Showing 258001 words to 261000 words out of 261165 words

Chapter 87 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1149

ya ɗauki tsahon shekaru yanayi da ita. Fuskarta fayau tamkar a yaune ALLAH ya ɗauki ranta. Bilkisu ta rungume gawar tana kuka abin tausayi. Da ƙyar Jawaad ya ɗagata akan gawar shima yana nasa hawayen da baisan suna zirarowaba. Alhaji babba kam yayi dauriya matuƙa, sai dai haɗiyar zuciya kawai yakeyi da kukan zuci. Umm-Anum tai mata wanka aka suturtata. Ɗunbin al'umma daga ɓangarori da dama suka sake sallatar gawar Rahama a karo na biyu, ta kuma samu rakkiyar ɗunbin jama'a zuwa makwancinta na gaskiya.
       An samo zunzurutun kuɗaɗe da kayan tsafi kala-kala da wasu abubuwan a gidan Dad, hakama Uncle Nasir da sauran abokan sheɗancinsu irinsu Kokino. Kamfanoninsu ma an samo abubuwa masu yawan gaske masu matuƙar tada hankali, ciki harda kayan shaye-shaye kala-kala da tabar wuwu buhu-buhu da adadinsa ya tasarma dubu goma. Sai wasu gurɓatattun abubuwan da bama zasu lissafuba gamai sauraro.
     Ƙasa tayi tsitt, manyan dake huɗar kasuwanci dasu data abokantaka sun fito sunata ALLAH wadai da nisanta kansu da ɓoyayyun ayyukan su Dad ɗin, komai dai ya fito fili, anyi walƙiya ijiya taga kowa da komai. Inda aka bar iyalansu da waɗanda aka zalunta irinsu Jay da jiyyar zukata.
     Idan kaga Bilkisu a irin wannan lokacin dole ka tausaya mata, ga laulayin ciki ga tashin hankali da damuwa, sauƙintama ƴan uwanta da mijinta kowa tattalinta yake da burin ganin farin cikinta. Takanyi kukan jin daɗi da ganin ƴan uwanta zagaye da ita, waɗanda ada ta rasa samu.

★★★★★★

         Ɓangaren Shahudah kam ba'a cewa komai, ita babban kukanta da tashin hankali bawai ya ta'allaƙa da halin da Dad yake ciki na halin rayuwa da mutuwa bane, babban tashin hankalinta shine ance babu aure tsakaninta da Jay sai dai idan sakin Bilkisu yayi kota mutu, amma bazai yuwu suyi zaman aure a ƙarƙashin miji guda ba ita da ƴar uwarta da suke Uban ɗaya.
      Hakan ba ƙaramin tada hankalinta yayiba, babu kunya babu tsoron ALLAH ta dinga tsinema Dad da jera masa ALLAH ya isa cikin hausarta da koma fitar kirki batayi. Ƙiri-ƙiri ta nema haukata kanta. Mom ta rasa inda zata saka kanta taji daɗi itama, da abinda ya dameta zataji kokuwa da haukar Shahudah, ko ciwon mama atika, ko kuma nisantarsu da Qaseem yayi?. Dan tun bayan lafawar komai Qaseem ya ajiye aiki yabar ƙasar gaba ɗaya batare da kowa ya saniba sai daga baya sukeji ta hanyar saƙon daya bar musu.

       A yanzu kam kowa burinsa Jawaad da mahaifiyarsa da ɗan uwansa su yafe musu a wannan family, musamman ma waɗanda sukasan sun muzguna masa bisa jagorancin makircin mama Atika da ƴaƴanta.
             Dan samun lafiyar Mama Badiyya ta sake bayyana abinda ta gani Uncle Nasir nayi a wani dare bayan ɗakunansu shinefa ya banka mata baƙin asiri itama ya tauye rayuwarta ta koma ita ba'a duniyaba ba kuma a lahira ba😪.
      Jay dai bai samu zaman sauraren kowaba, dan shi a yanzu ta matarsa ma yakeyi da fatan samun nutsuwarta da abinda ke cikinta.

★★★★★

          A kwanakin da aka cika kwana goma da sakama su Dad wuta shima ya mutu da safe yana ihu da kururuwa kamar yanda su Uncle Nasir sukayi lokacin da suma zasu mutu, ga wani irin kakari maiban tashin hankali, jikinsa kuma ya koma fari fat tamkar babu jini a jiki, gashi dama wuta ta gama ɗaye fatar gaba ɗaya. Da yamma Alhaji Kokino yabi bayansa da Abban Zuhrah, kamar yanda aka binne su Uncle Nasir babu wanka saboda ƙunar jikinsu haka shima Dad dasu Abban Zuhrah aka haɗasu akai musu salla aka biznesu da halinsu. Wata shari'ar dai kam lallai tafi ƙarfin alƙalan duniya, sai dai a jiraceta daga sarkin alƙalai kuma😭🙏🏻.

