Showing 123001 words to 126000 words out of 139192 words
duka tayi gaba, shima baice komai ba yariko hannun Baby, Baby cikin shagwaɓa tamika mishi kwalin hannunta tace "rike wannan"
Kallonta yayi yace "nifa ɗaukanki nazoyi ba ɗaukan kaya ba"
Hannunshi tariko duka biyu ta danka mishi kwalin tace flask ne aciki kuma bani kaɗai zanyi amfani dashi ba harda oya muje"
Turo baki yayi yace "aa nikam"
baby tace "oya before in cire bulala mutafi"
Rike kwalin yayi suka jera suna tafiya, Fadila datake cikin mota sai danna wayarta take, Baby zama tayi gaba shima yw zauna, nan yatada motar, tafiya suke babu wanda yake magana cikinsu, Baby ce tariko hannun Kabir tafara wasa dashi, yana jinta baice komai ba, Fadila ɗago kai tayi tagansu nan takara saukar dakai taci gaba da chart ɗinta da Abdul dayaketa zuba mata shagwaɓan tadawo gida shikam yagaji dazama,
Kabir ɗan janye hannunshi yayi, Baby ta haɗe fuska ta kalleshi, kara riko hannun tayi tana murzawa a hankali, ɗago idonshi yayi dayaɗan lumshe a hankali yace "stop it please"
Baby tace "Why?"
Kallon cikin idonta yayi yace "babu kawai de"
Ɗan dariya tayi tace "hannunka da laushi shiyasa nakeson wasa dashi"
Kallonta yakara yi, nan taga idonshi yanaɗan canja kala, da sauri tace "meya sameka? Bacci kakeji?"
Kalllon hannunshi datake murzawa yayi yace "Aa kawai ki daina"
Baby cikin yarinta tace "saika faɗamin dalili, ai ko Adda Fadila ma ina yawan rike hannunta itakam bata cewa na daina sai kai?"
Kabir shiru yayi mata dan ya fahimci yarinyan akwai dakikanci kamar ƴar fari, Baby tace "bakayi magana ba" still tana murza hannunshi a yanzu kuma hannunta yayi zufa hakan yasa hannunta yayi laushi sosai, janye hannunshi yayi da sauri yace "please"
Baby kallonshi tayi da mamaki tace "meyasa ne yaya?"
Yace "Babu"
Baby tace "hannunka yana zafi ne?"
Yace "Aa kibari idan na aureki sai kiyi kinji?"
Tace "tom amma meyasa Adda Fadila bata hanani sai kai?"
Yace "sabida akwai banbanci tsakanin mace da namiji"
Baby bata ganeba amma tace "tom"
Nan sukayi shiru har suka isa gida duk abinda sukayi akam idon Fadila, cikin ranta tace "Baby yarinta"
Fadila tana fita tace "thank you"
Baice komai ba, Baby juyawa tayi ta rungumeshi, cireta yayi da sauri yace "Kada dare yayi kije gida kinji?"
Turo baki tayi tace "yaya dan na rungumeka shine zakace natafi gida? Yaya Abdul kam idan na rungumeshi baya cemin komai"
Kabir yace "Baby na banaso Dady yayi miki faɗa shiyasa kinji?"
Tace "eh"
Yace "good girl"
Fita tayi a motar tana ɗaga mishi hannu harya tafi, Gida tashiga tasamu Fadila ta kwanta akan gado ta rufe ido alamar ta gaji, Baby ma faɗawa tayi kan gadon gefen Fadila tace "bari muyi salla"
Fadila tace "kun gama soyayyan ne?"
Baby tace "wani soyayya? Shida hannunshi ma narike yake kwacewa"
Fadila tace "may be bayason wasan ne ki daina taɓashi dan babu kyau"
Baby tace "yayana nefa dan na riko hannunshi shine matsala"
Fadila tace "Baby kenan bakiga yanda ya kallonki ba? Bakiga idonshi ya canja ba?"
