Showing 111001 words to 114000 words out of 154870 words

Chapter 38 - Kutkule Book One Complete Hausa Novel

28 Oct 2025

1162

tana rike cikinta, ta nunata da yatsarta ta ce" zan so na ga idannuwan hajiar gidannan, wai wai wai za.a zane mata elhaji a gabanta, kuma a cikin gidan ubansa

Mama ta harareta ta ce" ke ba zaki girma ba ko? Bana so
Ki ce da Abdallahn ni nace dan Allah ya yi hakuri ya daina biyewa kowa a gidan nan, idan kuwa dukan ne ya daki anmih dan kuwa ke ce bakya jin magana, maza tashi ki je ku zauna dan na tabata zaman nan da bawan Allahn nan ke yi a wajen nan dan kawai ya tare maki rigimarsu ce, kin ga kuwa da sauki dan ni kaina an jima ba.a zage ni ba bare ke.................

5?? 0??





Aunty kam murmushi take ita kuwa ta karasa ninke na hannunta ta juya tana tura baki gaba waima kar ya ga damarta ta fice a dakin

Murmushi aunty ta yi tana duban mamansu ta ce" ina mamakin shakuwarsu, mutun baban mutun irin wannan, da farko aban Fahad na fada min ko shi waye a kasar nan na ji tsoro ko wani abin yake kawo shi gidannan? Sai dai irin yanda mu.amalarsa da malan da kuma ita kanta Maman malan abin sai ya fara yi min haske, a hankali na gane shi din ne mai saukin hali domin kuwa da akama shi ya saka maman malan nutsuwa


Tun da ta tunkaro inda yake zaune ya tsayar da danna wayar da yake ya tsura mata ido,
Yanda ka san ta zauna ta tsara yanda halitarta zata kasance mata ,
Daga sama ba wani mugun tudu aman daga kasa ko batai niya ba sai sun shaida kansu

Kawar da kansa ya yi, dan baya so ya ringa irin wannan tunanin, yau dai alhamiss ce in sha Allah a gobe za.a zo tambayar aurenta a yi a gama shikenan

A haka ta karaso ta zauna bayan ta yi salama ciki ciki

Shareta ya yi ya ki amsa salamar a bayane saima ya fitar da wayar ya ci gaba da dadanawa

Ta kai dubanta kansa ya fi a irga , sai da ta gaji ta ce" meye?

Shiru ya yi mata ya ki kallonta

Hafsat ta ce" Abdallah, menene wai?

Dago da kansa ya yi, ya zuba mata manyan idannuwansa masu zama da launin ja kusan koda yaushe sannan ya ce" Hafsat, kin yi kyau

Bakinta ta turo ta ce" ba mun yi fada ba, shine ba zaka bani hakuri ba?

Abdul ya tabe bakinsa ya ce" shikenan kulun sai na ringa baki hakuri bayan nine yayanki ke kuwa kanwata?

Kanta ta juyar gefe sai kuma ta sauke ajiyar zuciya ta shiga dan jefa kafarta daya tanai mata gaba da baya a hankali
Kafar ya kaiwa idannuwansa kallo, yatsotsin kafar sun sha jan lale faratunan kansu sun sha jan lale sun yi tsaf da su, Hafsat ba dai tsafta ba

A hankali ya dan daga kansa har zuwa fuskarta, ya ga utama shi take kallo irin kallon kurullahn nan

Girarsa ya daga mata a hankali ya dan kane idonsa guda ya ce" kallon fa? Ko na maki ne yarinya?

Bakinta ta tabe a hankali itama ta ce" kallon fuskarka ne nake, cike da kamala kamar ba kai ba idan ka tafka tsiya wai Abdul ni zaka zane yayana? Kuma ka fadawa malan kiri kiri

Baya ya yi ya jijgina da kujerar da yake sama ya ce" ai kece yayanki, ni kuwa na girme shi, kuma ni ba soyaya nake da ke ba bale na kama kafarsa kar ya hana min , ke kanki dan bana iya dukanki aman da ina iyawa na fara kwalo da ke Hafsat sai na kwonce maki kusoshin kai kwaila kawai!

