Showing 222001 words to 225000 words out of 261165 words
Chapter 75 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete
Umm-Anum ta fashewa da kuka tana dariya kuma, cikin wani ƙarfin zuciya ta ɗaga murya wajen faɗin, “Rana dubu ta ɓarawo, ɗaya tak ta mai kaya”.
A take ɗakin yay tsit, suka juya gaba ɗaya suna kallonta a wani irin yanayi mai wahalar fassara a fuskokinsu................✍
Nima dai kam na tsinci kaina a yanayin har takai alƙalamina da faɗuwa a ƙasa batare da na shirya hakanba😳🚶.
Kuyi manegi babu editing yau🤒🚴🏼
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[2/12, 7:51 PM] Wasila: ƘWAI CIKIN ƘAYA
BILYN ABDULL
*_FARIN WATA SHA KALLO🤓🤗_*
ZAFAFANKU SUN DAWO GAREKU A 2021😋😋😋😋🚴🏼🚴🏼
*_ZAFAFA BIYAR 2021_*🔥🔥🔥
*_SABUWAR SHEKARA_*
*_TAREDA SABON SALO_*👍
✔️ *_A DUNIYAR RUBUTUN HAUSA SU NA DABAN NE,_*
✔️ *_A DUNIYAR NISHADANTUWA DA KARATUN HAUSA SU DIN NA MUSAMMAN NE,_*
✔️ *_A DUNIYAR FADAKARWA DA QAYATARWA NA KARATU SU DIN NA FARKO NE,_*
✔️ *_A 'BANGAREN NISHADANTUWA DA TSAFTATACCIYAR SOYAYYA MAI SHIGA RAI DA SANYA SHAUQI DA NUTSUWA TO SU DIN ZA'BABBINE,_*
✔️ *_A 'BANGAREN SANYA NISHADI DA BARKWANCI TO SU DIN QWARARRINE,_*
*_Shin ko kunsan su ake kira da zafafa biyar masu tashe?_*
_*Idan kin/ka san kai maabocin karatun littafan HAUSA ne to tabbas karku Bari ayi Babu ku*_
*_domin kuwa wannan karon sun dawo muku da wani sabon salon Wanda babusa a DUNIYAR karatu,_*
*_cikinsu Babu wadda bataga jiyaba bataga yauba a fagen nishadantarwa._*
*_ZAFAFA BIYAR 2021_*🔥
_*YANKAN BAYA*_💚
_BILLYN ABDUL_
( _kwai cikin qaya_ )
( _raina kama_)
( _wutsiyar raqumi_ )
*_SIRADIN RAYUWA_*💛
_SAFIYYA HUGUMA_
( _alqawarin Allah_ )
( _daurin boye_ )
( _Dangantakar zuci_ )
💙
_*KIBIYAR AJALI..*_💜
_MISS XOXO_
(Sulke baya tsare ta sai ta wuce)
( _Igiyar zato_)
( _Kaimin halacci_ )
( _Naufal_ )
*_ABIN DAKE CIKIN ZICIYA_*🧡
_HAFSAT RANO_
( _ruhi daya_ )
( _Sauyin qaddara_ )
( _Daurin goro_ )
*_MIN QALB_*❤️
_MAMUHGEE_
( _buri daya_ )
( _tarayya_ )
( _eznah_ )
Duka BIYAR 5 zaku samesu akan garabasar naira 700 kacal,
Guda hudu 4 Kuma 500,
Guda uku 3 Kuma 450,
Guda biyu 2 Kuma 400,
Guda daya akan 300.
