Showing 207001 words to 210000 words out of 261165 words

Chapter 70 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete

17 Dec 2024

1157

zaune surutu ya kaure tsakaninsu, Anuwar kuma ya tasasu a gaba yana kallon Nabeelah kamar ya samu wani majigi.
        Cak Umm-Anum ta tsaya tana kallon Nabeelah da itama tai mutuwar tsaye tana kallon mai tsananin kama da Ummahn ta. Kallon Jawaad Umm-Anum tayi cikin wani yanayi na alamar tambaya. Hannunta ya kama ya zaunar da ita yana ɗan murmushi, sai da ya tabbar ta zauna sannan ya kalli Nabeelah da ke ƙoƙarin gaisheta. Hannun Nabeelah ta kamo ta matso da ita jikinta, da ƴar rawar murya Umm-Anum tace, “Da ace mutum baya ƙara shekaru da girma ni dai da nace wannan Mariya ta ce Jawaad, kamar yanda nake kallon takwarata da kamannin Rahma”. duk da ba yaune karan farko da akace Bilkisu na kama da aunty Mah-mah ba a gabansa sai da ya kalli Bilkisun da tasha jinin jikinta, sai kuma ya ɗauke kansa yana zama kusa da Umm-Anum. “Ummuna ki kwantar da hankalinki kinji, dukkan abinda kike buƙatar ji zaki samu fiyema da hakan har sai kin gaji, yanzu dai kitashi a kaiki inda zakiyi wanka, kuci abinci ki kwanta ki huta, sai komai ya biyo bayan hakan kinji”.
      Kansa ta shafa da ja masa hanci tana faɗin, “Rigimammen Mama har yanzu dai ana taɓawa kenan”. Dariya duk su Anuwar sukayi, shi kuma ya zuba musu harara da kama hannun Umm-Anum ɗin ya miƙar da ita. Da kansa yay mata rakkiya har ɗakin bily, itama da tabi bayansu tai saurin shiga bayi domin haɗa mata ruwan wanka.

         Nabeelah na ganin Jay da bily sun shige da Umm-Anum tai saurin ɗaukar wayarta ta turama Ummah babba saƙo.
      Sai da suka tabbatar Umm-Anum ta shiga wanka sannan Jawaad ya fito, kayansu da Sadiq tuni ya gama shigo musu da su ya saka Anum ta ɗauka na Umm-Anum ta kai mata ɗakin Bilkisu, shi kuma ya kai Anuwar ɗakin baƙi inda zai zauna, Anum ma ɗakin baƙin dake cikin falon bily zata zauna. Bilkisu da Nabeelah da keta ALLAH, ALLAH su Ummah su iso sukai hidimar shirya abinci su kuma a tsakkiyar falon, dan yanda Umm-Anum ta gaji bai kamata a sakata zaman Dining ba.
       Tana son tabi Jay ɗakinsa dan ta nuna masa farin cikin data shiga na bazatar da yay mata akan zuwan su Umm-Anum amma haushinsa da takeji ya hanata aikata hakan, sai kawai ta sharesa ta cigaba da harkokin gabanta, dan farin cikin ganin su Umm-Anum ya shafe mata duk wani damuwarta kuma.  
           A ɓangaren Jawaad shima tun shigowarsa ɗakin ya ke zuba idanu ya ga bilkisu ta biyosa amma sai yaji tsit, duk da farin cikin ganin mahaifiyarsa da ƙannensa ya shafe masa duk wani ɓacin ran da ya samo daga Qaseem da gidan Dad hakan bai hana ransa sosuwa ba da ƙ

