Showing 1 words to 3000 words out of 139192 words
[16/09, 10:01 pm] Jiddah S Mapi: 🌸🌸🌸🌸🌸
*KANWATA*
🌸🌸🌸🌸🌸
Na
Jiddah S Mapi
*Chapter 1*
~awani gari Adamawa anyi wasu 'yanmata guda biyu, su kad'aine iyayensu suka Haifa, suna zaune a unguwar ganye road, Babbar sunanta FADILA, karamar Sunanta AMRA, Fadila yarinyace me hakurin gaske ita kuma Amra batada hakuri ko kad'an, kyawawa ne sosai, Asalinsu fulanai ne, sunada gashi sosai saidai Amrah tafi Fadila tsayi dakuma hasken fata, Mahaifiyarsu ma kyakkyawace shima mahaifinsu ba baya ba wurin kyau, duk Inda kaga Fadila tofa zakaga Amra a wurin, Fadila tana matukar son kanwarta sosai, wasu lokutan idan Amra tayi laifi Fadila tana iya d'aukan laifin ayi mata hukunci, koda kitsone ita takeyiwa Amra, iyayensu suna matukar jin dad'in yanda suke zama cikin Aminci da kaunar juna, Abu d'ayane yake basu haushi shine yawan hakurin Fadila, Amra tana iya yi mata Laifi saidai tayi hakuri ta share hawayenta, daga baya takara Jan Amrah jiki ta bata hakuri, Fadila tanada saurayi KAMAL ita kuma AMRA tana secondary school sai next year zata gama.
"KAMAL yarone kyakkyawa fari dogo me class, shi kad'aine a wurin iyayenshi, mahaifinshi ya rasu sai mahaifiyarshi HAJIYA SARA, Hajiya Sarah tana matukar son KAMAL hakan yasa duk abinda yakeso tofa itama tanaso, KAMAL yanason Fadila sosai shiyasa Hajiya Sarah take sonta, saidai wani abunda yake had'ashi da mahaifiyarshi shine tad'au duniya da fad'in gaske, batada kunya ko kad'an, Tana harka da manya manyan masu kud'i, kasancewar Allah yayi mata kyau, hakan yasa take Jan hankalin maza, Kamal abin yana bashi haushi sosai, yayi mata fad'a takiji yayi fushi har yanzu bata dainaba, sai kawai ya hakura yanayi mata addu'a.
"yau ranar Talata 1/12/2020 daidai da ranar baikon Fadila da Kamal, Kamal ne zaune da Fadila suna hira a harabar gidansu Fadila, "Gaskiya zanyi farin ciki sosai idan na Aureki, sabida nasamu Mata me hankali da nitsuwa, uwa uba ga kyau ga hakuri"
Murmushi Fadila tayi tace "nima nayi farin cikin kasancewarka Wanda zan Aura, Ina Alfahari da kai, saidai wani abu guda d'aya danake tunawa yana tadamin hankali sosai, hakan yasa har ina ramewa"
Kamal cikin mamaki yace "menene wannan matsalar Fadila? Ki fad'amin idan har zan iya magance miki"
Idon Fadila ne ya cika da hawaye cikin muryanta me sanyi tace "banason Rabuwa da Amra, ina matukar sonta, itama nasan tana jin zafin zamu rabu b'oyemin kawai takeyi, naso ace rana d'aya zamuyi Aure da kanwata abun zaifi zuwa mana da sauki" share hawayenta tayi da gefen gyallenta tace "Amma ba komai haka Allah ya tsara mana, koda bamu rabu Dan Aure ba zamu rabu Dan Mutuwa"
"Ki daina maganar Mutuwa a wannan lokacin Fadila, kinsan cewa yau, za'ayi mana baiko ko?"
Gyad'a kanta tayi tace "nasani Kamal shiyasa kaga nace haka Allah ya kaddara mana"
Amra ce ta taso daga makaranta, cikin tafiyarta a hankali ta hango yayarta dakuma Wanda zata Aura, murmushi tayi ta karasa wurinsu, "Yaya Kamal sannu da zuwa, tin acan na hango Ku ai kuna murmushin soyayya, to Amma meya samu yayata naga kamar tayi kuka?"
Kamal ne yayi murmushi yace "kanwata ai kukan nan da kikaga tanayi, to kukan farin ciki ne, kinsan ai idan ana baiko Amarya kuka takeyi"
Dariya tayi tace "su Amarya manya"
Fadila ma dariya tayi tanajin son kanwar tata yana kara shiga zuciyarta, "kije ciki ki canja kayanki Amra, sai kizo muyi firan tare ko?"
