Showing 87001 words to 90000 words out of 261165 words

Chapter 30 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1119

yay driving, kai tsaye asibiti ya nufa, sai da yaje suka gama magana da likita sannan ya nufo ɗakin da Bilkisu ke jiyya. Sallama yay suka amsa, kafin ya tura ƙofar ya shiga.
       Kasa ɗagowa nai in kallesa, dan wata matsananciyar kunyarsa nakeji a raina, cikin girmamawa ya gaida mama, aunty Batool ma ta gaidashi da tsokanarsa, gaisuwarta kawai ya amsa bai maida mata magana akan tsokanarsa da takeba, na ɗago ido kaɗan nai masa kallo ɗaya na janye da faɗin, “Ina kwana”. shiru kamar bazai amsaba, sai da ya ajiye kwalin maganina daya ɗauka yana dubawa sannan yace, “Lafiya ya jikin?”. Ahankali nace, “Naji sauƙi”.
         Jawaad ya ɗauke kansa daga Bilkisu ya maida ga mama, “Mama Doctor ya sallameta, saiku haɗa kayanku, zanje office yanzu, nanda awa ɗaya zuwa biyu zan dawo sannan ai kun kimtsa”. Mama tace, “To to Alhmdllh, ALLAH yasa haka shiyafi alkairi, to amma kayanta fa? Kasan komai yana can gidan”. Ɗan jimm Jay yayi idonsa akan Bilkisun, ya sauke numfashi kaɗan yana ɗauke idanunsa, “Inaga mu manta da zancan zuwa gidansu yazu, bara naje na samo mata wasu kayan kawai”.
         Jin abinda yake faɗama mama yasa na ɗago da mamaki na kallesa, hakan yay dai-dai da shima ya juyo gareni, idanunmu ne suka shige cikin na juna, nai azamar janye nawa da fargabar ina kuma zan koma? Badai gidan nasaba? yanzu har rashin gatana yakai irin haka da.......
    Katsemin tunani yay da cewar, “Dami-dami kike buƙata?”. Idanuna cike da ƙwalla na ɗago na kallesa, ganin har yanzu ni yake kallo saina maida kaina ƙasa, muryata cike da tahowar kukan da nake dannewa nace, “Miyasa bazan koma can ɗinba?”. Banza yay bai amsa minba, hakan yasa hawaye masu zafi suka silalomin akan kumatu. Sautin siririn tsakinsa kawai naji, cikin faɗa-faɗa yace, “Haka na gadama dole kuma hakan za'ayi, idan kuma kika nema dagulan lissafi ALLAH yau ɗinan zaki tare”. Babu shiri na ɗago kai da sauri, wata uwar harara ya zubamin. Dole na maida kaina ƙasa. Wata ƴar ƙwafa yayi, sai takunsa ya biyo baya, kafin naji buɗe ƙofa da rufewa alamar ya fice abinsa. Koda na ɗago sai naga ashe daga ni sai shine ma a ɗakin, sam banji sanda su mama suka fitaba, dukda inajin motsin ruwa a bayi alamar ɗaya na ciki ɗayane ya fita.
         Gaba ɗaya zuciyar Jawaad a jagule take, sai dai jarumtarsa ta ɓoye hakan, shi mutumne tamkar kowa, yana farin ciki yana baƙin ciki, yana shiga matsala yana  shiga tashin hankali, kawai dai ALLAH yayisa mai zuciyar dakiyane kamar yanda ALLAH yay mafi yawan maza da juriya akan abu komin zafin da sukeji akan al'amari. Tafiyar da bata wuce mintuna goma ba ya isa wani haɗaɗɗen boutique, yanda suka tarbesa zai tabbatar maka da an masa farin sani a waje, sai gaidashi suke cike da girmamawa. Wani mai tsananin kama da Jabeer ne ya fito daga wani lungu, ganin Jay ya sashi faɗin, “Yah Jay barka da zuwa”. Kallonsa Jay yay daɗan murmushi yace, “Yauwa Kabeer, ya kasuwar?”. “Alhmdllh Yayah, kanason wani abune?”. Kai kawai Jay ya kaɗa masa kafin ya miƙe a kujerar da yake zaune. Yana gaba Kabeer na biye dashi har wajen da kayan mata suke, tsala-tsalan jallabiya da ƙananun kaya harma da ɗinkakkun atanfofi da shadda duk sunda. Ahankali yake binsu da kallo ɗaya bayan ɗaya, karon farko a rayuwarsa da yazo saima ma