Baby tace "can tamatse mishi"
Daganan ta tashi taje tayi alwalanta, Fadila ta fahimci Baby girman jikine kawai babu na kwakwalwa, itama tashi tayi tayi alwalan tazo ta tada salla, suna idarwa Adul yaui sallama, Fadila fuska tahaɗe dan batason komawa gida, Abdul agaba yasata yace su tafi,badan taso ba tayiwa su Momy sallama taje ta buɗe motar tashiga tareda rufewa gau, shima shiga yayi ya kalleta ta ɗauke kai dan haushi yake bata, hannunta yariko yana murzawa yana tuki da hannu ɗaya, yace "My Deela"
Da sauri Fadila ta ɗago tana kallonshi haka kawai taji zuciyarta ta buga tunawa da Kamal haka yake kiranta, yau kawai sai taji muryan nashi kamar na Kamal, ɗan matse hannunta yayi yace "nasan kinason zama agidan su momy to amma kinsan ina bukatar zama dake"
Fadila shiru tayi, yace "kidaina fishi please kinji"
Fadila badan taso ba tace "tom"
Kallonta yayi yace "Smile for me"
Murmushi tayi yace "good gal"
Kabir tuki yake yana tunani, kwanaki idan Baby ta taɓashi bayajin komi, saide tunda yace yana sonta da zaran ta taɓashi zai fara fita a hayyacinshi, hakan yasa dole ya rinka kwaɓarta kada ta rinka taɓashi, ɗazu badan Fadila tana motar ba baisan yanda zasu kaya ba, dan bazai iya controlling ɗin kanshi ba, yace "Allah kaci gaba da kareni"
Nan yatuna yanda Fadila ta ɗauke kanta bata kalleshi ba, murmushi yayi yace "abinda yawuce yariga ya wuce princess" da sauri ya buge bakinshi yace "Fadila".
Jiddah Ce
08144818849
[16/09, 10:01 pm] Jiddah S Mapi: 🌸🌸🌸🌸🌸
*ƘANWATA*
🌸🌸🌸🌸🌸
Na
Jiddah S Mapi
*Chapter 78*
~Baby bakida lafiya amma baza kisha magani ba? To ya kike so nayi?"
Baby tana kuka tace "kaina yana ciwo bazan iya shan magani ba"
Fadila dukta ruɗe Baby bata taɓa rashin lafiya haka ba, gani take kamar mutuwa babyn zatayi, gashi Momy bata gida sunje gidansu Nabila itada Dady kasancewar basuje sunyiwa Dadyn Nabila sannu da zuwa ba,
Wayar Babyn ta ɗauka ganin jikin Baby yana rawa tama manta ita doctor ce, kiran Wayan Kabir tayi wanda taga Baby tayi saving da Hertbeat, Kabir yana ɗagawa yace "Bebi na"
Fadila cikin kuka tace "Yaya Kabir Baby ba lafiya"
Da sauri ya juya motarshi yace "meya sameta?"
Fadila tace "kanta yana ciwo tanata kuka"
"Okay ganinan zuwa"
Kashe wayar yayi yajuya zuwa gidansu Baby, be jima ba yayi horn megadi ya buɗe, da sauri yafita yaje yayi sallama Fadila tana kuka ta amsa zama yayi a gefen Fadila kusada Baby, hannun Baby yariko yace "Baby na ya jikin"
Baby tashi tayi tafashe da kuka, faɗawa jikinshi tayi ta rikeshi tana kuka, kokarin cireta yake amma taki, hakura yayi ya kyaleta ta lafe a jikinshi, Fadila tashi tayi tace "ina zuwa"
Tana fita a ɗakin taje kitchen ta mannu da jikin bango a hankali tafara rera kukan dabatasan dalilin yinshi ba, saide tana samun sanyi azuciyarta, saida tagaji kafin ta ɗau kankana ta yanka ta kunna blander tana markaɗawa,
Kabir yace "sorry"
Baby cikin kuka tace "kaina yana ciwo"
Rike kanta yayi yafarayi mata addu', rufe ido tayi tana hawaye, saida yagama yace "zakiji sauki insha Allah"
Kwantar da ita yakeson yi akan gadon amma taki ta rungumeshi gam, shiru kawai yayi yana kallon fuskarta, idonta taɗan lumshe alamar tanajin bacci "Alhamdulillah tayi bacci ko zan samu ta sakeni" yafaɗa acikin ranshi, Hannunshi ta riko tana wasa da farcensa, bai hanata ba dan yasan batada lafiya, wani shocking yaji lokacin data kai yatsanshi bakinta tana tsotsa, da sauri yafara janye yatsan Baby da hawaye a fuska tace "yaya ka barni Fadila ta shanyemin sweet ɗina kuma bazan iya bacci ba sai nasha"
Muryanshi yanaɗan rawa yace "bari naje nasiyo miki wani kinji?"