Amra tace "to".
Bayan mintuna goma sha biyar saiga Amra cikin kaya irin na Fadila, tayi kyau sosai kamarsu takara fitowa, Murmushi ta sakar musu kamar yanda suma sukayi mata, zama tayi a gefen Fadila ta d'aura a hannunta akan cinyarta tace "Adda nayi kyau?" (Kasancewarsu Fulani shiyasa suke fad'awa yayunsu mata Adda, maza kuma Hamma) murmushi Fadila tayi tace "kinyi kyau sosai kanwata, haka nakeso kirika zama kyakkyawa a koda yaushe"
Kamal ne ya leko fuskarta yace "ji jambaki kamar me tallan Awara"
Turo baki Amra tayi tace "Yaya Kamal wallahi ka daina Neman tsokana ta, Dan kaga nafi matarka kyau shiyasa kake fad'an haka, to nima Wanda zan Aura yafika kyau da Aji da kuma iya gayu"
Tana fad'an haka ta mike tashiga cikin gida, Kamal sai dariya yake yana cewa "ke ai sai d'an kauye zaki Aura"
Fadila ce tahad'a rai alamar abun baiyi mata dad'iba, kallonta Kamal yayi yace "lafiya Amaryata?"
Dakewa tayi tace "eh"
Kamal dariya yayi yace.
"Lalle Fadila kinason Kanwarki sosai, sanin kanki ne nida Amra mun saba fad'an wasa, yanzu zamuyi fad'a kuma yanzu zamu shirya, meyasa Dan ranta ya b'aci na wasa zaki b'ata rai?"
Fadila turo baki tayi tace "to ai koda wasa banason ranta ya b'aci, kuma bayan Amra babu Wanda nakeso sai kai, Kamal ina sonka sosai, bazan iya rabuwa da kai ba, kayimin Alkawarin duk rintsi bazaka gujeni ba"
"Nayi miki Alkawari Amaryata, bazan tab'a rabuwa dake ba"
Murmushi tayi mishi me sanyi tace "bari nashiga gida na baiwa Amra hakuri ko?" Shiru yayi mata, ita kuma bata kulashi ba ta wuce cikin gida, tana zuwa ta tarar da Amra tana shan lemon kwalba hankalinta kwance suna hira da Mama, Murmushi ta sakar mata tace "Kanwata? Kin huce ne? Dama nashigone Dan in baki hakuri, sai kuma naga kin huce"
Amra cikin mamaki tace "Adda kema ai kinsan fad'anmu da Yaya Kamal, shine kuma zakizo kibani hakuri? Ni wallahi nama manta yanzu ina yake?"
Fadila tace "nabarshi a waje"
Amra tace "muje in nemi tsokanarshi"
Suna fita sukaga wayam yatafi Amra ranta ne yad'an b'aci ta juya wurin yayarta tace "baga irinshi ba, yanzu akan wani d'an kalilan na Abu kin jawo ranshi ya b'aci, ni gaskiya idan baki dena wannan abun ba raina zaina b'aci matuka" tana fad'an haka ta juya tayi tafiyarta,
Bin bayanta Fadila tafarayi tana cewa.
"Dan Allah kiyi hakuri Amra zan kirashi a waya in bashi hakuri, kuma nasan zai hakura"
Juyowa Amra tayi tace "kin tabbata zai hakura bazaiyi fishi dake ba?"
Dariya Fadila tayi ta sunkuyar da kanta tace "eh zaiyi kizoma in kirashi a gabanki kiji"
Zuwa Amra tayi suka zauna a gefe d'aya, Fadila ce takira Kamal, ringing kusan sau Uku kafin ya d'auka, shiru yayi, Fadila cikin sanyin muryanta me had'e da shagwab'a Wanda yariga yazama mata jiki tace "Dan Allah my fiancy kayi hakuri bansan ranka zai b'aci ba, am sorry"
Kamal Wanda yake kwance akan Sofa ya lumshe idonshi a hankali ya kuma bud'ewa da yayi niyan bazai hakura ba, Amma jin muryanta yasashi yaji yama hakura gaba d'aya, a hankali yace "ba komai na hakura my fiancy" (Fiancy yana nufin Wanda zaka Aura, misali anyi muku baiko ko makamancin haka).
"Amra ce ta mika mata hannu alamar su tafa, tafawa sukayi dukka sunajin dad'i, Amra tanajin dad'in Yayarta sun shirya da Masoyinta ita kuma Fadila tanajin dad'in Kanwarta ta saki fuska tana murna, Mama ce ta leko tace "ku shigo to kuyi wanke wanke naga bakuda Alamar shigowa"
Amrah ce ta mike cikin had'a rai tace "Mama yaufa naje Makaranta nagaji sosai bazan iya yin wanke wanke ba gaskiya"
Fitowa Mama tayi gaba d'aya tace "me naji kina fad'a Amrah? Bazakiyi wanke wanke ba?"