in shigowar Bilkisun, sai huci yake da jera tsagwayen ƙwafa, ayyanawa yake a ransa sai yayi maganin miskilancin yarinyarnan a yau ɗin nan basai gobe ba, dan ya gama lura gadon barcinsa da ta gama ganine yasa take neman fara kawoma rayuwarsa raini (Ka manta wulaƙancin da kai mata kai ɗazun saraki🙄😜).
          Tashi yay da ga kwancen da yake saboda jin an fara kiraye-kirayen sallar Magriba. Alwala yayi sannan ya fito, a babban balo suka haɗu da Anuwar da shima ya fito daga sashen baƙi da alamar shirin tafiya masallacin. Yayma abincin da aka shirya a tsakkiyar falon kallo ɗaya ya ɗauke kansa batare da yace komaiba suka fice shi da Anuwar dan falon babu kowa cikinsa.
             Da taimakon Bilkisu Umm-Anum ta dawo falon bayan an idar da sallar Magriba, suna zama Ummah babba da Ummah ƙarama da Batool nayin sallama, cikin matsananciyar faɗuwar gaba Umm-Anum ta juya tana kallon ƙofar dan ko'a cikin magagin barci waɗannan muryoyin sunfi gaban mantuwa a gareta balle ma a zahiri.
        Kasancewar akwai hasken Genretor da aka kunna tas suke ganin junansu, da ga Ummah ƙarama har Ummah babba jikinsu rawa yake da tsuma sosai, sun ƙurama Umm-Anum idanu tamkar yanda itama ɗin kallonsu take bata ko ƙyaftawa. Su dai su Bilkisu kallonsu kawai suke da son ganin yaya za'a kwashe. A haka Jawaad da Anuwar suka shigo suka samosu. Jay ya kalli su Ummah da mamaki sai kuma ya kalli Nabeelah da ya tabbatar itace da wannan aikin. Aiko sai tai ƙasa da kai gabanta na faɗuwa dan tsoro ta koma bayan bily ta maƙale.
      Ɗauke kansa yay daga gareta, ya ƙarasa gaban su Ummah ya tsaya a tsakkiyarsu, hannayensu duka ya kama a cikin nasa, a take duk suka ɗago suna kallonsa hawaye na gangaro musu saman fuskokinsu. Yanda laɓɓansu ke rawa zai baka tabbacin magana suke son yi amma sun kasa saboda ruɗani. Jay yaɗan murmusa yana mai lumshe idanunsa ya buɗe alamar tabbatar musu da wadda suke hasashen ce ba mafarki bane ko gizago. Cikin ƙarfin hali Ummah Babba tace, “Yarona da gaske kake Yaya Bilkisu ce a gabanmu ba mafarkin da muka sabayi bane?”. Yanzunma kansa ya jinjina musu, ya kuma ja hannayensu har gaban Umm-Anum da alamu ya nuna suman zaune tayi. Hannayensu ya saka a cikin nata yana sake faɗaɗa fuskarsa da murmushi yaja jikinsa baya.
           A gaban Umm-Anum Ummah ƙarama da Ummah babba suka zube suna fashewa da kuka mai tsuma rai da cin zukata. Umm-Anum ta kawo nannauyan numfashi lokacin da suka rungumeta su duka biyun a jikinsu.
       Su Bilkisu dake kallonsu suma hawayen sukeyi, Jawaad kansa sai da ƙwalla ta cika masa idanu, amma jarumta ta saka shi haɗiye kayansa ya koma cikin kujera ya zauna yana jin wani irin matsanancin farin cikin da ƙirjinsa ma ke neman gaza ɗauka. Su Ummah sunkai kusan mintuna huɗu zuwa biyar a jikin Umm-Anum suna raira kuka kafin su saki juna, hannayenta ta ɗaura saman kumatunsu tana shafawa da murmushi saman fuskarta ga kuma hawaye, suma dai murmushin sukeyi hannayensu duka akan nata kumatun suna share mata nata hawayen. “Ashe Mariya ta da Wasila basu girmaba har yanzun? Ashe shagwaɓar nan da akema Yaya tana nan ba'a fasaba”. Dariya ta kwacema su Ummah lokaci guda da kuka, jikinta suka sake faɗawa ta rungumesu tana dariya. Su ma ƴaƴansu dariyar sukeyi da hawaye banda Jay da murmushi ne kawai a saman fuskar tasa.
       Da sauri Umm-Anum ta sake ɗagosu tana faɗin, “Ina Rahmah take ita kuma? Ko ba'a nan take aure ba?”. Duk ƙasa sukai da kawunansu hawaye masu zafi sosai na sake rige-rigen fitowa daga idanunsu, Umm-Anum ta shiga girgiza kanta a hankali tana kallonsu a tsorace, “Karku cemin na rasa Rahmah Mariya, kar kucemin rabuwa ta har abada nayi da Rahmah dan ALLAH” “Sai dai haƙuri Yayah, Rahma ta jima da barinmu gaba ɗaya, ta tafi tafiya mai nisan zango da babu iyakar sake ganin juna sai idan ALLAH ya ƙaddara hakan a can wata rana”. Ummah babba ta faɗa zuciyarta na mata zogi tamkar a yaune Rahmah tabar duniya. Yanzun kam Umm-Anum ce ta fashe da kuka mai tsuma rai da cin zuciya, tana son Rahmah, tana ƙaunar Rahma sosai, dan tafi shaƙuwa da ita a kaf cikin ƴan uwanta.
       Ganin kukan nasu yana neman yin yawa gashi ha