Billy Abdul, [12/15/20, 12:50 PM]
ce kaya shi ɗaya, ko sanda suna tare da Shahudah hakan bai taɓa faruwaba, dan ita a tsarinta bata sayen kaya anan saina ƙasashen ƙetare, hakan yasa koda yaga abu ya burgesa baima taɓa wahal da kansa wajen saya matanba.
      Ganin ya kasa ɗaukar komai kabeer yace, “Yah Jay aida ka kira ka faɗi duk abinda kake buƙata bama saika zoba”. Guntun murmushi jay yay masa kawai daɗan taɓa kafaɗarsa, kafin ya fara nuna masa duk abinda yay masa wanda ya ƙiyasta a ransa zaiyi dai-dai da jikinta, saida ya ɗauka kaya kusan kala goma sha biyar, sannan ya ɗauka takalma uku da hijjabai huɗu ya zaɓi akwatin da za'a zubasu. Yasan dolene ƴa mace budurwa kamarta ta buƙaci kayan ciki, to amma shi ta ina zai fara tunda ba sanin seize ɗinta yayba. Kallon sashen da kayan suke yay, gasunan kala-kala kuma duk seize ɗin da kake buƙata zaka samesu, yaɗan yatsina fuska kafin ya nufi wajen, amfani yay kawai da yanda yake hasasota cikin idanunsa ya ɗauka matasu aka haɗesu da waɗancan. Card ɗinsa ya bama Kabeer, ganin kabeer na wani noƙewa akan baza amshi kuɗinba dan harya kira Jabeer ya sanar masa ga Jawaad ɗin a wajen yace karsu amshi kuɗi su rubuta su aje idan yazo zai biya. (Wajen na Jabeer ne, ƙaninsa kabeer ke kula dashi sai sauran ma'aikata). Cikin sosa ƙeya Kabeer yace, “Yah Jabeer yace karna amsa”. Sosai Jay ya kafesa da idanunsa da yau gaba ɗaya babu haske a cikinsu saboda damuwa. “Kiransa kai ka faɗa masa nazo?”. Kasa cewa komai Kabeer yay sai faman susar ƙeya yake, Jay yay gaba a binsa zuwa mazaunin kabeer ɗin da yake shine mai amsar kuɗi. Ɗaya daga cikin yaran wajen ya kira ya duba masa kuɗaɗen duka kayan aka zubasu a akwati, shikuma ya saka card ɗinsa ya cire adadin kuɗin yay ficewarsa aka bisa da kayan.

★★★★★

        Fitar jay babu jimawa a asibiti Qaseem yazo, cike da mamaki Bilkisu ke kallonsa jikinta sai rawa yake dan tunda ta kwanta a asibitin nan sai yau ta gansa, baiko kalli mama ba balle ta samu darajar gaisuwarsa ya finciki hannun Bilkisu dake zaune bayan ta kimtsa suna jiran dawowar Jawaad, da sauri mama ta riƙe Bilkisun da faɗin, “Lafiya kuwa Qaseem? Ina zaka kaita?”. Wani banzan kallo ya mata yana figar bilkisu batare daya tankaba, itako kuka take iya ƙarfinta da roƙonsa ya sake mata hannu karya jimata ciwo, amma sam yaƙi sauraren kowa. Tun suna ɗaukar abin wasa har yanema fin ƙarfinsu, dan Doctor ma yazo ya basu sauran maganin bilkisun shima ta ritata dashi. Rikici bana wasaba ake kwasa da Qaseem har ALLAH ya maido Jawaad asibitin. Tunda ya gabato wajen yakejin hayaniya, cike da mamaki ya shiga dan ƙofar a buɗema take. Idanun sane suka fara sauka akan hannun Qaseem dake riƙe dana Bilkisu, tuni idon ƴan mazan ya rufe, a wata irin matsananciyar tsawa yace, “Qaseem sake mata hannu!!”. shi Qaseem ma sai yanzu yaga Jawaad ɗin, shima a fusace yace, “Anƙi a saki ɗin, koka saketa, koma karka saketa zan wuce da itane”. Saukar wani bahagon bugu kawai Qaseem yaji akan damtsen hannunsa, ai baimasan ya saki hannun Bilkisu ba saboda gaba ɗaya jijiyar hannunsa ta saki lokaci guda saboda azaba, kafin ya gama dawowa hayyacinsa Jay yaja hannun Bilkisu dake kuka sun fice daga ɗakin. Ganin haka yasa Doctor saurin rufe ƙofar ya kulle danya bama jay damar barin asibitin gaba ɗaya.
         Kuka bily take cin ƙarfinta har suka hau titi, jin ta cika masa kunne yasashi taka wani wawan birki da batasan sanda tai tsale ta koma jikinsa ba. Sai jinta kawai tayi zaune ɗare-ɗare bisa cinyarsa ta cusa kanta a ƙirjinsa tare da ƙanƙamesa. ALLAH ne yaso Jawaad ya tsaida motar, da babu abinda zai hana su kife a hanyarnan. Gaba ɗayama sai ya kasa cemata uffan, sai rumtse idanunsa da yay  yana mai cije leɓensa na ƙasa da masifar ƙarfi kamar zai hudashi.
        Jin shiru mun tsaya ga ƙamshin turarensa yay mugun addabar hancina haryazama shine iskar da nake shaƙa ya sani ɗagowa, sosai na zabura ganina a jikin boss ɗare-ɗare, innalillahi.... Na shiga ambata ina rawar jikin sauka, harna koma inda na baro bai motsaba, nikuma ban iya kallon fuskarsa ba saboda tashin hankali da matsananciyar kunyar dana tsinta kaina a ciki. Jin tsahon mintuna biyar yaƙi cewa komai yaƙ

