Showing 180001 words to 183000 words out of 261165 words

Chapter 61 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1114

shi yakeyi koda bai masaba. Tun a daren ya fara shirin komawa ƙasarsa ta haihuwa, dan dama hankalinsa bama a kwance yakeba a China'r saboda wata cuta da aketa raɗe raɗin ta ɓillo a wani yanki na ƙasar chain mai suna Corona virus, mutane duk a tsorace suke, daƙyar ya iya danne ransa yaje yayo wata ƴar sayayya da yake buƙata ya dawo hotel ɗin da yake ya kimtsa kayansa, insha ALLAH jirgin farko na gobe dashi zai tashi zuwa ƙasar Dubai cikin birin Abu-dabi, daga nan zai hau jirgin da zai sadashi ƙasarsa.
Ɗan-fir'auna ka sakamu a cakwalkwali😣🙄😏😒😠🚶🏻.
______________________________________
((°•°))((•°•))((°•°))(())(())((°•°))((•°•))((°•°))
______________________________________
Iya ƙofar ɗaki Anum ta tsaya tai min saida safe, kaina kawai na iya ɗaga mata batare da nace komaiba. Ƙofar na tura na shiga da sallama a bakina, falone madaidaici da aka zuba komai cikinsa, sai ƙamshi mai daɗi ke tashi a ciki. Na sauke kumburarrun idanuna akan boss dake kwance cikin doguwar kujera idanunsa rufe, nai masa kusan kallon mintuna biyu kafin na ƙarasa inda yake, durƙusawa nai gaban kujerar na ɗaura hannuna saman goshinsa, wani irin zafi naji zauu dan haka na rimtse idanu da sauri. Jin ya ɗaura hannunsa saman nawa na buɗe idonuna, hannunma akwai zafi shima, a rufe idanunsa suke har yanzu, “Yayanmu baka da lafiya ne?”. Baice min komaiba sai idanunsa dake jajur ya buɗe yana kallona. Hawaye naji sun cikamin idanu, yaɗan lumshe nasa idanun ya sake buɗewa a kaina da girgiza min kansa alamar kar nayi kuka. ban ankaraba naji sun silalo kawai, hannunsa ya ɗaura saman kumatuna ya shiga sharemin batare da yayi magana ba. Kusan mintuna biyar muna a haka kafin ya buɗe baki da ƙyar yace, “Kukan ya isa mana, haɗamin ruwa maiɗan zafi nayi wanka kozanji ƙarfin jikina”. Kaina na jinjina masa sannan na yunƙura na miƙe. Ƙofar dana gani a falon ya sakani tunanin itace bedroom, can na nufa kaina tsaye, koda na tura sai naga ƙaramin kicin ne, rufewa nai na nufi ɗayar ƙofar, itakam ina buɗewa nai tozali da bedroom babba. Numfashi naɗan sauke na shiga, ban wani zauna ɓata lokacin kalle-kalleba na shiga bathroom ɗin da shima ya kasance babba, komai tsaf an gyarashi, sai ƙamshin fresheners masu daɗi. Dai-daita ɗumin ruwan nayi yanda zai masa daɗi sannan na tara masa, komawa falon nayi na taimaka masa ya tashi zaune, dan da gaske bayajin ƙarfin jikinsa, amma duk da haka yamin nauyi sosai, haka dai na daure har muka isa bedroom ɗin, taimaka masa nayi ya cire kayan, ya rage daga shi sai singlet da boxer kawai, a haka na sake taimaka masa zuwa bayin. Duk yanda naso na zame na barsa yay wankan shi kaɗai bai yarda ba, yace na taimaka masa jikinsa sam babu wani ƙarfi, gashi yanajin jiri. Dole na daure nai masa yanda yakeso sannan na sake taimaka masa muka fito, har kayan barci an kawo mana dan haka na taimaka masa ya kimtsa yasha shayi da magani ya kwanta, bargo naja masa na rufesa na zauna gefen gadon ina kallonsa, shima dai idanunsa a kaina, bamu jima a hakaba barci ya kwashesa, ajiyar zuciya na sauke a hankali ina share ƙwallar da suka cikamin ido, duk wanda ya aikata al'amarin nan yacika baƙin azzalumi mai busashshiyar zuciya. Nima shayin kawai nasha, na ɗauki abincin na maida sashensu Umm-Anum sannan na dawo na shiga wankan nima. Gasa jikina nai sosai sannan na ɗauro alwala na fito, nima nai shirin barcin na haye gadon na kwanta tare da shigewa jikinsa da har yanzu yake zafi zau. Lumshe idanuna nayi ina sauraren yanda bugun zuciyarsa ke harbawa, a haka nima barci ɓarawa ya saceni.