Ma'ana
Each one is 300
2 is 400
3 is 450
4 is 500
5 is 700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO- *0812652655*
ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*
BANK NAME: *ACCESS BANK*
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
*09044191709*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
*09033181070*
Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO
TEAM#ZAFAFABIYAR🔥
Page 58
.................Muna tsaitsaye a inda aka bamu iznin tsayawa, Rose na mana bayani akan abinda zamu tunkara. Cikin takunsa na zaratan jami'ai da sukasan aikinsu ya fito Hafiz biye da shi da bullet proof jacket a hannunsa da alama ta boss ɗince, A boss ɗinsa dana fara sani yake yau, kura ga tsoro gaban tsoro, zakin da babu abinda ya sani face farauta a lokacin da yunwa ta ciyo cikinsa, gwarzon da baya alfarma ga dukkan wanda baima kansa alfarmarba, ɗaya tamkar da dubu abin buƙatar kowacce ƙasa, kowanne yanki, ko wacce zuri'a. Cike da izzarsa mai cike da tsantsar damuwa da ɓacin rai yazo gabanmu ya tsaya yana ƙare mana kallo ɗaya bayan ɗaya. Ya furzar da wani zazzafan huci daga bakinsa yana nunamu da yatsansa manuniya. “Kusa a ranku aiki zaku fita bakin rai bakin fama, sakacinku na nufin sakaci da ƙasarku, sakaci da yankinku, sakaci da garinku, sakaci da familys naku, idan kuka zama jajirtattu kun fido da martabar ƙasarku ne, yankunan ku, garinku da familys naku dama rayukanmu baki ɗaya da hukumarmu. Aikine mai cike da haɗari, ka kashe ko a kasheka wannan duk hukuncin ALLAH ne, shawarar kawai itace addu'a, ina fatan kuna faimta ta”.
“Yes Sir!!!” muka faɗa cikin haɗa bakuna tare da buga ƙafa ƙasa mukai salute nashi. Juyawa yay ga Rose yay mata maganar da bamaji kafin ya kalli oga Hafiz shima. Shima maganar sukai suka bar wajen kuma zuwa inda su Sir Ahmad ke tsaitsaye tare da manyan jami'anmu da sojoji kusan goma sha biyar.
Mudai muna nan tsaitsaye muna jiran umarni, a haka oga Jabeer ya zo wajen ya bamu damar zuwa mu shiga jirage masu saukar angulu (Helicopters) da za'ai tafiyar dasu. Mu matan an haɗamu ne a guda ɗaya, drivern mu ma ta kasance mace ce yarinya ƙarama da bazamu gaza sa'anni gudaba, sai baba ƙaura kaɗai daya kasance namiji a cikinmu wanda ya wuce muce masa uba kawai sai dai kakanmu. A yau babu zancen fira mu dasu Ummie, kowa addu'a ce ɗauke da bakinsa da fatan nasara, a can ƙarƙashin zuciya kuma tsorone da kowa ke ƙoƙarin dannewa. Sai da muka hangi tashin wasu jiragen kafin namu ya tashi, kusan duk sai da muka lumshe idanu kowa shi kaɗai yasan abinda ke a cikin ransa.
Kamar a wancan karon tafiyace mukai da hasashe bazai iya ƙididdigar iyakartaba, sai dai kawai muka tsinkayi saukar jirginmu a tsakkiyar jeji mai cike da surƙuƙi da haɗarin gaske. Mun firfito kowa na ƙoƙarin kare ƙurar da fankokin jirgin suka tayar da hannunsa domin samun damar ganin hanya da ƙyau, wasunmu da basa son ƙura har ƴan ƙananun tari sukeyi da atishawa. Su boss suma duk sun firfito a nasu. Sir Ahmad na ƙoƙarin buɗe taswurar jajenin da ya amsa a hannun oga Aliyu baba ƙaura ya dakatar dashi. “Ranka ya daɗe bama buƙatar wata taswura, insha ALLAHU komai zai kasance yanda muke fatansa, babu wani lungu ko kogo da zai layancemin a wannan jajenin kaf ɗinsa, inda muke buƙatar zuwan zamu dosa kai tsaye babu ko gargada a ciki”.
Sosai naga al'ajabi a saman fuskokin jami'anmu, muko da muka san wanene baba ƙaura hakan bai zame mana sabon abuba, fatanmu kawai samun kariyar UBANGIJI da nasara.
