Showing 255001 words to 258000 words out of 261165 words
Chapter 86 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete
ya kalleni na kallesa, sai kuma duk muka kalli ƙofar da muke jiyo kukan. Kukan jinjiri ya sakamu dawowa a hayyacinmu batare da mun shiryaba, Adamu ya matsa jikin ƙofar da sauri yana magana. Daga ciki aka amsa da faɗin “ko wanene ya shigo dan ALLAH” kamar bazai shigaba sai kuma ya afka kansa tsaye, duk kiransa da nake famanyi bai saurareniba. Haka nabisa na leƙa sai dai ban shigaba, daga ƙofa na hango mace durƙushe tana naɗe jariri dake cikin jinin hauhuwa a zane, ita kanta inda take durƙushen duk jinine. Adamu na tsaye hankalinsa a tashe yana kallonta. Ɗagowa tai ta miƙa masa jinjirar jikinta na rawa, sai kuma tai cak tana kallonsa, kallo irin na kamar na sanka kokuma ina nasanka? Da rawar baki tace, “Mai kama da Baba!”. Sai kuma ta girgiza kai da sauri tana hawaye. “Wannan ba lokacin tunanin hakan baneba, bawan ALLAH koma miya kawoka gidannan nasan UBANGIJI ne ya aikomin kai danka taimaki wannan baiwa da batasan komai ba sai iskar duniya data shaƙa a yanzun. Dan ALLAH ka ɗauketa, ka nisantata da gidannan, itaɗin ɗiyatace, mijina ke neman kasheta saboda matsafine, kaimin alfarmar saka mata suna BILKEESU, karka taɓa faɗa mata bakai ka haifetaba dan girman ALLAH har sai takai shekaru ashirin a duniya, ka binciki ɗan gidan tsohon shugaban ƙasa daya rasu, JAWAAD ABDUL-AZIZ ka haɗata dashi, ka sanar masa suɗin ƴan uwan junane, ɗiyar Rahama ƙanwar mahaifiyarsa Bilkisu ce. Suyi ƙoƙari su haɗa hannu wajen binciken mai gidannan da duk abokan da yake mu'amula dasu, babu isashen lokacin dazan maka bayani aka kaina da abinda ya faru, amma nasan komin daren daɗewa lokaci zai fiddo komai dan sharri baya ɓoyuwa a duniya. Ka ɗauki wancan akwatin akwai kuɗi da kayanta a ciki na baka halak malak, dan ALLAH ka bata tarbiyya irin ta addini, karka bar rayuwarta ta tarwatse da ruɗanin duniya, ka faɗa mata ina tsananin ƙaunarta fiye da komai dana mallaka a duniyarnan. Kai maza ka fita, suna gab da dawowa, idan suka iskoka zasu halaka ka da ita da ni baki ɗaya, ni kuma bana fatan hakan”. Ta ƙare maganar da wani irin kuka mai cin rai da zuciya. Motsin buɗe gate da mukaji ya sakamu fita da gudu, kafin mukai ƙofa mukaji ana shirin buɗewa, wani ɗaki muka shige da gudu muka ɓuya muna leƙen masu shigowar ta taga, a gaban idanmu Wannan (Uncle Nasir) da wannan (Dad) suka shiga ɗakin da matarnan take, duk maganganun da sukai ita dasu muna saurarensu, har lokacin da suka fita da ita daga gidan. Da ga ni har Adamu kuka muke rurus, sai dai bamu da wani ƙarfin ikon sakawa ko hanawa, sannan muna son cika mata alƙawarin fita da ƴarta daga gidan cikin aminci. Sai da muka tabbatar motarsu ta fice a gidan sannan muka fito muma muka fice da gudu, cikin amincin ALLAH mai gadin gidan yanzunma bai ganmuba ya shige cikin ɗakinsa kamar ɗazun da muka shigo yana ciki.
