Showing 75001 words to 78000 words out of 261165 words

Chapter 26 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1128

yanzu”.
     Miƙewa Jawaad yay cike da takun ƙasaita ya ƙarasa gaban Qaseem sunama juna kalon kallo tamkar wasu zakuna, baki ya taɓe yana binsa da wani banzan kallo, cikin kakkausan furuci yace, “Gurɓataccen tunani kenan Qaseem, domin kuwa wannan shine abinda bazai taɓa faruwaba koda a cikin mafarki, kayi wani tunanin amma ba wannanba” Yaƙare maganar da ɗan buga kafaɗar Qaseem ya raɓashi ya fice daga falon.

       Babu wanda ya iya yunƙurin hana Jawaad ɗin fita har Alhaji baba, dan a ganinsu garama ya tafi kar abin ya kuma ƙwaɓewa tsakaninsa da Qaseem. Asibiti Jawaad ya nufa domin ganin yaya su Bilkisu suka tashi. Saida ya tsaya ya sai abubuwa a hanya dukda yasan za'a kai abinci daga gidan Ummah, mintuna kaɗan ya shigo asibitin, da Nabeelah yaci karo ta fito sayama Ummah kati, ta amshi kayan hannunsa tana masa sannu da zuwa da gaishesa. Bai amsaba saboda waya yakeyi, hannu kawai ya ɗaga mata yay gaba, tabi bayansa tana gulmarsa a zuciya batare daya saniba, hardasu kwaikwayon tafiyarsa.
          A ƙofar ɗakin ya tsaya yayma Nabeelah nuni akan ta shiga domin sanar dasu. Da “to” ta amsa, shikuma ya cigaba da wayarsa a nutse, baifi minti biyu da shigartaba tafito tace ya shigo.............✍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.

   
        