Tafiya muka farayi a cikin jejin, su oga Aliyu da boss da wasu a cikin sojojin da baba ƙaura ne a gaba, sai su Sir Ahmad a bayanmu. Munyi tafiya mai nisa kafin mu isa wani ƙyaƙyƙyawan tsuburi dake da ƙaramar ƙorama a gefensa, sai tsuntsaye jefi-jefi dake shan ruwa. Da hannu boss ya tsayar damu kafin mu ƙarasa ga ƙoramar, Oga Jabeer ya matsa kusa da boss, bullet proof jacket ɗin dake a hannunsa ya shiga ƙoƙarin saka masa suna magana, nidai ina satar kallonsune da faɗin ‘Ɗan gata rigarma sai an saka masa’. Ya juyo saitin da muke yana bama Jabeer bayansa danya gyara masa can, ido muka haɗa nai azamar janye nawa, a bazata naji yace, “Miemaa!”. Abinda ya tsargamin nai saurin haɗiyewa, yayi masifar iya ambatar sunannan fiye da zaton mai tunani, kallonsa nayi na amsa da “Na'am”. Ya ɗauke idanunsa daga kaina yana faɗin, “Ki gyara wannan jacket ɗin taki bata zauna da ƙyauba”. Gaba ɗayansu suka zubamin ido banda su Sir Ahmad da hankalinsu ba wajanmu yakeba. Kaina na jinjina masa ina haɗiye yawu da ƙyar dan yanda duk suka zubomin ido sai naji na takura. Nazifa dake bayanace ta taimakamin na gyara, idonsa har yanzu a kaina yace, “Matan nan ku kasance kusa da wani komai rintsi, sannan banda harbi a kai, ciki, ƙirji, duk harbin da zakuyi karya wuce ƙafa ko hannu da inda baza'a mutuba”. Kai muka jinjina masa da faɗin, “Okey Sir!!”.
Rose ta taɓe baki tana harar Bilkisu ta gefen ido, duk da tasan abinda Jawaad ya faɗa musu dokace kasancewar a harbin da duk su bilkisu zasuyi babu kisa sai ankai maƙurar da babu mafita taji zafi a ranta, dan a ganinta Jay ya faɗama bilkisu ne ita kaɗai kawai cikin tsantsar nuna kulawa, tunda harda cewa ta gyara jacket ɗinta. ‘Mtsossw’ taja ƙaramin tsaki a ƙasan maƙoshi da matsawa gaba.
Da ga inda muke tsaye muna hango gini maiban mamaki da tu'ajibi, dajine sosai fa. amma sai ga gida a tsakkiyarsa, gida ginanne daya amsa sunansa gida da ko a cikin gari ya cancanci kallo bawai sakaran gini ba ne. Babu wanda al'ajabi bai sakashi kallon baba kaura ba. Cikin dattakonsa yay murmushi shima batare da ya kalli kowa a cikinmuba. “Wannan gini ginine da ya ɗauki kusan shekaru ashirin da bakwai a cikin jejin nan, magina aka kawo suka ginashi kamar yanda ake gina kowanne irin gida, duk shekarar duniya kuma sai an sabunta masa fenti da abubuwan ƙawa. Mabanbanta mutanene ke zuwa cikinsa ziyara, abinda suke aikatawa a cikinsa kuma, sai munje idanunku zasu gane muku komai a yanzun, domin yau ranace da suka ware ta musamman domin shaiɗancinsu, shiyyasama muke anan tsaye bisa ƙafafunmu batare da sun farga da zuwan namu ba”. Kawuna kawai muke iya jijjigawa kamar wasu ƙadangaru, shine yay mana nuni damu ƙarasa.
