Showing 27001 words to 30000 words out of 261165 words

Chapter 10 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1101

ƴan gidan kallon ƙwallo ko ɓarayin agwagi, nidai sai faman jan addu'a nake saboda jin yanda zuciyata ke bugawa da sauri-sauri tamkar ko yaushe idan na samu kusanci da shi.
     Ganin bazai tankaba sai muka shiga gaisheshi ɗaya bayan ɗaya, hannu kawai yake ɗaga mana amma bai sake kallon kowaba baikuma amsa mana da bakiba. Yaja kujerar dake gaban tebir ɗin Uchie ya zauna, bamusan mi suke tattaunawaba har kusan tsawon mintuna sha biyar kafin ya miƙe ya fice. Yana fita muka shiga sauke a jiyar zuciya, yayinda wasu suka shiga gulmarsa musamman ma matan cikinmu, nidai sabon cingam na ɓare na jefa a baki na cigaba da sabgar gabana.

________________________________

               A gidan su Jawaad kam taron meeting Mom ta tara da ƴan uwanta, sunɗau tsahon lokaci suna tattaunawa akan Jawaad da maganarsa da Shahudah, duk da dai da farko Uncle Nasir yaso bijirewa, a cewarsa suma sunada ƴaƴan da zasu bama Jawaad ɗin ai ya aura. Shahudah ta kiya musu hankalin da bai kamata su sake sakata a sabgarsu ba.
       Kuka mama Atika ta fasa musu, tare da ɗakko musu maganar data saka suka nutsu waje guda.
        “Munsan Sabira tayi laifi da tafka kuskure a baya, amma kuyi haƙuri munada tabbacin zuwa yanzu ta magantu za'a samu gyara musamman idan mukai dubi da yanda take son yaron, amma ni na yarda da shawarar Nasiru, mu fara ma Jawaad maganar auren wata a cikin yaran gidannan, idan ya nuna rashin amincewa saimu tirsasashi ya maida Sabira ɗakinta, dan baikamata mu zubamasa ido yana yawo sakaka babu aureba, shekararsu kusan biyar kenan da rabuwa, amma yaƙi aure, inba neman matan banza yaron nan yakeba yaza'ai mutum mai lafiya kamarsa ace yanaƙin aure?, su waɗancan dangin uwar tasa sakarkaru da yake tsoronsa sukeji sun gaza masa magana kuma, tomu bai kamata mu saka masa idoba, dan kuwa mune duniya zata zaga basuba, amma yaya kuka gani? Danni dai shawarace na kawo matsayina na uwa a gareku, da Badiyya nada isashiyar lafiyama tare zamuyi muku, yanzu saiku zauna ku yanke shawara a tsakaninku” ta ƙare maganar da tashi ta fice daga falon.
     Duk binta sukai da kallo harta fita, Uncle Sulaimam ya sauke numfashi yana faɗin, “Nidai ƴan uwana na yarda da maganar mama, dan nidai zaman Jawaad bayamin daɗi a haka, da Abdul-aziz nada rai bazai zubama gudan jininsa ido kamar yanda mu muka kasa riƙe amana mukaiba, duk da bana zargin Jawaad da neman mata, dan mu shaidane akan tarbiyya da sanin yakamata na yaron nan”. Duk shiru sukai basu ce komaiba, wasu na hararsa ta gefen ido wasu na ƙunƙuni a cikin rai, dan suma sunsan ƴaƴan Mama Badiyya sam nasa tare da burinsu a gidan, su kaɗaine masu ƙaunar Jawaad dan ALLAH badan dukiyarsaba. Jin shirun yayi yawane ya saka Mom yin magana. “Nima na aminta da maganar mama, kuma ina goyon bayan ɗan uwana Sulaiman”.
         Daga maganar Mom sai kowama ya fara faɗar abinda ke ransa, daga ƙarshe dai suka ajiye shawara akan zama da Jawaad ɗin idan ya dawo aiki da wuri yau, kokuwa weekend idan ALLAH ya kaimu.

