Showing 120001 words to 123000 words out of 261165 words
Chapter 41 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete
ɗaukeki, ki nutsu ki kwantarmin da hankalinki ki fahimci dukkan abinda akeson ki fahimta kinji, kinga lokaci ya ƙure sosai, inason kidawo ƙasarnan da cikakken sunanki BILKEESU MAI GADON ZINARI ba Bilkisu kawai ba kinji”. Cike da jin nauyinta nace, “Insha ALLAHU Ummu zanyi duk yanda kikeso”. “Yauwa ƴar albarka ALLAH ya bada sa'a kinji, jibi su Amaturrahman zasu taho su saboda makaranta, ranar litinin su Safah zasu koma hutu”. Kamar zanyi kuka nace, “Wayyo Ummu ni kaɗai za'a bari anan kenan?”. Murmushi tayi har ina jiyo sautinsa, tace, “Ohni Munaya, anya kuwa randa zan miƙaki gidan miji baza'a sha daruba? Karki damu itama Anum ɗinta zakuyi sa'anni, nasan zata ɗauke miki kewarsu, kuma kedama zaki maida hankali ga abinda za'ai miki ai baƙya buƙatarsu Amaturrahman kusa dake, koma sun zauna na ganin juna zakuyiba, inason suzo domin shirye-shiye, ki basu duka numbers ɗin ƙawayenki karki manta”. Godiya nai mata mukai sallama.
Kamar yanda ta umarceni haka na shirya dukkan abinda yake nawa, duk ji nake babu daɗi, banso ace batare zamu koma dasu Safah ba, to amma yaya zanyi tunda haka Ummu ta tsara.
Atare muka fito cikin shiga ta kamala, Marwah jaye da ɗan ƙaramin akwatina. Gida baifi huɗu bane a tsakaninsu, dan haka tafiyar mintuna ƙalilan muka iso gidan, Aunty Mahfuzah tai knocking haɗaɗɗiyar ƙofar falon, babu jimawa akazo aka buɗe mana, wani irin tsammm naji jikina ya bada saboda cin karo da fuskar budurwar jiya. Ta rungume Aunty Mahfuzah tana magana cikin harshen larabci, kafin ta saketa ta rungume Amaturrahman da Meenal cikin tsalle irin na nayi kewarku, sai dariya suke da faɗin yanda sukai missing ɗin junansu. Ta sake rungume su Safah suma kafin ta juyi gareni, idanu taɗan waro tana nunani da faɗin, “Lah kece?” murmushi nai mata kawai dan nikaɗai nasan mi nakeji, rungumeni tayi nima, sannan muka ƙarasa falon daya gama jin kayan more rayuwa, ga sanyin AC da wani ƙamshi mai kashe zuciya, tuni ɗan gumin da mukai harya tsane, labarin haɗuwarmu ta jiya taketa bamasu Amaturrahman saboda tambayar da sukai na ina muka san juna?.
Fitowar matar gidan ya sakasu Safah miƙewa gaba ɗayansu harsu Amaturrahman sukai kanta suka rungume, ba kowa bace face matar jiya data taimakeni, bayan sun zauna ta gaisa da aunty Mahfuzah cikin salon gaisuwar larabawa, nima gaidata nai kamar yanda na iya a nawa al'adar da tarbiyyar, kallon mamaki tai min dan da'alama sai yanzune ta lura dani ma, da turanci take tambayata wai dama tare muke dasu Safah?. Amaturrahman ce ta bata amsar da take buƙata harma da ƙara mata wadda bata tambayaba. Murmushi taita saki da ƙaremin kallon da kowa yaketa mamakinsa, tana ta maimaita sunana tamkar karatu a bakinta, bansaniba daɗi yaymatane kokuwa yaya oho, dan nasan suna Bilkisu dai sunane sananne da zaka iya jinsa a kowacce duniyar musulmai balle tace yaune ta fara jinsa sabo.
Ranar dai anan muka yini, har yamma su Amaturrahman basu koma can gidanba, danni dai an tabbatarmin da nazo kenan bazan koma canba, acewartama a daren zata kaini can makarantar da Ummu ta faɗamin. Banga saurayin nanba sai yamma lis ya shigo sanye da farar jallabiya sol da mayafi irin wanda larabawa kansa akai su saka baƙin abunnan a sama tamkar gammo, fara'ar da bangansa da itaba jiya sai gata yau a fuskarsa yanamasu Amaturrahman magana da kulawa kamar yanda suma suke masa, shima dai sai da ya nuna mamakin sake ganin nawa anan, su Amaturrahman da basa hutawa sukai masa bayani dai-dai fahimtarsa, shima dai murmushin yayta saki kafin ya nufi ɗakinsa wai zaiyi wanka.
