Showing 39001 words to 42000 words out of 261165 words
Chapter 14 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete
buɗe daga ƙasa bata wani matseniba sai a ƙirji kamar yanda tsarin ɗinkin yake, maɗaurin da akai mata na kama na ɗaure a bayana, sai ta kuma fita da ƙyau. Gashina dake a tsefe na kuma gyarama zaman ribbon, sanan na saka farar hula mai ƙyau, na kawo ƙaramin gyale baƙi na yana a kaina, tare da kalmashesa a ƙirjina ya rufe ruf na ɗora a kafaɗa ƙasanshi suka sauka bayana, basai an faɗaminba, ni kaina nasan nayi ƙyau, hakan yasa naita kallon kaina a mirror ina murmushi, a gurguje na ƙarasa kimtsawa na fito sagale da ƴar jikkata a kafaɗa ina ƙamshi mai sanyi, sai takalma masu ɗan tudu kaɗan, na riga na faɗama Mom zan fita dama tun da daddare, hakan yasa yanzu nai ficewata kaina tsaye tunda babu wanda ya tashi har Yah Qaseem da baisan zan fitaba, dan banfaɗa masabama gudun matsala.
Da ƙafa na taka har titi na tari napep na hau zuwa inda Oga Jabeer ya bani.
Bayan fitar Bilkisu daga gidan Mom ta fito daga ɗakinta, tanason tayi magana da Shahudah ne, shiyyasa tun ɗazun taketa dakon fitar bily, tana tsoron halin da Shahudah zata iya shiga da har bily zata sani, dan a ganinta bily ita kaɗaice bare a cikinsu da bai kamata tasan sirrinsu ba. Sam jiya batai barciba akan bayanin da Shahudah tai musu na zuwa ɓangaren Jawaad da tayi, ta fahimci sunyi kuskuren ƙin sanarma Shahudah gaskiyar lamari akan sakinta da Jawaad yayi tun lokacin da wancan al'amarin ya faru, ba damuwarta abinda Shahudah ta aikataba, damuwarta kar Jawaad ya sake gudun Shahudah akan hakan, dan ita kanta inhar zata faɗi gaskiya bata taɓa kama Jawaad da abun rashin gaskiya ba dangane da fasiƙanci, dan ko lokacin da basa ƙasar ma idan yaje musu hutu duk jarabar Shahudah da naci akan yazo suje club baya zuwa, ita kanta ma faɗa yake mata, shiyyasa da yaje take kame kanta. To tasan akan hakan Jawaad zai iya sake bijire musu ne dangane da maida Shahudah.
Tashin Shahudah kenan a barci tayo brush da alwala ta fito mom ta shigo, ƙarfe goma saura sai yanzune wai ake alwalar sallar asuba😭🤦🏻.
“Mom lafiya?” Shahudah dake ƙoƙarin saka gyale ta faɗa tana kallon mom. Mom ta zauna bakin gado tana faɗin, “Magana nazo muyi”. Zama Shahudah tai ta fasa sallan, Mom tace ba salla zakiyiba ne?” “Eh salla zanyi, amma muyi magana sai nayi daga baya”. “Karki damu tashi kiyi sallar zan jiraki”. Shahudah batace komaiba ta miƙe ta kabbara salla, wadda ALLAH kaɗai yasan mima take karantawa, dan a mintuna ƙalilan ta idar da kayarta ta dawo wajen mom dake zaune tai tagumi da juya abinda zai iya biyo baya a ranta. Motsin Shahudah ne ya maidota hayyacinta ta gyara zama, tare da kamo hannayen Shahudah duka cikin nata ta kafeta da idanu, “Shahudah magana zanyi miki, inason ki nutsu ki fahimta, domin muma a yanzu haka hanyar gyara ɓarnar da kikayi muke, munada tabbacin samun nasara kuma, abinda yasa muka yanke hukunci sanar mikin a yanzu dukda mun ɓoye a baya saboda gudun halin da zaki shiga, yanzu kam saboda karki sake ƙara tafka irin kuskuren da kikayi ranar na zuwa wajen Jawaad”.
“Mom ni dan ALLAH kimin magana kai tsaye, ki daina yimin wannan manya-manyan hausan naki da ba wani fahimtarsu nakeba, minene ya faru”. Yanda tai maganar da kumbura bakin shagwaɓa yasa mon yin ƴar dariya tana shafar kumatunta, “Nifa daɗina dake taɓara maman Dadynta, karki damu ai zan kaiki, kumani sonake ki iya hausar ai tunda yaren mamanki ce”. Shahudah batace komaiba sai ɓata fuska data sake yi. Mom ta ɗauka takardan data shigo dashi ta miƙama Shahudah. Babu musu Shahudah ta amsa tabuɗe takardan batare da tace komaiba.
