Showing 240001 words to 243000 words out of 261165 words
Chapter 81 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete
ta baya, da inda ta fito, da ahalinta.
Kuka kowa ya keyi hawaye shaɓe-shaɓe, duk da nariga nasan duk wannan tunda mu an faɗa mana sanda mukaje saudia nima saida nai kukan. Ummah babba ma ta labarta mata yanda abubuwa suka faru bayan barinta gida. irin neman da akaita mata da tashin hankalin da Mama maryam da Alhaji babba da Rahmah dasu kansu suka shiga, harma da ƴan uwan mahaifin boss. Rasuwar Mama Maryam da Auran Rahma.
Sai dai bayan wasu shekaru kuma sai kowa ya haƙura aka cigaba da binta da addu'a dansu tunaninsu koma ta rasune. Itama taci kuka, muma muka tayata.
Har kusan ƙarfe biyu na dare bamu kwanta ba. dan da ƙyar Anuwar dasu Aunty Haneefa suka lallaɓa Alhaji babba ya yarda zai kwanta ya huta daboda jikinsa, gashi Doctor yace ya samu isashen barci.
Muma duk tashi mukai mukaje muka kwanta kowa zuciya babu daɗi. cikin amincin ALLAH ni dai inama kwanciya barci mai nauyi yay awan gaba dani.
___________________________
Tafida family house
______________________
Lokacin da labari ya isa kunnen mama Atika akan ganin Umm-Anum sai tahau surutai tamkar wadda ta zare, tun su Uncle Uwaisu na ɗaukal al'amarin matsayin ruɗani harya koma basu tsoro. Dan sosai neman fita take daga hayyacinta.
Sake ruguntsumewa gidan yayi da tashin hankali, babu mai iya fahimtar yaren wani. Batun yunwa kuwa ai an manta da sunanta a wannan gida yau, dolefa aka danƙarama Mama Atika allurar barci ta ɓingire, har dare basa tare da nutsuwarsu, barema da Qaseem suka iso gidan Mom da itama take a jangwaɓe, ta tada hankalintane akan a maidata gida batason kwanan asibitin shiyyasa Qaseem ya kawota nan dan can gidan zamansa tashin hankali kawai zai ƙara mata.
Itama dai Mom maganar dawowar Umm-Anum ta nema maidata ruwa, dan ruɗani ta sake komawa ciki fiye da tunani, al'amarin sai ya sake bama su Uncle Sulaiman da basu san komaiba mamaki, a ganinsu dawowar Bilkisu cikin ƙoshin lafiya abin ayi murnane bawai tashin hankaliba, amma yarasa miyasa abin ke neman zama wani iri ga wasu daga cikin ahalin nasu?. Bashi da mai bashi amsa, dan haka yay gum da bakinsa kawai.
Saboda meeting ɗin da za'ayi shima dai Qaseem baro musu gidan yayi, sai da ya fara zuwa gidansa ya watsa ruwa yay sallar isha'i sannan ya nufi station batare da yay tunanin neman abinciba ma, dan shi sam a yinin yau bama abinciba ko ruwa sai ƙishirwa ta kaisa maƙura yake nemansa yasha.
______________
STATION
____________
Ɗakin meeting ɗin yay tsitt, tsumayen shigiwar oga kwata-kwata (Director General) daya iso garin a yammacin yau kawai sukeyi, kusan mintuna goma sai gashi ya fito tare da wasu manyansu. Duk miƙewa sukai tsaye domin girmamawa a garesu, suka ƙame tare da sara musu.
Shima murtani ya maida musu sannan ya zauna da nuna musu alamar suma su zauna. Zama duk su Jay sukayi, bawai matsayin rank ɗin Jawaad ya kai ai zaman wannan meeting ɗin da shi bane, kawai ƙwazo da suka nuna akan aikin ya kai shi ga shiga wannan tawagar, dan gaba ɗaya gurin manyansune nacan ƙololuwa, sai su Sir Ahmad dasu Qaseem, sai dai shi Qaseem ma gaba ɗaya yama kasa shigowa ɗakin meeting ɗin, koda yazo sai ya maƙale a office ɗinsa ransa duk a dagule.