     Haka rayuwa take su Dad sun tafi tamkar ba'ayusuba a duniyar dagasu har ayyukan da suka shuka, a hankali hankulan jama'a sun fara dawowa jikinsu daga abinda ya faru, sai kuma labarai da maida yanda akayi da har yanzun sun gaza ƙarewa. Yayinda akebin gidajen da suka bari ɗaya bayan ɗaya ana rushewa, wanda suke ciki kuwa ana barinma iyalansu dan su sami matsugunnin rufama kansu asiri. Masu ƙarfin imani a cikinsu kuwa sun tsame kansu daga komai na dukiyar acewarsu basa buƙata
[2/17, 3:01 AM] +234 703 966 0069: , dan dukiyace ta tsafi, sun gwammaci su ƙare rayuwarsu a talauci da su zauna a ƙarƙashin ikon dukiyar jinin al'umma.

BAYAN WATANNI BIYAR.

        Abubuwa sun sake lafawa, harma wasu da yawa sun faffaru, ciki kuwa harda komawar Umm-Anum Saudia tare da ƴan uwanta suka sauke faralin miƙama ALLAH godiya daya kawo musu ƙarshen komai cikin rahamarsa da hikimarsa. Bayan kammala aikin hajji su suka dawo ita kuma aka barta a can tare da mijinta da Anum, Anuwar dai kam yayi uwa yayi maɗaukiya a ƙasarsa ta haihuwa, harma an ware masa ɗaki guda a gidan Jawaad yana zaune tare dasu.

         Ansha bikin Nazifa da Ummie, harma da Zuhrah da wani ɗan uwansu da yake bala'in sonta dama abbanta ya ƙi bashi, yanzu bayan lafawar komai ya dawo, acewarsa ai ita yakeso, kuma ba ita ta aikata abinda ya faruba babantane, a yanzukam bashi a duniya, dukiyar daya barima sun ajiyeta ita da mahaifiyarta da ƴan uwanta.

      An kumasha bikin Amina da Yah Qaseem wanda Jawaad yaje yayo biko har ƙasar da yake, tare da zaunar dashi yay masa nasiha mai ratsa jiki, tare da bashi shawarar ya tallafi ƴan uwansa a yanzu da mahaifiyarsu dan shine uba, ya kuma nema musu malamin addini su koma islamiyya musamman ma Shahudah da har yanzu hankalinta bai gama kwanciyaba dan tana masifar son Jay. Lokacin da taga cikin Bilkisu da yanda Jawaad ke riritata ita da cikin ba ƙaramin shiga ruɗani ta sakeyiba, tasha kuka ranar harda shiɗewa kuwa.

     Batool ma ansha bikinta da Dr Bello daya dage akan shifa da gaske yanaso babu wasa. Ganin tsakani da ALLAH yake sonta ta bashi dama ya kawo kuɗi aka gwangwaje.

         Alhaji babba ma bisa takurawar Jay suka ɗaura masa aure da Maman su Amina, da da Maman yara za'a haɗa masa ita ta roƙa arziƙi akan a barta dan ba isashshiyar lafiyace da itaba har lokacin, tana dai lallaɓawane bisa taimakon da kulawar da Jawaad ke bata.

        Ƙungiyar su Bilkisu nata ƙara haɓaka da faɗaɗa akan daƙile fyaɗe da hukunta duk waɗanda aka samu akan laifin. hukunci kuma mai tsananin gaske. Inda manyan mutane da shugabanni suma suka ƙara basu goyon baya domin fata da samun damar daƙile matsalar kodan addabar da taima al'umma.

        Mama Atika bayan wahalar jinya da tasha na kusan wata huɗu itama ALLAH yay mata rasuwa, su Mom da su Shahudah ansha kuka. Komai nasu sai ya daɗa yin sanyi kuma, musamman ma ita da duk ƙwalisarnan yanzu babu ita, babu Dad babu dukiyar da ake taƙama da ita.