Ban tashi shiga damuwaba sai da su Amaturrahman zasu koma gidan aunty Mahfuzah su barni anan, hakan kuma na
nufin munyi sallama kenan dasu, sai naji ƙwalla ta cikamin idanu, sabo kenan turken wawa. Suma kansu na lura basuso hakanba, amma sai suketa dariyar ƙaramin ƙwarin gwiwa da tsokana. Haka mukai musu rakkiya har gidan sannan muka sake dawowa ni da Anwar da Anum mai shegen surutu, yanayin rawan kanta sai yakemin kamanceceniya da Nabeelah, gata da saurin magana saina nutsu sosai nake fahimtar magana idan tayi, dama dai maganar tamu sai da turanci. A falo muka sake zama, cikin son fidda abinda kecin raina na tambayi Anum da Anuwar da naga shima ya saki jiki dani yanzu kosun taɓa zuwa ƙasarmu?. Anuwar ne kaɗai yace ya taɓa zuwa shima sau ɗaya tare dasu Abdur-rahman, sunzo hajji wata shekara zasu koma ya bisu sukaje tare, satinsa biyu acan ya dawo daga nan bai sake komawaba har yanzun, amma yanada burin sake zuwa saboda ƙasar tai masa daɗi sosai.
Murmushin jin daɗi nayi sai dai a ƙasan raina ina mamakin to Mamansu fa? Ita bata taɓa kaisu wajen nata danginba kenan kokuwa?, da ƙyar na ture tunanin a raina muka cigaba da hira har sanda Umm-Anum ta fito cikin shiri, sanin inda zamuje ya saka duk muka miƙe, tana gaba muna biye da ita har inda Anuwar ya ajiye motar da zamu fita. Ni da ita baya muka shiga, Anuwar da Anum na gaba, dukda darene garin zirga-zirga aketayi tamkar rana, gashi ko'ina ƙwanyar da wuta abin birgewa.
Mun iso wani haɗaɗɗen gini babba da nake ƙyautata zaton makarantarce, Anuwar yay fakin duk muka fito, jin kamar ana kallona yasa na ɗago, Anuwar na kama idanunsa tsaye a kaina ƙyam, saida gabana ya faɗin dan wlhy sai naga tamkar Boss, murmushi yaymin. ɗauke kaina nai batare dana maida masa murtani ba, Umm-Anum dana fahimci tana kallonmu ta hararesa da kama hannuna mukai gaba. Ina jiyo dariyarsa shi da Anum, sai dai banajin mi suke faɗa cikin harshen larabci. Gaskiya ina sake jinjina wannan tsananin kama a cikin raina, kai gaskiya inason sanin wani abu dangane da mutanen nan, wannan kamar ta wuce kama kawai, anya kuwa babu wata alaƙa tsakanin...........
Shigarmu wajenne ya katsemin tunanina, Bansan yanda zan fasalta muku haɗuwar wannan makarantaba da tsarinta, na bama kowa dama ya ƙiyasta a cikin ransa kawai, dan idan nace zan lissafo komai shafin yau da gobe duk anan zamu ƙare. Tuni na zama baƙauya wajen kallon abubuwan birgewa, to lallai da ace munada irin waɗanan makarantun da mace-macen aure ya ragu muma a yankunanmu, da ansamu sauƙin rikin aurarraki a gidajenmu. Sashe na musamman aka buɗe mana mai madaidaicin falo guda da ɗakuna biyu a ciki.
Fuskar Umm-Anum ɗauke da murmushi ta kalleni, “Ɗiyata anan zaki zauna, dan da kaina zan miki aikinnan saboda ƙurewar lokaci, ga mamanki ɗinan sotake ta ganki tamkar zinare”. Murmushi nai mata kaina a ƙasa dan haka kawai nakejin nauyinta, nai mata godiya tare da addu'ar fatan alkairi. Batace komaiba sai murmushinta dake kasheni taketa sakarmin.
