Showing 75001 words to 78000 words out of 154870 words

Chapter 26 - Kutkule Book One Complete Hausa Novel

28 Oct 2025

1127

kina haka ki zo kai tsaye ki shiga har inda yake ba, ki juya wanda ya baki damar shigowar da ya sanki ya shigo ya hau wajen Sire ya tambayo shi ya kuma sako ki ciki, aman daga inda nake tsayen nan ba zaki shiga ba

Kallonta ta sauke saman kansa a yatsine, ta mayar da dubanta wajrn daidaikun sojojin dake yawo a tsakar gidan, haka kuma ta mayar da dubanta kan BS da kuna abokin aikinsa dake tsaye wanda BS ne kawai ya bata amsa kan ba zata shiga wajen Abdul ba, hakan ya saka take ta hayaniya tana karawa kan sai an barta ta shiga, domin gidan mijinta ne, tana da ikon zuwa a lokacin da ta ga dama, harma ta gayaci wanda ta ga dama

Dubansa ya maida wajen abokin aikinsa, yana tunanin sakawa a fitar masa da wadinnan yan matan yan rainin hankali

Abdul ne ya bude kofar dakinsa ya fito cikin takunsa na kakarfan namiji

Jikinsa sanye da doguwar riga ta sallah baka mai dan adon goldin

Fuskarsa ba fara.a ko ta naira biyar, ya hade fuska tamkar zai kai duka

Wata irin firgita Hafsat ta yi a lokacin da ta ga fitowarsa domin bata shirta hakan ba, sam bata yi tsamaninsa a irin wannan lokacin ba

Sai da ya ja ya tsaya kamar yanda ya saba, ya kai dubansa wajen Hasana dake tsaye ta shiga taitayinta jira kawai suke ya yi gaba su bi bayansa,
Haka kuma ya kai duban nasa wajen Hafsat,
Irin kallon dake bata wahalan nan dai ya yi mata, wani kallo mai kama da tsana tsana mai shige da harare hararenta,
Tsai itama idannuwanta ke cikin nasa kafin a hankali saman lebent ta furta" *ABDELLAH* ta karasa ta lumshe dara daran idannuwanta ta kuma budewa hakan ya saka ta tara masu ruwan kwallah a cikinsu

Gabansa ne ya ji ya rikida ya fadin masa, hakan ya saka shi kawar da dubansa yana mai jin wani ruwa ruwa kadan a goshinsa

Hannunsa ya kai wajen goshin ya dan shafo, ya kalla da idannuwansa, *ZUFA* ZUfa ce yake yi dan ya yi ido hudu da yari???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?nyar nan?

Juyawa ya yi da sauki ya nufi kofa hakan ya saka su mara masa baya da sauri


Yana fitowa BS na gama rufe bakinsa cewar a fitar da su

Yarinyar da ta baiwa wajen su BS baya kan ba zata iya yin cacar baki da su bane ta juyo da sauri jin an ce wai a fitar da ita

Sai da ta yi masu kallon sama da kasa kafin ta ce" *GIDAN UBAN NAWA ZAKU CE A FITAR DA NI?*

Abdul da ya sanyo kai ya fito da sauri ya kai dubansa saman kanta,
Itama idannuwan nata ta zuba masa cikin wani kallo na rainin wayo irin na ka.ide tabas shi ne,

Gyaram murya ya yi, hakan ya saka su Abdul ja gefe sannan suka sara masa

Kallon su ya yi a fakaice sai kuma ya kai dubansa wajen matar da ta gudu da igiyar aurensa kan wai yana cikin hatsari da kuma yar farar yarinyar da suke tare

Bai yi magana ba sai idannuwansa da ya jefa masu tambaya da su ta hanyar buda masu su baki daya ya dadage masu giraransa sannan ya dan gumtse bakinsa