An buɗe taron da addu'a a ɓangarorin addinan biyu, kafin D.G ya nuna kujerar data rage babu kowa cikin alamar son sanin wanda ya kamata ya zaunata. Sir Ahmad ne yay masa bayanin Qaseem, an ɗaga waya za'a kirasa Jawaad ya miƙe tsaye yana ɗaga hannu, damar magana Oga kwata-kwata ya bashi. “Sir ina neman alfarma”. “Muna saurarrnka”. “Sir Qaseem yana cikin tsananin ruɗani, inaga zamansa tare damu a wajen nan kamar zai ƙara tunzura tunaninsane ga wani abu daban, a ɗazun har mummunan hukunci yaso yankema kansa. mizai hana ai masa alfarmar barinsa kawai”.
Tsit ɗakin yay alamar jiran amsa daga bakin Oga. Sai da yaja kusan mintuna biyu kafin ya jinjina kansa yana gyara abin maganar gabansa. “Maganar Cpt gaskiyane, kasancewar abinda zamu tattauna ɗin yanada nasaba da mahaifinsa akwai damuwa, kuma shi jami'inmu ne daya taka rawar gani a wannan hukumar, ya cancanci koda sau ɗayane a nuna masa hallacin hakan”. Duk kawuna suka jinjina, inda wasu kuma a cikinsu hakan bai musu daɗi ba, dan su kam basuƙi ama kori Qaseem ɗinba daga hukumar gaba ɗaya.
Jawaad ne ya fara bayani akan matakan da sukabi dangane da kamasu akan dukanin bayanan sirri da suka samu, sai abubuwan da suka samo a gidan kama daga mutane zuwa wasu abubuwan daban, sai kuma adadin su Dad da suka kasance su 22 idan aka haɗa da shugabarsu data kasance mace. Sai ayyukansu da muƙaman wasunsu a cikin siyasa da kasuwancin wasunsu.
Bayan ya kammala ya miƙa takardar da dukkan bayanan suke ciki ga Sir Ahmad, wanda shi kuma ya miƙama D.G.
Amsa yay ya duba na tsahon wasu mintuna kafin ya ɗago yana kallonsu. “To duk kunji bayanai ga jami'inmu, mi zaku iya cewa ku?”. Hannu wani ya ɗaga aka bashi iznin magana.
“Sir ina ganin kawai mu miƙasu kotu mana, dan dukkanin bayanan da Jay ya bayar an samu mutanen nan dasu a zahiri kuma duniya duk ta gani, a ganina bama buƙatar wasu hujjoji kuma”.
Jin jina kai D.G ya shigayi, amma baice komaiba. Wani ya sake ɗaga hannu shima aka bashi izini.
“Ni kuma Sir a ganina kamar kaisu kotu ba mafita bace, dan za'a iya amfani da siyasa wajen kuɓutar dasu, ƴan ƙasa kuma su cigaba da kallonmu da laifin daba namuba, kawai mu riƙesu a wajenmu har iyakar rayuwarsu”. Nanma dai kawuna kawai suketa jinjinawa, wanima ya sake miƙewa shima ya faɗi ra'ayinsa. Haka sukaita faɗar ra'ayinsu ta kowanne fanni, inda maganganun su duk suna akan turbar gaskiya da kuma muhimmanci mai ƙarfi, shi dai Jay baice komaiba ganin duk manyansane keta magana, saida kowa ya lafa sannan D.G ya kallesa da kulawa. “Bakace komaiba Jawaad, bayan kuma kaine jami'in dayasan sirrin case ɗin nan fiye da kowa a cikinmu”.
Iska Jay ya zuƙa ya fesar, kansa a ƙasa yace, “Sir ai kune iyayenmu, zaku hango abinda mu sam bamu iya hangosa ba, duk hukuncin da kuka yanke muma zai zama dai-dai a garemu”.
“Hakane Jawaad, amma kuma da kuke ƙasanmu zaku iya bada shawara mai amfani da zatafi wadda mu zamu kawo, domin ku a yanzu kuke ganiyar ƙuruciyarku da kaifin tunani, sannan kuke shiga lungu da saƙo akan kowacce matsala, kune kuke ganin komai dangane da al'umma, kune kuke fita farautar masu laifi cikin kowanne irin runtsi da ƙalubale, mu muna office zaune, idan kun bada shawara ai bazai zama kuskureba”.
