Showing 81001 words to 84000 words out of 154870 words

Chapter 28 - Kutkule Book One Complete Hausa Novel

28 Oct 2025

1153

fito ya haye mashin ya bar gidan

Wasa wasa haka ake neman Hafsat tamkar ana neman zinari, ba inda basa dubawa, ba wanda ke zaune, du wanda ke gidan nan hankalinsa a tashe, GN da kansa ya tako ya zo ya kuma bada gudunmuwar neman Hafsat,

Abdul du ya wani firgice, harda lokacin da Muhammad ya tirke shi kan wai me yake haka? Ya fita lokacin da ya yi niya ba tare da an san fitarsa ba , a yi ta nemansa a rasa, baya tsoron masu farautarsa su samu galaba a kansa, baya gudun wani mugun abin ya same shi,?
Sai kawai ya karewa Muhammad kallo ya ce" da sun kasheta, da sun kawo gawarta kamar yanda suka saba, tana raye, yau kwananta hudu tana raye a hannun makiyana

Muhammad ya ce" ka tabata makiyan naka suka dauketa? Yarinyar da ta saba guduwa abinta ta yi tafiarta? Yau aka fara tsayuwa nemanta? Shaidar basu kasheta ba zai nuna maka cewa kawai ta yi tafiarta ne

Abdul ya kare masa kallo kawai ya sa kai ya barshi wajen tsaye

Yau an tashi lahadi, kwanan hafsat biyar kennan rabonta da gidan Abdul, ko yau tsaye ya kwana yana kaiwa Allah kukansa

Safiya na yi Ni.ima ta fara shigo masa daki, cikin shiga ta abaya a jikinta
Waje ta samu ya zauna bayan ta gaisar da shi tana kallon sa,
Sai da ya shafa fatihar azkhar dinsa ya kai dubansa wajenta sannan ya amsa gaisuwar tata ,
Yana kallonta ta ce" me ke faruwa haka ne? Kwana biyar kennan baka waiwayi inda nake ba, baka neme ni a komai ba, wani abin ne?

Tsuru ya yi yana kallonta cike da mamaki, kai kwanansa biyar bai nemi mace ba? Ikon Allah, dama akoy damuwar da zata gigita wannan bukatar har ta daina hayo masa a lokacin da ta yi niya?

Yawun bakinsa ya hadiya kafin ya yi mata nuni da ba komai

Kukan dake cin ranta ta hadiye sannan ta mike da niyar yi masa salama,
Har ta fara tafia ta kuma dawo ta duka tana kallon zara zaran yatsutsan kafafuwansa masu dauke da gashi baki sidik sun kwonta luf luf a yatsar ta ce" Abdul, ina son ka, sonka ya saka ni makancewa na bi ka, bani da jiyar gudun ka komai wuya Abdul, kar ka juyan baya dan kuwa a irin take take da kuma yannayinka da na karanta na girgiza na kasa baci, ni ban hanaka kara aure ba, dan kuwa ina son abinda kake so

Tana gamawa ta mike ta fice a dakin, inda Abdul ya bita da kallo a wajen a zaune tamkar mutun mutuni

Mikewa ya yi ya shiga wanka ,
Yana fitowa ya saka manyan kaya harda hirami saman kansa ya fito ya nufi dakin Ni.ima

A lokacin da ya shiga tana kwonce saman bed tana aikin, wato kuka

A hankali ya karasa inda take da irin kwonciyar da ta yi ya saka hannunsa ya dagota zaune,

Ido ya dan tsura mata kafin ya ce" ba kyau kwonciya saman ciki,

Kanta ta gyada tana kallonsa tamkar ta dauke abinta ta mayar cikin cikinta ko zata ji sasaucin zafin kaunar da kishinsa da take

Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan ya ce" kin san wani abu? Kyautatawa na saka so koda babu shi,
Ki lalubi sauran kyautatawar zaman aure, ki rike a hannun ki, ina mai baki albishir din tabas zan maki hira