        
[12/10/2020, 1:40 PM] HASNA✍🏻: Billyn Abdul:
Page 25

.............Na daɗe banji irin wannan matsanancin bugun zuciyarba idan na samu kusanci dashi.
     Tunda Nabeelah ta sanar da shigowarsa duk sai na nema nutsuwata na rasa, farfesun da Ummah ma ta tsareni naci sai naji ya fitarmin a rai, ƙasa-ƙasa nake kallon ƙofar ta gefen ido harya shigo da sallama, Sanye yake cikin ƙananun kayan nasa na fama, sai dai sun masa ƙyau kamar ko yaushe. Da hannu yake amsama kowa sannun da yake masa saboda waya yakeyi. Ummah ta tura masa kujerar da take zaune a kai ita kuma ta koma kusa dani a bakin gado.
            Gaba ɗaya na kasa cigaba da shan farfesun har sai da Ummah taimin magana, “Saifa kin cinye abincin nan tas dota, garama ki dage kafin nasa a riƙeminke namiki ɗura”. Murmushi nai ina satar kallon boss da ƙamshin turarensa ya addabi hancinanmu, kasancewar turaren maza yafi na mata ƙarfi duk sai ya danne namu. A bazata muka haɗa ido, saurin janye nawa nayi dan banyi tunanin kallona yakeba. Farfesun na cigaba da tsakura kaɗan-kaɗan, har yanzu inajin idanunsa na yawo a kaina ko kunyar su Ummah bayaji.
     Kusan mintuna biyar ya ɗauka kafin ya ajiye wayar yana faɗin, “Am sorry Ummana nazo ina waya”. Murmushi Ummah tai masa, tace, “Babu komai Son”. Guntun murmushi yayi yana mai risinar da kansa ya gaisheta ita da Mama, kafin ya ɗorama mama da godiya. Mama tace, “Babu komai Jawaad, ai yima kaine, Bilkisu ta cancanci ai mata abindama yafi haka dan yarinyar kirkice mai tarbiyya, mu saidai muce ALLAH ya sanya alkairi a wannan al'amari ya kuma baku zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba”.
     Gaba ɗaya ban fahimci kalaman mamaba, dan dama Nabeelah ta shigo ɗazu tana cemin amaryar yayansu, kallonsa naɗan sata sai naga ya amsa da “Amin” akan laɓɓansa. Tunanin ko da aunty Shahudah aka ɗaura masa aurene yasa naɗanji nutsuwa. Ganin ya gama gaisawa da aunty Batool nima nace, “Ina kwana sir”.
         Amsamin yay da “Lafiya, ya jikin naki?”. “Alhmdllh naji sauƙi”. Bai sake cemin komaiba ya juya sukai magana da Ummah, sai naga sun miƙe sun fita. Numfashi na sauke a hankali ina rumtse idona, dan fitar tasa yasa naji kamar an saukemin kaya. Babu abinda nake buƙata a halin yanzu kamar ƙarin bayani akan abinda ya faru jiya tsakanina da ƴan gidanmu, banga kowa a cikinsu ba kuma yau tunda na farka, sannan kuma miya faru har aunty Shahudah ta nemi jimin ciwo su aunty Aamilah kuma sukaimin wannan bugun da gashi ya kaini da kwana a asibiti?........
         Ring ɗin wayatane da Ummie ta kawo ɗazun ya katsemin tunani, Nabeelah dake kusa da wayar ta miƙomin tana ƴar dariya, “Matar Yayanmu waye kuma masarauta?”. Wayar na amsa dan karta tsinke batare dana bata amsaba, bayan mun gaisa daga can Amaturrahman ke tambayata a ɗakin da nake?. Mamaki ne ya kamani sosai, ta yaya akai sukasan banda lafiya to? Kodai jiya sunzo ana wannan rikicin da bansan tshensa ba? Tunanin ƙila Ummie ce ta sanar musu ya sakani amsa mata da cewar bara na turo a shigo dasu. Da ga haka muka ajiye wayar, Nabeelah na kalla cikin marairaicewa nace, “Sorry dear, dan ALLAH ki shigo da baƙi wai suna waje”. Cikin dariya tace, “Karki damu matar yayanmu, girmankine ai”. Kasa haƙuri nayi nace mata, “Wai nikam wannan sunan daga ina haka?”. Sosai ta kwashe da dariya tana nufar hanyar fita da faɗin, “A wannan ba hurumina bane, yayanmu zai baki bayani”.
      Aunty Batool ce tace, “Fitsararriya ALLAH yasa ya jiki dai”. “Ba amin ba” ta faɗa tana ficewa fuska a kumbure.
      Murmushi mukai ni da mama, danni taɓarar Nabeelah dariya take bani, na lura gatane kawai yay mata yawa, ga uwa ga uba ga yayu ga dangi gata auta kuma. Mintuna baifi goma ba sai ga Nabeelah ta shigo dasu Amaturrahman bakinta fal magana da ganin jama'ar kamar jinin sarauta, dan tare suke da hadimai mata uku tare da wani dattijo, sai hadimai maza suma guda biyu.
    Tun a waje Jawaad da Ummah dake zaune suna magana akan yanda za'ai da bilkisu kafin lokacin tarewar sukaga Nabeelah dasu Amaturrahman, cike da mamaki suka bisu da kallo, ganin da gaske ɗakin da bily take suka shiga yasasu tasowa suka biyo bayansu.
      A waje suka iske hadiman su duka biyar, basuce dasu komaiba suka sh

iga.
       Amaturrahman na zaune a bakin gadon da babu kowa a kai tare da aunty Batool, Marwah tsaye kusa da mama dake a ɗayar farar kujerar ta wancan gadon. sai dattijon kuma a  kujerar da Jawaad ya tashi, , sai Safah data ɗane gadon kusa da bily tana taɓa kumburin fuskarta kamar zatai kuka, Bilkisu dai murmushi take mata, dan har cikin ranta takejin ƙaunar yarinyar da wannan shine haɗuwarsu ta biyu.
     Jawaad ya ƙaraso suka gaisa da dattijon cikin mutuntawa, fuskar dattijo da murmushi yace, “Ina fatan kaine mijin nata?”.
     Wani irin muguwar bugawa ƙirjina yayi, babu shiri na zubama boss ido dan naji amsar da zai bada, saiko naji yace, “Eh nine ranka ya daɗe”. Idanun mamaki na zaro dan nama manta akwai mutane a ɗakin, wata ƴar harara naga ya zubamin ya ɗauke kansa, yayinda shi kuma dattijon ke faɗin yazo zasuyi magana a waje. Binsa yay suka fita. Cikin dawo dani hankalina Safah tace, “Aunty B mijinki mai ƙyau, zaki yarda na zauna gidanku?”. Dariya duk ƴan ɗakin sukayi, bandani dana kasa koda motsi, sai ɗan kaɗama Safah kai nayi kaɗan dan nikaɗai nasan a kalar ruɗanin da nake ciki. Buɗe ƙofar da aka sakeyine yasa duk muka kalli can, shine ya leƙo yay kiran mama da Ummah.
      Suna fita naji hawaye sun silalomin, da sauri nai ƙoƙarin gogewa dan banason kowa ya gani, sai dai na makaro dan Safah tarigada ta gani, da sauri tace, “Aunty B miyasaki kuka?”. “Ba kuka nakeba Safah, abune ya shigarmin ido” nai maganar da sauri. Tace, “Aunty B wai kema kina ɗaukata ƴar yarinyane? Nafasan kuka”. Tsawa Amaturrahman ta daka mata da faɗin, “Safah wai miye haka? Ke duk inda kika zauna saikin takurama mutane ne?........” Aunty Batool ce tai saurin katse Amaturrahman ɗin da faɗin, “Minene abin takura anan ɗin? Ai kulawama take bata”. 
        Marwah datun ɗazun bayan gaisuwa bata sake maganaba ta harari Safah ɗin da faɗin, “Aunty bakin yarinyarnan ne kamar bai gasuba”. Itama Safah ɗin harar Marwah tayi, tace, “Halan tarene ba'a gasa manaba, manya na magana kina wani tsoma musu baki mtsoww!”. Ƙwafa Marwah tai ta ɗauke kanta bata sake maganaba. Nai murmushi da riƙo hanun Safah nace, “A'a banda faɗa to, Marwah kema zo”. Babu musu ta bufoni, na kamo hanunta na zauna da ita ɗayan ɓangaren itama suka sakani tsakkiya.

