wanda aka fi sani da Spark Sam Ashraf asalin sunansa ya buya kowa da spark yake kiransa har iyayensa,sabo da kalar idanuwansa da kwayar idonsa suke kamar blue kamar baki Kuma irin kalar na wasu turawan, yace I'm good bro,Kamal yayi dariya yace dan wulakanci shine ka Kori Asmau? Kafin ya rufe Baki Spark ya furta mind your Business,ya ja tsaki ya Mike,shi dama bashi da mutunci baya ragawa kowa duk abinda yaga dama kawai zai yabawa mutum a haka ma Dan Kamal ne shi yasa ya raga Masa,mikewa yayi a fusace ya tattara tarkacensa ya bi steps zai haura sama
Kamal ya sheke da dariya yace an dai yi baiko ya zakayi rana za a saka Dan ubanka,Spark Yana bin steps yace sai dai a daura da ubanka,Ubana? Yeah you heard me clearly a daura da Ubanka, Kamal yaji haushi amma ya zaiyi da Dan uwansa abokinsa Kuma yasan halinsa ba wata rayuwa yayi a kasar Nan ba sosai shi yasa yake wasu abubuwan ba tunani,bashi da mutunci ko na kobo,Kamal kwafa ya ja tare da mikewa zai tafi sai ya tsinci Muryar Spark yace kazo upstairs,Yana fadan haka ya juya,Kamal kamar bazai je ba dai sai ya hakura ya haura sama, Saman lafiyayyen bed dinsa na alfarma suka zauna,kawai spark Yana daukan wayarsa yaga sakuna suna ta shugowa ta WhatsApp,budewa yayi sai yaga Asmau ce ta turo Masa pics dinta sun fi ashirin Nan take yayi cilli da wayar ya kwadata da kasa tayi kwatsa kwatsa, yace zan iya kashe yarinyar nan,can you Imagine,Kamal ya rude ya zaci wani Abu ne babba yace me tayi,pics ta tura min sunfi 1million shegiyar yarinya mayya,to taga handsome ba dole ta rude ba cewar Kamal.
A dinga sharhi pls bana son godiyar nan da stickers ni Kam 😅
BOOK 1
Free pages
300 ne ga me bukata
Accnt no
0175487861
Asmau Garba Muhammad
Gtbank
Katin MTN
08061929616
Yan Niger ku nemi
+227 90 79 59 39
AsmaBaffa
[12/4/2023, 1:28 PM] AsmaBaffa: 🏫 TANTIRIYA 🏫
A GIDAN TARI
Official
By
AsmaBaffa
SADAUKARWA
GAREKI❤️
AIDA MAMAN TASNIM
11-15
Page naki ne
BESTYNBEELAT
Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/J0ZFfbvon6ZGASEYAwZX5s
*Ina mata yan gayu yan kwalisa*
*Ina iyayen da suke so yaron su sufito fes*
*Albishirin ku kuzo gidan sauki da rahusa anan za a share hawayan ku*
*Munada kaya masu inganci nagarta gakuma sauki kayan mu sune kamar hak*
*Atampa*
*Les*
*Abaya*
*Sleep dress*
*Shoes*
*Mayafi*
*Hand bag*
*Misk*
* ETC*
MASU AUDIO BAN AMINCE A JUYA MIN NOVEL BA IZINI BA PLEASE.
Hannu Spark ya mikawa Kamal yace bani wayarka ya mika Masa ya danna wasu numbers yace a kawo Masa sabuwar wata waya wacce taci uwar iphone a tsada da komai,ba ko Ina ma aka San da irin wayoyin ba,a wani kwali take kamar kwalin turare,ba a dade ba aka kawo Masa ya cire layikansa ya Maida cikin sabuwar wayarsa ya mikawa Kamal yace jefa a Dustbin,Kamal yace kana raina min hankali wlh, ai bata wani fashe da yawa ba sabo da almubazzaranci sai a jefa a shara a siyar da ita kayi sadaka da kudin ai yafi,harara ya aikawa Kamal yace ance banda kudin sadaka dalla ka bawa me so bana bukata, Kamal yace an gama ni Ina so tsaf zan gyarawa budurwa ta,idan na bata har ihu zata yi, Spark yayi dariya tare da furta Dan gargajiya ne Kai ai,suka fara hira da surutunsu na abokai a haka Kamal Yana hakuri sosai,Spark yace wai wani ne ya kawo min aiki kaji kudin kuwa ya raina min hankali, Kamal ya kwashe da dariya,Spark baya dariya shi a rayuwa sai tayi bala'in kamawa kullum a Shirin masifa da rashin mutunci yake, yace ai wlh gwara na zauna kullum nayi ta danna ashar,Kamal ya saki dariya yace wannan Dan rainin hankali ne,Spark yace Allah yasa banyi signing ba Kuma kasan company ne,better cewar Kamal haka suka ta hirarsu ta abokai.