             A ɓangaren rose kam ta buga ta buga taga babu ci, mai shiga tsakanin soyayyar Jawaad da Bilkisu sai dai ALLAH. Babu kalar ƙulle-ƙulle da munafurcin da bataima bily ba a station ɗin sai dai babu tasiri, daga ƙarshema da Jawaad ya ganota sai yasa akai mata transfer waje mai nisa a tsakaninsu. Wannan abu ya sakata jin takaici harda kukanta kuwa, ballema randa taji anƙarama su bily girma da ƙyaututtuka susucewa tayi duk da itama harda ita, a ganinta bily batakai ta kamotaba, amma ya ta iya da abinda yafi ƙarfin wuta inji kishiyar ƙonanniya. tana kewar jawaad ainun. dan koba komai idan tana ganinsa kusa da ita tana ɗanjin sassauci.

______________
ZAFAFA 2021
___________

             Masoya naku taurarinfa sun sake dawowa da sabon salo a 2021.

       Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
  
          Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗

        Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗

        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗

         Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋

    Duka akan farashi mai rahusar gaske.

Kamar haka👇🏻💃🏻

Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700

Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇

ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.

saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇

0903 234 5899

IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇

  09033181070

Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO

TEAM#ZAFAFABIYAR🔥

★★★★

     A gidan Iyayen gayya kuwa ai ba'a cewa komai, cikin Bilkisu da har yanzu gata nanneda
[2/17, 3:01 AM] +234 703 966 0069: ya fito sosai, dan yana cikin wata na bakwai. Tattali sosai take samu a wajan Jawaad da duk ahalinsuma baki ɗaya, inda aka maido mata Nabeelah gidan tana tayata zama, gefe kuma tana shan soyayyarta da masoyinta Anuwar.
          Faruwar wannan al'amari ya sake maida bily miskilar gaske, dan ko Jawaad ɗin idan bata gadamaba saita yini batai masa maganar data zarta gomaba. Ta ƙara ƙwazo akan aikinta fiye da zaton mai hasashe, musamman ma da bayan lafawar abubuwa suka samu ƙarin girma itada duk jami'an da sukaje wannan aiki a waccan rana. Saboda cikinta dai bata fita operation, sai dai tayi ayyukan cikin gida kawai daga office. A gefe kuma tana sake samun ƙwazo da horo a wajen mijinta, wanda a kullum cikin sake nuna mata ƙauna da soyayya mai tsanani yake. Sam baison yaga tashin hankalinta ko damuwarta balle fushinta. Shidai fatansa ALLAH ya sauketa lafiya ta haifo masa little Beejay kamar yanda yake faɗa a kullum.

          Cikin Bilkisu nada watanni taƙwas Jawaad ya sakata ɗaukar hutun dole, acewarsa saita haihu ƴarsa tayi ƙwari sanan. Aranar da hakan ta faru harda kukanta, amma sai yaƙi kulatama yay kamar bai jitaba, sai Anuwar dake mata dariya shi da Nabeelah suka koma lallashinta da lallaɓata.
        Tana shiga watan haihuwa Ummah babba tace zata maidata can gidanta, dan bazai yuwu a barta ta zauna nan babu babba tare da ita ba. Babu kunya Jawaad ya murje idanu yace shifa bai yardaba, idan dan babbane ya amince asamo wata tsohuwar ta zauna da ita, amma shi bai yarda matarsa tai nesa da shiba gaskiya.
     Ranar Bily ta tasashi gaba ta dinga kwasar dariyar mugunta, dan kawai ta rama abinda yay mata na sakata ɗaukar hutu a office saita shiya kaya kusan akwai huɗu na tafiya gidan Ummah babba, aiko ya murje ido ya balbaleta da masifa kamar zai cinyeta ɗanya jagab🤣.
      Aifa ganin yanda ya harzuƙa dole Ummah babba ta janye ƙudirinta, aka samo wata dattijuwa zata zauna dasu, ga kuma Nabeelah da Anuwar tare dasu. Ummah ƙarama da babba kusan kullum saisunje ganinta. Hakama maman Amina, dan cikin na shiga wata tara sai ya ƙara girma kamar wadda zata haifa ƴan biyu.