Shiru ya yi cikin jan aji da jan maganar da ya yi sannan ya ce" ban san me yasa kowa ke gannin nuna damuwata wa batar yarinyar da ta damu da ni *So ne*, shi dama ba.a shakuwa sai soyaya? Na shaku da ita, ina walwala da ita, ta iya hira da ni
Wannan shi ne kawai tsakanina da ita,

Yana gama fada ya mike ya mikar da Ni.ima dake jin ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????wani irin kaunarsa da kara shiga ranta da yake da irin yanda yannayin jan ajinsa da kwaliyarsa ke kasheta ,
Cikin yannayin nutsuwa ya kai lalausan lebensa wajen goshinta ya mana mata kiss, sannan a hankali ya ce" Allah ya maki albarka

Bai tsaya ya kuma kara wani zama ba ya fice a dakin ya fice tare da masu bashi tsaro ba tare da ya fada masu ga inda zasu je ba, haka kuma bai yiwa Muhammad salama ba suka dauki hanya cikin tukin garari kamar yanda suka saba har suka dangana da aeroport

Jirgi na daukan su sai da ya kawo su Niger, ya sauka a Niamey

Suna sauka wasu motocin suka shiga wa.inda BS ua tanada ,

Tafia suka yi mai tsyain gaske, dan a kadan sun yi awa daya da minti talatin sunna tafe a cikin banban birnin kafin su karaso anguwar

A lokacin da suka karaso masalacin da akai masa kwatance da shi ya saka su karasawa direct har kofar tankamemen gidan

A lokacin da Abdul ya fito ya yi tsaye yana bin anguwar da kallo haka kawai murmushi ya kubce masa,

Salamar da ta doki dodon kunnensa ta saka shi saurin juyowa,

Yau gashi ga kamilin datijon, datijon da yake jin muryar sa a waya,

A lokacin da malan ya karaso inda Abdul ke tsaye kasa tsayawa kikam ya yi a gabansa kamar yanda ya saba, dan kuwa wani irin ni.imtacen kanshi ne yake bazawa gashi cikin wata farar shada an yi mata baban dinki gari da yar ciki, kansa da hula da carbinsa madaidaici a hannunsa mai kyan gaske, sai walwali yake na annuri yana karawa

Gaba daya Abdul ya kai kasa dan gaisar da Malan, hakan ya sa sauranma zuba masa ido da mamaki, dan basu taba gannin haka ba, du girmanka har sai ya wani karkace zai maka gaisuwar raini sai gashi yau ya dukawa wani datijo

Malan kam da ido ya bi shi yana murmushi, sai da ya amsa gaisuwarsa sannan ya mika masa hannu ya taso su kai musabaha ta kirki kafin Malan ya ce"
>د?=ؔ?>د?=?n? @&? *KUTKALE*=?n? @&?>د?=ؔ?>د?


*(PRISON)*

NA
*SAJIDA*

Marubuciyar

DUK KARYAR KADA

YAR MAHAUKACIYA

DAGA TAFIA DAUKAR SOJA

NEMAN NA KAINA

BANI DA ZABI

IDAN KA RAINA INDA KAKE

BAK'A CE

INA KUKE MASOYAN NOVELS DINA, GANI NA DAWO DA SABON SALO, SABUWAR TAFIA,
NA ZO MAKU DA SABON NVL DINA MAI TAKE *KUTKALE* WATO GIDAN PRISON,
WANNAN NVL ZAI ZO MAKU DA LAMURA DA YAWA, KU BIYO NI KU SHA LABARI........

*WANNAN NOVEL NA SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




3?? 6??