Kasancewar Jawaad da turanci ya rubutama Shahudah takardan saki sai ta fahimci komai dallah-dallah. Hannunta na rawa da bakinta ta ɗaga takardar, “Mom kina nufin BB ne ya aiko min da wanan dan naje wajensa?”.
Kai Mom ta girgiza mata, “Badan kinje wajensa bane, wannan takardar shekararta biyar kenan a gidannan, mune dai bamu bakiba tun lokacin da akai rikicin zubar da cikin nan, munƙi bakine saboda gudun karki sake shiga wani hali akan wanda kika tsinci kanki a wancan lokacin, dan muna
ta ƙoƙarin duk bin hanyar data dace ki koma ɗakinki, sai dai zuwan da kikai wajensa ya ɗakko hanyar ɓata dukkanin shirin namu, shi bazai fahimci bakisan ya sakekiba, zai fassara abinne ta wata siga daban”.
Matsanancin kuka shahudah ta fashe dashi, ta dafe kanta dake juya mata lokaci ɗaya, yanda tai baya zata faɗine yasa Mom azamar tarota tana kiran sunanta a razane, rungumeta shahudah tayi tana kuma kuka tamkar ranta zai fita, sai dai ƙarancin tunaninta na raya mata cewar tamkar sakin a banzane, dan Jawaad yayi ƙarya ya kwana da yunwa, aurensu baida maraba dana zobe, babu kishiya babu saki, ta daka tsalle ta dire a gaban Mom tare da wawaso rantsuwa ta sake direwa akan baima isaba. Yanda ta birkicema Mom tana kuka da rantsuwar Jawaad bai isabane ya jawo hankalin Aamilah data fito falon ƙasa neman abinci, sai Qaseem dake a d/table zaune yana karyawa shima, a guje Aamilah tay sama, Qaseem ma ya miƙe yabi bayanta. Yanda Shahudah ta rikice Mom na rirriƙeta sai abun ya basu mamaki suka shiga tambayar mom ko lafiya?. Basu samu amsa daga bakin mom ɗinba sai a takardar sakin da Shahudah ta jefar ƙasa, Qaseem yace, “K dalla malama nutsu mana anan” yanda yay maganar a tsawace yasa Shahudah nutsuwa sai dai ta maka masa harara tamkar zata makesa.
Bai kulata ba ya maida dubansa ga Mom yana kaɗa takardar, “Ita wannan ɗin kuma daga ina Mom? Wata ya sake aikowa?” mom tace, “A'a waccance dai, kasan bata saniba, shinefa ranar Alhamis datasa muka barta can taje.........” Mom ta zayyanema Qaseem komai daya faru tsakanin Jay da Shahudah a daren juma'a wato ranar alhamis, wanda shine sanadin ciwonta. Jiyay tamkar ya make Shahudah dan takaici, Aamilah kam da yake Shahudah ta faɗa mata komai sai bataji abun a saboba, ya nuna ta da yatsa yana faɗin, “Kedai wlhy daƙiƙiyace, wai ubanmiye a jikin wannan wawan Jawaad ɗin da sauran maza suka rasa har kika nace masa?”. A fusace Shahudah tace, “Sai dai idan kaine daƙiƙin, kaiɗin ubanmiye a jikin yarinyarnan da sauran mata suka rasa ka nace mata (Bilkisu take nufi) (hakan ba sabon abu bane dan babu wani girmama juna a tsakaninsu). Duka yakai mata yana faɗin, “Idan kinajin iskancinki a gidannan kibar sakkoni, inba hakaba wlhy saina ɓallaki watan Shahudah. “Ka ɓallani ɗin tunda kai ɗin ubanane, saika gayamin banza na kasa maida maka amsa da wofi, uwarwa yama sakaka cikin maganar? Bansan shishshigi”. Dukan ya sake kaimata Mom ta tare. “Wai wane irin iskancine wannan!! Taya zaku sakani tsakkiya da shirme, ku barni naji da abinda ya dameni mana!!”. Duk dakatawa sukai kowa na huci kamar wasu ƴan dambe. Daga ƙarshe Qaseem ya juya zai fita Mom ta dakatar dashi ta hanyar kamo hannunsa, ƙin juyowa yay yadai tsaya, “Kayi haƙuri, ni banason wannan saurin fushin naka Qaseem, kasandai halin rashin kunyar Shahudah a gidanan, yakamata ka cigaba da haƙuri dasu a matsayinka na babba a cikinsu, kaji”. Ajiyar zuciya ya sauke, ya kaɗa kansa kawai. Tace, “To ku zauna muyi magana, Aamilah jeki kira Salman”.