r ana kiran sallar isha'i sai Jay yay gyaran murya. ɗagowa sukai duk suka kallesa. Ya sakar musu murmushi da waro idanunsa waje kaɗan ya miƙa musu kwalin tissue da ya ɗauka saman centre table. Babu musu suka amsa. “Yauwa Momys ɗina ababen alfaharina, kukan ya isa haka nan kar ku ƙarar mana da hawayenku, lokacin kuka ya wuce yanzu farin ciki ake buƙata da godiyar ALLAH da ya kawo ranar da ba'a taɓa tunani ko tsamanin zuwanta ba, idan kuna kuka mu kuma mi zamuyi to?”. Cikin kaɗa kai Ummah babba tace, “Hakane Jawaad, ALLAH yay maka albarka kaida sauran ƴan uwanka kaji, a ina ka gano mana Zuciyarmu ne yaron albarka?”. “Ihhhmmm karku damu zan faɗa muku komai sweet Ummahs ɗina, amma ba yanzu ba sai tsohon can shima yana gefena”. Daƙƙuwa Ummah ƙarama tai masa tana faɗin, “Sai dai idan iyayenka ne tsoffi”. Dariya ce ta nema kufcema su Bilkisu, suka saka hannaye duk suka kare bakunansu banda Aunty Batool da tayi abunta sosai. Miƙewa yay ya dungurema Aunty Batool kai yay ficewarsa domin yin sallar isha'i.
          Bayan sallar isha'i natsuwa da ga UBANGIJI ta kuma saukar musu a zukata, duk da su Ummah suna ƙage da sonjin wani abu daga yayar tasu, kamar yanda itama a ƙagen take sai Jay ya hana, a cewarsa sai sunci sun ƙoshi sannan hakan zata kasance. Babu yanda suka iya suka yarda da batunsa, dan suma sunsan ya cancanci Umm-Anum taci abin ma ta kwanta ta huta, sai dai zukatansu bazasu iya jure hakanba.
      Ummah babba da kanta ta bama Anuwar da Anum abinci a baki cike da so da ƙauna, hakama Umm-Anum ta bama Aunty Batool da Nabeelah da Bilkisu, Jay kuma Ummah ƙarama ta bashi. Cikin wani irin farin ciki mai wahalar misaltuwa sukaci abincin suka ƙoshi, dan Umm-Anum har su Ummah ma sai da ta dinga basu a baki da kanta. Abin dolene ya sakaka kuka ya kuma birgeka. Sai da sukai nak da girki suka godema UBANGIJIN daya basu badan ƙarfinsu ba ba kuma dan sunfi kowa ba sannan su bily suka tattare wajen tas. Da taimakon aunty Batool da Nabeelah da Anum suka wanke komai tsaf. Yayinda a falo kuma Jawaad ke ta bama su Ummah labarin yanda komai ya kasance game da ganin Umm-Anum ɗin duk da dama tun a wancan lokacin ya labarta musu a sanadin Bilkisu ne. Wata iriyar ƙauna da soyayyar Bilkisu sai ta ƙara faɗaɗa da daɗuwa a cikin zukatansu. Duk yanda mai hasashe zaiyi tunaninta a zukatansu tafi gaban hakan ta wuce.
        Sabon babin fira aka buɗe a cikin falon ba tare da sunma tuna darene ba ranaba, babu mai kallon lokaci babu mai tunawa ma da shi. Ba suba ko Jay da baisan yawan surutu yau sai yaji hakan bai gunduresa ba, wani wajen ayi kuka wani wajen ayi dariya, wani wajen ayi tausayi da al'ajabi. Haka kawai bilkisu ta tsinci kanta da yin matsanancin kuka akan labarin Aunty Mah-mah (Rahmah), haka kawai taji tana ƙwaɗayin ganinta koda kuwa a hotone. Hakama Umm-Anum ta shiga matsanancin mamaki da jin wai Bilkisu ba ɗiyar Rahmah bace ba. Yayinda shi kuma Jawaad al'amarin yay masa tsaye cak a zuciya baisan dalili ba, kawai yanaji a ransa kamar akwai wani abu dake a binne game da rayuwar bilkisun, musamman idan ya tuna da maganar baba ƙaura akan duhun dake biye da Bilkisun, da kuma furucin baba ƙauran a jiya da yaje wajensa saboda kiran da yay masa. ‘Kai anya kuwa babu wani abu........?’ ya faɗa a cikin ransa yana kafe Bilkisu da idanu harta tsargu ta ɗan ɗago suka haɗa ido.
            Barci ma da kansa yasan inda yake zuwa yay sata, dan kuwa idanun waɗanan bayin ALLAH ko gyangyaɗi basaji balle ai maganar barci, suna zaune dingangan har agogo ya nuna ƙarfe uku saura na dare. Jay ne ya katse firar tasu da roƙonsu akan suje su kwanta haka da safe idan ALLAH ya kaimu saisu ɗora. Badan sunso hakan ba suka miƙe dan suma susan Umm-Anum na buƙatar ace ta huta kodan doguwar tafiyar da tayo wadda bata saba ba. Su mamaki ma abin ya basu dan basusan lokaci yaja haka ba, jima suke tamkar daren bai wuce ƙarfe goma ba. Dole dai yau su kwana gidan ɗansu.
       Ummah babba Umm-Anum da Ummah ƙarama ɗakin bily aka kaisu su kwanta tare da ƴar uwarsu, duk da dai ba kwanciyar sukaiba wani babin sabuwar hirar suka sake buɗewa ma su. Batool da Anum da Nabeelah kuma ɗaki