Idannuwanta ta zaro waje ta ce" ni ce kwailar?

Abdul ya ce" eh ke din,

Haushi ya kama ta, zata rama wayarta t shiga kuka,

Tana gannin sunnan BS ne ta gyara zamanta ta daga kiran

Sosai ta sanyayar da muryarta ta amsa masa,
Cikin nutsuwa ta shiga baiwa kowace kalma tasa mahinmanci tana sauraronsa

Irin yanda take wasa da idannuwanta da kuma lebenta ya kurawa ido,
Mamaki yake irin yanda take zance da Bashir,

Mikewa ya yi a hankali ya duka ya dauki kys din motarsa da ya yar wajen mikewar ,
Bai kuma koda kallonta sau daya ba ya juya da niyar tafia

Tana nan zaune tana kallonsa har ya bar wajen kafib ta sauke wata nanauyar ajiyar zuciya, ita kam a kulun tana tausayawa matarsa, zama da abdul wani gagarumin hore ne da za.a baiwa bawa kafin ya mutu bisa laifukansa , shi bakinsa ya kunshi abubuwan haushi da takaici!





Ranar juma.a,
Yau ne ranar da ya dace a karbi auren Hafsat, wace malan ya yi nuyar idan sun zi zai fada masu a yi abin a kusa kusa, kai shifa idan da hali sai ya daura mata aure a yau din nan dan bai ga me zai ci gaba da jira ba shi kam a shirye yake dukan abubuwan da za.a yiwa yar gata ya tanadarwa mamansa sai dai idan fangin mijin nata ne basu shiryawa hakan ba........


Bayan sallar juma.a, sanye suke cikin shiga ta alfarma, a yau shi kansa Abdallahn ya saka manyan kaya na gani na fada hakama malan ya saka fararan kaya sai murmushi yake cikin nutsuwa
Manya manyan tabarmi aka shinfida a kofar gida, aka ajiye kujeru inda anguwa ta dauka cewa Malan zai bayar Da Uwar malan a karo na biyu, hakan ya sa du wani mai jin kwakwaf ya hakarta a wajen mata kuwa suka ringa shiga cikin gidan, masu zuwa dan zumuncin Allah da taya murna ma du sun halara sai gashi kamar da wasa gidan malan da kifar gidansa yana neman mugun cikar da ba za.a iya saka tsinke ba

Zaune suke Malan sai Abdul a gefensa na hagu sai aminan malan a na dama, a kan tabarma daya, sai sauran tabarmin du mutane ne a zazaune ana ta zaman jiran zuwan angwaye

Ana zazaunen nan awa daya ta shige, ta biyu ta shige,
Abdul da malan na yawan duban hanya,

A haka lokacin sallar isha.i ta yi, aka ringa fitar da butoci kofa dan yin sallah wa mutane, nan suka ringa dauka suna alwallah karshe dai aka gyara tabarmin malan ya ja sallah

Ana salame sallah malan na kallon waje daya, idan ka bincika zuciyarsa zaka ga tana dokawa fiye da yanda ya dace ta doka

Abdallah ya mike ya fita daga cikin mutane ya ci gaba da neman layin BS, dokawa yake, layin na ringin sosai sai ya kusan tsinkewa sai a latse shi a kashe kiran,

Zuciyarsa ce ya ji ta fara daukan zafi, a haka ya nemi number GN, shima ya yi ta kira aman shiru tasa bata shigama bare har a daga

Dawowa ya yi yana gannin yanda ake binsa da kallo, ya ratsa ya shige cikin gidan malan

Yana zuwa ba ruwansa da yanda ake binsa da kallo ya samu ya ratsa matan nan da suka cika tsakar gifan ya shige bangaren mama