Make kafaɗa tayi tace "Umm umm kabarni kawai hakama yayi, sai gobe ka siyo"
Tana maganar ne yatsanshi yana cikin bakinta tsotsa take kamar tasamu sweet, a hankali gashin jikinshi yafara tashi idonshi yafara canja kala, Fadila ce ta buɗe kofar bakinta ɗauke da sallama hannunta rikeda Cup guda biyu cikeda juice, Ganin Baby tasa yatsan Kabir abaki tanata tsotsa yasa ta kawar da kanta, "Baby na tashi ga Fadila takawo miki abinci"
Baby tace "Umm umm kabarni nikam bacci nakeji"
Shi gaba ɗayama baya hayyacinshi ba dama ya tureta kuma sabon rigima zai tashi, Fadila ɗan ɗago kai tayi takalli Kabir, ganin idonshi ya canja gashi ya zubawa Baby ido yanayi mata wani kallon data kasa ganewa yasa tace "Dady yadawo"
Da sauri Baby ta sakeshi tace "da gaske? Bari naje yabani wani abu yace zai bani dira tayi daga kan gadon da gudu tayi hanyar waje, Kabir bin bayanta yayi da ido ganin yanda duk jikinta yake motsi yasashi kasa tashi daga inda yake, Fadila ta fahimci hakan shiyasa ta tashi tashiga toilet ta rufe, Kabir tashi yayi har baya ganin hanya yanufi wurin motarshi yasa key sai gida,
Baby da ɓacin rai tadawo tace "Adda Fadila ina Dadyn?"
Fadila datake goge jikinta tace "bai dawo ba!"
"To amma kefa kikacemin yadawo"
Fadila tace "baki ganin yanayin da kikasa Kabir ɗin aciki ne?"
Baby tace "kamar ya? Ban gane ba"
Fadila riko hannunta tayi ta zaunar da ita tace "Baby babu kyau kina yawan taɓa Kabir shi yayanki ne amma akwai bambanci tsakaninshi da Abdul, kinga akwai sharrin shaiɗan shikuma baya iya hanaki dan matsayin kanwa ya ɗaukeki, amma haramun ne a musulunci yin hakan kinji?"
Baby tace "Tom zan ɗan rage"
Fadila tace "amma bazaki iya dainawa ba?"
Baby tace "Adda Fadila inason Kabir yanda bakya tsammani ina matukar sonshi cikin zuciyata idan ban taɓashi ba wa zan taɓa?"
Fadila tace "maganan haramci ake ba maganar so ba"
"Tom zan daina amma gaskiya bazan daina wasa da hannunshi ba"
Fadila tace "wancan matsalarki ce"
Amma kidaina yin wasu abun,
Kwanciya Baby tayi ta janyo bargo ta rufa, daganan ta ɗau waya ta danna number ɗin kabir, "hello yaya? Shine katafi baka jirani ba?"
Kabir dayake kwance gaba ɗaya jikinshi yayi weak yace "Baby na zan kiraki anjima"
"Bakada lafiya ne?"
