Showing 117001 words to 120000 words out of 158722 words

Chapter 40 - Tantiriya A Gidan Yari Book1 Hausa Novel Complete

19 Dec 2024

380

dama,karatu Kuma da wuri ake saka su shi yasa zaka gansu yara amma sunyi Nisa a karatu,Ina kaje boko Ina zasu boko,Islamiyya a gidan ake musu sai sunga dama suke zuwa ma dake Islamiyya ce amma boko ko basa so sai sunje.

Mace komai kankantar ta matukar me kudi ya fito to dole aure zasu mata karatu tayi a gidan mijinta shi yasa su Badia ko secondary basu gama ba aka musu aure a hannun mazajensu suka yi karatu.
Idan talakane Kuma sai suce yarsu karatu zata yi sabo da baza su bashi ba.
Duk sun lalata family dinsu sun tarwatsa kansu.

Ci gaban labari

Ana Kai Invitation prison Azima me kwana ba wando ta cika Umarni ta raba na Beauty a gidan tace kowacce tayi addua da fatan Alkhairi tunda ba a samu zuwa ba, suna ta tayata murna,Zagawa tayi ta katangar bangaren Maza wata a ciki ta dagata sama ta watsa musu Iv ta ko wacce kusurwa ta bangaren mazan.
Dan Indo ya dawo daga cikin ball yaga IV da yawa ya dauka ya fara karantawa sabo da IV din gidan yarin daban suka bayar da kudi aka buga musu ba irin na normal mutane da aka raba bane,ya karanta yaga an saka
Iyalan General Ahmad Maleek
Na farin cikin gayyatar ku
Zuwa wajen daurin auren
Yayansu, Wanda an riga an daura shi tun 12Jul
Naila Hashim (Jamilu)
Da Angonta
Ashraf Ahmad Maleek(Spark)

Ku da baku samu damar halatta ba a tayamu da addua,yanzu haka an Kai Amarya dakin mijinta idan da rabo ma an samu tuni.

Sabo da takaici Dan Indo ta hannunsa ya yayyaga,ya kurma ihu tare da furta Kai Yan matan gidan yariiiiii.......kuzo nayi muku cikiiiii.....kun San yanda ake cikiiiii .....Kafin kace me gidan yari bangaren Maza ya dauka Jamilu yayi aure,kowa yazo Dan Indo yake nema.

Jamilu da yayi aure ba a kawo mana shi gidan yari ba mun more,Dan Indo yace ba labari gashi wannan Spark din ubansa ma Soja ne duk iskancina ai bazan kawo matar wani ba.
Scoler ne ya saki shewa ahayyeeee chass wa ya fada muku barno gabas take? Ai na fada muku Terror yayi gabas kunyi Yamma wlh na gaba yayi gaba na baya sai labari billahillazi,Jamilu tana can tana tsotsar madarar Nido,washer yace har milky me bukunboti ma yanzu ta zuki abarta da tsinken zuka straw .

Malam Sharu kuwa suna Gani suka fara Alhmdllh Alhmdllh wato aihin Allah ya karbi adduar mu ya shirya Jamilu da Spark,Allah ya Kara dankon kauna da soyayya har mutuwa,Malam Garzali yace Astagafrillah wato sai naji darshin hassada a raina, hassada ta darso a kirjina,naji Ina yiwa wannan yaro Spark Hassada da samun Jamilu Tantiriya naji wannan ni'ima dama kaina ta fada,Allah ya shiryeka Dan uwa cewar Malam Jilani.

Su Naila suna hanya Spark sai waya yake wa driver Wanda ya dakko Amarya da kawayenta kayi fa tuki a hankali karka cuceni Mubarak,Wlh ka kashe min Amarya sai ka mutu kaima, Mubarak Dan gidan yayan su Mima ne Uzairu,sauran biyu Kuma yayyen Wahida ne,dukkansu cousins din spark ne ba yanda suka iya haka ya tattaro su dakko Amarya.