BILKEESU
Gurin ya haɗu matuƙa, bawani mugun ƙato baneba, madaidaici ne da akayisa domin masu hutawa kawai, yasha gyara da korayen ciyayi da flowers masu ƙamshi, nidai saima na zama baƙauya, dan duk zamana garin bansan da zamansa ba, koda yake inama nake zuwa, dama yawona dasu Ummie ne idan mun dawo hutu, to ƙafarmu bata taɓa zuwa nanba kuma, sai dai a zahiri na kame kaina ina tafiya cikin nutsuwa, ƙarƙashin ɗaya daga cikin ƙananun bukkokin da aka ƙawata wajen na nufa, naja kujera ɗaya cikin huɗu dake a kowacce ruffa na zauna tare da ɗora jikkata akan tebir ɗin na buɗe na ciro waya. Motsi naji a kaina, dan haka na duba wanda yazo wajen, ɗaya daga ma'aikatansu ne, ya gaisheni yana mai dire tiren hannunsa. Amsa masa nai tare da jeho masa tambaya akan kuɗin abinda ya kawo, duk da bani nace ya kawoba, tunanina tsarinsu kenan. “Karki damu Madam, an rigada an biya” ya faɗa yana barin wajen. Binsa kawai nai da kallo harya shigema ganina, mamakina shine ‘waye ya biya?’. bani da mai bani amsa, hakan yasani kauda abin a raina na duba abinda ya ajiye ɗin. Popcorn ne sai robar ice-creem da Malt ɗaya da ruwa, n
a ɗauke idona inajan guntun tsaki tare maida hankalina ga wayata na fara tafama Oga Jabeer saƙo. Bayan na tura masa naga ya wuce sai kawai na shiga yin Game batare dana kula abinda aka ajiye min ɗinba dan a ƙoshe nake.
“Hy Babie!” aka faɗa dai-dai kunnena, a tsorace na ɗago idanuna dan a bazata abin yazomin, banji motsin kowaba. Ƙyaƙyƙyawan saurayi fari tas kuma ɗan gaye ya sakarmin murmushi da ɗage gira ɗaya sama, “Sorry na tsorataki ko?”.
Janye idanuna nayi daga kansa batare dana tanka masaba ko magana. “Kin cancanta” ya faɗa yana zama kujerar dake facing ɗina. Nanma dai ƙin kulashi nayi, yaja ɗan kwalin da Popcorn ɗin ke ciki ya fara ɗiba yana afawa a bakinsa tare da lumshe ido alamar dai akwai daɗi. Janye idanuna nai daga satar kallonsa na tura wayata a jikka na miƙe zan bar masa wajen. Da sauri shima ya miƙe yazo gabana ya tsaya, baya naja kaɗan ina ɓata fuska. Yace, “ALLAH bazaki tafiba sai kin kulani”. Na dafe kaina ina lumshe idanuna irin na ka kaini bango ɗin nan......
“Please babie kice wani abu mana”.
Nabuɗe baki zanyi magana kawai naji baƙon ƙamshin turare a wajen tare da motsi, waigawa nai saboda yanda, nakejin bugun zuciyata na sauya salo. Wanda nai tunanin kuwa shine na gani. ‘Boss!’ na ambata a cikin zuciyata, duk da ya rufe fuskarsa sosai da facing cap baƙa datai masa masifar ƙyau hakan bazaisa naƙi ganesa ba, ƙamshinsa ma kawai amsatace dan bana manta ƙamshin turarensa sam, dana jisa nake shaida yazo waje. sake ja baya daga gaban gayen da shima shi yake kallo nayi.
Jawaad kam yayi tamkarma bai gansu ba, sai ƙoƙarin buɗe gwangwanin Malt.. Ɗin da aka kawoma Bily kawai yake hankalinsa kwance, sai dai fuskarsa a matuƙar ɗaure take babu alamun sassauci, ya zaro wayarsa da ga aljihu tare da gyara zamansa, ya kwantar da bayansa jikin kujerar sosai ƙafa ɗaya kan ɗaya, sai kace wani saraki, yana sanye cikin ƙananun kaya da sukai masa masifar ƙyau da fidda cikar haibarsa, sai hula hana salla inji hausawa😂, a samanta an rubuta favourite da ruwan gwal mai ƙyalƙyali, idanunsa toshe da baƙin glasess, hakan yasa babu mai fahimtar ina idanunsa suke kallo kai tsaye. A zuciyata nace, ‘glass nama Boss ƙyau matuƙa idan ya saka, bansaniba koni kaɗai ke iya ganin hakan banda sauran mutane, amm.....