 
       ★★★★★★

A wannan ɗan tsakanin akasha bikin su Amaturrahman suma, inda Bilkisu ko sau ɗaya bata samu leƙawaba saboda cikinta, Jay yace idan ta haihu taje taima Ummu ALLAH ya sanya alkairi.
        Bayan anyi biki an shashshare Umm-Anum da itama ta halarta da Aunty Mahfuzah sukazo nan dansu gaisa da Alhaji babba. Randa suka cika kwana uku gidan Alhaji babban sai sukazo nan gidan Jay duba bily, danshi kullum yana zuwa can ya gaidasu, itako saita waya tunda bata fita sam.
        Ta taresu da tsantsar farin ciki, inda sukuma suketajin tausayinta da mata fatan sauka lafiya. Su Anuwar ne dai ke amsawa, itako kanta na a ƙasa dan kunya.
     Anuwar ya kumbura fuska yana kallon Umm-Anum daketa mammatsa ma bily hannunta daya kumbura. “Umm-Anum gaskiya nimafa amin aure, so kuke sai little tazo duniya taga Abbanta tuzuru”.
       Dariya duk suka sanya ƴan falon, banda Jay dake zaune gefen Umm-Anum yana latsa waya, yadai ɗan ɗago ya kalli Anuwar ɗin ya zuba masa harara ya ɗauke kansa. Sai da suka gama dariyarsu sannan ya sake kallonsa fuska babu wasa. “Kai baka da kunya ko......?” “A'a yayanmu nifa wlhy gaskiya na faɗa, yanzu dan ALLAH little zataji daɗine idan aka haifota ta iskeni babu aure, ita dai ai nasan tanason iske kawunta a dattijonsa ko”. Kai kawai Jay ya girgiza ya sake ɗauke kansa, dan indai shaƙiyancine akazo wajen Anuwar kowa ya shafama kansa lafiya, duk masifarsa kuresa yake shima har yagaza cewa komai.
     Umm-Anum da itama ke dariya yanzun tace, “To ni miye nawa, aiga mai maka auren nan a gabanka” tai maganar tana nuna Jay. Tasowa yay ya tsuguna a gaban Jay ɗin yana wani marairaice fuska. “Yayanmu dan ALLAH ka aurar dani kar a haifi little ina a ƙasa” yay maganar cikin harshen nasara da haɗawa da ƴar hausar daya fara kowa wajen Nabeelah”. Kunnensa Jay ya kama ya murɗa da ƙarfi, aiko a take yahau roƙo daban haƙuri. su Bily kuma namasa dariya.
     Cak ta tsaya daga dariyar tata jin bayanta ya riƙe, ta shiga yamutsa fuska tanason fiskewa amma haka
[2/17, 3:01 AM] +234 703 966 0069: sa. Kallon juna muke cike da shauƙi babu mai ko ƙiftawa, sai da naji bakinsa cikin nawa na dawo hayyacina da sauke nannauyar ajiyar zuciya, son tureaa nake amma yaƙi bada damar hakan, na rinƙa dukan bayansa amma bai barniba saida yayi san ransa sannan ya sakeni ya miƙe yana dariya damin gwalo. “Dama abinda ya kawoka kenan ai” na faɗa iana ɓata fuska kamar zanyi kuka. Gwalo yaymin dai-dai zai fita yace, “Eh naji ɗin”. 
       Fariya sosai nayi ina girgiza kai, na jawo ɗiyata na rungume ina sumbatarta dajin kamar na haɗiyeta na huta dan ɗunbin son da nake mata.

BAYAN WASU SHEKARU.