Tunda Malan ya saka Abdul a gaba da ido yana kallonsa cike da al.ajabin labarin da ya bashi nasa na ainahin waye shi dala dala har ya dire malan kallonsa kawai yake

Mikewa ya yi ya dauko goron ruwa ya mika masa tare da fadin " Sha

Bismillah Abdul ya yi ya sha ruwan nan sannan ya kokarta ya mayar da damuwar dake tare da shi ya dubi malan dake kallonsa zuru, sak irin idannuwan Yar malan

Malan ya lumshe idannuwansa sak irin na Hafsat kafin ya dan gumtse bakinsa sai kuma ya saki ya ce da Abdul" Sannu


Abdul ya yi murmushi ya sada kansa, dan shi wani irin nauyin Malan yake ji sosai,

Malan ya ce" bawa na haduwa da jarabawa kala kala yaro,
Tabas jarabawarka mai girma ce, ba kamar gannin gawar mahaifiyarka da harbi a goshinta,
Tabas Allah ya san da zamanka dan ka rayu cikin jarabawa Alhamdulilah,

Sai dai maganar da batai min dadi irin yanda kake magana da sunnan mahaifinka a cikin lamarin nan, ba zan so ka yanke hukunci a kansa ba, ba zan so ka zama mai fushi da iyayenka ba, ko mai ya yi zan so ka saurare shi sannan ka yi maza uzuri, jarabawar rayuwa ce shi kansa ta same shi, muguwar jarabawa ce mai saka bawa kauracewa mutane, kai wannan mahaifin naka yana da zuciya mai kyau da abi saka rayuwarsa a hatsari ba, ina nufin ya kashe kansa, ko ya idasa lalacewa ya shiga wata muguwar hanyar daban

Abdul ya sauke ajiyar zuciya yana sauraron Malan,

Malan ya ci gaba da fadin" sai maganar da muka yi da kai cewa an ce da kai makashinka na tare da kai, gashi an harbi tsohuwar matarka kuma an sace mai baka tsaro ko?

Andul ya tsura masa ido yana kallonsa,

Malan ya ce" in sha Allah, tunda har suka kai haka, zan iya ce da kai wata hanyar ce ta samun nasara, tabas ka sakawa ranka cewa za.a iya dacewa a kowani lokaci gaskiya na iya bayana,

A hankali Abdul ya ce" ta kasance mai kwana da tashi da sunnanka,
A kan dalilinta na ta dawo wajen iyayenta ta tarbi harbin da zai same ni ya sameta, fama take, ta shure makudan kudadan da take iya samu dalilin aikin da aka bata ,

Tsai malan ya yi da jan carbin da yake ya tsurawa Abdul ido

Abdul dake zaune saman abin salaya mai laushin gaske , ya kara tankwasa kafarsa yana kallon malan ya ce" ba zata gudu ba, ba kuma ta wulakanta kanta ba, rayuwar tsayaya da ta yi halitarta ce, iko ne daga Allah,
Ta kasance mai tsare kanta, mai tsare mutuncinta, mai hanawa a kama sunnanta kai tsaye dan malan, mai kuka da hawayenta tana kitan sunnan malan,

Carbin hannun malan ne ya kubuce ya fadi daga hannunsa yana kallon Abdul, unda hannunsa ya shiga rawa rawa haka kuma ya kasa magana ya kuma kasa motsawa

Mikewa Abdul ya yi daga inda yake ya matsa kusa da shi ya zauna sosai kusa da malan ya ce" na taso daga kasar Minna a irin wannan lokaci dan na kasa dangana,halayanta na gari sun saka na shaku da ita, na zo da kokon barana a kama mana da adu.a, Allah ya kuma fitar da ita da hannun da ta shiga, dan kuwa wasu na zargin ta tafi da kanta ne, ni na san ba zata tafi da kanta ba, dan kuwa tun fitar higar da ta yiwa gidan nan ta yi alkawarin za.a san da tafiarta in dai mai daukan lokaci ce

Idannuwa Malan ya lumshe a hankali, wasu hawaye ne suka zubo daga gurbin idannuwansa, kafin ya budi baki a hankali ya ce" *Uwata*

Abdul ya kali malan, sai da ya ji tsigar jikinsa ta mike gaba daya, dan kuwa karara tsantsar tsabar soyayar Hafsat ne ta bayana a fuskar mahaifinta, ya bashi magana a baibai bai shaida masa ko da wa yake ba, dan kuwa duniya ce mai cike da girma da kuma fadi, tabas ana iya samun masu halayenta birjik, sai gashi daga jin yannayin, makamancin halayenta ya zubar da hawaye, tsabar ya yi missing din gudan jinninsa, hakan na nuni da du irin wahalar da ta gana masu suna kwana suna kuma tashi da ita a ransu a tare da su ko?

