Showing 99001 words to 102000 words out of 261165 words
Chapter 34 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete
Zama yay a gefen gadon kusa da cikin bilkisu tare da ajiye robar ruwan a ƙasa batare da ya shafa mataba ya faɗa tunani. Abinda ya faru a jeji ɗazun, kalaman baba ƙaura, kalaman abokan ɗan fir'auna, ainahin abinda Gimba ya gani har yazo ya faɗa masa a randa aka shirya juya ɗaurin auren Qaseem da bilkisu zuwa Azeema da Qaseem bilkisu da ɗan fir'auna, Accident ɗin ɗan-fir'auna, mafarkinsa, sai abinda ya gani yanzu wanda ya firgita bily. Ya shiga saƙa waɗanan abubuwan dake gogayya da juna daki-daki a muhalli guda. Yay murmushi mai ciwo saboda amsar data zo masa a zuciya lokaci ɗaya. Cikin zafin nama ya miƙe, Ranƙwafawa yay kan bilkisu ya shafa mata ruwan daya dumtso a hannu, a take ta kawo numfashi mai ƙarfi.
A hankali na buɗe idanuna, sai kawai a bazata naci karo da fuskar boss dake ranƙwafe kaina daf da tawa, dan har inajin saukar numfashinsa akan tawa fuskar, gabana ya faɗi, nai saurin fara waige-waige danson kauda fuskata. Saukar tattausan tafin hannunsa naji saman fuskar ya sake juyo dani garesa. Duk yanda naso janye idanuna da suka shige cikin nasa na kasa, kallon ido cikin ido mukema juna karon farko, wani irin abu mai wuyar fassara ke fitowa daga ƙwayoyin idanunsa masu girma da sirkin jaa suna shiga cikin nawa, atake naji tsigar jikina na tashi, ƙofofin gashina na buɗewa gashin na miƙewa, jinina dukya tsinke lokaci guda yana wani irin gudu a cikin jijiyoyi, sai kawai na saki kuka a hankali.
Jawaad da har yanzu idanunsa ke kafe a cikin na bilkisu yaɗan murza babban yatsansa daga jikin hancinta har zuwa ƙasan idonta ya kwashe hawayen dake fitowar ya maida yatsan baya jikin ƴan uwansa, dan har yanzun tafin hannunsa na tallafe da kuncinta na haggu. Ahankali ya furta, “Tabbas ƙaddararki da tawa a haɗe take Miemaa, zan bada ƙarfina da lokacina wajen binciko abinda ya ƙullemu ƙarƙashin inuwa ɗaya insha ALLAH”. Yana gama faɗar hakan ya saka ɗayan hannunma a gefen kumatuna na haggu ya ɗauke duk hawayen dake zuba a idanuna guda biyu, sannan yaja baya tare da miƙewa tsaye yabar wajen.
Lumshe idanuna nai a hankali kalamansa namin kaikawo tsakanin zuciya da ƙwaƙwalwa, a hankali nima kalaman baba ƙaura da abinda ya faru yau a jejin suka shiga dawomin daki-daki. Jin an ruƙo hannuna nai saurin buɗe ida
nuna, boss ne riƙe da riga a hannu, batare da yayimin maganaba ya ɗaga kaina a hankali ya ziramin wuyan, sannan ya kamo hannuna ya taimakamin na saka, ɗayanma haka. Juyawa yay yana faɗin, “Ki tashi kiyi alwala ki sauke nauyin sallolin dake kanki”. Daga haka ya fice a ɗakin. Dukda tsoron dake a raina haka na miƙe dan nima rashin yin sallar cizon raina yake sosai, sauka nai daga gadon, rigarsa ce t-shirt mai guntun hannu, dukda a ido bata da girma sai gashi takai min har kusan quarter ɗin cinyata, na ɗauki wandon dana gani gefena, a raina nake raya ‘Ni balki, nice kuma da saka kayan boss yau?’. Sauƙina wandon irin mai taushin nanne da roba acan ƙasansa, sannan a sama ma robace harda zariya. zariyar naa ɗaure sannan a tsoro-tsoro na nufi bayin ina addu'a a cikin raina, saida na leƙa na tabbatar babu komai sannan na shiga batare dana rufeba na ɗauro alwalar na fito. Nayi namakin ganin hijjab a ajiye, da alama tun ɗazunma ya ajiyeshi, haka na ɗauka na saka na fara sallolin da suka shigemin.