Amrah shiru tayi, Mama haushi tabata hakan yasa ta karaso wurinta zata zabga mata mari Fadila tayi saurin kai fuskarta, Tass kakeji Mari ya sauka akan fuskar Fadila, abin yabawa Mama haushi matuka, duk lokacin da Amrah tayi laifi idan zata daketa sai Fadila tayi sauri ta tare dukan abun yana kona mata rai, Janyo Fadila tayi tafara dukanta tana cewa "ke kikayi laifin ne da zaki tari Marin? To yau sai jikinki ya fad'a miki, gobe idan tayi laifi nazo zanyi mata hukunci to zaki kara karb'a mata, dukanta takeyi da iya karfinta domin ranta ya b'aci sosai,
Amrah ce ta iso wurin tana kokarin kwatan Yayarta, Mama janyo Amrah tayi ta had'asu dukka tana dukansu, Fadila ganin ana dukan Amrah saita fara kakkareta duk dukan daza ayi bata bari ya tab'a Amrah.
*Free book ne, kyauta ne kusha karatu lafiya amma ayi comment sosai da likes shi zaisa nasan kuna so*
_jiddah Ce....✍️_
08144818849
[16/09, 10:01 pm] Jiddah S Mapi: 🌸🌸🌸🌸🌸
*KANWATA*
🌸🌸🌸🌸🌸
Na
Jiddah S Mapi
*Chapter 2*
*Free book ayi comment da share pls*
~Mama ganin ranta ne zaici gaba da b'aci yasata barinsu ta shige d'aki, Fadila mikewa tayi taje wurinda Amrah ta zauna tana kuka, Janyota tayi jikinta tana cewa "sannu kinji ciwo ne?"
Amrah shiru tayi tana kallon Yayarta yanda ya rud'e akanta bayan itace ma Mama tafi dukanta, far far tayi da idonta tace "ai dama idan ana dukanmu to b'uya nakeyi a bayanki bulala baya tab'ani sosai, kinsanni da tsoron bulala"
Dariyan farin ciki Fadila tayi "naji dad'i tunda bulalan bai tab'aki sosai ba"
Amrah kasa tayi da murya tace "nagodewa Allah daya bani Yaya wacce take sona fiyeda kanta, Adda ina matukar sonki kamar yanda kema kike sona, Bazanso mu rabu dake ba"
Rungumeta Fadila tayi "ki daina maganar Rabuwa Amrah, Auren nanma wallahi zan iya fasawa domin samun farin cikinki"
Mama ce tafito daga d'aki, kallon Takaici tayiwa Fadila tace "lalle Fadila bakida hankali, zaki fasa Aurenki? To idan kin fasa Aurenki itama Amrah kenan haka zata zauna? Sai kuyita zama min a gida da zarar nayi wanka Ku zubamin ido ko? Tofa baki isa ba Fadila, babban kuskuren da zakiyi shine kisa a fasa Aurenki, zakiga bakin ciki ranan, kutashi maza kuyimin wanke wanke"
Fadila tace "ni zanyi wanke wanken Mama, ita Amrah zata gyara mana d'akinmu" tafad'i hakane don tasan d'akinsu a gyare yake idan Amrah taje saidai kawai ta kwanta.
Mama batayi musu magana ba, kawai tashiga kitchen, Fadila tashi tayi tafara wanke wanke ita kuma Amrah kwanciyarta taje tayi a d'aki tanajin dad'in irin so da Yayarta take nuna mata.