Bahija ce ta shiga dan kara jan abayar dake jikinta tana kara rufe jikinta sannan du rawar kan nan da take yi nan da nan ta nutsu, ta sada kanta ta kasa kuma dago da kanta ma bale har ta dubi idannuwansa dake firgitata

Wace suke tare ce ta kalli yannayinta, murmushi ta yi a ranta tana ayyana lale na yarda matansa na tsoronsa tamkar rai, kamar ba Bahija ba ta wani nutsu nan da nan daga gannin mutun tsaye a gabanta,

Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta mika hannunta irin su yi musabahan nan ta ce" *hi kanina, sunana Furaira ana kirana da Fulawa, wato fleur, ni yayarka ce wace aka fara haifa kafin a haifi mamanka*

Hannun nata ya bi da kallo, nan ya ga baki bakin hannayen nata irin na kana shafe shafen nan sosai ya kasance jikinka ne farin banda hannun naka, sosai ya kone mata hannun du irin kinshin da akai mata dan boye shi kuwa tsaf ana ganninsa

A haka ya kuma binta da kallo ita din kanta,
Wata irin farar hoda ce akai mata mak up da ita ta yi mata bau da ita, sai gashin idon nan manyan wato na karshen tsayin nan an sakawa idannuwanta da suka fara dan jemewa irin man shafe shafe ya ci fatar idon du ya yamutseta,

Wani irin kwali ne aka saka mata mai mugun baki sannan aka ja shi saman idonta sosai kafin a dora mata far bau mai ruwan ja ya yi mata wani irin bau a fuskar, sai jan baki da aka saka mata a leben wanda ya saka bakin yin wani irin dambarere da shi , kai kana gannin fuskarta ka ga rikakiyar yar bariki

Abdul kam kallon tsaf yake mata tun daga kanta har kafarta, hakan ya saka hannun da ta miko da gatsali da iya yi ya fara gajiya har ta fara jin wani iri hakan ya saka ta bude bakinta da niyar yin magana tana dan satar kallon yan matan dake bayansa wa.inda ta tabata bodygurads dinsa ne ta yannayin shigarsu wato su Hafsat, da Bahija da su BS sai shi kansa wanda ta zo dominsa ta ji muryarsa a tsakiyar kanta inda ta yi gagawar kallonsa da yannayin mamaki Abdul ya ce"




*Dan girman Allah, ku yi hakuri yan uwana, walahi doguwar tafia ce na yi tun karfe biyar na suba sai karfe biyu na dare muka karaso, zaman mota hakan ya saka ina tare da gajiya sosai gabaina na ciwo=? ?, ku yi hakuri da kadan dinsa, kun san hannuna zaku ji da yawa daga na ji garai*
>د?=ؔ?>د?=?n? @&? *KUTKALE*=?n? @&?>د?=ؔ?>د?


*(PRISON)*

NA
*SAJIDA*

Marubuciyar

DUK KARYAR KADA

YAR MAHAUKACIYA

DAGA TAFIA DAUKAR SOJA

NEMAN NA KAINA

BANI DA ZABI

IDAN KA RAINA INDA KAKE

BAK'A CE

INA KUKE MASOYAN NOVELS DINA, GANI NA DAWO DA SABON SALO, SABUWAR TAFIA,
NA ZO MAKU DA SABON NVL DINA MAI TAKE *KUTKALE* WATO GIDAN PRISON,
WANNAN NVL ZAI ZO MAKU DA LAMURA DA YAWA, KU BIYO NI KU SHA LABARI........

*WANNAN NOVEL NA SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




3?? 3??