Jawaad kam koda ya fita sashen Uncle Nasir ya nufa, a falo ya iske yaran harda mamansu suna kallo, duk gaidashi suka shigayi da masa ta'aziyyar Gimba, ya gaisa da Ammi ma, sannan ya zubama Ameera harara da faɗin, “Wannan banzar shigan fa? Ko ɗan kwali babu kanki”. Cike da taoro Ameera ta miƙe tana faɗin, “Dan ALLAH kayi haƙuri Yah Jay”. Bai sake tanka mataba, amma kallon da yake mata ya isheta shiga uku, da gudu tai ɗakinsu domin suturta jikinta, dan dama ya hanasu shigar banza tun yana zaune a sashen (karku manta bayan rasuwar mama Maryam Uncle Nasir shine ya cigaba da riƙon Jay har yay aure). Baya musu wasa idan yaga kan mutum yana rawa, shiyyasa suke masifar shakkarsa, gashi dama baya shiga shirgin ƴammatan gidan saboda gudun raini, samarinma kansu ba kowa ke ganin fuska daga garesa ba sai sa'anninsa dana sama dashi, suma ɗin bai maida kansa sakarai a garesuba ana dai mutunta juna. Raihana da itama ta nutsu waje guda ya kalla, “Tashi ki samo min abincin mutum biyu”. Tashi tai da sauri ta nufi kitchen, itadai Ammi batace komaiba, dan macece mai mutunci da sanin ya kamata, yanda Jawaad ke tsaye kan ƴaƴansu ita daɗi yake mata, dan shakkarsa na hanasu aikata abubuwa masu yawan gaske, har ranta kuma ƙaunar Jay take dan ita dai halayyarsa birgeta yake sosai.
Suna ɗan taɓa hira da Ammi akan rasuwar gimba Raihana ta fito ɗauke da ƙaramin basket na kaba mai ƙyau a hannu, tace, “Yah Jay gashi, ko nakai can?”. Batare da ya bata amsaba ya miƙa mata hannu alamar ta bashi, kawo masa tayi tana godema ALLAH a ranta, dan dama bason kaiwar takeba kar taje can ya sakata wani aikin kuma, dan hankalinta nakan film ɗin da suke kallo. Yana amsa ya miƙe yayma Ammi sallama ya fita.
Bayan na kammala sallolin sai kawai na ɗauki Alƙur'anin dana gani a ɗakin na shiga karatu cikin sanyin murya da rauni, dan inayi hawaye na zirara tamkar an buɗe fanfo.
Wani irin sanyi Jay yaji a ransa, ya ƙaraso cikin ɗakin sautin muryar bilkisu na ratsa zuciyarsa, sai yaji wata nutsuwa mai daɗi na saukar masa har cikin gaɓɓai. Bai dakatar da itaba ya ajiye basket ɗin ya fita, mintuna kaɗan ya dawo ɗauke da kifuna biyu sunata turiri alamar tea ya haɗo musu. Motsinsa ya sani rufe alkur'anin saboda nakai inda zan iya tsayawa, sonake na roƙesa ya maidani masarauta tunda har yanzu da sauran dare, ƙarfe goma da mintuna Uku.
Ido muka haɗa dan shima kallona yake, na maida kaina ƙasa ina juya abinda zan faɗaɗin da lanƙwasa yatsun hannuna madaidaita, “Dan ALLAH Yayah dare baiyiba, tunda ruwan ya ɗauke ka kaini can koka kaini gidan Dad na kwana”. Jin shiru bai tanka minba na saci kallonsa, shayinsa ma yake sha tamkar bai jiniba, kuma tsabar wulaƙanci kallona yakeyi. Kusan mintuna uku yace, “Taso kici abinci”.
‘Yah ALLAH, wai da wane yare zan fahimtar dashi ya fahimtane?’. Na faɗa a zuciya idanuna na cika da ƙwalla, Ban karaya ba dai, duk dan ya barni nafi nabi umarninsa, babu musu na miƙe zuwa garesa, batare dana cire hijjab ɗinba nai yunƙurin zama ƙasa. Gadon ya nunamin da hannu yana sake tamke fuska. Yanzunma dai Umarni nabi na zauna dukda ba ha
ka nasoba, ya miƙomin kofin shayi kawai. Ƙananun kofunane dan basu wuci rabin kofi ba, tea ɗin ma kuma bai cikaba, cikin dauriya da fatan maidani masarauta na hau sha, sosai yayi daɗi abin mamaki, bansan na shanyeba balle dama yunwa nakeji.