WASHE GARI

Bayan mun tashi daga barcin da muka koma na safe wanka mukai, muna cikin tunani da zullumin kayan da zamu saka saiga sallamar Anuwar, boss ne ya amsa masa tare da zira jallabiya ya fita falon, babu jimawa sai gashi ya shigo da akwatinmu. Kallonsa nai da alamar tambaya, sai dai baice komaiba ya ɗora akwatin saman gadon tare da buɗewa ya ɗauka kayansa nima ya fiddomin nawa. “Kitashi ki shirya suna jiranmu, su Takawa ma sunzo” yay maganar cikin dasashshiyar muryarsa da tun jiya bata dawo dai-dai ba. Kaina na ɗaga masa na miƙe.
Tsaf muka fito cikin shiga ta kamala munata zabga ƙamshi, mun iske Anum a fallon su Umm-Anum zaune ita kaɗai da alama mu take jira, da girmamawa ta gaida Boss daketa faman kallonta ko ƙyafta ido bayayi. Nima muka gaisa sannan ta sanar mana duk suna falon baƙi mu ake jira.
Duk suna zaune an baje abinci kala-kala a tsakkiyar falon, yanda muka samu Umm-Anum zaune cikin kamala ya sakamu sauke ajiyar zuciyar jin daɗi muka bisu ɗai-ɗai muka gaisar.
Gaba ɗaya hankalin Jay akan Umm--Anum yake, kamar yanda itama nata hankalin na agaresu shi da Bilkisu, sai dai batace komaiba dan an bari sai anci abinci sannan ai zama akan hakan. Lafiyayyen breakfast ne da kowa ya tsinci kansa cikin jin daɗin cinsa, sai dai boss tsakura kawai yakeyi. hakama Umm-Anum bata wani ci sai kallon Jay take.
Bayan an kammala aka gyara wajen tsaf sannan kowa ya nutsu waje guda..............✍😓
wayyo idona wayyo yatsuna😢🚶🏻

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.
[1/16, 1:48 PM] HASNA✍🏻: Typing📲

ƘWAI cikin ƘAYA!!