Da kuɗin da matarnan ta bama Adamu akaima Asiya aiki, aka cire ɗanta mara rai, bayan an kamala mata aiki aka kaita ɗakin hutu. Adamu yakai jaririya da ya roƙa wata nos ta gyara ya kwantar kusa da Asiya. Bayan ta farfaɗo cikin dare bai ɓoye mata komai game da bilkisu ba, ita kuma saita amsa da daraja ta rungume tana kuka, dan koba komai ai ɗiyar ɗan uwantane. Abinda kawai Adamu ya ɓoye ga Asiya shine ɗan uwanta matsafine, bai faɗa mata wannanba, ya kuma roƙeni na ɓoye wannan sirrin dan ALLAH har sai lokacin da jaririya Bilkisu takai mizanin shekarun da mahaifiyarta ta roƙa kafin mu bayyana komai ga kowa. Na masa alƙawari da karɓar amanarsa, na rufe wannan zance a raina tamkar yanda shima ya rufesa ga kowa nasa suka cigaba da rainon bilkisu, har ALLAH yasa takai shekarun girma, sai dai kafin lokacin da Adamu ya cika alƙawarin sanar mata ita wacece ALLAH yay masa rasuwa sakamakon bigesa da mota tayi, itama kuma Asiya ALLAH yay mata rasuwa kafin shi. Musan ƴan uwan Adamu bazasu ɗauki Bilkisu ba, dan sun saka wasiwasi a ransu game da ita tun tana jinjira. Na ɗauki Bilkisu na cigaba da kulawa da ita kamar yanda Adamu yayta roƙona gab da numfashinsa zaibar jikinsa. Sai dai kuma na gaza cika alƙawarin lokacin da taƙadin yaron mai gidanmu ya shigo rayuwar gidan............” ya ƙarashe labarinsa da zaman Jazuga a gidansu, har faruwar komai na abinda bilkisu tai musu, da maidasu ƙauyensu da Alhaji Lado yayi, tare da gargaɗi da baza abokan Jazuga a ƙauyen suyi gadinsu. Doguwar jiyyar Firdausi da sukasha wadda tai kamar bazata rayuba har tsahon shekara kusan guda kafin ta warke ayi bikinta da ɗan uwanta, gashi a yanzu sunada yara uku, Musa (Fharhan), Abbas, sai bilkisu da firdausi taima bily takwara saboda ƙauna da soyayya haɗe da ɗunbin bege a gareta.
Jin wannan labari daga bakin Baba ya saka falon sake ruɗewa da koke-koke, Bilkisu kuwa data gigice tamkar wadda ciwon hauka ya sama lokaci guda ta miƙe zaram tana nuna Dad jikinta na wani bala'in karkarwa. “Baba kana nufin shine Mahaifina?”.
“Tabbas Bilkisu shine mahaifinki?”. Ai ganin Bilkisu kawai akai ƙasa wanwar ta sume. Dad kuma ya fashe da wani irin gigitaccen kuka da ƙwalla ƙara, ya shiga buga kansa jikin bango yana ihu maiban tashin hankali da faɗin “Tabbas Rahmah maganar ki ta zama gaskiya, Alaƙar ƙaddarar jiji dake cikin jini ta tabbata.....”. Ƙoƙarin riƙesa ƴansanda sukeyi, yayinda can kuma aka rufu kan Bilkisu ciki harda Jawaad daya ƙwace daga riƙon da Alhaji Babba yay masa.
Bayyana muku tashin hankalin da waɗanan mutane ke a ciki a wannan lokaci zaici tsahon lokaci bamu gamaba, komai ya sake hargitsewa da ruɗewa, dole ƴan-sandan dake a waje suka shigo cikin gidan tare da dogarawan sarki wanda shi yama rasa abin faɗa tsabar mamaki, a da gani yake babu wata ruɗaɗɗiyar rayuwa irin tasa, sai a yau yaga wadda tafi tasa muni da tashin hankali.
Da ƙyar aka iya fita dasu Dad daga gidan, suna kuka da roƙon a yafe musu amma babu wanda ya sauraresu, sai ma tsinuwa da sukesha daga bakin kowa harda ƴaƴansu kansu da matansu. An shiga ƙoƙarin yayyafama waɗanda suka suma ruwa harda Shahudah da Bilkisu, da Mama Atika. Wadda itakam da alama ma dai faɗuwar da tayi tazo da sakamakon paralysis, dan ta gaza motsa komai nata sai ido takebin mutane da shi kawai tana kuka.
______________
Komai fa ya sake rikicewa, gari ya ɗauki magana da ba'asan tayaya ta fita daga gidan Alhaji babba ba, sai daga baya aka fahimci camera aka saka jikin su Dad da ba'asan wanene ya sakaba, ta naɗe komai daya faru a gidan Alhaji babba, lokacin da aka maidasu office kuma a take aka fidda komai ta kafafen yaɗa labarai.
Lokacin da takawa ya baro gidan Alhaji babba zuwa inda ake jiransa zasuyi meeting da ƙyar suka kai saboda hargitsewar da garin yayi, matasa ta ko'ina sun fara fitowa zanga-zanga da makamai akan sufa sai an basu su Dad sun kashe. Kamar wasafa saiga zanga-zanga ta fara faɗaɗa, dan harda ƴammata da zawarawa a cewarsu suma sunabin kadin haƙƙin ƴan uwansu dasu Dad suka lalatama rayuwa ta hanyar fyaɗe. Idan ba'a basu su Uncle Nasir ba zasu bankama station ɗin da aka ajiyesu wuta.