Billy Abdul, [12/15/20, 12:50 PM]
i kuma ya cigaba da tafiya yasani satar kallonsa ta gefen ido ina share hawayena da sukaƙi tsayawa. A kife yake kan sitiyari bana ganin fuskarsa, tsorone ya sake kamani, murya na rawa nace, “Dan ALLAH kayi haƙuri, wlhy tsorata nayi”. A fusace ya ɗago yana watsamin wani irin harara, yanda idanunsa sukai matuƙar jazur fiye da farkone ya kuma ɗagamin hankali. A kausashe yace, “Idan baki rufemin bakiba saina canja miki kamannin fuska! Saboda na raboki dashi kikemin wani kukan banza da wofi?!!”. Da sauri na shiga girgiza masa kai ina mannewa da ƙofa, dan yanda yay maganar tamkar zai haɗiyeni ɗanyane, ni tun lokacin da naga fushinsa nake tsoron cigaba da ganin hakan. Yay ƙwafa da ƙara zubamin harara, “Share waɗanan banzayen hawayen”. Saurin saka ƙasan hijjab ɗina nai na goge tas kamar yanda ya buƙata, sake ɗauke kansa yay daga gareni Batare da yace komaiba ya tada motar da fusgarta muka cigaba da tafiya.

       Duk da hankalina a tashe yake da yanda yake zuba gudu a titi ban sake gigin yin wani abuba, sai kaina dana tusa a cikin cinyoyina ina addu'ar ALLAH ya kaimu lafiya dukma inda muka nufa.
      A halin da yake ciki yanzu bazai iya shiga masarauta hakaba, hakan yasa yay fakin daga waje, fita yay da waya a hannu, bayason kiran gimbiya dan haka ya maida akalar kiransa ga dattijon nan, bugu biyu kuwa ya ɗaga suka gaisa, Jawaad yay masa bayani a taƙaice. Dattijo ya amsa masa da sujirasa gashi nan zuwa. Babu jimawa kuwa yazo tare da Amaturrahman data rikice da murnar ganin Bilkisu. Basu wani ja zanceba ya basu Bilkisun batare da yace mata uffanba akan hakan, saida ya juya zai shiga motarne ya dubeta sau ɗaya ya ɗauke kansa da faɗin, “Ki shirya gobe zaki koma aiki, zan biyo na ɗaukeki” daga haka yay tafiyarsa. binsa tai da kallo har saida ya tada motar yabar wajen itama suka shiga motar dasu Amaturrahman suka fito da ita.