Ɗaya daga cikin ɗakunan muka shiga, kayayyakine ajiye da ban fahimci kona mineneba, ta umarceni dana cire kayana gaba ɗaya na shiga wani madaidaicin kwami dake cike da ruwa da bazamu kirashi normal ruwa ba, ita kuma ta fita. Dukkanin yanda ta umarceni nayi haka nayi babu musu, inayi ina ɗan waige-waige tamkar mai tsoron wani ya shigo, saida na cire komaina kafin na fara saka ƙafa cikin kwamin, ajiyar zuciya na sauke a hankali saboda ɗan ɗumi-ɗumin ruwan mai warware gajiyar jiki, na ida saka ɗayar ƙafar sannan na shige gaba ɗayana, sihirtaccen ƙamshin da ruwan keyine ya sakani lumshe idanu ina karanto addu'ar godiya ga ALLAH da ni'imominsa masu yalwata ta fuskoki da dama ga ɗan adam. Sai da nai kusan mintuna uku da zama sannan ta shigo da sallama, ta canja kayanta da wata doguwar riga mai kama da leda, hannayenta sanye da safar hannu ta leda itama, murmushi taimin ta tako inda nake. Ɗan kwalina daban cireba ta zame daga kaina, ta warware gashina da Alhmdllh yanzu ya cika sosai kuma yanada tsayi gwargwado saboda kulawar da naita bashi bisa koyarwar su Ummie tun muna boarding, wani ɗumi mai daɗi naji ya ratsa kan nawa, hakan yasani kallon madubin dake gabana da nake iya hango kaina da ita kanta.
Tace, “A cikin ruwannan zaki kwana, babu abinda zai sameki insha ALLAH karkiji tsoro, ruwane mai ɗauke da sirrika kala-kala da duk macen da aka gyara dasu dolene mijinta yasan ta isa mace, sirrikane na ƙamshi masu daraja a jikin ƴa mace, ƙa'idar makarantarmu watanni ukune domin mace ta samu damar koyon abubuwa masu yawa, ba sirrin gyaran jiki bane kawai mace tafi buƙata a rayuwar aure ɗiyata, zakiga wata macen komai ta iya ta kuma ƙware, amma idan batasan yanda zataima miji maganaba kawai sai ya rusa mata komai, dan wani namijin shi abinda ke ƙololuwar birgesa ga mace shine iya magana, wani kuma a kallo kawai zaki gama dashi, wani tafiya, wani girki, wani ƙamshi, wani shagwaɓa, wani kwalliya, wani kwanciya. Karki sakama ranki cewa tarayya da miji a gado shine kawai farin cikin aure ko shikaɗaine auren, hakan kuskurene, wani namijin ƙanƙanin abun da kika raina shike sakashi farin ciki. Karkiyi tunanin gyara kanki yana nufin kin mallaki namiji ya zama naki ke kaɗaine, macen data isa mace bata shakkar zama da kishiya ɗiyata, dan wani lokacin zama da kishiya nasake bayyana darajar macene a wajen mijinta. Karkuma kiyi tunanin babu wata mace data isa raɓar mijinki dan yana sonki ko kin iya komai, wani namijin badan baya sonki yake miki kishiyaba ko yake budurwa, a'a halayyar san mace fiye da ɗaya a jinin maza yake, ko bazasu ƙara aureba saisun kalla. kizama mai gyara aurenki ta kowanne ɓangare, idan nace kowane ɓangare ina nufin kowanne fanni hatta da ƴan uwansa da duk abinda ya shafesa. Inason ki cire komai a cikin ranki ki nutsu ki bani dukkanin hankalinki a kwanakinan goma sha biyu da zamuyi tare, sonake komai na cikinsa ya zama tamkar rubutu bisa dutse a cikin ƙwaƙwalwarki, ki ɗaukeni tamkar mahaifiyarki, kuma ƙawarki aminiya wadda zaki iya magana kowacce iri da ita batare da kinji kunya ba, inhar kika riƙe duk abinda zaki koya a kwanakinan ina mai tabbatar miki bazaki taɓa goguwa a zuciyat mijinki ba koda zai auri mata uku ku zama huɗu bayan ke”.
Idona a risine na ɗaga mata kai alamar to, inajiyo sautun murmushinta itama. Abu ta fara shafamin a fuska tana cigaba da min magana cikin nutsuwa, sosai kunya ta lulluɓeni, dan abubuwane masu matuƙar nauyi a gareni take faɗa a buɗe, ta haɗe fuska a yanzu babu wasa tattare da ita ko kaɗan. Saida ta gama tsaf sannan ta fita suka sake dawowa da wata mata. Matar ta nunamin da faɗin, “zata zauna dake anan, ni zan koma gida sai da safe idan ALLAH ya kaimu zan dawo”. Kaina na jinjina mata dan ta hanani magana tunda ta shafamin abin fuskarnan.