Ararrabe muka fara dosar ginin muna zagayesa kamar yanda commander'n (boss) tafiyar ya bada umarni, ɗai-ɗai muka ringa shiga cikin dabara na salon aiki, ina niyyar bin bayansu nima aka riƙo hannuna, waigowa nai da sauri dan bansan waye da aikinba. Ya harareni damin alamar na dawo bayansa da idanu. Bani da zaɓin da ya wuce bin umarninsa, na dawo ta bayansa yana gaba, duk da gani a baya sai ya raba hankalinsa wajen kallon bayansa da gabansa, da haka muka shiga ciki muma kamar yanda oga hafiz da Aliyu, Jabeer sukayi, sauran kuma suna daga waje su da su sir Ahmad. Tafiya muke a sannu-sannu, babu wanda yay harbi dai a cikinmu kamar yanda har yanzu nidai banji motsi na alamar akwai mutum a gidanba.
Cikin matuƙar zafin nama da ALLAH ya bama boss ya fisgoni tare da duƙar da ni saboda tahowar wuƙa da aka wulwulo a bazata wadda sam hankalina baya wajen, bakuma musan dga inda take ba, jikinsa na faɗa, shi kuma ya cafe wuƙar a hannunsa. ɗagowa nai ƙoƙarin yi idanuna suka sauka akan ƙafa dake ta wani ɗan lingu, komawa nai na duƙe har yanzun hannun hagguna na cikin na boss. Handkherchief ɗin aljihunsa nasa hannu na ɗauka, tsayawa yay yana kallona yaga mizanyi, na zare hannuna daga nasa na ƙarasa takawa inda ƙafar take cikin sanɗa, sai da naje gab sannan na miƙe sosai cikin zafin nama na ratayo handkherchief ɗin a wuyan wanda ke tsayen, kafin yay wani yunkuri na ɗaure masa wuya da ƙarfi yanda ko ƙara zaiyi babu maiji. Sukur-sukur ɗin da mutumin keyine na neman ƙwatar kai ya saka boss kallona, fuskarsa ɗauke da murmushin dana jima ban ganiba yaymin jinjina👍🏻. Nima sai nayi murmushin dan ya bani dariya a salon da yay da idanu da murmushin harma da jinjinar. Zagayawa yay ta ƴar ƙofar daya gani wajen wanda har yanzu nake ɗaure da wuyansa harya suma, yaymin nuni dana cire handky ɗin, ya kamasa ya kwantar ƙasa nima na zagaya.
Jinjina ya sake min, cikin magana raɗa-raɗa yace, “Aikinki yayi ƙyau Babie”. Ɗan murmushi nai masa sannan muka shige ta ƙofar da muka gani cikin sanɗa. Saurin dakatawa yay yaɗan ja baya kaɗan muka koma jikin bango da ɗauke numfashi. Baƙin mutumin da sam babu imani tattare da shi yazo ya wuce ta kusa da mu sai dai bai kawo inda muke ba, har yay ɗan nisa sai kuma ya dawo baya yana waige-waige. Yana zuwa gab damu boss ya jawo masa riga ta baya, cikin wani irin zafin nama ya juyo sai kawai ya buga masa kansa yay baya, oga Hafiz daya ƙaraso wajen ya taresa da saurin ɗora masa handkherchief ɗin hannunsa a hanci, da alama wani abun ya shaƙa masa, dan a take jikinsa ya saki. Ƙasa ya kwantar da shi yana ɗagowa, ya matso kusa damu sosai cikin magana raɗa yace, “Boss kuzo gasu tanan”. Binsa mukai cikin sanɗa ta hanyar daya biyo boss nata faman murza goshinsa da yayma mutum can gware alamar yana masa zafi wajen har yanzun.
Tsaye muka tadda su Jabeer cikin matsanancin ruɗani, ni da boss muka ƙarasa jikin glass ɗin wajen da akayisa domin kwalliya kawai muka leƙa. A take tsigar jikina ta tashi, ƙirjina yay wata irin dokawa nai saurin yo baya ina ambaton ‘Wa'iyazubillah’. Boss kam tsaye yake kyam akan ƙafafunsa ya dasama wajen ido baya ko ƙyaftawa, sai dai jikinsa shi kansa tsuma yake, gashin duk sun mimmiƙe alamar shima tsigar jikinsa tashi take. Duk mai imani dolene ganin wannan shaiɗancin ya tada hankalinsa.