Ji ya yi ba zai iya boye masa kamar yanda ya zo da niya ba, ya zo ne da niyar saduwa da shi ya bashi labarin kansa ya kuma roki alfarmar a kama masa da adu.a a taya shi kan Allah ya bayana Hafsat dan kuwa idannuwansa sun rufe, ya kasa gannin komai, ya kasa fahimtar du wa.inda yake tare da su bare har ya ware daya ya bibiye shi, sai gashi datijon ya canza masa abinda ya yi niya

A hankali Abdul ya fuskance shi ya ce" a lokacin fa ta fita daga gidan nan, ta hadu da kadara wace ta yi sanadiyar zamanta a gidan yari na tsayin watani, kusan shekara,
Bayan wannan gwamnati ta dauketa ta horeta zama cikakiyar mai baiwa mutane tsaro wato Bodyguard, sai dai mutanen manyan mutane wasun bama a cikin kasar niger ba, ta haka na dauketa aiki, ita ce wace muka baiwa juna labarin juna

Malan ya miko hannunsa ya riko na Abdul, wanda hakan da ya yi ya saka Abdul bin hannayen nasu da kallo,
Malan ya ce" yaro, kana nufin...UWATA na raye a doron kasa? Uwata na tine da mu har tana faman zuwa garemu? Yaro kana nufin Uwata ta nutsu har tana yi mana adu.a? Yaro wai Uwata ce ta zama mai baiwa mutane tsaro? Yaro ita fa? Uwata mace ce, Uwata yarinya ce, ita ce ta yi kaso? Innalilahi wa.ina ilaihi raj.une,

Abdul ya jimke hannun Malan yana kallonsa sai dai bai ce da shi komai ba

Malan ya sauke ajiyar zuciya sai kuma ya saki wani murmushi ya ce" tun da na ga na kasa dangana cewa ta mutu na yi hakuri na bar tunaninta zuciyata ta aminta da tana raye,
Sai dai sake sake ba wanda ban yi ba, dan Uwata ta nuna cewa idan ta bale ba zat yi mana da dadi ba,

Abdul ya saki murmushin shima a hankali ya ce" bata jin magana

Malan ya kale shi da kyau ya ce" Uwata? Bata san mene jin magana ba, Alhamdulilah, Allah ya kara shiryar min da ita,

Abdul ya amsa da amen,

Malan ya ce" ka san meye? In sha Allahu zata fito, ba abinda adu.a ta bari, hakuri da adu.a su ne makamin bawa

Abdul ya gyada kansa har zuwa wannan lokacin hannunsa da na malan na cikin juna,

Malan ya kali hannayen shima sai kuma ya kara yin murmushi, wato da ka karanci datijon zaka gane yana cikin wani irin farin ciki dan kuwa sai sakin murmushi yake duda an bashi abin a dunkule an kuma bashi labarin tana wani hannun mai hatsari, aman da yake mutun be mai tawakali, sai ya saki du wata damuwa ya ringa barin zuciyarsa na turo masa da sakon murmushi yana karba yana yi yana karawa,

Malan ya ce" ka san da sai da na daurawa Uwata aure?

Abdul ya kafe malan da ido, dan kuwa ya san da maganar an daura mata aure, aman ce masa aka yi mijin ya saketa, kar dai malan ya fadi abinda ba haka ba, kai lale da ba.a kyauta ba, da aurenta tana irin aikin nan?