“Babie!” saurayin ya ambata da ɗan ƙarfi ganin hankalin Bily baya tare da shi. Kallona na maido kansa, nace, “Ba sunana Babie ba” yay murmushi mai ƙayatarwa, “To a faɗamin sunan mana uhum”. “Bana doguwar magana da wanda bai iya sallama ba”. kansa ya dafe alamar ya fahimci kuskurensa, yace, “Sorry Assalamu alaiki”. “Wa'alaikassalam”. Na amsa masa.
Murmushi ya sake yi, yace, “Na gode da kika tunatar dani abinda na manta, hakan na sake tabbatarmin na samu abokiyar rayuwa ta gari, irin wadda ta cancanci zama uwar ƴaƴana. Sunana Kamaludden shehu Manya, matar tawa fa?”. ni dariyama yaso bani wlhy, wai matarsa, daga ganin sarkin fawa sai miya tai daɗi. kaina na girgiza masa kawai na juya zan bar wajen, amma sai yay azamar sake shan gabana, “Haba babie, naga na gyara kuskuren da yasa aka ƙi kulani tun a farko ai, koda bazaki kulani a nanba ki bani Number mana. Sonake ya barni, shiyyasa na miƙa masa hannu alamar ya bani wayarsa na saka masa. Cike da ɗoki ya ciro wayarsa a aljihu ya miƙomin, sai dai kafin na kai hannu na amsa wani hannun ya amshe wayar..............✍
ALLAH ka gafartama
iyayrnmu😭🙏🏻
[11/30/2020, 12:57 PM] HASNA✍🏻: Typing📲
ƘWAI cikin ƘAYA!!
Bilyn Abdull ce🤙🏻
BOOK TWO
Page 15
To yau page ɗin ƙwai cikin ƙaya na ƙuɗine, duk wanda ya karanta ina roƙonsa dan girman ALLAH ya biya da addu'ar ALLAH ya kawo mana iyakar tashin hankalin dake damun wasu yankuna namu na arewaci, dan ALLAH ina roƙon har ƴaƴanmu ku saka suyi wannan addu'ar a dukkanin sallolinsu biyar na wannan yinin, domin addu'ar yara abuce mai muhimmanci a garemu mubar sakaci da ita, idan baki aureba ki roƙa mana jama'ar gidanku suyi da kanninki, duk da munsan anayi dama, sai dai ina fatan wannan ta zama ta musamman domin ALLAH, dan ALLAH kar'a manta, kar'a manta, kar'a manta.
Ya rabbi ka kawo mana ƙarshen waɗanan tashin hankali, ya ALLAH ka ruɓanya rahamarka da rangwame a garemu, ya Rabbi ka yafe mana kurakuranmu, ya Rabbi kaimana maganin abinda bazamu iyaba harma da wanda zamu iya ɗin, ya rabbi ka taimaki bayinka dake cikin gararin rayuwa da hali na buƙatar agaji, ya rabbi ka kawoma muhallansu zaman lafiya, kasaka kwanciyar hankali a zukatansu suma su sami cigaba da rayuwa a yankunansu kamar kowa, ya rabbi ka kawoma ƙasarmu zaman lafiya baki ɗaya da dukkanin duniyar musulunci, ya rabbi ka bamu ikon cinye jarabawa kasa ta zama rahama a garemu duniya da lahira🙏🏻😭.
Idan kasan bazaka biyaba karka karanta, bayin ALLAH na buƙatar tallafin addu'oinmu, dan girman ALLAH karmu wofantar da lamarinsu saboda mu muna barci a gidajenmu da iyalanmu bayan munci mun ƙoshi, ba'a zahiri kawai nakeson ayiba har abaɗi ma ita mukafi buƙata😭.
Masu 6am sunyi winning, wannan shine zaizama lokacin posting ɗinmu kafin na daina fushi da kamfanin masu yellow'n tambari 🙄🙄🙄.
................Daga ni har shi kallonsa mukai. Nidai na sauke idanuna da hannuna a hankali ina haɗiyar yawu da ƙyar. Kamal yace, “Haba malam ya haka?” Jawaad bai tanka masaba, sai wayar daya daddana alamar wani abun yayi a ciki ya miƙa masa. A ƙufule Kamal ya amsa yana faɗin, “Wanan rainin wayone ai, ya zakazo ka shiga abinda bai shafeka ba?”.