              Yarane kusan uku keta wasan basket ball a madaidaicin filin wasa dake a cikin wani ƙaton gida mai ɓangarori kusan huɗu. ina tsaye a wajen kusan mintuna huɗu saiga mata da miji sun fito daga ɗayan ɓangare na gidan, ba kowa bane face Anuwar da Nabeelah, suma suna sanye ga j.c. ihu yaran suka fara, biyu na kiran Abbah! Abbah! Abbah. Biyu na kiran Mamma! Mamma! Mamma!! Cikin ɗaga hannu irin na jinjina da ɗokin isowar abokin wasa. Anuwar yaja ƴan team ɗinsa, Little Bee, da ƙaninta na biyu Abdul-aziz suna kiransa (Awwab). Nabeelah kuma taja nata ƴan team, ƙanwar Little bee mai bimata Maryam suna kiranta (Khairiyya) sai yaron su Anuwar ɗin mai sunan Jawaad, suna kiransa (Khalifa). Wasansu suka fara cike da nishaɗi, basufi mintuna talatin da farawarba sukaji horn. Maigadi dake kallonsu daga gate yay saurin zuwa ya buɗe. Farar mota tas ta shigo gidan wadda Bily ke mazaunin driver cikin kayan aiki, Jay na gefenta shima sanye da suit yanata faman danne-danne a laptop.
      Da gudu yaran suka nufi motar suna faɗin, Abie! Miemaa! oyoyo. Bily dake murmushi ta kalli Jay shima ya kalleta, kafin su maida idanunsu ga yaran nasu dake tunkarosu. Awwab da Khairiyya suka nufi sashen da bily take suka buɗe mata, Little Bee da Khalifa kuma Jay suka buɗemawa. A tare suka fito fuskarsu ɗauke da murmushi. Jay ya ɗaga khalifa tare da sumbatar kumatumsa, shima yaron ya sumbaci Jay ɗin yana dariya da faɗin, “Abie i love you”. “I love you too second Jawaad” ya faɗa yana lakace masa hanci, kafin ya duƙa ya sumbaci Little bee ƴar kimanin shekaru goma itama. “Little BeeJay ɗina”. Fuskarta washe da murmushi sak irin na Bily tace, “Sweet Abie na i love you” tai maganar da sumbatar hannunsa itama. Ta matsa jikinsa ya rungumeta ta gefen hannun damarsa, na haggun kuma yana ɗauke da khalifa.
     Acanma dai Awwab da khairiyya suna maƙale da Bily, saida suka gama ɗokin ganinta sannan suka dawo wajen Abie, ya sumbacesu suma a kumatu kamar yanda yayma su Khalifa. Kafin su Anuwar su ƙaraso suna musu barka da dawowa.
     Cikin tsokana bily tace, “Iyayen da basa girma da shiriritar ƴaƴansu”. Dariya Anuwar da Nabeelah sukayi, Jay dake murmushi shima yace, “Karki ja mana yanda muka dawo a gajiyanen yanzu su tara mana ciwon kai suda ƴaƴansu, zomu gudu muje mu hutama ranmu princess”. Cikin dariya Anuwar yace, “Idanma kun gudu binku zamuyi, dan yau a falonka aka haɗa dinner. Idanu Jay ya zaro sosai. sai kuma ya ɓata fuska yana kallon Bily cike da langaɓe kai. “Miemaa kinajifa, nidai ALLAH ban yardaba hutawa zanyi”. Kafin bily ta bada amsa yaran suka shiga ihu da tsalle suna faɗin suma basu yardaba a falon Abie zasuyi dinner yau”.
       Ƙwafa Jay yay yana kallon Nabeelah, “Auta kece kika haɗamin wannan aikin ko, maganar gaskiya ayi hutu na tarkataku ku tafi Saudia wajen Ummuna muma muɗan huce gajiya da matata a gidanga. A waje dambe da ɓarayi a gida dambe da iyayen yara da yaransu”.
    Sosai Nabeelah da Anuwar ke dariya, Nabeelah tace, “ALLAH babu ruwana, Abban Little ne”. “Kai ko?”. Jay ya faɗa yana kama kunnensa. “ALLAH da zafi Yayanmu” Anuwar ya faɗa cikin marairaicewa yana riƙe hannun Jay. Yaran suma duk sai suka marairaice suna faɗin, “Sorry Abie Abbanmu yanajin zafi sosai”.
     Dariya Bily takeyi. Jay dake murmushi ma ya saki kunnen Anuwar ya kama hannun matarsa suka shige dan anfara kiran sallar magrba. Kayansu yaran suka kwasa daga mota tare da tsarabar da aka yo musu sukabi bayansu. Anuwar da Nabeelah ma suka nufi ɓangarensu dansu watsa ruwa  tu fito.✍😭🙏🏻

ALHAMDU
[2/17, 3:02 AM] +234 703 966 0069: LILLAHI ALA KULLI HALIN.

Na godema UBANGIJIN al'arshi daya bani ikon kammala wannan littafi daya jani dogon zango, kuskure. dana tafka a cikinsa ALLAH ka yafeni, abinda nayi dai-dai ALLAH ya haɗamu a ladan daku masoya da mukai tafiyar tare.

Nagode, nagode, nagode irin trillions trillions trillions ɗinan da haɗin kai da ɗunbin soyayyar da kuka nunamin akan wannan littafi. Alkairin ALLAH da rahamarsa su tabbata a gareku a duk inda kuke.

Duk wanda na ɓatama rai a yayin rubuta wannan Littafin ya gafarceni dan ALLAH, nima kuma na yafema duk wanda ya ɓatamin😭🙏🏻😍😍😍😘😘.

inajin kewarku tun yanzu, sai dai kuma nasan insha ALLAH zamu haɗu a ZAFAFA 2021🤗.

Masoya na Telegram, Wattpad, Facebook, WhatsApp dama duk wata manhaja da wannan littafi ya leƙa ina muku fatan alkairi da sake miƙa godiya a gareku.

Zakuga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login