Bilyn Abdull ce🤙🏻

BOOK TWO


Page 50
.................Shiru kakeji falon ya ɗauka bakaji motsin komai saina ajiyar zuciyoyi dana AC dake aiki. Sai da Abu-Siddiq yay doguwar addu'a kafin kowa ya sake maida hankalinsa ga takawa da yay gyaran murya alamar zai fara magana. Wata gyaran muryar ya sakeyi kafin yay sallama a garesu duk suka amsa, Cikin nutsuwa Takawa ya sake gyara zamansa.
“Alhamdulillahi ala kulli halin, duk da dai bamu da tabbacin har yanzu Umm-Anum ta gane Jawaad matsayin jininta ina ganin ya kamata na fara warware abinda mu muka sani game da ita kafin muji abinda zai fito daga nata bakin yanzun”. Jinjina kai kowa ya shigayi cikin gamsuwa da jawabinsa.
“Mun tsinci Umm-Anum a wasu shekaru da zan iya ƙiyastasu da kusan shekaru ashirin da takwas idan ban mantaba, a lokacin nazo gida daga india domin halartar bikin salla babba kamar yanda na saba a duk shekara, saukar dare nayi a ranar, dan sai kusan tara na dare ma na iso, amma kamar ko yaushe na iske sarkin mota na jiran isowata a airport ɗin. A gajiye nake matuƙa gaya dan haka bamu ɗau lokaciba muka bar airport ɗin, tafiyar mu bata wuci ta mintuna goma ba akan titi sarkin mota yaja wani wawan birki. Sosai gabana ya faɗi saboda ƙarar da aka ƙwalla mai nuna tabbacin mun bige wani, daga ni har shi fita mukai cike da tashin hankali. hakama mutane dake ɗan kai kawo a titin harsun fara taruwa a wajen. Ganin mace ce kuma cikin shiga ta kamala duk da babu lulluɓi tare da ita sai muka fara bincikar mutane ko akwai wani nata a wajen?, amma babu wani mai alaƙa da ita. Mun ɗauketa zuwa asibiti, duk da gajiyar da nake ciki bamu bar asibitinnan ba sai da muka tabbatar ta samu dukkan kulawar da ake buƙata a daren sannan muka wuce raina duk a dagule. A dalilin bige baiwar ALLAHr nan gaba ɗaya bikin sallar nan baimin daɗi ba, dan tun bayan farkowarta daga magagin ciwon bugetan da mukai sai muka fuskanci tanada taɓin hankali ma, taɓin hankali irin mai ban tashin hankali, dan duk da cikin halin ciwo da take ƙoƙarinta kawai ta gudu daga asibitin ita dai, dalilin hakan takai har sai da aka saka mata hand corps a hannu da ƙafa sannan aka samu ɗan kwanciyar hankalin ta, a hakanma fisge-fisge take ita kawai a barta ta tafi duk ta jima hannayenta ciwo da ƙarfen ankwa dana gado. Doctor ɗin shine ya faɗamin gaskiya da tabbatar mana cewar matarnan akwai wani babban al'amari tattare da ita, mizai hana mu haɗata da malaman musulinci. Wannan shawara tasa itace ta zame mana haske a kanta, sai kuwa na samu abokina Muftahu akan ya bincika min malamin da zamu kaita wajensa, shine kawai ya bani shawarar mizai hana mukaita Saudia wajensu Abu-Siddiq. Na amshi shawarsa da hannu biyu babu ɓata lokaci mukai duk wani ciku-ciku dagyar muka samu damar fita da ita zuwa nan saudia. A ganin farko dasu Abu-Sufyan sukai mata suka tabbatar mana akwai sihiri tattare da ita, dan kuwa tunda ta buɗe ido daga barcin da take dan allurar barci a kai mata tun da ga can kafin mu taho saboda gudun matsala, sai muka sameta a nutse babu wani bige-bige da takeyi sai dai alamar rashin lafiya na haukan yana tare da ita, alamun hakan na nufin can ƙasarne ba'ason ta zauna kenan ko wani abun daban da bamu da ilimi a kansa. Bayanin da mukaima Abu-Sufyan akanta ne yasa yace mubarta a wajensa na wani lokaci zasu cigaba da kula da ita. Nai masa godiya sosai bayan kwana biyu na koma india nabar Muftahu anan saudia. shima kuma bayan wani lokaci saiya koma. A koda yaushe muna magana da Abu-Sufyan ko Abu-Siddiq akanta da yanayin jikinta, sannan Muftahu nata ƙoƙarin bincike game da ahalinta acan gida, sai dai babu wani haske da muka samu game da samunsu. Bayan wani lokaci jikinta yay sauƙi sosai ta koma normal Alhmdllh, sai dai kuma ta manta komai dangane da kanta, batasan ko itaɗin wacece ba, daga ina ta fito? duk ta manta har sunanta, wannan shine ya ɗarsa tausayinta a zuciyar Abu-Sufyan yace shikam zai aureta har ALLAH ya kawo iyakar komai ta gane ahalinta. Tunda yaymin bayani sai ban musaba, dan uba nike kallonsa bawai yayan aboki kawai ba, na kuma tabbata shine kawai zai iya riƙe amanar baiwar ALLAHr da bata da kowa tunda hatta kanta da sunanta tama manta, ya bada gudunmawa sosai gameda jiyyar mahaifina shima, har kawo yanzu kuma yana badawa a dukkanin al'amurana dana zuri'ata, babu abinda zance a garesu sai addu'ar fatan gamawa da wannan rayuwar lafiya su samu sakamakon aljanna a ranar sakamako”.
Tunda Takawa ya fara magana hawaye kawai kowa ke faman sharewa, Abbu yace, “Tabbas duk abinda ya faɗa hakane, abinda kawai ya manta bai faɗaba shine ciki dake tare da ita, sun kawota da ciki kwantacce da bamusan adadin wataninsa ba, kamar yanda ya nuna, dan sai da muka dage da addu'oi da magani matuƙa sannan ya fara motsi alamar abinda ke cikin yana raye, da alama dai akwai sharrin jinnu a al'amarin kokuma wata hikimar UBANGIJI daya ɓoye game da cikin wadda zuwa yanzu munga ƙalilan daga ciki shiyyasa ya ɓuya a jikinta, tashin da cikin yayi sai yazam watanninsa ya koma baya, dan saiya koma wata uku, sai da tai wata shida sannan ta haihu Namiji, shine yaci suna Muhammad Anuwar gashi nan, bayan haihuwarsa ne mukai aure da ita ta haifi Anum kuma, ga tanan tana da shekaru ashirin da uku, daga ita dai bata sakeba har zuwa yanzun”.