_________________________________

             A makare yau Jawaad ya tashi a wajen aiki, saboda fitar da sukai shi da Hafiz zuwa wani waje da yamma, basu dawoba sai bayan magriba, akwai abinda zai ɗauka a office shiyyasa suka dawo, amma da daga inda sukaje gida zai wuce. Bayan ya tattaro abinda zai ɗakko a office ɗin nasa sai yaga lokacin sallar isha'i ma yayi, dan haka suka tsaya sukai a station ɗin.
           Koda suka fito yunwar dake cin cikinsa yasa yace su tsaya wajen wani haɗaɗɗen gashin kaji, gimba ya amsa masa da girmamawa.  gimba ne ya fita domin

amsowa, kasancewar wajen ba baƙonsu bane akaima gimba tarba ta sanayya, kamar yanda Jawaad ya bashi umarni takeaway biyu akayi sai fura da yogurt masu sanyi aka saka ɗaɗɗaya a ciki, gimba ya bada kuɗin sannan ya dawo mota suka ƙarasa gida.
         Ganin da sauran mutane da keta shigi da fici a sassan gidan sai ya bashi mamaki, a ganinsa dai tunda anyi addu'an bakwai mikuma mutane keyi tunda ba taron biki bane. Saurin kauda abin yay a zuciyarsa dan a ganinsa hakan ba huruminsa bane, yaso shiga sashen Uncle Usman ya gaida Mama Zainab matarsa kamar yanda yakeyi kullum tunda akai rasuwar, sai dai a matuƙar gajiye yake, ga masifaffiyar yunwa dake cin hanjinsa.
         Tare suka shiga sashensa da gimba dake ɗauke da tarkacensa, bayan ya ajiye masa a falon ƙasa yay masa sallama ya fita, shima bai iya ƙarasawa bedroom ba ya yada zango a falo, sai da ya huta na wasu mintuna sannan ya miƙe ya haura sama, duk da yana buƙatar fara cin abinci haka ya daure, dan shi mutumne mai yawan cin abinci, idan bai samu bane dai yakanyi haƙuri kawai. Ɗakin barcinsa ya ƙarasa ya watsa ruwa, kusan ƙarfe tara ya fito tsaf dashi sai baza ƙamshi yake. Ya shiga kicin ya ɗakko kofi da filet, a falon ƙasa ya zauna ya kunna tv domin kallon labarai, yana kallonne yana cin abinci, lokaci-lokaci kuma yakan amsa waya idan an kirashi, ya daɗe zaune a falon har aka kammala labaran kafin ya miƙe yay ciki dan yana matuƙar buƙatar hutawa.

SHAHUDAH

      Saboda son haɗuwa da Jawaad yasa yau taƙi binsu Mom gida, a cewarta nan zata kwana, Mom bata hanata ba, suka tafi ita da Aamilah kawai saboda Salman ne yazo ɗaukarsu dama ba driver ba.
     Wajen ƙarfe goma ta kammala kwalliyarta, tai shiga cikin kayan barci masu taushi da ƙyau, dan sunyi masifar fidda mata surarta, sai ƙamshi take kamar jikar gidan mai turare, a ranta ta ƙudiri aniyar maido hankalin mijinta kanta yau, dan ta gaji da wannan wasan ɓuyan da sukeyi, ta kuma shirya karɓar cikin da yake buƙata. (Karku manta Shahudah batasan Jawaad ya saketa ba fa😥🤦🏻, ɓoye mata shine kuskuren dasu mom suka tafka).
     Hijjab ɗin mama Atika da ya kai mata har ƙasa ta ɗauka ta saka, babu kowa a sashen na mama Atika, itama tayi barci ma tun ɗazun, kai tsaye Shahudah ta nufi sashen Jawaad tanata zuba murmushi, dan ita kaɗai tasan abubuwan data shirya masa, yau ɗinan basai gobeba sai ta zautar da gayen nan, ta sake sakin tattausan murmushi lokacin data murɗa ƙofar taji ta buɗe. Jawaad ya manta shaf bai rufeba ya haye sama, sai da ta gama ƙarema falon kallo, komai tsaf tamkar ba namiji ke zauneba, tasan Jawaad yanada tsafta, sam bayason ƙazanta, duk jin kan nan nasa baya ƙyashin tashi yay shara yay morping wa sashen,, ya samu wannan horonne a zamansa da kakarsa Mama maryam, hatta da girki Jawaad ya iya, kawai rashin isashen lokacin kai ne ke hanashi yi. batasan miyasa bayason masu hidimaba. Ta sake sakin murmushi kafin ta fara taka steps ɗin a hankali tana wani yauƙi saikace tarwaɗa, a falo ta cire hijjab ɗin ta jefa saman kujera, ta kuma gyara rigarta da gashinta sannan ta nufi hanyar ɗakinsa.