n dake kusa dana Bilkisu, Anuwar yana a ɗakin baƙi. Jay ya nufi nasa ɗakin, Bilkisu na shirin shigewa wajensu Nabeelah Ummah ƙarama ta korata ɗakin Jawaad.

        Sosai kunya ta lulluɓeni har inaji kamar ƙasa ta tsage na shige, to amma yaya na iya suɗin ba abin wasana bane balle nai tunanin musu gardama ma, haka na nufi sashen nasa kamar na nutse dan kunya. Ina jiyo su Nabeelah namin dariya harda Yah Anuwar. Sam banso hakanba, dan naso ace mun samu nisa da juna ni da shi koda na kwanaki biyu ne dan ya fahimci inajin zafin abinda ke faruwa tsakaninsa da ƴan uwana, ƙila ta hakan zan samu ya faɗamin abinda ke faruwar. Badan a ciwon kan da nake ji ba da falo zanyi zamana na ƙarasa daren, haka dai na daure fuska a ciskule na nufi bedroom ɗinsa, ciki ciki nai sallama na shiga, yana kwance a saman gado da ga shi sai noxer kawai, idanunsa a rufe suke amma na tabbata ba barci yake ba, na ɗauke kaina daga garesa na nufi bayi. Ban wani jimaba na fito dan fitsari kawai nayi da abinda baza'a rasaba. Yanda na barsa haka na fito na samesa, bani da kaya a ɗakin, sai naita tunanin mizan saka na kwanta dan bazan iya barci da kayan jikina ba. Ganin lokaci na sake ja ga zazzaɓi nama neman saukarmin yasa na nufi Wadrobe ɗinsa, cikin sa'a kuwa idanuna saka sauka akan t-shirt ɗinsa mara nauyi ruwan toka, nasan indai na saka zata sakkomin dan babbace kuma girman ba ɗaya ba.
        Zagayawa nai ta ɗayan gefen na kwanta can ƙarshen gado na juya masa baya.....
       “K har kin isa mu kwanta a gado ɗaya ki juyamin baya!”. Na tsinkayi saukar muryarsa da furucinsa a fusace cikin kunnuwana. Ɗan rintse idanu nayi ina haɗiyar yawu da ƙyar, zuciyata sai harbawa take da sauri-sauri na tsoro. A hankali na juyo ina tura baki da sake ɓata fuska sosai, abin mamaki har yanzu yana a yanda yake. A ƙasan ido naɗan hararesa naja bargo na rufe har fuskata ma.
         Wani haushi ya sake kume zuciyar Jay, jiyake kamar yay mata filla-filla ɗin da saita ƙarasa daren da kuka, sai dai yanata ƙoƙarin danne fushinsa kawai.
        Ba ƙaramar razana naiba jin an fincike bargon, na waro idanuna dake cika da ƙwalla a kansa, fisgoni yay na faɗa jikinsa ya matseni tsam-tsam, wani marayan kuka na buɗe baki zan sakar masa sai dai kuma ya hana hakan ta hanyar baƙar muguntarsa da ya ƙware a iyawa, nasan bani da wani ƙarfin ƙwatar kaina daga garesa musamman ma a irin wannan lokacin da sam banajina ma garas. Ɓacin ransa baisa shi kasa bidani cikin salon natsuwa da salo mai tsayawa a zuciya ba.............