Cikin murmushi, da yannayin raini Abdul ya dora yatsarsa saman lebensa ya ce" shiiiiiiit,
Sai da ya kikifta ido sannan ya ci gaba da fadin" Huraira? Not Furaira, u.r wlcm yar uwa, ku ware mata daki, wannan da kuke ganni an sameta ne ta hanyar kauna, ita din yar kauna ce

Wani dan murmushi ta saki , a hankali ta janye hannunta ta ce" thanx

Kafadunsa ya daga yana tsaye ya ga soja biyu sun nufi dayan bangaren dan ware mata dakin da zara zauna

Juyawa suka yi ita da Bahija dan zuwa wajen, yana kallon su

Sai da ya ga Bahija ta kusa shiga ya kalli gefen da Hafsat ke ciki, cikin yannayin basarwa ya ce" kirawota

Nunatan da ya yi ya saka ta gane wace yake nufi, juyawa ta yi ta nufi wajen su ta kirawotan saannan ta dawo ta tsaya inda take tana mai satar kallonsa

S lokacin da ta zo daf da shi, hannunsa ya mika mata yana kallonta

Hannunta na rawa ta saka cikin nasa, da yannayin nunin soyaya ya janyota a hankali jikinsa yana mai daga kansa ya hangi window din Ni.ima dake tsaye tana kallon du abinda ke faruwa, ya kuma maida dubansa wajen masu tsaron ba tare da wani dar ba ya dan saki wani dan karamin murmushi ya sakata cikin jikinsa ya bata kyakyawar runguma

Ajiyar zuciya ta sauke ta yi luf a kirjinsa tana shakar kanshin turaransa mai dadin gaske,

Bakinsa ya kai daidai kunnenta, wanda du bawan da ya ga haka zai dauka wani kalaman soyaya ne yake shirin rataba mata dan har dan rausayawa kadan yake da ita a cikin kirjinsa

A hankali ya ce" me kika zo yi gidana ne Bahija?

Bahija da ta lumshe ido tana jin wani irin mugun kaunarsa a ranta a hankali ta amsa shi da" na yi missing dinka ne, ka yi hakuri

Abdul ya dan saki murmushi ya ce" kin min laifi ne?

Kanta take gyadawa a hankali a jikinsa sannan ta ce" ban gujeka da son raina ba, na gudu ne dan tsoro Abdul Jabar

Abdul ya lumshe idannuwansa irin kalamanta sun masa dadin nan, sannan ya ce" ba laifi, *Bahija, ni Abdul Jabar mijinki, na tsinke igiyoyin auren da aka daura min da ke saki uku bisa dalilina na bin maza da kike, daga yanzu idan kika samu miji zaki iya aure, ban lamunce maki zaman minti daya a gidana ba, sannan idan na sake ki abu daya zai hana ni damun rayuwarki, ina nufin bin rayuwarki na tagayara ki shi ne ki mana min kiss a kuncina ki juya da niyar kin tafi ki dawo, idan kika kuskure da nu kike magana!*


Gaba daya jikinta ne ya kwashi rawa, tana so ta dago da mugun firgicin da ya daketa sai dai ta kasa hakan ya sakata yin wani irin lakwas tana limshe idannuwanta da suka cicika da kwallah,

A hankali ta ce" Abdul,

Abdul ya ce" shuiiiiiiiiiiiiiiit


Idannuwanta ta lumshe ta kuma budewa ta ce" *ABDUL, MAKASHINKA NA TA...*

ABDUL ya kuma wani irin matseta a jikinsa ya kara cewa" i said .....Shuittttttttttttttt

A hankali ya sasauta rikon da ya yi mata ya saketa baki daya yana sakar mata murmushi, sannan ya saka hannayensa ya share hawayenta a fili murya a dan dage ya ce" to meye na kukan? Ba gashi kin dawo ba? Ki je gidan zan zo
Ya karashe yana kashe mata ido daya

Murmushi ta kakaro itama ta matso jikinsa sosai ta yi dadage saman dogon takalmin dake kafarta ta mana masa kisss a kuncinsa kamar yanda ya umarta mata ta juya ta nufi motar da suka zo da ita cike da faduwar gaba da fatan Allah ya fidata lafia daga gidan

Hafsat dake tsaye a hankali ta jinginar da bayanta jikin garun wajen ta lumshe idannuwanta tana mai jin zuciyarta na wani irin dokawa tamkar zata ballo kirjinta ta fito