       Jawaad kam a gajiye yake matuƙa. hakan yasa yana shigowa bayan yay brush da alwala yay adduar barci ya kwanta, bai wani jima da kwanciyaba barci yay gaba dashi, fitilar gefen gado ce kawai a kunne, itama ta ɓangare ɗaya, hakan yasa ɗakin yay dim babu haske sosai, bai kumayi dunɗum ba. Shahudah data murɗa ƙofar ta shigo a hankali ta sauke ajiyar zuciya tana mai shaƙar ƙamshin da ɗakin keyi, komai na Bb'n ta daban yake dana kowa, bata ganin fuskarsa, dan ya juya ma ƙofar bayane, sannan ya lulluɓa da bargo saboda uban AC'n daya ƙure ɗakin da shi, ‘ko tsoron murama bayayi’ ta faɗa tana ɗaukar remote ɗin acn ta rage ƙarfinsa.
       Jawaad da baisanma hidimar da akeba barcinsa yake hankali kwance da mafarki mai daɗi, hakan yasa yaketa faman sauke numfashi a hankali. Ya sauke ajiyar zuciya lokacin da Shahudah ta hawo gadon a hankali ta kwanto bayansa bayan ta ɗaga bargon ta shiga, itama ajiyar zuciyar ta sauke ƙwallan kewarsa na taruwar mata a idanu, jitake tamkar ta haɗiyesa ta hutama kawai. Cikin salon data shirya masa a wa

nnan dare ta fara yawo da hannunta a jikinsa, Jawaad dai bai motsaba, amma da alama jikinsa na karɓar saƙwannin Shahudah kamar yanda tai fata. Mafarkin da Jay keyi da saɓanin Shahudah yay dai-dai da abinda take masa a zahiri, hakanne yasa ta samu haɗin kan gangar jikinsa har takai ya gyara kwanciyarsa yana sake rungumeta, hakan yayma Huda daɗi kuwa, ta ƙara ƙaimi kan abinda takeyi, kamar wasa saiga tafiya tayi nisa a tsakaninsu, dan tuni ya fara maida mata murtanin sumbatarsa da takeyi.
          Yanda take sauke numfashi ne da sauri-sauri akan fuskarsa ya sakashi farkawa, dan kuwa tabbas wannan al'amarin ya wuce a mafarki kawai, a matuƙar razane ya hankaɗeta daga jikinsa yana ambaton “Innalillahi wa-inna ilaihirraji'un. Wace ƴar iska ce haka ta shigomin ɗaki?”. Yay maganar yana ƙoƙarin kunna fitilar ɗakin.
       Shahudah daya jefar gefe duk da taji zafi tai ƙoƙarin tashi zaune tana sauke numfashi a gwame, hasken daya gauraye ɗakin ne ya basu damar ganin juna. Kansa ya dafe yana ƙara ambaton “Innalillahi....” Shahudah ta matso jikinsa tana neman kwantawa a kafaɗarsa ya sake tureta a fusace, “Wai ke wane irin dabbanci ne wannan? shin baki da hankaline Hudah?”. Tabbas maganganunsa sun mata zafi, amma saita daure cikin dakewa da tsiwarta tace, “Dan nazo wajen mijina zakacemin banda hankali?, to ka ɗauka ni da kai duk mun zama mahaukatan”.
      Karon farko Jawaad ya waro idanu waje, yace, “Miji!?, Hudah rashin ilimin addinin naki harya ƙara faɗaɗa haka? Kinga bani da lokacin wannan haukar tashi ki fitarmin daga sashe kafin na saɓa miki kamanni, kuma wlhy wannan yazama na farko na ƙarshe da zaki sake shigomin nan”.
       Kuka Shahudah ta saki, ta nuna kanta tana faɗin, “Yanzu nan tsanar da kaimin bb har ta kai haka? To wlhy babu inda zanje, dan inada haƙƙi a kanka ai, duk ma abinda zakayi sai kaitayi, amma ka sani niba ƴar iska bace, amma wlhy da tuni naje na nema wani namijin a waj.......”
      Mari ya kai mata tai saurin kaucewa, cikin daka tsawa yace, “Tashi ki fita a ɗakinan kafin na raba kanki da wuyanki wawuya kawai!!”. Saurin sauka tay a gadon, dan yanda ya harzuƙo ɗinan zai iya maketa, batasan ma bashi da wannan ƙarfinba a yanzu, dan ta sakashi a kwale-kwale. Da ƙyar Jawaad ya iya sakkowa a gadon saboda tashin hankalin da Shahudah ta sakashi, duk ƙoƙarin kame kansa da dauriyar da yakeyi yau ta kwanto masa liƙi, ya murzama ƙofar key ya dawo saman gadon jiki babu ƙwari. Gaba ɗaya kansa ya toshe, yama gaza yin tunani akan Shahudah.
       Duk yanda Jawaad yaso yayi barci a wannan daren ya kasa, gashi maganin da yake sha ya barsa a office saboda ya ƙare ya sayosu jiya, sai kuma ya manta bai ɗakkoba, ya watsama jikinsa ruwan sanyi yafi sau shidda kafin asuba, sosai mararsa ke masa masifar ciwo, ko sallar asuba bai fitaba a ɗaki yayi, sai bayan ya idarne barci ɓarawo ya sacesa, shima a matuƙar wahale yayisa.
       