Sai kuma rukunin magidanta da tasu zanga-zangar ta ɗauki manufa akan kisan tsohon shugabanƙasa Abdul-aziz Yousif Tafida, a cewarsu sumafa sai sunbi kadin jinin adalin shugabansu. Tofa jama'a sun fusata ainun, kowane titi ka zagaya mutane ke tittiɗowa zuwa station ɗinsu Jawaad da aka ajiye su Alhaji Kokino, tun jami'an tsaro na ƙoƙarin kwantar da tarzomar dake nemans harfa al'amarin ya nema gagararsu sai da aka kawo wasu jami'an tsaron kala-kala. Amma duk da haka al'amarin ya gagara. daga ƙarshema sai suka zagaye hall ɗin dasu Takawa sukai zaman meeting, acewarsu su fito su bada damar a fiddo musu dasu Kokino kokuma su haɗa dasu. Dan bazasu taɓa yarda sai ankai su Dad Kotu ba, su duk duniya basuga alƙalin da zai iya yima su Dad shari'a ba sam. Gara kawai su kashesu a haɗu a kotun UBANGIJI kawai.
★★★★★★★
Har dare gari yaƙi lafiya, tamkarma ƙara ƴan zanga-zangar akeyi. Jawaad na gida tare da ƴan uwansa dake cike da ruɗani da tashin hankali wannan al'amari har yanzu kira ya samesa daga office. Duk yanda yaso ƙin fitar Alhaji babba sai da ya takurashi, acewarsa babufa yanda zasuyi, wannan al'amarin su barma ALLAH kawai shine zaiyi maganin waɗannan mutanen bawai ƙarfinsuba ko dabararsu. Haka ya fita jikinsa duk babu wani daɗi, ya sumbaci goshin bilkisu daketa barci yana haɗiye hawayen da suka cika masa ido, tausayin kansu yakeji daga shi har ita, musamman ma ita da nata al'amarin yazo a yanda basuyi zato ko tsammaniba, kenan Shahudah da Bilkisu ubansu ɗaya fa kenan? Bilkisu jininsa ce, jini mafi kusanci da muhimmanci a garesu, jinin wadda take da daraja a garesa, wadda ta yarda ta rasa ranta da farin cikinta a dalilin salwantar da mahaifinsa.
Bai iya jan motarba sai Hafiz ne yazo har gida ya ɗaukesa, shi kansa halin da yaga garin yake ciki ba ƙaramin sake tada masa da hankali al'amarin yayiba, dare harya rufa amma mutane basu da niyya komawa gidajensu. Da ƙyar motarsu ta samu hanyar shiga station ɗinsu.
Sun sami su Sir Ahmad cikin tsananin tashin hankali da damuwa, sune sukaimasa bayanin yanda akai komai ya fita har jama'a sukayo wannan gangamin na farautar rayukan su Dad. Ajiyar zuciya kawai Jawaad keta saukewa, tausayin su Qaseem da sauran iyalan waɗanan mutane kawai yakeji, dan haka ya bada shawarar a fita dasu Dad ta ɓarauniyar hanya abar station ɗin dasu zuwa cikin prison dasu ko hakan zaisa a samu sassaucin da hankulan mutane.
Da wannan shawara ta Jawaad akai amfani, sannan D.G da kansa ya fita yayma jama'a bayani daban haƙuri akan su bari suga idan ba'a yankema su Dad hukuncin daya daceba sai su ɗauki matakin da duk sukai niyya, amma dan ALLAH yanzu su kwantar da hankulansu kodan dare.
Da ƙyar suka amince akan safiyar gobe su farka da batun shigar su Kokino kotu, kokuma su su ɗauki doka a hannunsu game dasu. Garin baiyi lafiyaba sai da aka sake baza jami'an tsaro, duk yanda su Jay sukaso kwana a gidajensu yau kam ta gagaresu, sunata kai kawo akan mutane har garin ALLAH ya waye.