__

            Asibiti Jawaad yay niyar komawa dan yayma Qaseem dogon gargaɗi, sai dai tunanin barinsa ya samesa har gida ya sakashi sharewa, juya kan motar yay zuwa station zuciyarsa fal tunane-tunane, ga aiki jibge a gabansa da baisan iyakaba, ga kuma matsaloli kala-kala da yarasa makamar dazai kama domin fara warwaresu. Saƙon ɗan fi'auna ne yazo masa arai, har ya shiga office ɗinsa yana juya zancen a ransa, ‘Mi ɗan fir'aunan ya sani a kansa da haryake iƙirarin ya basa har naira miliyan hamsin domin ya sanar masa? Shin waishi yaron nanma wanene shi? Kuma a ina su Momy suka samosa?’. Wannan tunanin da yazo masa a raine ya sakashi dakatawa daga ƙoƙarin kunna Computer gabansa da ya kai hannu zaiyi, komawa yay jikin kujera ya kwanta yana lumshe idanunsa.
       A haka Aliyu ya shigo ya samesa, sai da yay masa sallama har biyu sannan ya farga da shi, ya buɗe idanunsa da tashi zaune sosai, tie ɗin wuyansa ya sassauto ƙasa yana kallon Aliyu daya zauna. “Boss lafiya dai?”. Aliyu ya faɗa idonsa akan Jawaad, sassanyan numfashi jay ya sauke da cewa, “Lafiya lau Aliy”. Badan Aliyu ya yardaba ya ƙyalesa, saima takardun hanunsa ya miƙa masa yana masa bayani. Jawaad ya amsa ya duba ya sake miƙama Aliyun, magana suka ɗanyi Aliyu ya tashi ya fita.
        Koda Aliyu ya fita Jay kasa haƙuri yay ya ɗauka waya ya shiga neman ɗan-Fir'auna, tana gab da katsewa aka ɗaga, daga can wanda ya ɗaga ɗin ko sallama baiyiba balle batun gaisuwa yace, “Mai wayar yayi Accident yana asibiti”. “...Accident?” jay ya maimaita da maɗaukakin mamaki tare da sake kiran wayar dan har an katse.............✍

ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.

SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
        ƊAURIN ƁOYE
      ALƘAWARIN ALLAH.

HAFSAT RANO tazo muku da;
         SAUYIN ƘADDARA
        ƊAURIN GORO

MAMU GEE tazo muku da;
           BURI ƊAYA
         ƘAUNAR MU.

MISS XOXO tazo muku da;
           KAIMIN HALACCI
           IGIYAR ZATO.

BILYN ABDULL tazo muku da;
          WUTSIYAR RAƘUMI...
         GUDU DA WAIWAYE....

abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai

Billy Abdul, [12/15/20, 12:50 PM]
iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.

Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899

sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.

Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300

Sai kunzo😍😍😍😘.

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻[12/16/2020, 2:27 PM] HASNA✍🏻: Bilyn Abdull 📚:
Page 29