Yana zuwa bai tsaya wata wata ba ya shige ya karasa inda mama take zaune saman kujera, gefenta Hafsat ce nanade da lafaya ruwan maroon ta dukunkune kanta sai sauke ajiyar zuciya take, sai yan uwanta mata uku ciki harda aunty suna zaune jigum jigum

Karasawa ya yi inda mama a
Ke zaune ya tsuguna a gabanta hakan ya saka du suka juyi suna kallonsa banda Hafsat da ta kara labe kanta a ranta tana fadin yau Abdul har a dakin mamana ya shigi ne ya mun jan ran ko? Na shiga uku kar dai da gaske malan har ya daura min aure?

Kafin Abdul ya yi magana , muryar hajia mama uwar gidan aba ce ta karade gidan da budar da sai da ta baiwa mutane mamaki,

Mikewa ta yi tsaye ta daga murya ta ce" kowa sai ya kama gabansa, ai ba yau aka fara ba a tara jama.ar da ba.a taba tarawa ba dan yar gwal aman a kwashi kunya,
Daurin auren da aka so a yi daidai salar juma.a dan a samawa yar albarkar juma.ar sai dai Allah ai ba lale ya yi maka abinda ranka ke so ba dan kai ka bambanta abu kana so na daya ya fi na kowa ai Allah ba zai yarda a yi haka ba, mata ku watse kowace ta je gidanta ta dora sanwa an fasa auren uwar malan yar gwal domin da za.a daura da an daura shi! Hehehe dadina da gobe saurin zuwa, ba zaka je ka gama yawon ta zubar dinka ba kuma ka dawo a rurufe a yi maka gata duka Allah na kallonka ba!

Nan da nan yar hayaniya ta ringa tashi, kowace na tofa albarkacin bakinta wasu na tambayar da gaske an daina? Dama wai wa zai kwashi saura? Abubuwa dai babu dadin ji

Da sauri ta bude lulubar da ta yiwa kanta, yar rigar cikin lafayar ce kawai ta yi saura sai na tsatsonta dake nanade,

Dubanta ta fara ajiye kan mahaifiyarta dake kokarin jan hijabinta da kyau ta kara rufe fuskarta dan bata so a fahimci halin da take ciki

Da sauri ta kai dubanta wajen agogon bangon dakinsu, har magariba ce ke neman yi,

Dubanta ta kai wajen Abdul ta ga ya kama hannun mahaifiyarta yana magana kasa kasa sannan ira kuwa tana gyada kanta a hankali,

Wajen yan uwanta da suka nufota ta kai dubanta , da sauri ta diro daga saman bed din ta kali auntynta ta ce" aunty, ina wayana? Bani wayana dan Allah

Auntyn tata ta bita da kallo sai dai bata bata wayar ba

Muryarta ta daga ta ce" aunty wayana nake tambayarki aman kin zura min ido? Ki bani wayana

Cikin daga murya mama ta ce" uban me zaki yi da waya?


Da sauri ta juyi wajen maman nata, kafarta ta daga ta karasa wajenta Abdul ya dan ja gefe daya, tana zuwa ta kama hannun maman ta ce" mama, zan yi kiran Bashir ne, na tambaye shi lafia suka yi dare haka? Mama kin ji abinda hajia ke fada wai an fasa aurena? Mama bani na kitaye shi ya zo a daura min auren nan ko zata ji kunya ta shafa min lafia, mama na rantse da Allah ba karuwanci na je ba, ni ba yar bariki bace, ban yarda na zubar da mutuncina ba, kuma Allah bai basu ikon zubar min ta karfi ba

Dubanta ta kai wajen Abdul da sauri ta damko hannunsa na dama ta rike gam a hannunta ta ce" Abdellah, ka saka su bani wayata na yi kiran shi, maza ya zo da sauri kar dare ya yi, ya zo a dauran aurena , kai ka san yana so na ko? Kai ka san ya fada min shi koma me ake kirana ko ake kalona da shi yana sona a haka, kuma a dazu muka gama waya da shi da sasafe, da sasafe sai da ya fadan yau zai kawo kudin aurena Abdul, ko bashi da lafia ne? Ko bashi da kudin ne? Ka bashi ya aure ni ka ji? Idan bashi da lafia ne a kai ni wajensa ka ji?