_________________
Tunda na farka kallon kowa kawai nake, jinake tamkar an kwashemin ƙwaƙwalwa da zuciya an jefar gefe, kukan zuci zanyi kona zahiri? Wane kalar tunani zanyi akan wannan juyayyen al'amari ruɗaɗɗe? Iyayen dana tashi na gani ƙaddara ta juyasu sun zama ba nawa ba, waɗanda ban taɓa kawowa a tunanin hankali da ƙwaƙwalwa ba sune suka zama iyaye na gaskiya. Dad fa? Jama'a kuji wani batu tamkar a tatsuniyiyi da hikayoyin marubuta. Ashe shiyyasa nakejinsa a raina tun lokacin dana fara tozali dashi matsayin yayan innata? Shin murna ya kamata nayi shin kokuwa kuka? Baƙinciki kokuwa takaicin kasancewarsa Ubana ni jininsa? Wane hukunci ya dace dashi game da mahaifiyata da sauran al'ummar da suka cutar suka zalinta saboda son zuciya da ƙwaɗayi da burin duniya da kayan cikinta? Anya badan kalmomin bakina sunyi nauyin da zasu iya zama tuntuɓen harshe wajen aikata zunubiba da ban zazzagesu ga azzalumin uba irin nawaba kodan duniya taji tasan na tsanesa. Inama gaskiya bata fitaba na ciga da kallonsa matsayin yayan inna ba Mahaifina ba, inama ace banga wannan ranarba Mamana ta bari yayi tsafin dani nima. Inama.... Inama..... Inama.....?
Bilkisu ta faɗa a fili tana rushewa da matsanancin kuka mai cin zuciya. Rungumeta Umm-Anum tayi suka cigaba da rerawa a tare. Kowa ka gani a gidan idanunsa a kumbure babu ko ƙyan gani, su Uncle Sulaiman tun a daren jiya duk sun koma gidansu, anan su kaɗaine zuri'ar Alhaji babba sai su firdausi kuma da Maman Yara da tun jiya tana nan, ganinta ba ƙaramin daɗi yayma Umm-Anum ba, inda itama a wajen maida yanda akayi ta sake buɗe komai dangane da abinda ta sani game dasu Dad ɗin da zamanta gidan Alhaji Kokino na tsahon shekaru dan kawai ta samu damar ɗaukar tukunyar tsafin da akaima Umm-Anum. Ganota da Alhaji Kokino yayi gameda taimakon da suke bama Jawaad ita da ɗan ƴar uwarta Gimba, kashesa da sukayi da kamatan da sukayi sukaita azabartarwa, harma da wasu manya-manyan sirrikansu da taji.
Nanma dai ansha kuka mai ban tausayi, tare da jera ɗunbin godiya a gareta da addu'oin fatan alkairi. Duk yanda sukaso ganin kwanciyar hankalin bilkisu hakan ya gagara, daga ƙarshema saita fara bleeding, a matuƙar tashin hankali aka kwasheta zuwa asibiti, inda ta samu taimakon gaggawa a wajen Dr Bello. Jawaad baisan mike faruwa ba saida Nabeelah ta kirasa ta sanar masa, hankali tashe kuwa ya iso asibitin.
To cikin dai ikon ALLAH an samu damar tsaida jinin, inda Doctor yay musu albishir da cewar cikinta na nan bai zubeba, sai dai tana buƙatar samun hutu dan gaskiya ƙwaƙwalwarta da zuciyarta suna cikin tsagwaron ruɗani, har jininta yama hau, idan da bama suyi gaggawar kawota asibiti ba da ba cikin kawai za'a rasaba ita kanta zasu iyama rasatan. To amma Alhmdllh yanzu kam komai ya dai-daita, sai kawai a jira farkowarta kuma aga abinda ALLAH zaiyi..................✍
Ku dakaceni da sauran zuwa safiya idan ALLAH ya kaimu idan na kammala editing😊😍😍😘🚴🏼.
ALLAH ka gafartama iyayenmu[2/17, 3:01 AM] +234 703 966 0069: Page 63
....................Su Jawaad basu san wainar da ake toyawaba a gari, sai iface-iface suka dingaji da tashin hayaniya, sai kuma hayaƙi daketa turnuƙe sararin samaniya a hankali. Sai sukaga kuma mutane nata fita daga asibitin.
Gaban Jay ya faɗi, ya zaro waya daga aljihu yay kiran Jabeer dan yaji ko lafiya?. “Boss wlhy akwai matsala, an fito da mutanen nan daga prison za'a kaisu kotu jama'ar gari sun tare motar sun banka mata fetur sun saka wuta. Wlhy duk yanda jami'an tsaro sukaso tsaidawa al'amarin ya gagara, harma an raunata mana ɗan sanda guda daketa ƙoƙarin basu kariya da roƙon mutane su kwantar da hankalinsu kotu za'a kaisu, kuma a yau za'a yanke musu hukunci. Amma sam basu sauraresaba, saima suka nema haɗawa dashi shima, dan acewarua shima nasune”. Innalillahi Jawaad keta ambata zufa na keto masa a duka sassan jikinsa. Dole yabar asibitin ya nufi inda al'amarin ke faruwa..