Cikin rawar jiki Anuwar ke kallon Jawaad, sai kuma ya kalli Abbu ya kalli Umm-Anum da ke zaune shiru ta zabga tagumi tana hawaye, dan abubuwa da dama ne keta dawo mata cikin rai tun a daren jiya, hatta da sunanta ta manta sai a daren jiya ta tuna shi. Hannunta dake rawa ta miƙama Jay dake kallonta ko ƙyafta idanunsa bayayi, a hankali ya miƙe ƙafafunsa tamkar an dokesu ya nufota, ta riƙe hannunsa ta zaunar da shi kusa da ita tare da rungumesa ta fashe da kuka, shima Jawaad hawayen yakeyi. A take falon ya ɗauki sabon koke-koke har saida Abbu ya fara musu nasiha akan hakan sannan suka tsagaita. Anuwar ya taso shima ya zauna kusa da Ummu, kafin ya tashi ya koma jikin Jay yana sharɓar kukansa, Jawaad ya rungumesa da ƙyau yana murmushin farin cikin samun ƙanne. Tasowa itama Anum tayi tazo ta zauna ƙasa ta ɗaura kanta saman ƙafar Jawaad, ya sake murmushi da shafa kanta yana lumshe idanunsa da kai hannu ya share mata hawaye itama. Wata irin ƙaunarsu mai tsananice ke ratsa dukkan ɓargonsa da jini, ji yake a duk duniya yau babu kamarsa a cikin masu nasara, jinsa yake tamkarma su kaɗaine a cikin duniyar babu wani mahaluki mai numfashi da ya rage bayansu ɗin, wani sanyi mai sanyaya kuzari na shiga cikin tsokar jikinsa tana ratsa dukkan ɓargonsa da jijiya.
Cikin dasashshiyar murya Umm-Anum tace, “Tabbas niɗin na taɓa aure, bankuma taɓa tuna hakanba sai a daren jiya, na auri wanda yake matsayin yayana a gidanmu dukda ba iyayenmu ɗaya ba, matar babanmu ce da ya aura bayan rasuwar innarmu ce mahaifiyarsa, itama kuma mijinta ya rasune, shine iyayenmu sukai aure, suka kuma haɗemu suka riƙe tamkar tare suka haifemu, Auren soyayya mukayi da Abdul-aziz, shiɗin mutumne mai himma wajen neman nakansa, sannan mutumne mara hayaniya da damuwa da gudun ƙyale-ƙyalen duniya, mutum ne ma'abocin son noma da kiwo, mai tsananin son ƴan uwa da zuminci, shine auta a gidansu kaf, shi kaɗai kuma mama maryam ta haifa a gidan, baida wa baida ƙani dan haka yay mana gata sosai ni da ƙannena lokacin da mahaifiyarsa ta dawo aure gidanmu. Bayan aurenmu mun samu jarabawar rashin samun haihuwa na tsahon wasu shekaru harma dana abubuwan more rayuwa, kafin na fara haihuwar kuma yaran su rasu, sai daga baya harma mun fidda rai da wata haihuwar sannan ALLAH ya azurtamu da samunsa (ta nuna Jawaad) lokacin da muka samesa Abdu-aziz ya bunƙasa, dan harkokinsa na noma da kiwo sun kaisa har ƙasar turai dalilin zaman mutunci da wasu turawa da sukai aikin dam ɗin ƙauyen garinsu, abinda kawai zan iya tunawa bayan wannan game da rayuwata shine, sunana BILKEESU, sai mahaifina, sai ƙannena uku mata, Mariya, Rahmah, Wasila, sai Mama maryam, saiko shi dana bari, sai Abbansa dana tabbatar ya rasu, wannan shine kaɗai abinda zan iya tunawa game dani da rayuwata ta baya kafin gushewar komai”. Ta ƙare maganar hawaye na ziraro mata.
Jawaad da shima ke hawayen ya saka hannu ya share mata yana girgiza mata kai alamar ta bari, muryarsa a ɗashe yace, “Na godema ALLAH da yasa kika tunani Ummuna, na kwana da tsananin fargabar kar kice baki tunani ba koma baki sanni ba gaba ɗaya, da hakan ta kasance na tabbata sai dai ku binne gawata a yau Ummuna, na godema ALLAH da yasa kina raye, na godema ALLAH da ya ƙaddara sake haɗuwarmu a duniyar nan, na godema ALLAH daya jarabceni da son wadda ta silarta yau nake a jikinki Ummuna, (yay maganar yana nuna Bilkisu) na godema ALLAH daya haɗa dangantakarta da zuri'ar Takawa har nima nakai ga zuwa garesu, su ɗin shugabannine da adalcinsu yakai kowanne yanki, kowacce ƙabila, suyi fatan zamowa masu mulkinsu Ummuna, mutanen nan uku haskene babba a gareni da suka haskamin hanyata zuwa gareki”.
Share masa hawayen shima tayi tana miƙama Bilkisu dake kuka hannu alamar itama tazo, da ƙyar BILKEESU ta miƙe zuwa garesu tana haɗa hanya, Umm-Anum ta sakata a jikinta tana maijin ƙaunarta har ƙarƙashin ruhinta, “Ɗiyata ashe ƙaunar da nake miki tun ganinki na farko bata wasa bace, ALLAH yay miki albarka kinji, ALLAH ya ɗaukaka rayuwarki ya saka mata albarka ya baibaiyeki da alkairi da rahamarsa mai tarin yawa”. Gaba ɗaya falon aka amsa da amin.
Ummu dake murmushi tace, “Haka rayuwa take, ƙanƙanin abu sai yazama silar warware babba, kunga dai yanda aka ɗauki tsahon shekaru wajen addu'oi da neman ahalin Umm-Anum, amma sai gashi cikin sauƙi Wallet ta zama silar komai......” Ta shiga bama su Umm-Anum labarin komai game da haɗuwar Bilkisu da su Safah a Ladies mirror, da dagewar Safah akan saita tafi da Wallet ɗin bilkisu masarauta, har silar komawarta hannunsu...
Sosai al'ajabi ya kama su Umm-Anum sukaita sake jinjina al'amarin da girmama hukuncin UBANGIJI mai shirya yanda yaso a lokacin da yaso ga wanda yaso cikin hikimarsa.
Duk godiya suka shiga sake jera ma su takawa da addu'oin fatan alkairi, dasu Abbu ma kansu suma har saida takawa da Abbu sukace ya isa haka sannan. Akwai sauran magana sosai a bakin Takawa dan ya fahimci akwai wasu abubuwan da yawa dake a ɓoye wanda Umm-Anum bata iya tunawa ba, shima kansa Jawaad dai akwai magana a bakinsa musamman game da haukar mahaifiyarsa da abubuwa ma da dama, sai dai yayi shiru ya barma ransa, so yake ya samu nutsuwar zama sake nazari da fashin baƙi akan komai, su kuma keɓe da matarsa su tattauna kozai ƙara samun haske daga gareta dan kowa da irin baiwarsa. To yanda duk tunaninsu yake hakama na Abbu da Abu-Siddiq yake, su kuma sunason su keɓe ne da Jawaad sumasa tambayoyi game da family ɗinsa, dan sunji Umm-Anum bata tambayi komaiba akan komai ma, alamomi da yawa kuma sun nuna akwai abinda ke binne, bazasu fahimci hakanba sai sun sami sanin ainahin tarihin komai tun daga tushe sannan.