Naila kuwa hirarsu kawai suke da su Rayya sai fulatanci suke,Chika kuwa Misam ta dinga nemowa a social media ta ganshi kuwa a Instagram tayi following dinsa,tana duba pics dinsa da videos dinsa gasu Nan latest,sai dai tana yawan ganinsa da Yan mata,ana shigowa garin Abuja Naila ta fara murmushi harda rawa da kafadu anzo.. anzo... Mubarak yace Spark ya samu daidai shi wlh,Naila tace ai dama nace bazan bacci ba idona kirrrrr sai anzo,Mubarak Yana dariya ya kira Spark a waya yace Ango munzo muna Abuja amma gidan Mummy zamu fara kaita sun ce,Spark yace to kuje Gani nan, Mubarak yace Kai Spark harka ta mata me zaka yi Kuma,Yace baka da hankali Mubarak ance ma Amarya wasa ce ya ja tsaki ya kashe wayar.

Naila ya kira a waya yace Amaryata? Naila ta kama dariya tace nazo ai no more damuwa,yace yeah mun daina fada ai Kuma,wani wuri suka yi parking,Dattijai mutan kauye basu San haka ba a rayuwarsu sai yau,Motocin Spark ne guda hudu masu tsadar gaske sababbi gal suka karaso wajen da su Amarya suke,Mota Daya Kamal ne da Rafeeq sai wani Abokin Spark shima farook,Daya motar Kuma sojoji ne mutum uku Helux baka me rufaffen baya tana Shining,Ango Yana cikin farar mota Yar ubansu an mata wata uwar kwalliyar flowers kana gani kasan ta Amarya ce.

Gaba driver ne shima Soja ne ke tuka shi,kofa driver ya bude Masa ya fito,Ya Sha wata Gezna kalar adon leshin Naila milk,yau ya sa hula a Saman tarin sumarsa wacce ta Sha gyara,Sajensa da dan gemu yasha gyara sai sheki yake,Naila tace ga nawan nan,Chika tace uhmm muna kallon sabon salo yau duk akan Amarya Allah ya bamu itaku Naila,Rayya tace aradu dama ance duk Wanda yaje gidan yari Bada hakkinsa ba sai ya daukaka.

Chika tace nima nan na hango tawa Daukakar Rayya,dole sai na auri kanin mijin yarinyar nan Naila,baza ta sabu ba,ai ko Misam ya shirya ko Rafeeq cikinsu dole wani ya Kara rage mugun iri idan ba haka ba na tambade,Dije tace ni kuwa Ja'e ma da zai dawo to ni wlh da na gama tawa Daukakar aradu na Saba da Hallaren Ja'e,duk kudin mutum,duk kyawun Da namiji ke ko da Larabawa za a tara min a jefa Ja'e cikinsu to Ja'e zan zaba,Rayya tace yo me za ayi da mutum ba saniya sai motoci.

Spark ne ya tako cikin takunsa na Yan gayu ya bude bayan mota yaga Dije ce ya Maida ya rufe yace shi yasa naga motar ta min duhu,dayan side din ya zaga ya bude yace lantarki haba yanzu naga haske,dariya Naila tayi a hankali tace bari nayi kunya tunda Amarya ce,Mayafinta ta lulluba a kanta fuskarta duk ta rufe sai ta mayafin kawai take kallon mutum,Hand bag dinta ta dauka sannan ya riko hannunta ta fito a hankali, Spark Yana tsotsar alawa a bakinsa Naila tace San min abinda kake ci,ya ma manta shi Yana Shan abu,cirowa yayi da hannu ya sa mata a baki yace haba in kayi aure shike nan baza a barka kayi kiba ba, komai Kaci sai matar ta ci,mata ku dai zuciyar ku a mace take kullum a baku,Naila tace Dan Allah karka sa Amarya ta dinga dariya ana ganinta,Su Goggo ana mota suna ta salati.