Duk yanda zan baku labarin abinda ya gudana a kwanakinan da wahala ku iya fahimtata, abubuwan dana koya kam ba'a magana, sam Umm-Anum bata wasa dani idan akazo ɓangaren abinda zan iya jin kunyarta balle naga fuskar yin sakaci da abinda ake koyamin, tsaye take kaina ɗari bisa ɗari, komai buɗemin shi take babu hijjabi, aduk lokacin da takemin bayani aka abinda yafi ƙarfin kaina tamke fuska take tamau babu wasa, kai jama'a hatta da salon tafiya ba'a barniba sai da aka koyan, komai a tsare yake. Matar da take bari ta kwana dani kasa haƙuri tayi ranar dai take tambayata wai kodai ni ƴar uwar Umm-Anum ce? Dan ita yanda take ganin tanamin ya ninka yanda takema ɗalibanta fiye da zato. An kawoni ɗaki na musamman, sannan komai ba'a sakani cikin ɗalibai ni kaɗai ake koyamashi a nutse, daɗin daɗawa da kanta take min komai bata yadda kowa yayminba sai abubuwan da ba'a rasaba, dan takance kowa a rayuwa da irin basirar da ALLAH yay masa, abinda suma sauran malaman makarantar suke koyamin zai amfanar dani ta fannoni da dama. Murmushi nayi nidai bance komaiba, dan nikaɗai nasan mi nakeji game da matar nan, ita kanta lokuta da dama nakan kamata ta shagala da kallona, kallo maiban mamaki, kallo irin na shagala da zurfi ason tunano wani abu, idan tai irin wannan zurfin kuma zakaga daga ƙarshe ta dafe kanta tamkar zata fita cikin hayyacinta. Akwai randa naga kallon har yaso yimin yawa, sannan ni kaina yanda takemin ɗin nasan ba kamar yanda takema kowa baneba, tana sakin jiki dani fiye da hasashen mai hasashe. Akwai randa tazo tana koyamin
girki sai muke ɗan hira kaɗan-kaɗan, cikin dabara nake tambayarta ko zasuje ƙasarmu nan kusa?. Shiru tai bata bani amsaba, na kasa daurewa dai na sake mata tambayar cike da ladabi. Yanda ta juyo ta kalleni fuska a haɗe saida naso firgita. Kaina na duƙar ƙasa ina faɗin, “Kiyi haƙuri dan ALLAH Ummu, bansan tambayar zata ɓata ranki ba”. Sautin murmushinta na jiyo, hakan yasa na ɗan ɗago na kalleta, ta ajiye cokalin hannunta tazo ta kama hannayena, murya a sanyaye tace, “Ɗiyata ba laifi kikayiminba, ƙasar takuma ni ban taɓa zuwantaba ai, duk amintakar dakika gani tsakanina da ƙanwata Gimbiya Munaya ban taɓa ziyartarta ba, sai dai ita idan tazo nan mu haɗu, duk lokacin danai yunƙurin zuwa nakan tsinci kainane a wani mummunan hali da baida fassara”. Tana gama faɗa ta saki hannuna ta juyamin baya, aikin da mukeyi ta cigaba dayi batare da ta sake min maganarba.
Ajiyar zuciya na ɗan sauke hawaye na ziraromin, haka kawai yanda tayi maganar sai naji abun daban, to amma ai Ummu ta sanarmin itaɗin ƴar ƙasarmu ce, sanadin neman magani ya kawota nan hartai aure, itakuma gashi yanzun tace bama ta taɓa zuwa canba, anya kuwa babu wani sirrin dake ɓoye?.......
Ajiyar zuciya na sauke da saurin kallonta jin ta taɓanu, tace, “Kinama fahimtar abinda nakeyi kuwa?”. Da sauri na ɗaga mata kai alamar eh na tattara hankalina gareta baki ɗaya.
____________________________
A ɓangaren Jawaad ma dai shirye-shirye sun kankama, an gama gyaran gida tsaf, ya canja kamanni gaba ɗaya tamkar bashiba, amarya kawai yake jira ta shigo cikinsa. Gaba ɗaya a tsakaninan a busy yake matuƙa, ga aiki ga shirye-shiryen biki dasu Jabeer ketayi naban mamaki, dan gayya suke ta gaske da gayya tamkar wannan shine auren farko da Jawaad ɗin zaiyi. Shidai ya zuba musu idone kawai yana kallon ikon ALLAH, dan dayay magana ca sukai babu ruwansa, kawai dai yama shirya dan bai isa cewa bazaije wajen abinda suke shiryawanba ehe. Bai sake musu maganarba kuwa ya cigaba da nasa harkokin, maganar kayan da za'a saka a gidan kuwa gimbiya Munaya tace Takawa yace zaiyi komai, kayan kicin kuwa itace zatayi. Da yay mata maganar lefe tace masa ya dakata, zasu nema Dady suyi magana, sai ana saura kwana biyu tarewar za'a kaisu can gidan Dad ɗin dan sune sukafi cancanta da amsar lefen, koyayane zasu bashi matsayinsa na uba kodan ɗawainiyar da yay da Bilkisun. Jawaad baice komaiba shi dai sai ALLAH ya kaimu.