“Hakane Sir. To nidai idan har shawarata bata sauka a layiba ina ganin kaisu kotun shine babbar mafita, amma kafin hakan ya dace a faɗaɗa bincike dangane da masana'antunsu, da wajejen ayyukansu, akwai business da wasu a cikinsu ke gudanarwa a cikin ƙasa da wajen ƙasa, mizai hana musan mi suke fitarwa da shigowa ne? Masu ayyuka a gwamnati musan wane irin aiki suke gudanarwa a ofisoshinsu suma, daga haka mu basu damar neman lauyoyi muma mu samu namu ƙwararren lauyan. Hujjata anan itace dukansu waɗanan mutanen akwai zargin fyaɗe akansu wanda sam bama asan adadinsaba, sun lalata yara da yawa da mummunan aikinsu, ciki harda ƴaƴan ƴan uwansu. Duk yanda muke tunanin kare kanmu ga al'umma bazamu fitaba sai anyi komai akan idanunsu.........”
“Tayaya za'ai komai akan idanunsu?, fili kakeso a ɗiba a tara duka talakawa ai zaman kotun a gabansu komi?”. Wani ya faɗa aɗan fusace yana kallon Jay ɗin.
Murmushi Jawaad yay yana mai girgiza kansa, “Ba haka nake nufiba yallaɓai, abinda yasa na kawo wannan maganar ta al'ummah saboda idanma muna gudun manyan ƙasar zasubi ta ƙarƙashin ƙasa wajen saye alƙalan da zasu gudanar da wannan shari'a muryoyin ƴan ƙasa zai daƙile hakan, sannan suma manyan zasu tsorata domin inba waɗan nan jama'ar ai babu su, musaman idan mukai dubi da mafi rinjaye a cikinsu wannan shine hawa na farko da sukayi. sunason komawa na biyu, bazasu so sunansu ya ɓaci ba ai kodan mulkin da suka ɗanɗana suke kuma ƙulafuci da ƙwaɗayin komawa”.
Sir Ahmad dake murmushi ya kalli D.G, “Sir Jay yazo da maganar hankali, dominfa wannan faɗan sam ba namu baneba, faɗane tsakanin al'ummar ƙasa da waɗanan mutane, idan kuma har mukai tunanin shiga ciki wajen kare mutuncinsu to lallai zamu fuskanci ƙalubale harma a ringa zargin muma da namu dalilin mara ƙyau a ƙasa, amma idan min fidda komai ga al'umma muka kuma nuna musu suma sunada ƙarfin iko akai su kansu alƙalan zasu shiga hankalinsu sosai, sannan ƴan siyasa bazasuyi wani tasiriba wajen yaɗa farfagandar da suka saba. Kaga mun jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, mun kuma ƙarama hukumarmu kima da daraja a duniya baki ɗayama ba wanan ƙasar kawai ba”.
“Wannan gaskiyane wlhy” wani ya faɗa cike da goyon baya akan zancen su Jawaad da Sir Ahmad.
D.G yace, “Okay, inaga to zamu tsaya a wannan matsayar, zuwa gobe sai mu yanke hukuncin daya dace ko ya kukace?”.
Duk kawuna suka jinjina masa cike da gamsuwa. Daga haka taron ya tashi. lokacin ƙarfe kusan uku na dare.
Jay baibar station ɗinba saida yaje office ɗin Qaseem ya fiddosa, shine da kansa ya kaisa har gida sannan ya wuce gidan Alhaji babba, ya iske duk sunyi barci, dan haka ya wuce ɗakin da yake tunanin Bilkisu na a ciki. Kwance ya sameta ita kaɗai a saman gado ta cure waje ɗaya kamar maijin sanyi, yay ɗan murmushi da cire kayansa sannan ya raɓa ta gefenta ya kwanta tare da turata cikin jikinsa. A take ta shaƙi ƙamshinsa, sai ta gyara kwanciya kawai ta lafe tana mai sauke tagwayen ajiyar zuciya kamar wata mage.
Murmushi ya sake saki mai sanyi, ya sumbaci kanta yana sauke tasa ajiyar zuciyar a jere.
________________
WASHE GARI
____________________
Washe gari ta kama Lahadi, tunda safe Jay ya samu kira daga Gimbiya Munaya akan takawa da kansa zai yoma su Abbu rakkiya gidan Alhaji babba.