Abdul dake tsaye ya kuma mayar da dubansa dakin da aka kai yarinyar wace ta yi ikirarin ita yayarsa ce wato yar Abdul Basid, a hankali ya kara satar saitin tagar dakin Ni.ima, nan ya ga bata wajen, dubansa ya dan saci kallon dakin Muhammad,
Tsai ya tsayar da idannuwansa wajen, kallon wajen yake sosai inda kansa ya sara,
Dubansa ya kara maidawa dakin Huraira,

Juyawa ya yi ya koma cikin dakin inda su Hafsat suka bi bayansa gaba dayansu

Sai da ya kama kofar zai shiga ya juyo ya yafito Hafsat da hannunsa guda sannan ya juya ya shiga dakin

Hafsat sai da gabanta ya yanke ya wani irin faduwa kafin ta daga kafarta da kyar ta kawar da dubanta daga hararan da Hasana ta gala mata ta juya ta shiga dakin itama

A lokacin da ta shiga dakin yana zaune saman kujera ya janye jalabiyar nan sosai ta yi sama hakan ya bayanar da cinyoyinsa fili cike da gargasar gashi kwonce lufluf a jikinsa, hannunsa dauke da waya da kuma irin abin sauraron nan dake bada damar a ji inda mutun yake din nan

Takunta ta kara daukakawa ta karasa inda yake zaune,

Bakinta ta buda da niyar yin magana sai dai saurin kallonta da ya yi , ta kuma nuna mata abin hannunsa ya sakata yin gum, haka kuma ta ki yin wani motsin da zai saka a gane ko da mutun ko babu

Wayar dake hannunsa ya mika mata
Tana dubawa ta ga message ne rubuce saman screen din kamar haka " meye dalilin ki, una son sannin hujarki na cewa ba Abdul basid ke neman rayuwana ba,

Sai da ta kalli fuskarsa sannan ta saki murmushi hadi da ajiyar zuciya,
Waje ta samu ta zauna ta rubuta masa message kamar haka" *SHI NE DA KANSA YA FADA MIN*

Cikin sauri ya yi mata typing din cewa" ya dauki shekaru yana zaune da Ummih cikin karya da ha.inci, ina son sannin a matsayin girman aikin ki, kin yarda da maganar da ya fada ne?

Da sauri ta gyada kanta a lokacin da ta karanta tana kallon cikin idannueansa

Shima wani irin tsai ya yi ya zubawa kwayar idannuwanta ido,
Su kansu basu san sun jima sunna kallon cikin idon juna ba har sai da ta ji idannuwanta na neman bushewa da ruwan cikin ido ya sakata lumshe idannuwanta tare da dan gumtse bakinta kadan

Hannunsa ya dora saman screen din ya fara typing din message kamar haka" *kina da kyau Hafsat, ina sha.awar kasancewa a haka da ke*

Hannunsa ya tsurawa ido gannin yana ta rawa rawa , a hankali ya shiga bin harufan daya bayan daya da kallo kafin ya saka hannunsa ya shiga gogewa cikin sauri,
Sai da ya gama gogewar ya kuma kallonta ya ga ta kawar da kallonta kwata kwata daga kansama, haka kawai ya ji ba dadi, ta daina kallonsa dan me?

Message ya rubuta cewa " *Budurwar BS, na kara shiga duhu, tsohuwar matata ta dauko kalmar cewa Makashina na tare da ni, hakan na iya nufin ke ce, bs ne, Mubarack ne, Hasana ce, Ni.ima ce, bakuwar da ta zo yanzu ce, ko cikin sojojin dake gadin gidana?*

Da maimaita maganar ya fi a kirga sannan ta dago ta dube shi,

Mayar da yatsunta ta yi , jiki a mace ta saka" *INA TA JE NE? A ZANEN DA KA YI KA MANTA MUHAMMAD.*

da sauri ya dago ya dubeta, mikewa ya yi ya nufi bayi da sauri ya nitsa abin cikin ruwan wanka hakan ya saka ya daina aiki, fitowa ya yi ya yi tsaye gaban Hafsat yana kallonta tana kallonsa,

Sai da ya hadiyi wani irin yawu ya ce" kina tunanin, Muhammad, dan uwana, yaron da muka girma tare, muka yi karatu tare, muke kwana muke tashi tare, zai nemi dukan wannan lamari da ni ne Hafsat?