Kofin da yasha nashi tea ɗin ya ajiye, ya buɗe kular dake cikin basket ɗin ya ɗiba abinci dai-dai misali, nidai kallonsa nake ƙasa-ƙasa, tashi yay ɗauke da filet ɗin a hannu ya koma saman kujerar ɗakin, “Ga abinci nan” yay maganar batare da ya kalleniba. Duk da inajin kunyarsa yunwa nakeji sosai, idanma nace bazanciba zan cutar da kaina matuƙa. Kofin na ajiye na ɗiba dai-dai misali. Koda wasa ban ɗago kainaba harna kammala, na miƙe na tattare har filet ɗin daya gama shima na fita dasu duk da a tsorace nake.
Jay ya bita da kallo harta fice, a ransa yake faɗin, ‘Ahaka sai ka ganta kamar wata saliha, sai dai shegen taurin kaine da ita da tsoro ko farar kura ta shafa mata lafiya’. (Jay a rage sa ido dai. Lol😂).
Babu jimawa na dawo ɗakin, zuciyata na sake tunzurani akan na sake roƙonsa dai. Yana zaune inda na barsa ya baza takardu a table ɗin gaban kujerar yanata rubutu, na ƙaraso bakina ɗauke da addu'ar neman nasara a kansa, jikin hannun kujerar na duƙa ina mai narke murya dan yaji tausayina. “Amaturrahman ta kirani akan sunga ban dawoba, ni kuma na sanar mata muna hanyar dawowa, kuma zan koma masarauta, nasan sunacan suna jirana”. Aikin gabansa kawai yake kamar bai jiniba, na kuma raunana murya da faɗin, “Boss Please, idan na kwana a gidannan da safe wace amsa zanba mutanen gidan dasu Amaturrahman ɗin?”.
Karon farko Jawaad ya saki lallausan murmushin da har haƙoransa suka bayyana, dukda yana cikin halin damuwa da alhinin rasuwar gimba sai ta bashi dariya, fuskarsa ɗauke da murmushin har yanzun ya ɗago yana kallonta.
Wani irin daɗi naji ganin yana murmushi, a tunanina naci nasara, sai gani nai ya ɗauke kansa ya maida ga abinda yakeyi batare da yace komaiba, “In faɗa miki amsar da zaki basu idan sun ganki kin kwana anan da safe?”. Ya faɗa tamkar bashine yay maganarba. Ganin bance komaiba ya ɗago yana kallona, “Ko bakiso na riƙe kayata? Dan ƙyautace, idan ta ƙara wasu mintuna zata zama ta kuɗi”. Baki na tura masa dan haushi, nace, “Inaso”.
Jay dake kallonta har yanzu yakai yatsansa dab da bakinta ya ɗallah yana faɗin, “K kullum bazaki daina bani ciwon kaiba yarinyarnan?”.
Saurin ɗaura hannuna nai saman bakina dan zafi, idanuna har sun cika da ƙwalla, saurin rufesu nayi dan karsu zubo, boss mugune yasin, ina tausayinsa ashe bama abin tausayi baneba........
Ture takardun gabansa yay ya miƙe, a gaban bily dake durƙushe jikin kujerar da yake zaune yaje yay wani ɗan dirƙuso da kowa yasan maza da iya salonsa, da sauri-sauri zuciyarsa ke gudu, lumsassun idanunsa nakan fuskarta datai fayau saboda ramar da taɗanyi.
Saukar numfashinsa a saman fuskata da mayen ƙamshin turarensa ya sakani ware idanu dan mamaki, ko kaɗan ban san sanda yazo daf daniba, a take jikina ya fara tsuma, ya saka hannunsa akan haɓata ya ɗago fuskata da ƙyau, saurin lumshe idanuna na sakeyi ina ambatar sunan ALLAH a raina, dan wannan al'amari nasa yafi ƙarfina da wayona. Cikin taushin muryar da bansan yanada itaba, yay magana a hankali “Na maida amsata bakiso?”.
Da ƙyar na iya haɗiye yawu ina jinjina masa kaina alamar “eh” banason, dan burina kawai ya tashi wlhy.
Jay da shima baisan mike damun kansaba ya kuma matsar da fuskarsa daf data Bilkisu, a hankali ya busa mata iska saman idanunta dake rufe, mar-mar ta farayi da idanun saboda iskar da yake busa matan.
hancinsa ya ɗora saman nata yana gogawa, cikin magana raɗa-raɗa da ko kana kusa dasu da wahala ka jinsa yace, “Duk masu suna Bilkisu jarumaine, miyasa ke kike matsoraciya?”..................✍
(😂😂Saura naji wani yace maganar Jay ba gashkiya bane, kowa yasan mu jarumawane masu Suna Balkisu. Lol🚴🏼😜).