Hakan ba ƙaramin mamaki ya bama Jawaad ba, dan haka ya sanarma dasu Alhaji babba halin da ake ciki, su kansu sunyi mamaki, to amma idan akai dubi da matsayin su Abbun a wajen Takawa hakan ba komai bane face girmamawa.
★★★★★
A family house ɗin su Jawaad ma sun wayi gari da shirin zuwa gidan Alhaji babba wajen Umm-Anum kamar yanda Uncle Sulaiman ya bada shawara shi da wasu a cikin sauran ƴan uwa.
★★★★★
Ɓangaren su Firdausi ma tun da farar safiya suka kammala nasu shirin na nufowa birni, sai dai su saɓanin ƴan masaurata da familyn Jay ne, su gidan Jawaad sukai shirin zuwa tamkar yanda Muktar mijin Firdausi yay ƙoƙarin sama musu adireshi a daran jiya ta dalilin wani abokinsa ɗan sanda.
★★★★★★
Maman Amina ma sun tashi ne da shirin nufar gidan Alhaji Babba kamar yanda Jay ya kirasu ya sanar musu suje dan Mama Safara'u ta gana da Umm-Anum.............✍
“Hummmmmmm!!!!! Wannan shine ake kira da ga wuri ga waina, to masu karatu, idanfa bakusan gariba to ku saurari daka, dan yanzu zamusan ma'anar ƘWAI CIKIN ƘAYA. su wanen ƘAYOYIN? su wanene ƘWAYAYEN?. Amsoshinku na'a page 61, saiku shirya kuma domin yin gangamin tafiya gidan ALHAJI BABBA mu gani wace wainar za'a toya shinnnnnnn?🚴🏼🚶🏻😢.
Masoya ZAFAFA 2021 fa sunata gagarumin shiri da yafi rukunin farko dana biyu da suka kawo muku a baya, mun shirya shiri na musamman domin ƙayatar daku da nishaɗantar daku da daɗaɗan labaranmu a wannan karonma, naga baƙwa motsawa😪, bayan kuma gagarumin shirin da muketa shiri dominku🤗.
ALLAH ka gafartama iyayenmu🙏🏻😭.[2/17, 9:22 AM] HASNA: Bilyn Abdull 📚:
Page 61
...............Cike da mamaki matuƙa Aamilah ke kallon Shahudah dake zaune gaban mirror'n ɗakin Mama Atika tana tsara kwalliya, taci jan wando da farar top ƙal mai ƙyau da akaima hoton zuciya a gaba, gefe kuma madaidaiciyar jikka ce mai azabar ƙyau da aka ƙawata da zanen furrani na zuciya.....
“Sister! Wai mi kikeyi hakane?”.
Ɗago manyan idanunta tai da sukasha kwalli ta kalli Aamilah, sake maida fuskarta tai ga mirror tana dai-daita janbakinta da yay mata ɗas a baki. “Harma tambayata kike Aamilah? Kin manta yau Valentine day?. A duk irin wannan ranar kema shaidace ai ina shiryama BB wani abu, sannan muɗan fita yawo koda dakene idan shi yace bai zuwa. Tunda matsalolin nan suka fara kema kinsan hakan bata kasanceba, to amma yanda aka maida auren nan namu ai wannan ranar ni tazomin a dai-dai, koba komai zan sake tabbatar masa yana nan daram a raina, a shirye nake kuma nai waje da waccan jakar baƙauya daga garesa da baƙin asirinta”. Cike da takaici ƙarara a saman fuskar Aamilah ta girgiza kai ƙwalla na cika mata idanu, “Sister yanzu nan duk tashin hankalin da muke a ciki keta soyayya ma kikeyi? Wlhy bantaɓa sanin akwai kunyaba a duniya irin jiya, hatta da ƴan gidannan kunyar haɗa ido nake da wasu dalilin halin da su Dad suka jefa kansu da mu, amma ke tun a daren jiya nagama kin ware kamar komai bai faru ba, ga Mom can kwance yanzu haka zazzaɓi ne ma a jikinta, wlhy badan su Uncle Sulaiman sun matsa fitar nanba nasan babu inda zataje. Duk shirmen Salman jikinsa a sanyaye yake tun jiya ya kasa fita ko ina yana tare da Mom, amma ke........”