Goggo tace yau ni Ramatu naga abinda ya isheni ni 'yasu,rashin kunya kiri kiri,wallahi Kin Gani Tani hannu ya rike mata,Tani tace yau ni Ina zan iya kallon wannan fitsara,dole Kakan Naila yaji zancen nan cewar Goggo,Tani ta rafka salati ganin Spark ya rungume Amarya suna dariya a Jikin mota,mayafinta ya daga ya shigar da kansa shima,Goggo tace haka duniya ta koma? Shike nan duniya tazo karshe an kusa tashin kiyama,ke Kinga Dan Allah mun bani Ramatu,ai muna kauye ta nan yajuju da majiju zasu fara bullowa,Goggo tace na fadawa Naila idan ta fara ganinsu ta bugo mana waya mu kimtsa,Me tuki dai yana ta dariyar su Goggo,bangaren su Dije ma sai salati suke suna Jin kunya,Chika kuwa ficewa tayi da su Kamal suna ta daukan Amarya da Ango pics da video iri iri,sai da suka gama sannan Spark ya sa Amarya a motarsa ya shiga gefenta suka tafi gidan Mummy.

Mummy ya ta iya Danta ne ya fada mata zasu zo haka ta kira kawaye da wasu Yan uwan suka je gidanta za a kawo musu Amarya,Mima kuwa duk dangin kusan suna gidanta itama suna jiran Amarya,suna cewa wannan bikin arna kawai aka yi Amarya ya gama kwashewa da ita sabo da iskanci yanzu ace za a kawo musu ita,Mima tace mu da muka gansu akan gado ai magana ta kare Kuma,ni wlh tunda ake haihuwa ban taba ganin yaro irin Spark ba, kace zaka Masa Baki yace zai afka Maka.

Maman Rafeeq tana ta dariya tace kar ki Masa baki wlh hukuncin Allah ne,Kuma Dan kin gansu akan gado sai kice yayi wani Abu ba fa lallai bane zafi ya rage maybe,Mima tace ai kune Yan zamani Kuma ba wasu manya bane Kun San ya matasan yanzu suke,Maman Rafeeq tace sai addua wlh yaran yanzu,Lateefa tace ai Ubansa ne ya daure Masa gindi shi yasa ko me yace sai ya hau ya zauna,duk yaran da basa gabansa yafi kaunar su,da wuri yake musu Abu,ko Rafeeq Dan yaki karba ne amma ya damu,baya son sana'ar Nan tasa wai Shawarma Joint kiji iskanci,wlh duk kudi ne yasa su yin haka,basu da matsala ne shi yasa suke wannan iskancin cewar Kawar Mima.
Mima tace yanzu haka Amaryar da dan cikinta a gaba irin dai ta Christian,gata tsagera idonta kar ni dai na shiga uku banyi dacen suruka ba cewar Mima tana zuba tagumi.

Har gidan Mummy suka shiga tare da parking,Chikar gayu ita ta shiga motar kayan Naila sun wuce gidan Amarya ita da me Jan motar.
Spark fitowa yayi ya budewa Naila tare da riketa ya fito da ita,Mummy suna leke ta window Baki ta tabe tace kuzo kuga duk Yan kauye ne suka kawota amma dai sunga kawayen Umma duk su Yan birni ne basu da mukusa,Oh ni na shiga uku ya kwaso min matsafa yaran talauci,dama wata yar film ce Yar gidan masu kudi, Ni tunda tayi yankan Kaunar ma wlh ban sake Ganinta ba,ita a Yan film din ma ba wata popular bace domin tunda naji ita ya aura na shiga bincike Ina tambayar kawayena ko sun San wata Nasiba Yankan kauna ba Wanda ya ganeta,wata tace maybe irin sababbin Nan ne Yan giggiwa ba Wanda ya sansu sai karya,idan kin kure su baifi a Waka suke fitowa ba,ai kyau ya bi da wanka,indai wanka ne basu da na biyu,Mummy tace ku gyara gasu Nan dangin tsiya anzo za aci arziki.

Zama suka yi suka nutsu, Spark cikin mota ya koma ya zauna,Goggo tace tafi a hankali Naila,cikin kawayen Umma daya sun rike hannunta sai zuba guda suke ayiririri,Spark yaji guda har kunnensa yace yanzu nasan Amarya ta iso harda Kara sauke glass yace bari naji da kyau.