              A waje kuwa dattijo ya miƙama Jawaad takarda yana faɗin, “Saƙone daga Sarauniyar gagara badau, tace na miƙa wannan takardar ga mijin Bilkisu Adam makaho, ka karanta sannan ka bada amsar da za'a koma mata dashi”. Cike da mamaki Jawaad ya amshi takardar dake nannaɗe an ɗaureta da zare ruwan gwal, yace, “Sarauniyar gagara badau kuma? Ni kaina ya sake kullewa”. Dattijo dai baice komaiba sai murmushi da yayi. Jawaad ya buɗe takarda tareda karantawa a fili domin Ummah da Mama suji abinda ta ƙunsa.
       Saida yakai har ƙarshe sannan suka shiga kallon-kallo, dan tayi bayanine a taƙaice gameda sanin Bilkisu da sukai har zuwan su Amaturrahman jiya da sukai tsozali da ruguntsumin da ya faru, a ƙarshe ta nuna buƙatar ganin shi Jawaad a yau zuwa masarauta domin suyi magana.
     Jawaad ya kasa cewa komai, sai kallon inda dattijon ya koma gefe danya basu damar tattaunawa yayi, mamace ta katsesa da faɗin, “Jawaad nikam ina ganin kaje ɗin sai kaji minene takeson ji ɗin”. A sanyaye Jawaad yace, “Shikenan Mama zanje, bara na kira Alhaji babba shima na sanar masa”. “Hakan yayi” cewar mama, Ummah dai tama kasa cewa komai dan mamaki, saida mama tace, “Hajiya Mariya bakice komaiba”. Murmushi Ummah tayi, tace, “Abinne aini ya ɗauremin kai, daga tsintar Cards sai kusanci har irin haka ya shigo? Lamarin manyan nanne baka musu gaggawa, amma nima nagoyi bayan maganarki akan yajeɗin sai muji mitakeson su tattauna ɗin”. shidai Jawaad gefe ya koma yayma Alhaji baba bayani ta waya, shi kansa saida ya jinjina abin a ransa, kafin yace to Jawaad ɗin ya jirasa gasunan zuwa asibitin shi dasu Dad zasu duba Bilkisu.
      Ciki Ummah da mama suka koma akabar Jawaad tare da dattijo anan waje suna tsumayen zuwansu Alhaji baba.

★★★★★★★

              Kasancewar su Alhaji baba a hanya suke lokacin da Jay ya kira sai gasu babu jimawa sun iso, gais