Yace "no am fine kawai de zan kiraki"
Kashe wayar yayi, da kallo tabi wayarta tareda taɓe baki nan bacci yayi gaba da ita.
Dahaka sukayi sati biyu koda ta kirashi baya ɗauka, shikuma Kabir guje mata yake dan gudun ɓacin rana,
Yau saura sati biyu ɗaurin aurensu, Fadila datake zuwa gidan kullum dan ayi shirye shirye da ita, tana zaune agefen Baby cikin tausashen murya tace "Baby watakila bayason damuwa shiyasa baya ɗaukan kiranki"
Baby cikin kuka tace "nice damuwan? Dan ina sonshi shine zai rainamin hankali ina kiranshi ma baya ɗauka"
Fadila tace "calm down Darling watakila akwai dalilinshi nayin hakan"
Suna cikin maganar Wayar Baby tashiga ruri, ɗagawa tayi tasa a handsfree tace "me?"
Kabir yasan tayi fishi a hankali yace "Baby na banida lafiya two days kamar zan mutu, Abdul be faɗa miki ba?"
Da sauri tace "meyake daminka be faɗamin ba, gamunan zuwa"
Kashe wayar tayi da sauri taɗau dogon riga roba roba hannun armless tasa dogon hijabi tariko hannun Fadila tace "muje yaya Kabir ba lafiya"
Fadila kallonta tayi tace "saina tambiyi Abdul tukun dubi yanda kika ruɗe?" Baby tace "Adda ki kirashi tom"
Waya ta ɗaga takira Abdul tace "wai kabir ba lafiya zamuje dubashi da Baby"
Abdul yace "laa na manta wlh jiya naje amma kujirani yanzu zanzo na kaiku"
Kashe wayar yayi Fadila tace "yana zuwa zaizo ya kaimu"
Baby tace "bazan iya jira ba gaskiya"
Fadila tace "to kiyi yagane kina sonshi sosai saikin gane kuranki"
Baby safa da marwa tafara acikin ɗakin saida taji karan tsaiwar motar Abdul kafin tafita da sauri, gaidashi tayi ta buɗe motar ta zauna a baya, Fadila ma fitowa tayi da hijabi a jikinta saide bai kai na Baby tsayi ba, Shiga gaba tayi ta kalli Abdul daya jingina kai da jikin kujera tace "Hi! Mr Abdul tunanin me kake?"
Kallon idonta yayi yace "Tunanin matata nake"
Dariya tayi tace "Allah yasa"
Jan motar yayi suna tafiya suna fira, Yana isowa yayi parking da sauri Baby ta buɗe tafita, da gudu gudu tashiga bedroom ɗinshi, Kabir dayaketa murkususu ciwon ciki ya dameshi, tun lokacin da Fadila tayi musu wa'azi tun daga ranar bai kara neman mata ba hakan yasashi cikin damuwa sosai, Baby tana shiga ta zauna a gefenshi jikinta yana taɓa nashi, hannu tasa ta taɓa wuyarshi jin zafi yasa tace "yaushe kafara rashin lafiyar?"
Kabir beyi zaton zatazo ba, da mamaki yace kwana biyu dasuka wuce"
Baby cikin tausayawa tace "Sorry"
Kwanciya yayi ya lulluɓa jikinshi da blanket, ganin zafin yayi mishi yawa yasa yacire rigan, Baby ce ta ɗauka ta ajiye akan wardrobe,
Abdul yace "zan shigo anjima idan nazo ɗaukanku, yanzu Dady yana kiran"
"Tom" Fadila tafaɗa tareda tafiya ciki, ɗakinshi tawuce taje ta tarar da Baby tana goge mishi jiki da Ruwan sanyi duk tabi ta ruɗe, gaidashi tayi tace "ya jikin?"
Da kyar yace "da sauki"
Tace "inane yake maka ciwo?"