Kida gaba daya motocin suka saki gaba daya iri daya wakar yan Nija,Rafeeq Yana mota harda rawa a zaune,Yana cewa layi yazo kanmu,Mummy su kansu dariya suke tace wannan yara namu anyi Yan iska, yanzu dan Amarya shine aka sa mana uban kida haka duk sun hanamu Jin kunne, Dangin Amarya suka shiga da sallama ga katon carpet, a nan suka zaunar da Amarya tana zuba kamshi,duk sauran mutanen dakin sun yaba da Amarya amma Banda Mummy ta dai danne ne kawai sabo da Spark kar yazo ya mata tijara,amma da sai ta jefar da magana,amma duk da haka sai da tace ai da baku batawa kanku lokaci ba ma ya dauki abarsa ai mun ganta a gidan nasa tuni tasan har gadon kwanansa.

Goggo tace yo ko ba komai ai tazo ta gaida iyayen Angon nata, ta ganku ku ganta ai wata girmamawa ce daga wajen Iyayen Amarya Hajiya,Badan yace muzo ba ma baza mu zo ba, sai mu wuce dakin mijinta kawai,idan badan zamani ba ma waye yake wani Yan biye biye da Amarya har wajen uwar rainon Ango,wai bama uwar da ta haifi Dan ba,sai zamani yanzu a fara wani biye biye da Amarya ana samu gantali a hanya,Mummy mukus suka yi sunji Goggo ta Maida martani,Mummy taji ciwon maganar Goggo wai uwar raino wato sabo da bata Haifa ba ake mata gori.

Kawar Mummy malamar makaranta ce itama tare suke koyarwa a primary school,tace please arziki ya kawo mu ba wani abu ba,Amarya ce gata nan yarku ce dai,ba wani abu ba, a bude taro da Addua,aka yi addua aka shafa Banda Mummy dake danna waya tana chat da Basiru Kusan ta, wata ce a dangin Ango babbar mace tayiwa Amarya nasiha sosai,tace Allah ya kade fitina kinji.

Naila ta fara kukan karya tana shesheka,su Goggo duk sun zaci da gaske kukan take,harda cewa yi hakuri yar nan kowa da haka ta Saba,Tani tace 'ya mace ai 'yar gidan wani ce, duk haka aka yi mana Naila aure sai hakuri,Goggo tana cewa rabuwa da iyaye ba wasa ba,Allah sarki sabo da gidane da iyaye,ko Kaka 'yar Nan ta tuna ai tayi kuka,Mummy ita dariya ma suka bata yarinyar da suka samu kwance a kirjin mijinta wai yanzu itace take kuka, Mummy tace ai fa Amarya sai da kuka ai,Rayya ce ta taba Naila tana girgiza kafadarta tace ki daina kuka kinji nima zaki sani kuka shike nan mun rabu an raba mu,ta rungume Naila ta fara kukan gaske ita,Naila ta kankame Rayya tana kukan karya,Goggo tace dole kuyi 'ya'yan nan,saurin kuka ne dani karku sani nima Dan Allah.

Mummy baki ta saki tana mamaki tace a ranta amma yarinyar nan anyi Karuwa kaga yar iskar yarinya,yau naga Bariki,lallai bariki iyawa ne wlh,Bariki ba sai an nemi Mazan banza ba,a fili tace to Alhmdllh mun gode Allah ya bada zaman lafiya,sai a kaita can gidan Mima din,suka yi godiya suka mike tuni matan dangin Ango suka rako su da Abinci anyi wrapping dinsa a wasu paper masu kyalli na musamman,ruwan roba da lemuka carton sunfi biyar, Mummy komai sai anyi karya,a bayan mota aka zuba,Amarya kafin tazo Ango ya bude mata ta shugo, yana cikin mota bai fito ba kidansu suke Sha kamar zasu tsaga gidan,Rayya ce ta rufewa Amarya murfin tana share hawayenta na gaske ta shiga mota suka fita sai gidan Mima.

Kidan suka rage sai kadan kadan kowa suke ji a motocinsu,Naila mayafinta ta janye kadan tace na Sha kukan karya kowa ya daka ta Tantiriya zai kashe kansa watarana,Spark yace au Kuka kika yi? Naila tace na karya ba sai bani hakuri akeyi,Rayya mahaukaciya wai kaji ta fara na gaske,Spark yayi dariya yace kin birgeni keep it up,Naila taji dadi ya yaba a ranta tace ka shiga uku idan muka je gida tunda kace naci gaba ai yau kwana zanyi Ina kuka sai na Kara birgeka.