"Kamal da Maman shine sukazo da yammacin ranar, Zobe me kyau Kamal yasawa Fadila a hannunta Tafi akayi musu, Maman Kamal ce taciro wasu lafiyayyun Leshi guda biyar ta baiwa Fadila, Fadila aunkuyar da kanta tayi cikin jin kunya tace "nagode Umma"
Maman Kamal kallonta tayi tanajin son yarinyar yana kara shiga zuciyarta, "karki damu 'Yata kidaina godemin"
Fadila dukar da kai kawai tayi, Amrah ce tafito da Pure Water a hannunta, mikawa su Kamal tayi, karb'a yayi yana dariya yace "kaga matar d'an kauye"
Murgud'a baki tayi tace "eh d'in"
Fadila dariya kawai sukayi, an gama baiko kowa ya watse, Fadila ce ta baza kayan da Maman Kamal tabata a cikin gida, kiran Amrah tayi tace "zoki zab'i duk Wanda yayi miki kyau a ciki"
Amrah kawar da kanta tayi gefe tace "gaskiya Adda nikam bazan iya sa kayanda Maman Kamal takawo gidannan ba, sabida da kud'in Zina ta siyesu"
Fadila waro manyan idonta tayi tace "Amrah me kike fad'ane haka? Kinada tabbacin tanayin Zina ne? Zatofa zunubi ne"
Amrah tab'e baki tayi tace "ai ni da idona na ganta da Alhaji Mamman me zinari, kuma duk garinnan waye baisan shi d'an iska bane d'an kawali"
Fadila tayi shiru tana mamaki, Mama na zaune a gefe tana jinsu da gangan takiyin magana tana jiran taji me Fadila zata fad'a.
"Shikenan Kanwata idan ke bazaki sa ba to nima banaso, mu siyar ko kuma mu kyautar, hakan yayi miki?"
Amrah saida tayi tunani kafin tace "eh yayi min"
Mama ce wacce taji ranta ya b'aci ta taso tazo wurinsu, zare manyan idonta tayi tace "ke Amrah Amma bakida tausayi kuma bakida tunani, kinsan yanda Fadila takeson Kamal duk kyautar data shigo idan ta hannunshi ne dolene taji dad'inshi, Amma ke kina amfani da yadda take sonki kina cutar da ita"
Fadila ce ta d'ago kanta tace "mama wani irin magana kikeyi haka? Amrah ce zata cutar dani? Gaskiya fa take fad'amin batason na hallaka ne shiyasa, Amma Mama Dan Allah kidaina fad'an haka"
Amrah tashi tayi a wurin ranta a b'ace ta wuce d'aki, Fadila tace "Mama kingani ko? Gashi yanzu daga fad'an gaskiya an b'ata mata rai, tashi tayi itama tashige d'aki tana baiwa Amrah hakuri, sukabar Mama tsaye tana ganin ikon Allah, da kyar Fadila tasamu Amrah ta hakura, haka suka siyar da leshin gaba d'aya.
"Yau takama ranar laraba, su Amrah sunada Walima a islamiyyar su, Dugayen Riga sukasa itada Fadila rigan komai nashi kala d'aya kwalliya sukayi me kyau, sunyi kyau ba wasa, Fadila tadafa abincin Walima wa Amrah, flasks d'aya kowa ya rike a hannu Fadila tarike babban na shinkafa ita kuma Amrah tarike karamin na Miya, sunyi kyau kamar ka sace ka gudu, Kamal ne yazo yayi parking na motarshi, shiga sukayi suka rike abincin a cinyarsu, Fadila amaikon ta zauna a gidan gaba, sai tace wai idan ta zauna a gaba kanwarta zatayi zaman kad'aici a baya, Kamal juyawa yayi yana kallonta yace "nan da islamiyyansu shine zatayi zaman kad'aici?"
"Eh" shine Amsar data bashi, Amrah tace "Adda nikam babu wani zaman kad'aici kawai dai kije ki zauna"
Fadila Sam taki zaman duk yanda sukayi da ita, Shikuma Kamal yace idan suka zauna a baya dukansu tofa za'ace shi driver d'insu ne, daga karshe Fadila tace "saidai Amrah ta zauna a gaba"
Amrah ganin zasuyi latti kuma gashi tana daga cikin wad'an da zasuyi karatu yasata bud'e motar tashiga gaba ta zauna, fira sukeyi da Kamal tana bashi labarin yarantarsu itada Fadila, sai dariya Kamal yakeyi ita kuma Amrah ta zage tanata surutu, Fadila sai murmushi kawai takeyi tana jin dad'in kanwarta da Wanda take so a rayuwarta suna dariya, abun ba karamin burgeta yayi ba, har suka iso Wurin walimar, Amrah ce ta d'auko flasks d'in duka biyu tashige cikin islamiyar dashi, Fadila ce ta koma gaba ta zauna tana dariya, a hankali suka fara firan su na masoya wad'anda suka jima suna son junarsu, Fadila ji takeyi idan bata Auri Kamal ba komai zai iya faruwa da ita, shima Kamal jin Fadila yake a cikin zuciyarshi "Kamal ina sonka, Dan Allah kada ka gujeni a kowani hali"
Kamal rufe idonshi yayi yanajin soyayyarta a zuciyarshi bud'e bakinshi yayi tareda idonshi ya zuba mata, itama kanta ta d'ago tana kallon cikin idonshi, wani sako suke turawa juna ta cikin idanunsu, Fadila ce tafara saukar da kanta kasa cikin muryanshi me sanyi da kuma dad'i yace "Ina sonki nima my fiancy, idan kinga ban Aureki ba, to saidai idan nadaina numfashi, mutuwace kad'ai zata rabamu itama ina addu'ar ta d'aukemu lokaci d'aya"
Fadila rufe idonta tayi tanajin wani yanayi a jikinta, cikin sanyin muryanta tace "ka daina maganar mutuwa yanzu sai munyi Aure mun haifi yara" tana fad'an haka ta rufe fuskarta da hannayenta biyu alamar taji kunya,
Dariya Kamal yayi yace "ki bud'e fuskar mana ai gaskiya kika fad'a kodai kinajin kunyata ne yau?"