A yau tunda safe Su Amaturrahman suka shirya yima Mami (Munubiya) rakkiya gidan kamar yanda Gimbiya da Takawa suka buƙata, zataje su haɗu da kamfanin da zasu shirya gidan. bayan sun duba saisu zaɓa mata kalar data dace a tsara komai yanda ya dace..............✍
Bara dai na baku hakanan, inata ƙoƙarin typing ɗin bayan tafiyar baƙi amma kiraye-kirayen waya ya hanani nutsuwar yi da yawa, takaima harna daina ɗaga wayoyin mutane wlhy🤦🏻😑😓.
[12/25/2020, 6:15 PM] HASNA✍🏻: Billyn Abdul:
BARKA DA JUMA'A
Page 37
..................Sosai su Amaturrahman ke santin gidan Jawaad na A.Y Street, badan yafi kowane gidaba, bakuma dan an cikasa da ƙawa ba, ginine dai tamkar kowanne gini da kowa yasani, sai dai yanda akai tsarin gyaran sai ya kuma fiddo da ƙyawun gidan fiye da yanda yake a da, (masu karatu karku manta wannan shine gidan da aka haifa Jawaad, a cikinsa iyayensa suka rayu, dan shine gidannan da turawannan suka bama Abba Abdul-aziz, shine kuma sanadin wannan arziƙi daya tsolema mutane ido). Sai da suka shiga ko'ina da ina dan babu komai cikinsa sai ƙamshin sabon fenti.
Suna tsaka da dubawa Jay ya iso gidan, zaune yake a bayan motar sai Sadiq sabon drivern sa dake tuƙi cikin nutsuwa, dan shima dai baida matsala, amma hakan bai hana Jay tuna Gimba ba a kowacce daƙiƙa ta rayuwarsa, yasan gimba bazai mantu a zuciyarsa ba, dan yawuce duk tunanin mai hasashe a zuciyar tasa. Yauma kamar kullum yana cikin gayunsa da ƙyamshi, sai dai ya ɗan rame, hakan yasakashi yin wani fayau dashi, (bamu saniba azumin da aka shane kokuma ɗokin amaryarne. lol😂).
waya yakeyi, hakan yasa har Sadiq ya fito ya buɗe masa bai fitoba, sai da yaja kusan mintuna huɗu sannan ya fito bayan ya ajiye wayar, Safah data dage sai anzo da ita da gudu tayo kansa, fuskarsa ɗauke da murmushi harta iso garesa, hannunsa ta kama tana gaishesa. Shidai kallonta yake kawai, dan sosai ƙiriniyarta ke bashi mamaki, ko gajiya batayi, girma take amma abun tamkar ƙaruwar mata yakeyi. (Hhhhh tunda Jinin Munaya na yawo a jikin Safah ai kaga abinda yafi hakama, sarki Sameer ne zai baka labari dalla-dalla😂🤐). Cikin ɗoki tace, “Yayanmu gidanka kaida aunty B ya haɗu sosai, nima harna zaɓi ɗakina dan kasanfa nan zan dawo. Murmushi yay mata mai sanyi ya jinjina mata kai amma baice komaiba.
Sosai mamaki ya kama Jay lokacin da suka shiga ciki shi da Safah yay arba da Munubiya, shi tunaninsa Gimbiyace da kanta, itama ɗindai kallon mamaki take masan sai dai ita bamusan kona minene ba. Su Amaturrahman ne suka katse tunaninsa da gaisuwar da suke masa, ya amsa musu da kulawa kafin shima ya gaida Munubiya cikin girmamawa. Kasa haƙuri yay dai yace, “Ummu da kanki? Su Amaturrahman ma aisun isa basai ke kinzoba”. Munubiya tai murmushinta mai kama dana Munaya, kafin ta bashi amsa Safah tace, “Lah Yayanmu bafa Ummu bace, wannan Mami ce sweetheart ɗin Ummu”. Cikin rashin fahimta yake kallon Safah amma baice komaiba. Amaturrahman tace, “Yayanmu ai Ummu ƴan biyune, Mami itace hassanarta”. Ɗan waro idanu Jay yayi waje