....
..........✍

ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[2/12, 7:51 PM] Wasila: Bilyn Abdull 📚:
Page 57
          
_______________________________
SHAHUDAH
_______________

                 Saukar su Umm-Anum ƙasar haihuwarta tayi dai-dai da komawar Shahudah gida. Mom da Aamilah ne kawai a gidan, Dad ya fita tun bayan barin su Jay gidan. Waya Mom keyi da Mama Atika. A take ta saki wayar ƙasa ta tarwashe bisa tiles jikinta na tsananin tsuma.
         Shahudah da ke cikin wani yanayi kamar ba'a hayyacintaba ta ƙaraso cikin falon tana tangaɗi ta zube saman carpet. Da ga Mom har Aamilah zubewa sukai a gabanta jikinsu na rawa, sai kuma Aamilah ta miƙe da sauri taje ta leƙa waje. Babu kowa sai maigadi daya taimakama Shahudah ta shigo ya juya zai koma wajen gate. Komawa falon Aamilah tayi bayan ta rufe ƙofar ruf ta garƙama mata key. Ta koma wajen su Mom da gudu tana faɗin “Mom ita kaɗaice fa wlhy babu ɗan iskan”.
     Mom tace, “Nashiga Uku ni Aysha, Shahudah daga ina kike haka? Miyayi miki ne?”. Bata da mai amsa mata waɗanan tambayoyin dan Shahudah sai faman lumshe idanu kawai take. Mom ta ƙanƙameta a jikinta ta fashe da kuka tana jama ɗan-fir'auna mugayen addu'oi. Suna cikin haka akai knocking ƙofar, duk ɗagowa sukai suka zubama ƙofar falon ido kawai, sai dai daga Mom ɗin har Aamilah babu wanda ya iya motsawa. Shiru ba'a sake bugawar ba, hakan yasa suka share suka maida hankalinsu ga Shahudah.
        Salman dake buga ƙofa ganin ba'a buɗeba sai ya zagayo ta kitchen, shikansa ba ƙaramin mamakin ganin Shahudah yay ba, jikinsa har rawa yake wajen ƙoƙarin kiran Dad ya sanar masa Shahudah ta dawo.

        Cikin mintuna ƙalilan sai ga Dad a hargitse kamar zai tashi sama, yanda yake buga ƙofar kawai kasan babu lafiya, Aamilah ta buɗe masa tana matsawa ta bashi hanya, da sauri ya shigo. A gaban Shahudah ya durƙushe tare da maido kanta jikinsa idanunsa na kaɗawa lokaci guda dan ɓacin rai. “Shine ya kawota?”. Yay tambayar yana kallon Mom. “Nima ban saniba Dadynsu, shigowarta kawai muka gani ita kaɗai. Leɓe Dad ya taune da ƙarfi, ya kalli Salman dake tsaye cikin damuwa shima, “Kai Salman kiramin Dr Tayyib, ke kuma Aamilah kiramin maigadi, ai bazai rasa sanin wanda ya ajiyeta ba”.
         Babu jimawa maigadi da Aamilah suka dawo falon, cikin girmamawa Maigadi ya rusina yana gaida Mom. Bata amsa masaba, sai Dad ne ya jefa masa tambaya, “Yaya akai Mamana ta dawo gidan nan?”. “Wlhy Alhaji ban saniba, kawai naji nishin mutumne a jikin gate, shine na leƙa nama zata ko yaran nanne masu addabama mutane, sai naci arba da ita kwance jikin gate ɗin, sai kuma ƙurar mota da nake zargin a ita aka ajiyeta”. Ran Dad ya ƙara digunzuma sosai, yay ma maigadi nuni da hannu alamar ya tafi kawai.
     Maigadi na fita Dr Tayyeb na isowa gidan, bai zaman ɓata lokaciba ya shiga bama Shahudah taimakon gaggawa bayan an kaita ɗakin Mom an kwantar a gado. Duk wani taimakon da ake buƙata Dr Tayyeb ya bata, ya kuma tabbatar musu da cewar babu wata matsala normal zata farka insha ALLAH, ruɗanine ya sakata shiga wannan halin kawai. Hakanne ya basu ƴar nutsuwa, har suka kira su Mama Atika suka sanar musu

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login