Shirka ƙuru-ƙuru ga waɗanan shaiɗanun mutane da a zahiri suke ambaton kayinsu musulmai harsu shiga masallaci suyi salla cikin jam'i ma. Gaba ɗayansu zindir suke sai wani ƙyale ja da suka ɗaura a ƙugu ɗan guntu da iya al'aurarsu kawai ya rufe, sai wani ɗaure a kansu, durƙushe suke gaba ɗayansu sunyi Sujuda, tsakkiyarsu ƙaton kaskon tukunyar ƙasa ne da aka kunna wuta a ciki tana ci, sai babban shiɗaniyar tasu da kasancewarta tsirara yasa muka gane mace ce zaune bisa kujera kanta a duƙe itama riƙe da sandar da maybe itama ta tsafin nasu ce. Hawaye na gani suna sakkowa a kumatun boss, jin damshi a tawa fuskar ya tabbatar da nima hawayen nakeyi ashe. Ganin zasu miƙe boss yay saurin maidoni baya muka koma jikin bango, muna kallonsu ta haka. duk suka miƙe tsaye suna wani yare da su kaɗai sukasan mi suke faɗa, da fuskar Alhajin da naje gidansa na ɗakko tukunyar nan na fara cin karo, ganinsa da nai a hoto a gidansa yasa ananma na shaidashi, sai wanda ke a kusa da shi daya kasance shima mutum mai tarin faɗa aji a ƙasar nan, zuciyata wani irin luguden daka take kamar zata faso ƙirjina ta fito nakai dubana gana uku, shidai ban sanshiba kam, sai na huɗu shima ban sanshi ba, a na biyarne kam ƙafafuna suka nemi gaza ɗaukata, dan kuwa ba kowa bane face Uncle Nasir, bankai ga fita a ruɗanin dana shigaba na ganin Uncle Nasir idanuna suka sake sauka akan Dadyn Zuhrah, sai yayan Dadyn su Ummie dana taɓa gani a ranar bikin yayemu daga Jami'a. A haka na cigaba da binsu da kallo, wasu na riga da na sansu a tv, wasu kuma ɗai-ɗaiku a zahiri, wasu ko ban taɓa ganinsuba sai anan, nabi wanda ya juya mana baya riƙe da ƙoƙo da kallon sani, sai dai bana ganin fuskarsa, amma hakan bai hanani jin zuciyata raunana ba matuƙa akansa, so nake naga wanene amma ya juya baya.
Durƙusawa yay yayi sujuda (Wa'iyazubillah😭) ga wannan la'ananniyar tsohuwar mata dake a kan kujera kamar basarakiya, sai kuma ya miƙe da ƙoƙon hannunsa yaje gabanta kansa a rissine ya miƙa ƙoƙon. Ƙyalƙyalewa tai da wata irin mummunar dariya da sam muryar tata bata kama data mata, sai kuma ta haɗe fuska tana faɗin, “Jariri!! Kai mutum ne mai daraja a wannan Bakandamiyar tamu, kaine farkon fara nasara ga dukkan matakai da tsare-tsarenmu da ƙa'idoji, kowane aikinka ka gudanar da shi babu kuskure ko sau ɗaya, sai a na ƙarshe da ya zama cikamakin ayyukanka ya gagareka?, ta dalilin yarinya ƙarama a cikamakin ayyukanka mun fuskanci asarori masu yawa. Hhhhhhhh Mun baka dama tun a watan jiya Jariri amma ka kasa damawa, munce ka nemo mana asalin yarinyar kace asalinta na farko daka kawo shine asalinta, sai dai mu bamu amince da hakanba. Lallai Jariri wannan yarinya bincikenmu ya gano mana akwai sirri mai nasaba da mafarkin mu na watan jiya dangane da ita. Jariri wannan itace dama ta ƙarshe da zamu baka akan wannan yarinya, Bakandamiyar mu na buƙatar jininta tunda budurcinta ya gagara, Jariri, idan ka gaza hakan daga nan zuwa kwanaki biyu zaka fuskanci mummunan hukunci daga Bakandamiya, zakuma mu saukeka daga shugabancin da kake kai. Sannan Jariri a yau ɗinnan ka tabbatar an sake ɗaura igiyar aure tsakanin gudalliyarka da yaron nan, inba hakaba bazamu yafe makaba a wannan karon dolene ka bamu jinin gudalliyarka........”