         Shahudah kuwa da kuka rurus tabar sashen zuwa sashen mama Atika, a falo ta zube tacigaba da kukanta har barci ɓarawo ya saceta.
  

_______________________________

                       Yau ma har muka fito Office banga kowa a cikin ƴan gidanba, cikin nishaɗi muke ƴar firarmu da Yah Qaseem har muka iso, saida na rakashi har office da tarkacensa sannan na fito nima zuwa namu.
       Ummie bata isoba, hakan yasa na zauna bayan mun gaisa da waɗanda na tarar, ƴan abubuwan da baza'a rasaba na shiga yi, gefe ɗaya kuma ina amsa hirarsu Dawood sama-sama akan aiki, a hankali mukaita ƙaruwa har kowa ya gama isowa, Ummie ta zauna saman tebirina tana faɗin, “Bily gulma da ɗumi-ɗuminta fa”.
         Kallonta nai ina faɗin, “Ƴar sa ido mikika samo mana?”. Ƙaramar dariya tayi da sauke murya ƙasa tace, “Ankawo kuɗin Nazifa”. “Dan ALLAH da gaske?” nai maganar cikin waro ido waje bakina washe da fara'a. Ummie tace, “Wlhy da gaske nake, kema tace ta kiraki bai shigaba, amma ta tura miki saƙo ai”. Wayata na ɗauka ina faɗin, “Kashewa nai da zan kwanta, tunda na tashi kuma ban buɗe data ba, oh ni su Nazifa an mana wayo, da Al-mustaphan dai?”. “Shi kuwa” cewar Ummie tana dariya.
       Fita mukai zuwa can baya nai

kiran Nazifa a waya, bugu biyu ta ɗauka tana faɗin, “Inba gulmaba Bily miye na kirana da farar safiyarnan?”. Dariya mukai ni da Ummie, nace, “Ai gara dai muci gulmar da ɗuminta basai ta huceba, yarinyarnan da gaske dai kin dage aure kikeso?”. “Ban isa bane?” Nazifa ta faɗa tana dariya. “Kin isa kuwa tsaf” Ummie ta bata amsa. Haka muka cigaba da hira cikin so da ƙaunar juna har bamusan lokaci yaja ba.
           Daƙyar muka iya katse hirar muka koma office gudun kar'a nememu.

JAWAAD

     Kamar da wasa ƙaramar magana ta zama babba, dan kuwa dai daga kwanciyar da Jawaad yay bayan sallar asuba sai zazzaɓi mai azabar zafi ya rufesa, duk yanda yaso ƙoƙarin tashi yay shirin office lamarin ya gagara. Wani wahalallen barcin nema ya sake awan gaba dashi bayan ya koma saman gado yaja bargo.