BARKANMU DA JUMA'A.
Kunata jira ko😑, ALLAH ina fara editing barci ya ɗaukeni, saida na tashi na tsinta wayar a gehe🤣.
Asha weekend lahiya🚴🏼🚴🏼🚴🏼😍😍😍😍🤗
ZAAF
[12/19/2020, 3:04 PM] HASNA✍🏻: +234 909 304 4460:
SURPRISE💁🏻
Wannan page sadaukarwa ne ga iyayen yaran da suka kuɓuta, gaskiya ina tayaku murna matuƙa gaya, mungodema UBANGIJI daya maido mana dasu garemu da gaggawa cikin ƙoshin lafiya kuma, ƴan uwa wannan yana sake nuna mana mu duƙufa addu'a wa ƙasarmu, aikin bana shugabanni bane kaɗai, dan idanma munƙi addu'ar mune zamusha wahala, shugabanninmu mutanene tamkarmu, suma basu isa tsaremu ba sai wanda ya haliccemu, aduk yanda rayuwa tazo mana mu amsheta matsayin jarabawa mu godema ALLAH, UBANGIJI yafi kowa sanin halin da muke ciki, muyi ƙoƙarin cinye jarabawa sai muzama masu nasara, zage-zage marasa amfani nakasace irin ta zuciya, ALLAH yay mana ni'imomi masu yawa miyasa bazamu gode masaba sai ƙoƙarin aibanta waɗanda suke mutane kamarmu da hangen gazawarsu, sai dai taimakon addu'oinmu zamu samu tsaron da muke buƙata a yankinmu, muyi haƙuri mu duƙufa wajen faɗama ALLAH kukanmu, mu gyara mu'amulanmu ga junanmu mu kanmu, dan bazamu kasance azzaluman junaba sannan muce zamu samu shugabanni adalai, mugyara sai ALLAH shima ya gyara mana danshi mai rahamane. ALLAH ya kawo mana haske da kwanciyar hankali, ya dafama shugabanninmu suma akan ƙyawawan ayyukansu, saɓanin haka ALLAH ka magance mana badan halinmu ba😭🙏🏻.
Page 32
.................Ganin yanda ta tsume sai ta bashi dariya da tausayi, ya dungure mata kai yana miƙewa da faɗin, “Yarinyarnan ki rage tsoro”.
Ni kaina bansan na sauke wani kakkauran numfashiba tare da komawa na zauna daɓar, nai azamar cusa kaina tsakanin cinyoyina ina mai godema ALLAH daya tashi. A raina sai ayyana rashin kunya irin na maza nakeyi, suyi abu kuma su fuske abinsu tamkar basuyiba.
Jay da tuni ya koma kan aikinsa yaɗan kalleta ya maida kansa ga rubutun da yakeyi, haka kawai yanaso ya ganta a yanayin tsoro dan ƙyau take masa. Bai sakebi takantaba ya cigaba da haɗa bayanai akan case ɗin mutuwar Gimba, ya ɗaukama kansa alwashi sai yabi kadin jininsa, duk masu hannu a cikin wannan al'amarin kosu ubanwaye saiya soya musu gyaɗa bisa tafin hannu. Ganin lokaci yaja sosai Bily na a yanda take tun ɗazun ya sashi sake kallonta, muryarsa babu alamun wasa yace, “Miemaa!”.
Gajiyar dake tattare dani tasa har barci ya saceni a haka ban fargaba, a bazata naji ya kira sunana, na ɗago da sauri na kallesa, shima ni yake kallo, sai dai fuskarsa babu walwala sam. “Tashi kije ki kwanta” ya faɗa yana nunamin gado da idanu. Yanda ya tsuke fuska babu sauƙi yasa na miƙe babu musu dan nasan dai kwana anan dole ya tabbata, zuwa nai na kwanta a bakin gadon sosai, naja bargon na rufama jikina batare dana cire hijjab.
Jay daya kuma maida hankalinsa ga aikinsa yace, “Kicire wannan hijjabin tunda ba cinyeki za'ai a ɗakinba”. ‘Boss matsala’ na ayyana a cikin raina ina zame hijjab ɗin naja bargon har saman wuyana.