Shahudah da kema Aamilah wani banzan kallo tunda ta fara maganar taja gajeren tsaki tana ɗaukar sosan hoda da ƙara gyara fuskarta. “Aamilah kenan, harma kece kike da bakin faɗamin ban damu ba? A kaf ɗinku nafi kowa shan kunya a al'amarinnan, dannice kullum mai posting pictures ɗin Dad a kowanne shafina, kinsan kuma yanda nake da ɗunbin fans. sannan a dukanin shafukansa hotunana yafi na kowa yawa a cikinku, wlhy tsabar baƙinciki gaba ɗaya shafukana na rufesu, ke a jiya saida na karya duka layikan na fasa wayar sannan na samu nutsuwa. Bayan wannan mikikeso nayi? Na rasa Dad, nakuma rasa BB a karo na biyu? Impossible dear, dolene na tsira da ɗaya, domin ina ƙaunar mijina. Nasan duk bayanin dazan miki ba fahinta zakiyiba tunda ba auren kikayi ba, dan haka karki bari a jimu a gidan mutane”.
Baki a matuƙar hangame Aamilah da Mama Atika dake a kwance tana duk saurarensu suke kallon Shahudah data jefa Cingam a baki tana ƙara gyara zaman gashin dokin dake a kanta da siririn mayafin data yafa. Juyawa tai tana kallonsu kanta tsaye, “Kumuje. dan nifa namafi son mu fara isa dan naga Maman BB sosai naga kuma kalar tarbar da zatamin. Sannan naɗan faracin uban yarinyarcan kafin zuwa dare na tare”.
Uffan babu wanda yace mata a cikinsu, Aamilah ta taimakama mama Atika ta tashi zaune dan dama tuni ta shirya, badan tasoba zata bisu, sai dai kawai waɗanda suka bada shawarar zuwa gidan Alhaji babba a yau sunfi su da basa son zuwa rinjaye, batason kuma tace bazataje ba a fassara al'amarin da wani abu daban, ko aga kamar tana baƙin ciki da dawowar Bilkisu ne.
Sun iske mafi yawan jama'ar gidan suma duk sun fito harabar gidan, fitowarsu ta saka kowa ya zubama Shahudah idanu, dan taci wani uban dogon takalmine bayan ɗamewa datai cikin wando da riga. Uncle Sulaiman ya kalleta cikin ɓacin rai zaiyi magana Uncle Sadiq yay saurin riƙe masa hannu yana girgiza masa kai alamar karya ce mata komai, dan yasan yin maganar kan iya janyo wata fitina daban musamman ga mama Atika da tun jiya taketa datsama mutane magana a gidan tamkar ba uwace a garesu ba.
Haɗiye maganarsa Uncle Sulaiman yayi, badan yaso hakanba. A sauranma babu wanda yay yunƙurin cewa komai, sai dai sunata kallon Shahudah data toshe da baƙin eyeglasess ga cingam a baki tanata tauna hankalinta a kwance.
______________
ZAFAFA 2021
___________
Masoya naku taurarinfa sun sake dawowa da sabon salo a 2021.
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO
TEAM#ZAFAFABIYAR🔥
__________________
Gidan Alhaji Babba
_____________________
Kasancewar mai martaba ya sanar da wuri zasuzo saboda yanada zaman meeting da su manyan jihar zasuyi game da abinda ya faru akan su Dad, tun daga sallar asuba bamu koma barci ba, aunty Batool da Boss suka fita suka haɗo kayayyakin da za'a buƙata na haɗa abinci, kasancewar munada yawa dandanan muka shiga hada-hadar haɗa breakfast. Koma nace dai sunayi, dan nikam bama wani aikin kirki nakeba dan sam banajin daɗin jikina. Wasu na gyaran gida wasu na haɗa abinci haka akai aikin, zuwa takwas na safe komai yayi tsaf kowa nata ƙoƙarin yin wanka. Da yake boss ya ɗakko mana kaya ni da shi tun fitar da sukai da aunty Batool sai banji damuwa da tunanin mizan sakaba, nai shirina tsaf cikin doguwar rigar lass ɗin daya ɗakko mini, sai dai bayan fauda babu abinda na ƙara, turarema kaɗan na saka na yafa mayafi na fito falo inda nake ɗanjin maganganun su Anum.
Zamana baifi da mintuna uku ba mukaji ƙarar buɗe gate, miƙewa duk mukayi, Boss da Anuwar ma suka fito tare da Alhaji babba