Washe gari Monday sai 11am Mummy ta kirashi a waya bai daga ba sai lokacin da ya tashi a bacci, yayi wanka ya shirya tsaf cikin kana Nan kayansa na kirki Yan gaske kana ganinsa kasan ba pure Dan Nigeria bane,ya fito ya Sha kyau Yana kamshi tare da taku cikin kasaita ,da gudu Securities suka bude Masa bayan motar da suka ga ya nufa wata bakar mota,Yana shiga bayan motar shi kadai sai driver,Wata motar securities dinsa suka shiga suka wuce,a hankali yace gidan Mummy,Driver yace okay Sir, Yana hakimce a bayan mota Yana kallon gefen titi karaf ya hango wata budurwa tasha gayu tana tafiya wata tsohuwa tukuf da kyar take tafiya tazo wucewa da abincinta a kwano tana tsaye tana ci,jiri ya kwasheta tayi sauri ta rike budurwar, a haka hannayenta da manja ta shafawa matar manja a Jikin kayanta, budurwa ta saki wawan ihu ta juyo tare da shararawa Tsohuwar Mari ta hankadeta ta Fadi da abincin nata,Nan take Spark yace da driver kayi parking a wajen waccen matan,driver yayi sauri ya tsaya a hankali ya karaso saitinsu sannan yayi parking,Spark ko gama parking ba ayi ba ya bude mota ya fito, nan take budurwar data juya baya taji an fisgota da mugun karfi sai da gwiwarta taje kasa,ta mike zumbur kawai taji Mari ta ko Ina kamar ba mutum bane yake marinta ta zaci Tsohuwar data mara Aljana ce itace ta rikide haka ta dawo namiji saurayi kyakyawa,kyawunsa data Gani ta tabbatar sai aljani,tace iya Dan Allah ki yafe min,Iya kiyi hakuri,sai kace ubanta cikin sojojin da suke tsaronsa ya karbi bulalarsu da suke tafkar mutum da ita ya samu budurwar Nan ya zaneta tas duk sai da ya fasa mata jiki har fuskarta kafin kace me kamanninta sun canja mutane sun taru a wajen ana kallo,su tunaninsu ma kanwarsa ce sabo da yanda ya zaneta,yace mahaukanta jahilai kawai tsohuwa dan ta rikeki zata fadi mummuna irinki ma har wani yanga zakiyi,wahala tasa budurwar ta kwashe takalmanta a hannu ta zura da gudun tsiya tana kuka har tayi gaba sai ta dawo tayi reverse ta juya sai hanyar gidansu Inda ta fito.
Tsaki yaja ya juya ya Kalli Tsohuwar dake yashe a kasa tana ciwon kafa da kyar take tafiya,zuwa yayi ya dagata yace Iya tashi,ku ma tsofaffin nan bakwa ji wasu duk Kuna da gata sai ku fito titi Kuna wulakanta kanku,Tsohuwar tace Dan nan Allah Maka albarka na gode wannan ba yinka bane yin Allah ne,shi ya turoka ka rama min, na tabaka da Alheri wajen Dana nazo tunda ya taho cirani yau Shekara biyu kenan bai dawo ba babu aike ba waya,ya manta Dani uwarsa,shine abokinsa ya taho Dani wajensa ka ganshi can ma shine ya bani abincin nawa Allah ya Masa albarka, Spark yace Uhm tsallakawa zakiyi wajensa? tace ae Dan Albarka,kawai Spark ya dauketa kamar ya dauki tsinke ya tsallakar da ita,ya zaro kudade sababbi Yan dubu dubu Bai ma irga ba ya bata,ya juya abinsa,tana Masa godiya ko waigowa baiyi ba ya koma mota suka Kara gaba.