Hannunta da ta rike shi ya bi da kallo, kafin ya kai kallon nasa wajenta, irin yanda ta rikice take sakin zance na bata cikin hayacinta

Aunty ya kala hakan ya sanar mata fa yana so ta kamata ne,

Mikewa aunty ta yi ta riko hannunta sai dai maimakun ta sake shi sai gaba dayanta ta afka kirjinsa ta rukunkume shi tana wani irin jijiga shi gaba daya ta yakune masa gaban rigar tasa shadarsa mai ruwan sararin samaniya du ta aniya yakuneta tana jijiga a kirjinsa tana maimaita ya kira mata Bashir tana son magana da bashir!


Da wani irin karfi ya cireta a jikinsa ya dauketa cimak ya direta saman bed din da take a dazu kafin ya juyo ya kali yan uwanta irin yanda du suka fita a hayacinsu tsabar tashin hankali sai mahaifiyarsu dake zaune kanta a kasa bata dago bama bare a fahimci halin da take ciki
Bakinsa ya buda da kyar ya ce.......
>د?=ؔ?>د?=?n? @&? *KUTKALE*=?n? @&?>د?=ؔ?>د?


*(PRISON)*

NA
*SAJIDA*

Marubuciyar

DUK KARYAR KADA

YAR MAHAUKACIYA

DAGA TAFIA DAUKAR SOJA

NEMAN NA KAINA

BANI DA ZABI

IDAN KA RAINA INDA KAKE

BAK'A CE

INA KUKE MASOYAN NOVELS DINA, GANI NA DAWO DA SABON SALO, SABUWAR TAFIA,
NA ZO MAKU DA SABON NVL DINA MAI TAKE *KUTKALE* WATO GIDAN PRISON,
WANNAN NVL ZAI ZO MAKU DA LAMURA DA YAWA, KU BIYO NI KU SHA LABARI........

*WANNAN NOVEL NA SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




5?? 1??


*Yan uwa=?-?=?-?=?-? ya bakwa comment zaffaafa ne? Ko labarin ba siger ne? Haba kuma na fns, ina mugun yi da ku, ku kuwa kun daina bani comment zafafa? Idan har yanzu cikin sallah muke na dakatar idan aka gama shagulgulan sallah sai mu ci gaba =??=??=??=??=??*



Bakinsa ya buda da kyar ya ce" menene haka? Haba aunty, ku yi hakuri, zamu yi jiransa daga nan har karfe goman dare

Yana gama fada ya juya ya fice , nan Hafsat ta kara mikewa da niyar dirowa daga bed din, sai dai kafin ta karasa hanzarin nan nata ta ji saukar wani gigitacen mari,

Kuncinta ta dafe da sauri ta kali fuskar mahaifiyarta, sai da gabanta ya yanke ya fadi domin kuka mamanta ke yi hawaye ne sosai ke zuba daga gurbin idannuwanta

Yatsarta ta nuna mata ta ce" binsa zaki yi? Kuma bace mana zaki yi? To ki je ANMIH! na ce sai ki tashi ki kara fita a irin wannan halin, ke dama zagin mutane ko magangannunsu ba damunki ya yi ba, sai ki mike ki je ki raba abin fadan kin ji? Zaki nuna min rashin hankali da rashin da.a ne? Ko kuwa tarbiyarki ce ta koma haka? Ke idanma wahainiya kike mai canza kala a dukan wani lokacin da ta yi niya dan ubanki a yau ba zaki je neman namiji ba, meye? Me kike tsoro? Me kike gudu? Menene baki gani ba?