Kabir yace "cikina"
Tashi tayi tana kallonshi, kallon Baby tayi tanaso tace tafita tabarshi zai samu sauki dan tagano abinda yake damunshi amma tasan da wuya Baby tabarshi a wannan halin, Firstaid box ta ɗauko taciro allura taja ruwan allura tace "tashi nayi maka alluran pain killer in Allah ya yadda zaka samu sauki"
Da sauri yarike Baby yace "no banason allura"
Fadila tace "guda ɗayane fa"
Da sauri yace "Aa"
Ganin haka yasa takalli Baby takashe mata ido, Baby hannu tasa a hankali tana shafa bayanshi, shiru yayi yana jinta, a hankali ta zauna da kyau ta kwantar da kanshi a cinyarta, hannu tasa tana shafa lallausan gashin kanshi, sauke ajiyan zuciya yayi yakara riketa sosai, bakinta takai saitin kunnenshi tafara hura mishi iska, lumshe ido yayi, Fadila ganin haka yasa ta ciro alluran tayi mishi, ihu yayi yace "wayyo akwai zafi"
Fadila bayan tacire tafara dariya, Baby ko tahaɗe rai wai anyi dariyan saurayinta, Fadila tace "bari naje kitchen"
Tana fita yariko hannun Baby yasa hannunshi cikin nata, Baby tace "me kake so?"
A hankali yace "kince kinason hannuna kiyi wasa dashi"
Ɗan murmushi tayi tafara murza hannunshi a hankali, bacci yakeso yayi amma yaki zuwa cikinshi har yanzu yana damunshi, hannunta ɗayan ya riko ya ɗaura a cikinshi, Baby tace "me kuma?"
A hankali yace "ki shafamin"
Baby jitayi jikinta yayi sanyi, da sauri tacire hannunta tace "Babu kyau"
Cikin yanayin ciwo yace "Please kaɗan kaɗan yana ciwo"
Tausayi yabata hakan yasa tasa hannu tana shafawa, lumshe ido yayi yana jin sauki yana zuwan mishi, Fadila ce tashigo tambayar abu, ganin haka yasa ta juya baya tace "Baby zo inason magana dake"
Baby tashi tayi taji ya riko hannunta yakara ɗaurawa acikinshi, Baby tace "Cikinshi yana ciwo"
Fita kawai Fadila tayi, tarasa meyake damun Baby,
Baby leko fuskarshi tayi tace "kayi bacci?"
Girgiza mata kai yayi alamar Aa, murmushi tayi tace "kasamu sauki?"
Kara girgiza kai yayi, Baby taɗan daga kanshi daga jikinta tasa akan filo tace "to kwanta"
Kwanciya yayi hannunshi yana cikin nata, matsowa tayi kusa dashi ta kwanta, blanket ta janyo ta rufa musu, Kabir sai lallonta yake, matsowa tayi ta rungumeshi, lumshe ido yayi jin yanda jikinta yake gogan nashi, Hannunshi tariko tafara wasa dashi, mintuna kaɗan tayi tasa yatsanshi a bakinta tanasha, Kabir gaba ɗaya ya rikice yana kallonta da idonshi wanda suka kankance, signal tayi mishi alamar "ya dai?"
Da sauri yafara janye hannunshi, Baby cikin shagwaɓa tace "bakace zaka kawomin sweet kaki ba? Saika barni nasha ai"
Kabir ya harhaɗo zance yace "to ai yatsana ba sweet bane"
Baby tace "sweet ɗina ne"
Nan taci gaba,
Yace "ki daina zan siya miki sweet gobe"
Baby tace "Um um ni wannan nikeso"
Ganin da gaske take yasa yace "shh yanamin zafi"
Yazata ko zata daina amma yaga taci gaba tace "zanyi a hankali"
Nan tafara sha a hankali wanda ya gwammace gara da saurin dan wani tashi tsigar jikinshi yake, muryanshi yana rawa yace "sha da sauri"
Baby ɗan murmushi tayi,
kyaleta yayi kawai shima dan bazata gane mishi ba,
Abdul ne yashigo yana kallon Fadila wacce ta zuba tagumi tana tunani, zuwa yayi ya zauna a kasa yana kallon fuskarta yace "Mrs Fadila! Meyake daminki?"