Kiran sallar zuhur ne ya tashesu daga wannan zama, matan suka shige cikin gida sukuma mazan suka fita massallaci.
Bayan an idar suka dawo akaci abincin rana, Jawaad dai tsakura yay tayi yanzun ma, baici na kirki ba, hakama Bilkisu, Umm-Anum da take jinta sakayau yau tanata lura dasu sai dai batace komaiba har aka kammala aka tashi.
Takawa, Abbu, Abu-Siddiq suka fice masaukin su takawa dan su masa rakkiya yaje ya huta. Bilkisu kuma Umm-Anum ta tsareta ta kwanta barci, acewarta yanayin bily ya nuna barci takeji, kasa mata musu tayi ta kwanta, itako ta ɗaura kan bily saman cinyarta tana shafa mata kai har barcin mai nauyi kuwa yay awan gaba da Bilkisun, Anum dake ta tsegumi Umm-Anum tabar yayinta itama tazo ta raɓa bayan Bilkisun ta kwanta da yake a ɗakin Umm-Anum ɗinne. Ummu da Aunty Mahfuzah kuwa sun tafi can gidan aunty Mahfuzah ɗin suma.
Anuwar da Jawaad kuwa suna can sashen baƙi suma, Anuwar ya tsare Jay akan ya bashi labarin Abban su, sai shagwaɓa yake masa. Jawaad dake kwance cikin doguwar kujera yay murmushi idanunsa akan Anuwar dake zaune a ƙasan darduma jikin kujerar da yake a kwance hannunsu sarƙe dana juna. Cikin muryarsa dake a sanyaye yace, “Dear nima bansan Abba ba sosai, abubuwan da zan iya tunawa game da shi basu da yawa, dan banfi shekara bakwai ba ya rasu, sai dai kakanrmu mama maryam bata gusaba sai da ta maidamin tarihinsa tamkar karatu, dan sai da na haddacesa a cikin kaina tsaf, daga ni har kai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login