uwa sukai da dattijon da babu wanda yasan daga ina yake sai Alhaji baba, da ido yayma Jawaad nuni dasu jirashi. Jawaad ya ɗaga kansa alamar amsawa. Shikuma yabi bayansu Uncle Sulaiman ciki domin duba Bilkisu.
     Dole su Ummah suka fito waje suka bama su Alhaji baba ɗakin dan yamusu kaɗan, Safah da Marwah kaɗai aka bari tare da Bilkisu daketa faman gaishesu kanta a duƙe, dan bata yarda ta kalli kowaba sai da Dad yake matsawa kusa da ita ya ɗago fuskarta yana duba kumburin daya fara sauka da jera mata kalamun ban haƙuri tamkar zai ari baki sannan ne ta ɗago tana ɗan murmushi. “Dan ALLAH Dad kabar damuwa, wlhy ni kawai na ɗauki hakan matsayin ƙaddara da kuskure kawai, kuma nama yafe musu”. Babu wanda bily bata birgeba da kalamanta, wata irin faɗuwar gabace ta riski Alhaji baba lokacin da yay tozali da fuskar Bilkisu, ya kafeta da ido ko ƙyaftawa bayayi, dukda kuwa a kumbure take kaɗan ta gefen haggu saboda duka hakan bai hanashi hango wani abu tattare da itaba. Sam yama daina fahimtar sauran maganar data biyo baya tsakanin Bily dasu Dad, haka kawai ya tafi wani bahagon tunani da shi kansa yasan akwai kuskure a cikinsa. Saurin ture abin yay a ransa suka fito, saida ya kuma waiwayawa ya kalli Bilkisu da batasan yanayiba sannan ya fice.
         Dad wajen likita ya nufa dan yaji yaya ake ciki? Su Uncle Sulaiman kuma suka fita domin tafiya gida, a wajen su Jawaad suka bar Alhaji baba shima.
       Takardar Jay ya bama Alhaji baba, bayan ya karanta ya kalli dattijon, “Ƙanina zance ko ɗana yaushene akesan ganin nasa?”. Dattijo yay murmuahi da faɗin, “Baba yanzuma zamu iya tafiya, dan zanbar yaran anan muje mu dawo”. Kallon Jay baba yayi, yace, “Shikenan kabisa Muhammad”. Jawaad ya kaɗa kansa da faɗin, “To baba, amma zan koma gida na canja kaya tukunna”. Alhaji baba yace, “Ato ai maganinku kenan, ƙiri-ƙiri kun ajiye suturar mutunci kun biyema ta yahudu, saboda irin haka muke muku faɗa akan kuna tunawa da naku suturar kuma, dan sune kayan da zakuje gaban ko wanene batare da kunji nauyin hakanba”. Shidai Jawaad baice komaiba, sai dattijon masarautane keta murmushi da faɗin, “Wannan gaskiyane baba”.

★★★★★★

               Sosai nake a cikin ruɗani da neman mai min ƙarin bayani akan wannan rikiɗaɗɗen al'amari, ina Yah Qaseem ɗina ya shiga da har ake jinginani matsayin matar boss?, shin wai mike faruwa hakane ni bilkisu? Mizaisa aitamin magana a curkuɗe?, a rasa maimin bayanin dazan fahimta. Koda su Oga Hafiz ma sukazo dubani harda matansu, matan sai faman yimin addu'ar fatan alkairi suke da faɗin, wai boss ya dace da matar da suka dace da juna, hakama da Ummie ta dawo tare da ƴan gidansu Momynta da Dady sunata min addu'ar ALLAH yasa hakan shine mafi alkairi, musamman ma Daddyn Ummie danaga tsantsar farin cikin hakan a garesa har suka tafi. Amina ma da Yayansu sunzo sunyi nasu kalar farin cikin, hakama Ummah ƙarama da naji suna faɗi da yaranta da tazo, sai murna suke da kasancewata wai matar ɗan uwansu. ‘Oh ALLAH! wannn wane irin ruɗanine haka?; Ina ƴan gidanmu suke? Dad kawai na gani, amma ko Yah Qaseem ban ganiba, shin ina ya shigane??. Haka naita juya wannan tunanin a raina, yawan jama'a da keta shiga da fici ya hanani sakat ɗin dazan samu na tambaya. A gefe kuma inajin daɗin ganin nima ashe mai mutanece? Ashe inada gatan dazan kwanta ciwo har mutane irin haka suyita tururuwar dubani?. ban sake ganin boss ba har sai bayan sallar zuhur.

★★★★★★

 
              A ɓangaren Jawaad kam kamar yanda ya roƙa alfarma ga dattijo saida suka biya ta gida ya shiga ya sauya kayansa da ɗanyar shadda fara tas da tasha ɗinkin zamani, yaukam hardasu hularsa zannah ainahin nutsatstsiyar saƙar barnawa ta asali sai ƙyalli take, duk wanda ya gansa yaga sabon ango dukda bai shiga daga cikiba😂, shi kansa dattijon tunda Jawaad yafito daga gate ɗin gidan kasa ɗauke ido yay daga kallonsa, a fili ya furta ‘Masha ALLAH ’. Drivern dake jan motarma bai iya ɗauke idanunsaba har Jawaad ya shigo.
                    Sun isa katafariyar masarauta mai daɗaɗɗen tarihi da gininta na ɗaya daga cikin manyan gine-ginen da ake lissafasu a sahun farko na yankin masarau