Wuta taci su Alhaji kokino sosai kafin ƴan kwana-kwana suzo da masu bada taimakon gaggawa na jami'an tsaro, da ƙyar aka iya samun hanyama motar ta ƙarasa, police kuma suka fara jefa barkonon tsohuwa, da wannan damar aka samu mutane suka fara darewa har aka ƙarasa gasu Dad aka basu taimakon, sai dai kuma ina komai ya gama ƙurewa, dan wutar ta cisu sosai, sunta ihu da neman taimako basu samuba. Waɗanda basu mutunba ma da wahala ace zasu rayu, dan su Dad ko iya gane fuskokinsuma ba'ayi sam. A haka dai aka kwasosu zuwa General hospital inda su Bilkisu suke.
Faruwar hakan yasa aka baza jami'an tsaron sintiri a kowane titi, tare da kafa dokar hana shiga da fita gaba ɗaya, kasuwanni da kowacce ma'aikata an rufesu ruf an kora mutane gidajensu. Garin yayi tsit, sai gidajen redio dana tv kawai ke aiki, anan mutane kejin halin da ake ciki.
Kafin a ƙarasa dasu Dad asibiti wasunsu suka sake mutuwa, ciki harda Uncle Nasir kuwa. Suma dai an shiga da sune kawai, amma likitoci sunma rasa ta ina ya kamata su fara basu taimakon daya dace, gaba ɗaya jikinsu ya sale tas, yay jazur tamkar naman dake kusa da wuta ana masa gashi😭.
Ba ƙaramin tashin hankali su Umm-Anum suka sake shigaba da ganin su Dad, duk da zalincin da sukaima rayuwarsu har hawaye sukai musu. Bama suba duk mai hankali yaga wannan bahagon al'amari dolene ya shiga ruɗani mai tsanani, ya kumaji tsoron wannan mummunar rayuwa da waɗanan mutane suka ƙirƙirar ma kawunansu. Gadai duniyar an tara, kuɗi, mulki, zuri'a, da komai amma an ƙare da tafiya a barsu cikin tozarci da wulaƙanci. Basu karesu daga faruwar kowanne irin bala'iba ko masifa ba, abinda suka tara da wanda suka shuka bai hanasu mutuwaba, bai hana ƙarshensu muniba, wannan shinefa ake kira da BA FARKON BA ƘARSHEN, yakai ɗan uwa bari murna akan aikata mummunan aiki kuma babu abinda ya sameka, bari tinƙaho da taƙama akan kai haƙƙin wani bai sakaka komai sai ƙiba da kwanciyar hankali, bari farin ciki kaine sama dakowa saboda kasancewarka azzalumi, bari taƙama da tinƙahon ka tara kai babu yanda aka iya da kai. Rage buri da hangen haramun domin kawai burge duniya ko morarta dayin bishasha a cikinta. Daure ka nema halak komai wahalarta da ƙaracinta, nisanta kanka daga haramun komai sauƙinta da zaƙinta. Ji tsoron UBANGIJI koda ace baka ganinsa to shifa yana kallonka. Kiyaye ruɗin duniya dana abokan banza ka kama ALLAH da abokan ƙwarai masu nuna maka muhimmancin tsoronsa. Ya ALLAH ka gafarta mana, kasa muyi ƙyaƙyƙyawan ƙarshe. ya rabbi ka ɗauki rayukanmu muna masu cike da ɗunbin tsoronka da soyayyar MANZON ALLAH (S.A.W)🙏🏻😭.
______________________________
Al'amura sun sake ƙwaɓewa, a gaba ɗaya kwanakin satin da suka biyo baya, babu wani farin ciki daga jama'ama balle su Jawaad da iyalan waɗanan mutane. An samo gawar Aunty Mah-Mah (Rahmah) a gidan Dad cikin wani akwatin tsafinsu, ashe lokacin da suka halakata wata gawar daban suka kawo a zuwan itace, shiyyasa Dad ya hana kowa yimata wanka shine yay mata a lokacin. To ashema ba gawarta baceba, gawarta na nan cikin ɗakin sirrinsa da ko Mom ta rantse bai taɓa barinta ta shigaba, ita kuma duk tunaninta bai taɓa kaiwa ga hakanba.
Abin sha'a
[2/17, 3:01 AM] +234 703 966 0069: wa da tsarkake sunan UBANGIJI gawar Rahma fes aka sameta dukda sheɗancin da Dad