       Gimba yay shiri da wuri kamar yanda yasan suna sammakon fita, sai dai yafi tsayuwar awa guda wajensu baba maigadi babu alamar boss ɗin nashi, dama kuma bai gansa a massallaci ba yau da asuba. Bai dai tambayi kowaba ya cigaba da jira har zuwa ƙarfe tara, zuwa lokacin dai kam abin ya fara bashi mamaki, abinda zai riƙe boss har ƙarfe tara bai fita office ba to lallai dole ya saka kokwanto a zuciyar duk wanda yake tare da shi, wayarsa yay kira har sau uku ba'a amsaba, ya sake daurewa dai ya zauna awa ɗaya ta kuma shuɗewa goma tayi. Yanzu kam tilas ya miƙe ya nufi sashen, yay knocking har kusan sau goma baiji motsin kowaba, hakan yasashi murɗa ƙofar, cikin sa'a kuwa ta buɗe, sai dai koda ya shiga babu kowa a falon, babuma alamar wani ya fito cikinsa. Nan kawai yake da hurumin shiga dan haka bai ƙara gaba ba ya juya ya fita. Yabar wayarsa a mota har baisan su Oga Aliyu nata kiransaba suma jin Boss baizo office ba, sun kuma kira wayoyinsa duka babu wacce ya ɗaga, shine suke kiran Gimban suji ko wani waje sukaje? Amma shima kuma bai amsa musu ba.
           Misalin sha ɗaya da wasu mintuna sai ga Nabeelah da Ummansu sunzo gidan domin sake yima mama Zainab gaisuwa, dan rabonsu da gidan tun ranar rasuwar. Bayan sun shiga sashen mama zainab sun fito sai suka shiga wajen mama Badiyya don su gaisheta da jiki, basu jimaba suka fito zuwa sashen mama Atika, ananne suka iske Shahudah babu lafiya, tana kwance cikin doguwar kujera lulluɓe da bargo, sun mata addu'ar samun lafiya suka miƙe zasu tafi amma sai mama Atika ta tsaidasu da zancen auren Jawaad, murmushi Ummah tayi kawai, tabama mama Atika haƙuri akan zasu masa magana, baki kawai mama Atika ta taɓe, su Umma kuma suka fito abinsu Nabeelah nata ƙunƙuni akan ansama yayansu ido. Basuyi zaton samun Jawaad a gidaba, dan haka sukai yunƙurin barin gidan, Gimba daketa dakon jiran fitowarsu yay azamar isowa garesu yana gaida Umma, da mamaki ta amsa masa, “A'a gimba baku fita office bane ko dawowa kayi kai?”.
       “Wlhy mama bamu fitaba, har yanzu boss bai fitoba, bansan ko lafiya ba? Nai knocking na kirashi amma duk babu wani amsa”.
     Shiru Ummah tayi na wasu sakanni, sai kuma ta fasa shiga motar ta nufi sashen Jay, Nabeelah ma data tuƙosu harta shiga mota ta kunna ta kashe ta fito tabi bayan Ummah.

________________________________

             kasancewar  juma'a ce yau ɗin bayan an sakko salla mun fito zamu fita neman abinci saboda yunwar da nakeji mukaci karo da Oga Jabeer zai shiga mota, har mun gaishesa munwuce sai kuma yay kirana. Dawowa nai ina amsa masa da girmamawa, yace, “Shigo mota ki rakani wani waje”.
     Duk da banso ba sai ban masa musuba na shiga Ummie kuma ta wuce tana min dariyar mugunta............✍


“Saura muji wani yace Hudah🙄 ehe😏.


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
    
[11/30/2020, 12:59 PM] HASNA✍🏻: Bilyn Abdull 📚:
Page 11

         ...............Tafiyar da batafi mintina talatin ba muka iso inda ya bani mamaki, bandai cema oga Jabeer komaiba har aka buɗe mana gate muka shiga. A dai-dai sashen da mukai salla ranar rasuwar Uncle Usman yay fakin, ya kashe motar yana faɗin, “Muje ko”.
          Bance komaiba na buɗe murfin na fita kamar yanda shima yayi, yana gaba ina biye da shi har zuwa ƙofar falon, sai kalle-kalle nake ina ƙara jinjina girman wannan gida, koba'a faɗaba kasan an narkar da dukiya wajen ginashi, Oga jabeer ne yay knocking, babu jimawa akazo aka buɗe ƙofar.
         Cikin murmushi Nabeelah data buɗe ƙofar tace, “Yah Jabeer sannu da zuwa”. “Yauwa Nabeelah” ya amsa yana mata murmushi shima. Sai da ya shige sannan ta ganni, cike da mamaki ta waro idanu alamar ganina a bazata da tai,  kafin ta daka tsalle ta ɗaneni tana dariya, “Lah ƙawata dama rai kanga rai?”. Murmushi nayi ina mai jinjina wautar Nabeelah a raina, cikin surutunta tace, “Dama kinsan Yah Jabeer?”. Amsa na bata da cewar, “Eh, wajen aikinmu ɗaya”. Zata sake jehomin wata tambayar Jabeer ya katseta, “To Akku mai bakin magana kaimu ɗakin da yake”.
          Yanda tayi da fuskane ya sakani yin murmushi, ita a dole taji haushin ance mata Akku, hannuna ta kama tana tuttura baki gaba tai mana jagora har sama, bansan minene ya kawomuba balle tunanin wajen wa mukazo, ni dai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login