tun afirika baki ɗaya saboda ƙawatuwarsa da gini mai nagarta data samu, gashi a koda yaushe cikin sake fidda masa wasu tsare-tsaren akeyi masu matuƙar sake ƙawatata. Wannan shine zuwa na biyu da Jawaad yayi cikinta, dan sun taɓa zuwa gaisuwar salla wa sarki Sameer tare da tawagar Gwamna a shekaru uku kenan da suka shuɗe. Sai dai a wannan karon sosai yaga sabbin tsare-tsare da tarin cigaban da yafi na wancan lokacin, bayi sai zubewa suke suna gaisuwa a garesu saboda wanda suke tare, shi kansa Jawaad ɗin kallon wani jinin sarauta suke masa saboda kama yake dasu ta siffofi da dama.
       Jawaad mutumne shi mai nutsuwa da aji, sanan yanada tsari, bai damu da abinda babu ruwansaba komai ƙawarsa da abubuwan kallon cikinsa, wannan halin nasa na yima abu kallon ko in kula yasa sam bai zama ya rikice wajen kalle-jalleba a masarautar dukda ta cancanci a tsaya ƙare mata kallo harda son yin hotunama a cikinta. Tafiyarsa yake kai tsaye tamkar ko yaushe a kuma ko ina ya tainci kansa, bajinta, nutsuwa, da tarin ƙasaita kawai zaka hanga a takun nasa, waɗanda basu da fahimta akan halayyarsa harma zasu iya haɗawa da Izza da girman kai, sai dai kuma sam ba haka baneba, tun asali haka ALLAH yayisa tamkar wani jinin mulki wajen girmama nutsuwa a dukkanin al'amuransa koda akwai ruɗarwa a cikinsu kuwa.
           An saukesa a katafaren falo mai cike da abubuwan ƙawa da birgewa, cikin mintuna ƙalilan aka cika masa gabansa da kayan ciye-ciye da har yake tsogumi a ransa wai ‘Kamar wani mai cikin zani’ (😂kujifa daga abun arziƙi. Lol🤣)
           Bai taɓa komaiba bayan ruwa a kayan da aka jibge masa, dan shi ba ko ina yake sakin jiki yaci abuba (Yau naga mai irin halin babana a iya fulako😍, ALLAH ya gafarta maka baba😥🙏🏻). Cikin nutsuwa yake ɗanbin falon da kallo da jinjina daular dake ciki tamkar babu talaka mai buƙatar abinci da rigar sawa da kuɗin magani a duniya, yaɗan taɓe baki yana gyara zamansa, sam shi fariyya bata birgesa, dukda kasancewarsa mutum mai tarin dukiya bai taɓa sha'awar yin abinda ya fice hankaliba a hidimar rayuwarsa, dai-dai da motar hawansa guda biyuce kacal a duniya, hakama suturar sakawarsa akwai adadin da yake ajiyewa, ya gwammace duk sanda zai ɗinka wasu kayan ko ya saya to ya fidda tsoffin ya bada kafin ya ajiye wasu, baya sha'awar tsube sutura a drawer harya mance randa ya sake maimaita wata.........
       Tunaninsane ya katse saboda sallamar da akayi a ƙofar falon, ya amsa yana gyara zama da tsumewa cike da kame kai. Hadimai mata guda biyune suka shigo, cikin girmama suka gaidashi kafin su sanar masa zai iya tasowa gimbiya ta fito.
     Kansa kawai ya iya jinjina musu, ya miƙe tare da jefa wayarsa cikin aljihu yabi bayansu. Ƙaramin falone madaidaici, sai daifa ya haɗu harma ya gaji da haɗuwar, Hamshaƙiyar mace mai cike da tarin kamala da kwarjini da bazata gaza shekaru arba'in da biyar ba a duniya tana zaune, sai ƙamshi da walwali take cikin alƙyabbar da kallo ɗaya zakai mata kasan an sayeta da kuɗaɗe masu daraja. Gimbiya Munaya Awwal fharok kenan, sarauniyar gagara badau mai lokaci da amfani da damarta tana damawa yanda ya kamata, matar sarki Sameer saifudden Abubakar adalin sarki mai mulkin dake tafiya da koyarwar addinin islama da zamani, cikakken sarki mai iko da ƙasaita, adali mai tarin ilimin addini dana zamani, wanda yasha gwagwarmayar rayuwa tunkan rayuwar tagama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login