Ban jira amsar da boss zai bashiba nabar wajen nidai, saboda wata muguwar harara daya makamin dan ya cire madubin idonsa.
Jawaad ya maida kallonsa ga kamal yace, “Karka damu ka kira Number dana saka maka zaka sameta”. Kamal yay ɗan shiru alamar nazari, sai kuma yay saurin taɓa hannun Jawaad dake shirin barin wajen, Jay ya juyo yana kallonsa, sai dai baice komaiba. “Sorry, dan ALLAH ko ƙanwarka ce dai?” wani munafukin murmushi Jawaad yayi tare da ɗagema kamal gira ɗaya sannan ya wani juya kansa da lumshe ido yabar wajen. Sam Kamal bai fahimci komai daga yaren na Jawaad ba, sai dai kuma ya haƙura akan zai nema waje ya zauna harsu tashi tafiya ya bisu a baya, dan shifa yaga matar aure.
Tsaye yazo ya sameni ina waya da Zuhrah, baiko kalleni ba yaja kujerar da ya fara zama ɗazun ya sake zaunawa yana maida glasess ɗinsa a ido kamar ma ya manta dani, nima ɗin dai ƙasa-ƙasa nake satar kallonsa yanda nasan bazai fahimtaba ina wayata, a ƙasan raina inata tunanin komi ya cema Kamal? Number wa kuma ya saka masa a waya? Dan nidai nasan baisan tawaba. Zuwan ɗaya daga ma'aikatan wajen ne ya sakani janye idona a kansa, umarnin kwashe kayan wajen ya basa tare da sake kawo wasu, dai-dai lokacin da muka ƙarisa wayar, sai da yabar wajen ne cikin dauriya nace masa, “Ina kwana sir”.
Shiru bai tanka minba, saima ya kalli agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunsa ya ɗauke kansa, duk a tsorace nake, gani nake zaimin faɗa akan ganina da Kamal, amma har aka sake kawo abinda ya saka ɗin baice dani komaiba.
Ni kuma har lokacin ina tsaye duk da ƙafafuna sun gaji haka na fuske abina, shiko ya buɗe sabon Popcorn ɗin da aka kawo ya hau ci yanayi yana danna waya, baifi ɗiba uku ba wata mata mai sanye da hijjab har ƙasa da niƙaf ta iso wajen, sallama tai mana, na amsa mata, shiko bangama ya motsaba har sai da taja kujerar gefensa ta zauna, sai da ta ɗage niƙaf ɗin tana gaishesa sannan na fahimci wadda muke jirace.
Batare da ya amsa mata gaisuwarta ba yace, “Kinsan irin ɓata mana lokacin da kikai?” haƙuri ta bashi. Kallona yay ya ɗauke kansa batare da yace komaiba, hakan ya sakani gyara kujera nima na zauna.
Munja tsahon lokaci tare da ita yana mata tambayoyi kala-kala, wasu ni kaina idan yayi hanjin cikina saisun kaɗa balle ita da akemawa, gaba ɗaya duk ya gama rikitata da gizagonsa, sai dai ina jinjina masa akan yanda ya samu ƙwarewa akan kutse cikin al'amuran mutum yay bincike, har kai da yakemawa ɗin ka kasa saita kanka wajen bashi amsa ta gaskiya, dan lokacin da yarinyar ta iso a take-takenta na farko banga alamun zata bada haɗin kai ba, amma yanda ya fara bi da ita sai naga tuni ta zurma tana faɗin harma wanda bai tambaya ba ɗin. Ina kuma ƙara samun ilimi na aiki nima a wajensa sosai. Lokacin da muka kammala anata kiran sallar zuhur, dan haka mukayi a cikin wajen har shima da wasu mutanen, dan akwai masallaci ƙarami da sukayi, hakan yasa wajen ya sake burgeni da ƙaramin nutsuwa. Koda muka idar tafiya tayi, nima na samu waje na zauna ina jiran ya fito nai masa sallama na wuce.
Kiran da ya shigomin a waya na ɗaga, Ummie ce, bayan mun gaisa take tambayata ina inane? Dan taje gidanmu akace na fita. Amsa na bata da cewar naje wani wajene, yanzu kuma zanje na wanke kai na wuce gidan inna Zainabu, daga haka mukai sallama akan zata sameni a wajen saloon ɗin ko gidan inna zainabu, na amsa da to na ajiye wayar. Ina ɗagowa muka haɗa ido da boss dake magana da wani da nake ƙyautata zaton sunsan junane. Janye idona nai