Spark yace saura su Mima Kinga kunkan karya yasa kinyi zufa,driver karo AC,driver ya karo AC yace to shafa wata powder kar aga Amarya da gumi kamar na wani kwalbe,Naila powder ta sake shafawa sama sama ta gyara sosai harda gyara pink jambakinta tace yayi? lekawa yayi yace yawwa,Mayafin ya gyara mata yace badan kayan Nan suna da kyau ba da tuni sun yi dukun dukun a tafiyar motar nan,Naila tace na gaji ma wlh baka ji kafata ba,Yace wannan karki damu da gajiya Hallare zata sauke miki ita tsab,Naila tace sai kace wani magani da ake cewa Daga,tafi Daga ai.

Gidan Mima a cike yake da Yan uwa kaf Maza da mata sabo duk ba a San Amaryar ba,kowa ya baza Ido zaiga Amaryar Spark,za dai muga karyar Spark a Ina ya kare,Badia kanwarsu wacce itama tun daga Bauchi tazo har Abuja da yaranta kawai Dan taga matar Spark wacece,dama idan mutum yayi fice a iya shege da tsirfa to kowa zuba Masa Ido ake aga zabinsa.

Anam tace munzo bikin amma tsabar haushi Bai auri Wahida ba yasa duk muka koma, ko gidansa bamu je ba bare mu ganta, Munji dai ance Yar aikinsa ce,Yar kauye ce ma,tab yanzu haka ma mummuna ce,mazan Nan suna ta dariya suna jira su sha kallon Amaryar Spark,taron na Mata ne amma duk sunki tafiya kamar mayu.
Harda sake kunna fitilun palon,duk ranar da take gari,wani Arham yace tunda naga ko status Spark baiyi da ita ba nasan bata hadu ba, ai gudu yake kar ayi Masa dariya,Dan Allah Mima kuce ta yini a Nan mu ganta sosai zuwa yamma sai a kaita gidansa.

Mima tace ai dama yace anan zasu yini sai yamma za a kaita can,wai ko uban me ake saka Masa a bed masu aiki basu gama hada gidan ba,Badia tace lallai Yaya duk tsadar kayan gidansa? Mima tace ke kuwa zai kawo 'yar gold ya bazai canja komai ba,ai gidan ya koma sabo wlh ya canja komai na gidan,Kuma in Kinga kayan da ya canja sai kin rantse 'yar shugaban kasa ce zata tare a gidan.

Har kofofi duk an canja ke har su globes bai bari ba,ai naje gidan na Sha kallo, nan kusa baza ki samu gida me kyau da aka kashewa kudi haka ba,ni mamaki ya bani ma,mutumin da watarana budurwarsa ta Ghana ta yaudare shi, karshe ya gane kudinsa ta ci kawai, yazo nan gabana yana cewa Mima I swear na gama love har abada bazan Kara son wata ba, tana gwada yanda Spark ke magana,wai budurwarsa ta karshe Lilly?Anam ta tambaya, Mima tace ita fa.

Spark ya Sha wahalar soyayya mata hudu ne suka yaudare shi, Kuma duk da haka gaskiya Banga wacce yake so irin wannan da ya aura ba,cewar Mima,Yana sonta sosai,idan ta kirashi jikinsa har rawa yake,amma waccen kuwa wlh ko sun kira sai yaga dama yake dagawa,kiji Yana musu tsawa,sannan suna yaudararsa idan ya gane zaki ga ya rabu dasu ba wahala Kuma zai ci gaba da rayuwarsa normal kamar komai bai faru ba.

Wannan Naila kuwa akanta zai iya haukacewa na tsorata da Spark akan yarinyar nan,sai yanda tayi da shi,mu da a gabanmu ya fada mana ni da uwarsa Mummy yace ya zama Sallamamme,sai abinda tace,mu ja girman mu idan ba haka ba ko me tayi mana bazai iya magana ba,shi yasa ba ruwana da gidansa,badan ma yace muje muga gyaran gidan ba bazan je ba.
Badia tace to ko dai asiri suka masa kin San 'yan Fulani fa.

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login