Shiru ta yi sakamakon kukan da babar yarta ta ????      

                  ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ? fashe da shi tana rike mahaifiyar tasu,

Dubanta ta mayar wajenta, tanai mata kallon nan na abin tausayi

Tana hawayen ta ce" baki koya mana daga murya ba, ki sasauta muryarki ummah,
Menene bamu gani ba muka kashe muka birne tsakanin mu? Daga muryarki na iya tona sirrin mu,
Ummah, rayuwa ce, jarabawa ba irin yanda bata zuwa, na sani , uma na san kina cike da tashin hankali yannayin rayuwar maman malan, sai dai kuma ina so mu zauna mu zubawa sarautar Allah ido, malan kanda ya yanke hukunci yi mata aure ne dan ya fitar da ita a gidan nan ko zata ji sanyi da ranta,
A wajenmu ne take samu sanyi, ba zan yarda wajen namu ya koma ya zame mata gidan kurkuku ba! Ummah, ai maman malan ta yi sauki, a ganina an samu ci gaba a halayar maman malan

Hannunta ta janye a hankali ta juya ta shige bayin dakinta ta dauro alwallah

Tana fitowa ta dube su muryarta sanyi kalau ta ce" ku tashi ku yi alwallah, sallar magariba ake kira, kar ta shige

Daya bayan daya suka ringa shiga ciki suna dauro alwallah suna fitowa domin sun kasa fita waje bale har su yi anfani da bayin wajen

Ita kanta Hafsat alwallar ta dauko ta zo kusa da yan uwanta ta tayar da sallar magariba,
Gaba daya ta cire du wani abu mai iya sakata kyalkyali ko annuri,
Bayan ta gama sallah a hankali ta ja jikinta ta jingina da jikin gado ta kurawa waje daya ido,
Tana jan carbinta tana tana kaiwa wayarta dake saman gado kallo, idonta na kara lumshewa tamkar zata fasa ihun kuka sai dai ba hali

A haka aka yi kiran sallar isha.i, cikin gidan sai kakayatu ake magangannu sai isko su suke da shewa kala daban daban, sai dariya ake shekaya ana kashewa kowace ta sha ado ana buga waya ana fadin yau malan ke aurar da yar gwal aman ana jiran angwayen tun rana har yanzu basu karaso ba

Dakin mama sun yi shiru, ba mai yiwa dan uwansa magana, suna lazumi dai kowa na neman sauki a wajen Allah

Mama ce ta dubi yayanta baki daya, cikin murya a shake ta ce" dare fa na yi, ku tashi ku lalubi gidajenku mana Mariam?

Nana Mariama ta dubeta, ta kai dubanta wajen agogon dakin , karfe tara da rabi ce ta yi,

Mikewa ta yi a hankali ta matsa kusa da maman nasu da niyar yin magana

Wata irin buda ce aka saki a tsakar gidan, buda mai karfin tsiya, buda ce irin ta harshen buzaye wace ake kada harhen ana ajiyewa ana kuma dauka ba tare da an sauke lumfashi ba

Matar da ta shigo daga waje, wace take marokiyar anguwar ce, macen da ta zo tun da rana dalilin daurin auren aman gannin an fasa kamar yanda hajia mama tace kowa ya watse sai yan tsegumi dake lekowa jifa jifa suna jin kwaf suna fita

A yanzu haka ta dawo ne sakamakon mai yar lasifikar da ya shaida za.a daura aure,
Za.a daura auren Hafsat a irin wannan lokacin
Ba wanda bai yi mamakin irin lokacin da angon ya saka ba, du mutanen dake kusa sun halarci daurin auren da ya gigita su,

Hafsat? Yar gidan malan, yarinyar da ta kwashe tsayin shekarun rayuwarta tana rayuwa mai hatsari, rayuwa marar tsari, rayuwa tamkar wace ta fito a tsatson arnawan da basu san kalmar musulunci ba, yarinyar da baki da yawa a dazu sun

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login