Gidan Mummy ya nufa ya isa gidan cikin takunsa na mazaje masu ji da kansu,gidane na alfarma me tsari Wanda ba kowa sai masu gadi mutum biyu,Yana parking masu gadin suna gaishe shi ko kula su baiyi ba ya dai mika musu hannu kala bai ce ba ya wuce abinsa,Wani Babban mutum ne ya fito Wanda yasha wankan shadda da alama me gidan ne zai fita shima, Clashing suka yi da Ashraf Spark kenan Nan ma bai kulashi ba shima Alhajin bai kula Spark ba kowa ya wuce abinsa ba Wanda ya nuna alamar yaga wani,direct part din Mummy ya nufa,har yayi nisa yaga bai dace ba sai ya juya ya samu me gidan Yana bude mota yace Ina Kwana Daddy,Ko kulashi dattijon baiyi ba,shima sai juya abinsa ya tafi wajen Mummy, sallama yayi a katafaren palonta ya shiga Wanda kamshi ke tashi ta ko Ina,tana Dining cikin shiga ta alfarma cikin Less me tsada white and Golden,Ransa a hade ya isa wajenta yace good morning...kanta ta dago a hankali ta kare Masa kallo sannan ta hade rai itama
Ta mike tsaye tace bari na mike Kafi ganin tsayi na sai ka raina min hankali da kyau, wato sabo da wulakanci shine jiya kayiwa Asmau korar kare ka sani aure ba fashi gwara ma ka so ta, wallahi ka kiyaye ni karka ga wai ubanka babban Soja ne,kaima ka fara aikin soja kayi resine ba abinda ya dameni,ni na raineka Mahaifiyarka kawai haifarka tayi baka isa ka min iskanci ba,Dan karamin bakinsa ya tsuke yace Ohhh Mummy kin san bana sonta, ki daina jawowa Ina bata miki rai a kanta,ni fa ba yaro bane babba ne,Ina aiki Ina da kudi ku daina rainani komai kice sai yanda kika tsara zanyi bazai yuwu ba fa Ina fada miki kar kuyi Kuskuren daura auren nan wlh zan iya sakinta a wajen nan take,zaku ji kunya ki daina turota gidana haba ai ba tsari ba class mace tana bin namiji har gidansa Kuma gida ni kadai a ciki,duk ranar da ta sake zuwa sai na mata tsirara sannan zan jefota waje idan baku yarda ba ta sake zuwa ku gani, Kai ya girgiza kamar Wanda ya Sha kwaya yace nayi warning naku a daina takura min bana so a kiyaye, ya juya ya fice abinsa ba tare da ya saurari me zata ce ba.
Mummy ta zauna jiki a sanyaye tace innalillahi na cuci kaina Dana dinga barin yaron nan a kasar waje gashi nan yafi karfina ayi yaro duk ya gagari kowa ta zuba uban tagumi.
Shi kuwa gogan gidan Mima ya nufa wacce itace ta haife shi,gidan ko Ina sojoji ne birjik sabo da Babansa Babban Soja ne,sannan yayansa da kannensa ma mazan Sojoji ne, Yana shiga ya iske kannensa mata da Maza har da matan duk da kayan sojoji a jikinsu suna ta faman rawa a Palo sabo da tabara,Yana shiga suka kashe kidan sabo da sun san rashin mutuncinsa ba Wanda ya bari, part din Mima ya shiga tana bedroom tana shiryawa mijinta kayan tafiya zai bar kasar, sallama yayi ya shiga itama a tsaye yace morning Sweety
Murmushi tayi tace ka tashi lafiya? Ni fa bana son gaisuwa yanzu da ba lafiya nake ba ai bazanzo ba,to zauna mana ,bashi ya kawo ni ba,ki fadawa Kanwarki tunda ke yayarta ce ta daina matsa min bana son Asmau ki fada mata Ina ganin girmanta tunda ita kuka bawa rukona kawai an bata ni kyauta duk ta matsa min,bana so a fada mata.
Kai Dana ne dama? ai ni sanda na mallaka mata Kai har abada na bata ni ba ruwana da safgarku, ku kuka sani kunfi kusa ai,kar ka sake kawo min karar uwarka, Kai da Rafeeq me yasa bakwa son a zauna lafiya ne,ga Rafeeq Kuma ma ko Yan Nan gidan bai saurara sai yaga dama daga shi sai Islam abokinsa to ya fika ta wani bangaren shi Yana yiwa wacce ta rike shi biyayya baida kamarta,amma banda Kai you are so stubborn.
To kuwa an kusa sawa na fara neman mata nima indai za a aura min Asmau neman mata zan fara,Yar uwarka ce fa cewar Mima,yace Yar uwar me ni Ina ruwana da wasu Yan uwa,tace toooo zagi ya matso kaina,juyawa yayi ya fice abinsa ko bangaren mahaifinsa bai saurara ba ma yasan ba zama yake ba,duk Yan gidan basa gaisuwa daga Hey shike nan,ba Wanda ke safgar wani sai da dalili,ko sun hadu baza ka gane Yan uwa bane sai dai a kamanni,shi kuwa Spark bai ma fiye kama da su ba,kamar ba Dan kasa ba haka yake kamar a wata kasar aka haife shi can Jinin nasara,ga tsirfa wani irin murdadden mutum ne.