Fadila kallonshi tayi da idanunta kamar mejin bacci tace "Nagajii jikina ciwo yake"
Da ganinta kasan akwai gajiya, hannunta yariko yana kallon idonta yace "kwanta"
Akan three seater ɗin ta kwanta tana kallonshi, hijabin jikinta ya cire tareda juyata ya buɗe zip ɗin riganta, kwantar da ita yayi yacire rigan tarage daga ita sai wani bakin vest da skin tied baki, farar fatarta takara haske sosai, sai glowing take, ribborn na kanta yacire nan gashinta ya bazu akan sofan, Hannu yasa a hankali yafara shafa jikinta, lumshe ido tayi tanajin duk wani motsi da zaiyi, tausa yafarayi mata saida taɗanji sauki kafin yazo yasa kanshi a cikinta ya rufe ido kamar me bacci, hannu tasa tana shafa kanshi, ganin haka yasa ya matso ya rungumeta tana kwance akan sofa yana zaune akasa, a hankali yace "ina Baby da Kabir?"
Fadila cikin muryan bacci tace "suna ɗaki"
Zuciyarshi ce tabada sautin dumm, da sauri yace "ɗaki kuma?"
Fadila tace "um"
Sakinta yayi yace "ina zuwa"
Shiga bedroom ɗin yayi da sallama a bakinshi, Baby tayi bacci ajikin Kabir shikuma bacci yaki ɗaukanshi, hakan yasa ya zuba mata ido yana kallonta, Abdul ne yayi sallama a hankali Kabir ya amsa, Abdul shiga yayi ya zauna abakin gadon yana kallon yanda Baby tarike Kabir tana bacci, kawar da kanshi yayi yace "ya jikin?"
Kabir yace "da sauki"
Abdul yace "kaida zakayi bacci kuma ka kyale wannan yarinyar tana bacci?"
Murmushi Kabir yayi yashafa kan Baby yace "barta tayi baccinta".
Jiddah Ce
08144818849
[16/09, 10:01 pm] Jiddah S Mapi: 🌸🌸🌸🌸🌸
*ƘANWATA*
🌸🌸🌸🌸🌸
Na
Jiddah S Mapi
*Chapter 79*
~Abdul so yake yafita amma bayason barinsu su kaɗai, Kabir sai kallonshi yake da lumsassun idanunshi a hankali yace "Dude! Bakada lafiya ne?"
Abdul yace "no ina lafiya"
Cikin bacci Baby ta mirgina takuma rike Kabir, hannunta tafara yawo dashi a jikinshi a hankali ta sauke yatsunta akan nipples ɗinshi, saurin runtse ido yayi yace "Auchh" cikin bacci tarika wasa dashi, Kabir jiyayi kamar an jona mishi shocking ajiki, A hankali ta ɗaura bakinta akai tafara tsotsa, jikin Kabir ne yafara tsuma runtse ido yayi yana riketa, Abdul da karfi yace "ke!!! Tashi kifita a ɗakinnan ko inci ubanki, kitashi nace!!!"
A firgice ta mike jin muryan Abdul kamar a mafarki, da sauri ta dira akan gadon taɗau hijab nata tafita da gudu, Kabir blanket yaja ya rufe jikinshi a hankali yake sauke numfashi, Abdul kallonshi yayi yace "Ka daina sa kanka a damuwa, barin yarinyar nan tanayi maka irin haka zai iya saka cikin matsala yanzu ma yaka kare da ciwon ciki bale ta dinga raɓarka tanayi maka wannan iskancin"
Kabir cikin kasalalliyar murya yace "to ina ruwanka? ai nanda sati biyu zata zama matata"
Abdul yace "amma ai bata zama matar taka bako?"