Muryar malan ce ta katse masa tunani inda ya ce" sai dai yarin ya ki yin hakuri, da yake Allah bai yi ba sai zigar mutane ta yi tasiri a kansa ya haye ya zauna ya mayar min da Uwa bazawara

Wani murmushi ne Abdul ya sake saki sai kuma ya yi gagawar rufe bakin nasa ya daina murmushin, aman a ransa hasasowa yake inama inama tana nan aka fadi maganar nan, yana kuma nan, da zai mike ne ya kali tsakiyar idonta ya ce da ita" *kauriyata, bazawara!*

Wata zuciyar ce ta ce da shi" kai Abdul, tana fa iya baka kunya ta ki tankaka, ta yi tafiarta abinta ta bara maka wajen,

Sai wata ta kuma fadin" kai ina, ba zata iya ba, sai ta tsaya ta kama tsatso ta ce" *kai=?D?, ni ce Bazawarar? Ka daina bana so Abdellah*


Haka Abdul ya roki Alfarma wajen malan cewa, ya rike bakinsa, dan kuwa yana son koda Allah ya yi an ganta a wanketa a wajen gwamnati na irin wahalar rayuwar da ta gani har ta rayu a *KUTKALE*

malan sai da ya zabura ya saki hannun Abdul ya ce" bawan Allah, *KUTKALE?* gidan kason nan da ake fadi a gari,? Gidan yarin da sai ka giga ake kai ka? Me Uwata ta yi da zafi haka ta shiga gidan yarin nan da ake fada a cikin gari? Wanda baki da yawa ke fadin irin hatsarinsa? Wani irin rike mutunci neza.a iya yi a wajen da ba mai hanawa ko mai sakawa? Mai karfi shi ke mulki, ga Uwata yarinya? Wace kake nufi a tsare mutuncin?


Abdul ya sauke ajiyar zuciya yana kallon yanda datijon ke jefo masa tambayoyi, a ransa ya ce" ku ji fa, shi da ya dace ya yi ta murna, aman da yake ya shafi Mamansa du ya rikice abinsa, dan Haka Abdul ya ce" ai ina ga a yi murna kawai tunda ta fito a raye,

Jikin malan kam ya yi kalau da shi, a haka har Mama ta zo da kulolin abincin da aka dafa dan kuwa sun tarbi Abdul yanda ya kamata ya fado ranar aikinta ne, ita da kanta ta yi girkin ta hada komai ta shigo da zumbulelen hijabinta wanda ya rufe mata kafafuwanta ba.a ganninsu ko kadan sai fuskarta da hannunta

Gaisawa suka yi da Abdul cikin mutunci kafin ta juya ta tafi bayan ta ajiye komai da komai bata tsaya zubawa ba dan kuwa malan da kansa yake zubawa baya so matansa su tsaya wajen da ya yi baki , sam baya son matansa su kasance a wajen da maza ke wajen, hankalinsa baya kwonciya da hakan....................................................................................
>د?=ؔ?>د?=?n? @&? *KUTKALE*=?n? @&?>د?=ؔ?>د?


*(PRISON)*

NA
*SAJIDA*

Marubuciyar

DUK KARYAR KADA

YAR MAHAUKACIYA

DAGA TAFIA DAUKAR SOJA

NEMAN NA KAINA

BANI DA ZABI

IDAN KA RAINA INDA KAKE

BAK'A CE

INA KUKE MASOYAN NOVELS DINA, GANI NA DAWO DA SABON SALO, SABUWAR TAFIA,
NA ZO MAKU DA SABON NVL DINA MAI TAKE *KUTKALE* WATO GIDAN PRISON,
WANNAN NVL ZAI ZO MAKU DA LAMURA DA YAWA, KU BIYO NI KU SHA LABARI........

*WANNAN NOVEL NA SIYARWA NE, DU MAI SO ZAI IYA TURA KUDINSA TA wannan acct NAIRA DARI BIYU : Usman Muhammad 3072998062 First bank. Sai ya turo shaidar ya biya ta wannan number +22791466605....sannan a yi adding dinsa cikin grup, MUTANENA NA NIGER KUWA SANADIYAR RASHIN SAMUN ORANGE MONEY DA KUKE YI, KUNA IYA TURO HOTON KATIN SAHELCOM KO NA AIRTEL TA NUMBER KAMAR HAKA 91466605 SAI A SAKA KU A GRUP DIN, .....* taku ce, Sajida=?
?=?
?=?
?=?
?




Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login