...............Yanzunma dai saida taje gab da yankewar aka sake ɗagawa, sai dai yanzu ba'ace komaiba, cikin ɗan zafi-zafi Jay yace, “A wane asibiti ne?”. Ɗan jimm wancan yay, sai kuma cayay General”. Yanke wayar kawai Jay yayi batare da shima yace komaiba, maida akalar kiran yay ga Jabeer, bigu biyu ya ɗauka, bayan sun gaisa Jay yace ya fiyo zasu fita. Iyakar abinda yace kenan ya katse kiran ya miƙe, rigar suit ɗinsa daya cire tun shigowarsa yay hanging a bayan kujerar zamansa ya ɗauka, tare da ƙaramar bindiga ya tura a gefen ƙugunsa ya fice.
       Tare suka fita shi da Hafiz da Jabeer, dan Aliyu akwai aikin da yakeyi. Koda suka isa General hospital emergency suka nufa kai tsaye, tunda ance Accident can tunaninsu ya fara basu su duba farko. Hafiz ne yay tambaya duk da basu da tabbas ɗin cikakken sunan ɗan-Fir'auna bayan Habib, sudai ma'aikatan asibitin dake Emergency ɗin basu ganeba, amma alamun da suka gani na cewar su hafiz jami'an tsarone yasa doctor zagayawa dasu kaf gadajen dake cikin Emergency room ɗin suna dubawa, babu ɗan-fir'auna anan ɗin. Doctor yace, “To akwai dai wani da aka kawo tunda safe yayi accident, mun bashi ɗaki awa ɗaya data wuce, al'amarinsa akwai ruɗarwa, daga baya ƴan uwansa sukazo suka ɗaukesa duk da yana cikin mawuyacin hali”. Jabeer ne yace, “Suka ɗaukesa kamar ya? Baiji ciwo bane?”. “Yaji ciwo sosai yallaɓai, dan ko farfaɗowa ma bai gamayiba mundai dubasa babu karaya sai raunika?”. Kafin Jabeer ya sake magana Jay dake gefe yana latsa waya tamkar ba saurarensu yakeba yace, “Miye sunansa?”. Yay maganarne ba tare da ya ɗagoba, dan yasan idan har Dr Tayyeb ya gansa tsorata zai yaƙi faɗar komai.
      Dr Tayyeb dai yasha jinin jikinsa akan Jay, sai dai da yake bai ganin fuskarsa da ƙyau sai ya daure yace, “Kamar dai Habibu ƙaura suka bada a jikin katin”. Jay baice komaiba dan ya fahimci dai ɗan fir'auna ne, sai kawai ya nufi hanyar fita. Ganin haka yasa su Jabeer yima Doctor sallama suka biyoshi. Acikin mota suka iskoshi, sai da suka shiga suma Hafiz yace, “Boss yanzu a ina zamu ganosa kenan?”. Jawaad da har yanzu hankalinsa naga waya batare daya ɗagoba yace, “Anguwar kuke”. Tada motar Jabeer yay sukabar asibitin batare da sun sake cewa komaiba, dan sun lura akwai abinda yakeyi mai muhimmanci a wayar.
      Sun shiga Anguwar Kuke, inda Jay ya sanar musu dai-dai inda zasu tsaya, a tare suka fita a motar, Jawaad yay gaba suka bisa a baya har zuwa jikin jan gate, gidan bawani gidane mai ƙyauba, dan irin ginin da ɗin nanne, sai dai a da ɗin maishi ya kasance mai arziƙi, a rufe ƙofar take, hakan yasa Hafiz ƙwanƙwasawa. Kusan mintina biyar suna tsaye kafin a buɗe a fusace, kodamar tambayarsu suwanene su? wanda ya buɗe ɗin baisamuba Jay ya turashi gefe ya shige su Jabeer na biye dashi. Duk tsagerancin tsagera idan yay gamo da wanda ya fisa tsageranci nutsuwa ya keyi, hakan yasa saurayin bai iya cewa komaiba ya maida ƙofar ya rufe shima yabi bayansu dan ya gane Jawaad.
       Ɗunbin mamaki da al'ajab ne ya sakasu tsayawa cak a ƙofar falon, dan kuwa gungun samarine da adadainsu zai iya kaiwa goma  tsai-tsaye da candles kunne a hannu sun zagaye katifar da Ɗan-Fir'auna ke kwance a tsakkiyar falon, dukansu idanunsu a rufe suke babu mai magana bare motsi. Jabeer da Hafiz ne kawai sukai magana tare da jan birki, Jawaad kam uffan baiceba sai kafawa matasan idanu da yay a ransa yana nazarinsu. Hannu yasa da ƙarfi ya bugi ƙofar falon, a take duk suka dawo hayyacinsu, suka juyo suduka suna kallonsa. Su Jabeer dai abin ya firgitasu, amma a mamakinsu sai sukaga Jawaad ya danna kai cikin falon kamar baiga abinda yake faruwaba. A baɗini shima kuma lamarin ya firgitashi, sai dai ya danne saboda shi mutumne mai kasadar tunkarar abu kai tsaye, ko aiki suka fita duk haɗarin waje baya shakkar shigewa gaba.
          Cike da takun nutsuwa Jay ya ratsa ta tsakkiyarsu yana addu'a a ƙasan ransa har zuwa gaban katifar da ɗan-fir'auna ke kwance samɓal jikinsa duk raunika wasu ansa bandage, yay wani irin kukkumburewa a fuska saboda buguwar da yayi. Sai da yay masa kallon mintuna uku kafin ya ɗago ya kalli samarin da suma

suka kafeshi da kallo tamkar zasu cinyesa ɗanye. Yi yay tamkar bai fahimci kallon da suke masaba, cikin Kakkausan lafazi yace, “Dami yay Accident ɗin?”. Wanda yake gaba gab da katifar sosai ne ya fara hure candle ɗinsa, sannan ya juya ga sauran yay musu nuni dasu zauna. Babu musu duk suka zauna ƙasa suka tanƙwashe ƙafafunsu hannayensu riƙe da candles ɗinsu har yanzu kuma a kunne. Sake maida dubansa yay ga Jawaad yace, “Yakamata mu fara sanin baƙonmu ai”. Sake ɗaure fuska Jay yayi, kamar bazai tankaba sai kuma ya gyara tsaiwa da faɗin “Nine na kira waya ɗazun”. Karon farko saurayin da babu alamar mutunci tattare dashi yay murmushi da cema Jawaad, “Hutawarka lafiya babba, haɗari yay da mashin yau da asuba, sai dai abin ya haɗa da mabiya sahu”. Jawaad tsaf ya fahimci ma'anar kalamsa, amma sai yay kamar bai ganeba yace, “Amma miyasa kuka ɗakkosa daga asibiti? Suwaye ke bibiyar sawun nasa?”. Gayen yace, “Babba! wannan wasane tsakanin rindunar mafarauta guda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login