Duk da azabar ciwon kai da ya keji haka ya jure yana cigaba da haɗa bayanan, sai kusan ƙarfe ɗaya saura ya miƙe, kallo ɗaya yayma sashin da Bilkisu take kwance ya fahimci har yanzu idonta biyu, baice komaiba ya cire jallabiyar jikinsa yasa t-shirt fara akan boxer ɗinsa ya haye gadon shima, sai dai ba kwanciya yayba, zama yay ya jingina bayansa jikin fuskar gadon ya kashe fitilar ɗakin yabar iya ta gefen gado. Bargon yaja ya lulluɓe iya ƙafafunsa zuwa cinya, ya lumshe idanunsa yana maijin zafi da ƙirjinsa ke masa wanda yaketa ƙoƙarin dannewa, tunɗazun dannewa kawai yake dan bayason ya ƙuntata zuciyar yarinyarnan da laifin daba nataba, yana buƙatar jin wasu abubuwa daga garetane shiyyasa ya kawota nan dama. Rayuwarsa da gimba ta shiga kokawar dawo masa cikin zuciya, yarone mai mutunci da sanin mutuncin duk wanda zama ya haɗashi dashi, yasha saka Gimba manyan ayyuka masu haɗari akan aikinsa kuma yay masasu cikin ƙwazo, gimba na ɗaukarsa tamkar yayansa da suka fito ciki guda, tabbas yayi rashi wanda yasan bazai taɓa maye gurbinsaba har abada, danshi tuni yabar ɗaukar gimba matsayin drivern sa kawai jinsa yake a jininsa tamkar ɗan uwansa abokin farin ciki da baƙin ciki. Wata ƴar ƙwalla ta taru mai akan fatar idanu kaɗan, hannu yasa ya shareta yana mai jero masa addu'oin ne
man gafara a cikin zuciyarsa. Ya ɗau tsayin mintuna goma a haka kafin ya juya ya kalli Bilkisu, ɗauke kansa yayi murya cike da ɗaci yace, “Miyasa kika dawo gidan su Hudah da zama?”.
Banyi tunanin ya fahimci idona biyu ba har yanzun, na rumtse idanuna da ƙarfi ina sauke ajiyar zuciya, batare dana motsaba nace, “Ƙaddarar maraici”.
Idanu Jay ya tsurama bayanta, tsawon sakanni ya ɗauka a haka kafin ya sake ɗauke kansa daga gareta, “Ina dangin mahaifinki suke? Misa basa cikin rayuwarki?”.
Hawayene masu zafi suka silalomin, dan yau kan Boss ya taɓomin inda yafi ko'ina ciwo a zuciyata, zaune na tashi na jingina da fuskar gadon nima, hawaye na ƴar tseren fitowa na shiga bashi amsa kai tsaye, dan na fahimci so yake kawai yasan wacece niɗin kafin zuwana gidan su aunty Shahudah, batare dana kallesaba nace, “Har iyayena suka bar duniya su dukansu basu taɓa sanar dani wata matsala dake tsakaninsu da duk danginsu ba, dukda nasha musu tambaya sai dai babu wanda ya taɓa bani amsa ƙwaƙwƙwara a cikinsu, kullum amsarsu a gareni itace, (komai da lokacinsa, idan lokacin yayi zan sani) tun ina damuwa da abun harma na ciresa a zuciya, dama ba komai ke sakani kwaɗayin son jiba sai yanda nake ganin sauran yara ƴan uwana sukan shirya a ranakun juma'a da Sallah suje gidajen danginsu, sai dai ni daga gareni ba haka baneba, tunda na girma nai wayo a gidan haya mai ɗauke da ɗakuna kusan arba'in na buɗi ido na ganmu, bara dai na maka gwari-gwari zakafi farimtata.
Ni dai sunana Bilkeesu ɗiya ga malam Ado makaho, ƙwarai mahafina makahone da ko tafiya baya iya yi sai da ɗan jagora, Sai mahaifiyata Asiya.
A shekarun baya can mahaifina yana ɗan gani da ido ɗaya, amma da ga baya wahalhalun rayuwa suka ida rufe ɗayan idon yazam gaba ɗaya, mahaifiyata ma tana da nakasar ƙafa, dan kuwa gurguwace bata ma iya tafiya sai dai jan jiki. A matsayin da iyayena suke kawai zai nuna muku ni ba kowan kowa bace ba, dan kuwa muɗin talakawane irin tiɓis ɗinan da a kullum sai an nemo za'aci. Abin da zai matuƙar birgeka a rayuwar iyayena shine sam mahaifina baya bara balle aje kan mahaifiyata, duk da baba baya gani bai yarda zama maroƙi ba, dan a ganinsa UBANGIJI ya masa dukkan gata da ya bashi rai da lafiya, idaniyar ganice kawai bashi da ita. Sana'ar mahaifina itace sai da kayan ɗinki irinsu zare, allura, almakashi da dai sauran kayan nau'in ɗinki tsiraru dai-dai