Bayan sati daya Spark yayi shiri ya bar kasar ya tafi Germany,ba wanda ya fadawa sai dai aga baya nan kawai, Kamal kadai ya fadawa,Indai suka ga shuru bai zo ba to baya kasar kowa yasan wannan amma indai Yana gari dole sai yaje ko fada anyi da shi.
Naila dai Umma ta sata gaba sai tabi Hajiya Tagwadas zuwa Abuja haka Mohsin yace tayi hakuri taje tunda sati biyu ne kawai zata yi,waya Yar karama keypad ya siya mata da layi rike wayarta na farko a duniya kenan ya koya mata yanda ake amfani da ita,ta hada kayanta a Yar jaka da Umma ta Bata.
Yau zasu tafi da wuri ta shirya taje har dakin Abban su ta same shi Yana Shirin fita aikin gadinsa da ya Saba tace Abba zan tafi ayi mana addua,yaran yanzu ana musu addua ma ya muka kare kana dai gani yanda dole sai mun lalace bare ace ba a yi min addua ai lalacewar Abba sai tafi haka,ni kaina tsoron kaina nake yi,Abba in kana jin Yar hau to nice sabo da haka a surfa min addua ta cire mayafinta tace dafa Abba sa min albarka.
Abba yace to.. to ya dafa kanta yanda tace ya furta Naila Allah ya tsare,iya albarkar kenan?ta tambaya, ya zazzaro idanuwansa Wanda suke kamar yayi zawo na shekaru yace a dai dinga kula,abi duniya a sannu,a Dinka taka duniya a hankali,yawwa na gama shike nan jeki cewar Abba, Naila bata gane hausar ba tace to Abba sai ta fito tana sanda tana tafiya kamar barauniya zata saci kayan wani.
Lokacin Mohsin ya shugo gidan ya iske abinda Naila keyi tana faman sanda yace ke Kuma mene haka? tace Abba ne yace nabi duniya a sannu na takata a hankali,dariya ta kama Mohsin ya dinga sheka dariya yace to Yar kauye ba haka yake nufi ba fada ya miki fa lokacin ya ganar da Naila me ake nufi,ta dinga dariya da maganarta ta yan Fulani tace aradu ni kwai wawiya bani da Kai sai na daukan kaya ai Affa shi baya min haka sai dai ya dinga washe min Baki.
Tace Abba kuwa harda zazzaro Ido duk akan zai sa min addua ya Ilahi wlh sai naga kamar Wanda ya Shekara a gadon asibiti yana jinya,gaskiya Umma tayi babban Jihadi data iya auren Abbanmu kan uba wlh da nice gwara na tafi yawon ta zubar, Mohsin yayi dariya kamar ba gobe,Naila tace Allah Yaya kirjin Abba kamar na fara,baki ta toshe da hannunta tana dariya a hankali tace a haka wai shine bargon Umma ai yasin ko quarter din Umma bazai rufe ba,ya Umma take yi da Sanyi? Allah ya bani kudi na siyo mata bargo babba na gaske karta dogara da kirjin Abba,ta sake rufe bakinta da tafin hannu tana dariya Kallon Mohsin ta yi tace Yaya da alama Kun shirya da matarka ko?
Rada ya mata a kunne yace ae maganin gargajiya za a bani,dariya tayi tace bana murna kishi nake yi da hassada me yasa kuka Jone? Ai tunda naga ka shugo kana yaye mana hakora nasan jiya an rufe kofa,baki ya make mata, tace nidai kishi nake ta fada tana harararsa.
Mohsin yace baki tambayi Amal yarki ba yau,Naila tace wai Kai Yaya Nan murna kake yi kayi abin kunya ya fito fili? Ban gane ba ya furta,tace abinda kayiwa Hanan matarka ta samu ciki ta haifo Amal ai rashin kunya kuka yi a daki sannan aka samu cikin gashi ta haihu kaga kowa yasan me kuka yi abin kunya ya fito fili,Mohsin dariya yayi yace ke kika sani ni dai na haifi 'yata, kallonsa Naila tayi tace uhmm kaji da shi, nifa shi yasa Sam ba sosai nake kiranka da Yaya Mohsin ba tunda ka haifi Amal nasan kaima A ne kana rufe kofa,Mohsin gashinsa me yawa ya shafa.
Hidaya yau ba school su hudun suna gida,tana ta aikin gida Hidaya komai ba abinda bata iya ba a rayuwa na aikin gida,ita kuwa Naila ko wanke wanke komai sai dai ayi mata.
Mohsin ne yaja Naila gefe yace ai dai gidan Yan uwanta zaki raka kawar Umma ko? Naila tace ae haka tace shine fa Umma tace masu kudi ne gidan suna da Maza wai na