Fadila bud'e motar tayi ta fice da gudu, Kamal sai dariya yake da karfi yace "idan kun gama ki kirani zanzo in d'aukeku"
Fadila bata juya ba kuma tajishi, motarshi yaja yayi tadiyarshi yanajin farin ciki, a duk lokacin da Fadila tayi Abu farin ciki yake sashi.
"Amrah sunyi Walima tayi karatun kur'ani itace tazo number 2 sun samu gift me yawa, Fadila ce tajata gefe tabata wani Abu acikin kwali tace "congratulations ga gift nawa"
Amrah bud'ewa tayi taga wata lafiyayyen waya spark 3 sabo dal, tsalle tayi ta rungume Fadila tana jin dad'i, Fadila ma rungumeta tayi tace "kibi wayar a hankali domin yanzu waya yana lalata 'yanmata"
Amrah dariya tayi tace "insha Allah Adda zan kiyaye"
Fadila ce takira Kamal tace sun gama, ba jimawa shima ya karaso suka shiga motar, a hanya yace "number nawa kikazo Kanwa ta?"
Amrah cikin murnar wayar da Fadila tabata tace "number 2, kaga har Adda tabani kyautar waya sabuwa dal" ta Ciro wayar ta nuna mishi,
Murmushi yayi yace "ai baki dace da wannan wayar ba kamata ace burin kwaila tasiya miki ko"
Amrah turo baki tayi tace "saika kwace ai d'an bakin ciki kawai"
Dariya yayi yaciro wata sabuwar Leda babba yace "nikuma ga gift d'in danayi miki"
Mika mata yayi, yakuma Ciro irinshi ya mikawa Fadila yace "fiancy kema ga naki" Murna sukayi gaba d'ayansu sukayi mishi godiya, yana dropping Nasu yatafi basuyi wani fira sosai ba,
Fadila da Amrah suna shiga gida suka bud'e ledar, na Amrah wani kwalin wayane kiran Samsung shigen na hannun Fadila Amma na Fadila yafi nata fad'i, sai turare kala biyu manya masu kamshi, sai kwalin chocolate da sweet Leda d'aya, murna tayi tanata jin dad'i, Fadila ma bud'ewa tayi taga wani babban kwalin biscuit Wanda aka fitar da shape d'in kwalin kamar heart, sai turare itama guda biyu da kwalin chocolate, tayi murna sosai itama, fita sukayi da kayan sukaje d'akin Mama, lokacin Mama tana kwance akan Sofa sai Abba daya kwanta shima a gefe d'aya, Amrah ce tace "Mama Abba kunga gift Dana samu yau kuwa?"
Abbane ya mike yace "idan banda abinki tayaya zamu gani baki nuna mana ba Amrah"
Amrah washe baki tayi tashigo da kayan duka ta nuna musu, Kallonta Mama tayi tace "yanzu wani wayan zaki rike, na yayarki ko kuma na Saurayin Yayarki?"
Amrah kallon Mama tayi tace "Mama ai na Yaya Kamal yafi girma da kuma kyaun camera shi zan rike kinga saimuyi anko da Yayata ko?"
Fadila ce tace "eh mana ki rike nashin yafi kyau kuma zamuyi anko"
Mama ce tayi dariya tace "Allah yayi muku Albarka yarana"
Suma suka Amsa da "Amin"
Abbama Addu'a yayi musu, sun Amsa suka kwashe kayan suka tafi.
_Washe gari_
Kamal ne yakira Fadila a waya "hello fiancy"
Fadila tace "na'am fiancy"
"Dama nakiraki ne don in sanar dake yau Ummana zasuzo asa ranar Aurenmu"
Murna Fadila tayi tace "da gaske?"
Kamal yace "aa da wasa ne"
Dariya tayi tace "gaskiya yau ina cikin farin ciki"