“Tuba nake uwargijiyarmu, tuba nake uwa maba da mama, tuba nake mai share kukanmu, ina sake roƙon alfarmar a barni da gudalliyata dan itace zuciya ta, zan iya yarda na rasa abubuwa da yawa amma banda gudalliyata ya shugata, nayi rantsuwa da shugaban shaiɗanu a yau sai igiyar aure ta ƙullu tsakanin gudalliyata da halattaccen jinin Bakandamiya. Ina mai sake rantsuwa da a gobe saina kawo jinin wannan yarinya wa Bakandamiya shine zai zama abin kalacin mabiya Bakandamiya yake abar bautarmu”. (wa'iyazubillah😭🙏🏻)
“Bakandamiya ta amsa maka, ta kuma baka damar ƙarshe ta dawowa da martabarka tare da dukkan muhimman abubuwan ƙungiya dake a hannun yarancan da jininsu ya halatta ga Bakandamiya. Kurakuranka zasu goge a dutsen rubuta laifuka bayan ka cika alƙawuranka da jinin babban ɗanka Jariri kamar yanda yake a rubuce a sharuɗan Bakandamiya”.
“Naji na karɓa yake mai biya mana dukan buƙatunmu”.
“Hhhhhhhhhhhhhhhhh!!!!!!!!!!!!!!” ta kece da wata mahaukaciyar dariyar da ta saka duk saida muka toshe kunnuwanmu saboda yanda dajin gaba ɗaya yake amsawa bama gidan kawai ba, tanayi tana tsiyaya masa wani abu mai kama da jini a cikin ƙoƙon hannunsa. Da baya baya ya baro gabanta yana wasu surkulle da shi kaɗai yasan abinda yake faɗi, sauran na amsa masa.
Mamaki, tsoro, al'ajab da ruɗani duk suka saukarmin lokaci guda ganin Dad a inda tunanina ko tsammani bai taɓa raya minba, saurin ɗaura hannuna nai na rufe bakinna jin kuka na neman kufce min. “D... Da...Daddy!!”. na faɗa cikin rawar murya dana jiki ina mai matsawa jikin boss dake tsaye abinsa yana kallonsu Dad ɗin shi da su Oga Hafiz.
Cikin matsanancin furgici Dad ya saki ƙoƙon hannunsa da kai dubansa inda yaji muryar da bai zatoba ta ambaci sunansa. Ido huɗu sukai da bilkisu da jikinta ke wani irin matsanancin tsuma.
A take Dad ya zazzaro idanu waje cikin tsananin firgici da ruɗani, jikinsa sai wata iriyar tsuma ya keyi domin ganin wadda bai taɓa zato ko tsammani ba. duk da glashi ya raba tsakaninsu, bai gaza gane bilkisu da Jawaad ba harma da jin furucinta raɗam a kunnuwansa, dan basu da wani shamaki wajen iya jiyo maganar juna duk da akwai hilashin daya rabasu.
Bansan sanda wani ƙarfi da zafin nama yazomin cikin jini da jiki ba na bigi gilashin wajen da ƙafa jikina karkarwa saboda wata irin mummunar tsanar sa ce ta saukarmin lokaci guda da ƙyamarsa.
Sauran abokan shaiɗancin nasa da tuni suma sun mike suna kallonmu a cikin matsanancin firgici na alamun bazata a fuskokinsu suka shiga ƙoƙarin motsawa cikin