Hafsat ta girgiza kai tana kallonsa sannan ta ce" ban ce ba, na ga kana zane ne ya saka ni tina maka sunnansa dan kar ka maanta kowa,

Abdul ya gyada kai yana kallonta , dan sam bai karanci abinda take nufin nan da gaske bane, dan haka ya dan kankance idannuwansa yana kallonta

Murmushi ta sakar masa sannan ta dan matso kadan kusa da shi ta ce" *ka bani dama mana, dan Allah ka bani dama na shiga cikin lamarin, ina son binciken nan a kusa da ku, ina son binciken kowa ciki harda ni kaina*


Fuskarta ya karewa kallo yana jin yanda wata irin zufa ke son keto.masa, tamkar wanda ya yi gudu,

A hankali ya kai dubansa wajen kafadarta inda aka harbeta,

Hannunsa ya kai da niyar taba wajen sai dai tuna cewar hakan na iya bata mata rai ya saka shi jimke hannunsa a hankali ya tsura mata ido,

Hannunsa dai ya kuma dagawa ya kai wajen goshinta ya dan dora yatsar wajen gashin gaban goshin da ya yi luf luf da shi a hankali ya fan shafa shi sai kuma ya janye hannunsa,

Tsura mata ido ya yi yana kallon yanda take kallonsa tana jira ya bata amanar shiga dumu dumu cikin harkar hargitsin dake tare da rayuwarsa,
A hankali, cikin wata irin murya ya ce" wanda kika yi na jiya da shekaran jiya, ban so ba,
Sai dai na yafe maki Hafsat,
Ifan kika kuma saka kanki cikin wannan lamarin, Ba zan iya yafe maki ba Hafsat,
Ba zan iya kuma shakar numfashi ba idan har ya kasance wani abu ya same ki,

Idannuwanta da ta lumshe tana kallon cikin idonsa ne ya saka shi cewa" ba zan iya kuma walwalaba idan har wani abu ya kuma samun wani ta dalilina ba ke kadai ba Hafsat!

Hafsat ba zan iya jura ba a ce wa......

Ihun da suka jiyo daga tsakar gidan ne ya saka su gaba daya kallon kofar,

Da wani irin sauri ya daga kafarsa da niyar zuwa hakan ya yi daidai da itama ta damko hannunsa tana girgiza masa kai ta ce"""""""""


Comment jama.ata na tuba>?#?>?#?>?#?
>د?=ؔ?>د?=?n? @&? *KUTKALE*=?n? @&?>د?=ؔ?>د?


*(PRISON)*

NA
*SAJIDA*

Marubuciyar

DUK KARYAR KADA

YAR MAHAUKACIYA

DAGA TAFIA DAUKAR SOJA

NEMAN NA KAINA

BANI DA ZABI

IDAN KA RAINA INDA KAKE

BAK'A CE

INA KUKE MASOYAN NOVELS DINA, GANI NA DAWO DA SABON SALO, SABUWAR TAFIA,
NA ZO MAKU DA SABON NVL DINA MAI TAKE *KUTKALE* WATO GIDAN PRISON,
WANNAN NVL ZAI ZO MAKU DA LAMURA DA YAWA, KU BIYO NI KU SHA LABARI........

*WANNAN NOVEL NA SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




3?? 4??






Hannun suka kalla a tare,
Da sauri ya janye hannun dan wani irin tsam gaba daya jikinsa ya ji, dan kuwa ba tsintsiyar hannunsa ne ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login