Showing 42001 words to 45000 words out of 261165 words
Chapter 15 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete
kamar yanda shima ya ɗauke nasa, basu wani jimaba wancan yay ciki shi kuma ya nufi hanyar fita. Bin bayansa nayi ina ƙunƙuni, danni ɓatamin lokaci aketa famanyi.
Kusan a tare muka ƙarisa jikin motar da nake ƙyautata zaton da ita yazo, nayi zaton gimba ne ya kawosa, amma sai naga saɓanin hakan, dan mazaunin driver ya buɗe ya shiga, ta gefen nasa naje na tsaya, nace masa zan wuce gida nima.
Kallona yay ya ɗauke idonsa, sai da yay ma motar key, batare da ya kalleni ba yace, “Kina ɓatan lokaci fa, ko jira kike na ɗaukeki na sakaki ne?”.
‘Innalillahi...’ kuji sabon sharri, na faɗa a raina ina kumbura fuska, danni dama abinda nake gudu kenan yace mu tafi tare, to amma yaya zanyi, babu fuskar wargi a garesa, dan haka na zagaya na buɗe gefen mai zaman banza na zauna.
Baice komaiba yay reverse tare da harba motar saman titi da ɗanbanzan gudu. Idanu na lumshe ina faɗin ‘Ga wanda yafi Yah Qaseem shegen gudu da mota’. Babu mai magana a cikinmu, sai shi da ke murza sitiyarin a hankali tamkar bayaso. Bai tambayeni ina zaniba, nikuma ban sanar masaba inajin shakkar magana dan sai wani shan ƙamshi yakeyi fuskarsa a ɗaure sosai.
Tafiyar da bata wuce mintuna goma sha biyu ba muka iso wani waje, da mamaki na kalli abinda aka rubuta (LADIES MIRROR) sannan na kallesa shima, ta yaya akai yasan saloon zanzo to?, cikin ƙarfin hali nace, “Nifa ba nan nake zuwa ba”.
ATM ya miƙomin batare daya kula maganata ba, nai ƙasa da kaina ina sake faɗin, “Ai ambani kuɗin a gida”. Bai tanka minba nanma, sai ajiyemin atm ɗin da yay a kan cinya tare da ƙaramar takarda. Tamkar zan fasa kuka haka naji, na buɗe motar na fice ina sake juya al'amarin mutumin nan a raina, aunty Shahudah tasha wahala yasin, ni saima ta bani tausayi, ƙilama wannan halin nasane ya sakata gudowa gida ‘Mtsoww’. Da wannan tunanin na ƙarasa cikin wajen da ya gama haɗuwa, dan yafi inda nake zuwa nesa ba kusaba. gashi ƙaton gaske. Yanda ma'aikatan wajen suka tarbeni sai abin yaban mamaki, abin akwai birgewa. Sai da na zaunane bayan na sanar musu abinda nake buƙata sannan na sami duba takardar daya haɗomin da ita, sai naga ashe password ɗin Atm ɗin nasane ya rubuta min, samun kaina nayi dayin murmushi.
An wanke min kaina tsaf da tafin ƙafa, aka gyaramin ƙumba, wadda ta wanke min kance ta bani shawarar nayi kitso, a cewarta su inhar zasu maka aiki suna duba yanayin gashinka su ɗoraka a ƙyaƙyƙyawan tsarin da bazai karye ba, kuma zai dinga tsaho, daɗin hakan da mutane ke shigane ke sakasu sake dawowa daga nan saisu zama basu da wajen zuwa sai nan. Murmushi na mata, ina cewa “Kodai za'amin daɗin bakin ƴan kasuwa ne?”. Kanta ta girgiza tana murmushi, “Sam ba haka bane auntyna, duk abinda zakiji daga bakina shine gaskiya, Gimbiya tana ajiye ingantattun kayan aiki da nagarta a wajen nan, waɗanda daga kowacce duniya kake zaka yaba”. Kasancewar nasan boss ba jirana zai tsaya yiba sai nace, “Okey babu damuwa amin kaɗan to”.
Wani sashen daban da inda akai min wankin kai aka kaini, mutum uku kawai akema kitso, muka gaisa sannan na zauna nima, wadda zataimin ce ta iso kusa dani, muna cikinyi idanuna suka sauka akan ƙaton hoton dake sama a wajen, wanda naga wanima a can inda na baro, sai dai nesa da yay danine yasa banga waɗanda ke a jikiba, anan kam ras nake kallonsu kamar nayi magana su amsa, ƙyaƙyƙyawar mace hamshaƙiya ta gaske ce, tasha alƙyabba mai azabar ƙyau dake nuna jinin sarautace ita, gefenta ma ƙyaƙyƙyawan namijine mai tarin kamala da cikar haiba, kai tsaye na ganesa shi, dan kuwa dai sarkinmu ne Muhammad Sameer Saifudden, a raina nace ‘to ko matarsa ce wannan ɗin?’....... Maganar wadda kemin kitso ta katse min tunani da faɗin, “Duk wanda ya zauna nan baya gajiya da kallon hoton nan na sarauniya MUNAYA uwargida ga adalin sarkinmu, ita kanta wani lokacin har kishin hakan takeyi idan ta shigo takan juya hoton ya ɗau tsahon lokaci a kife”. Duk yanda naso shareta saina kasa, nai guntun murmushi, nace, “To miyasa zata barshi tunda ba dokar ƙasace ta tilasta a ajiyeba?”. kafin ta samu damar bani amsa, ƙyawawan ƴammata uku da yara biyu suka shigo wajen, biyu masu tsananin kama da Sarki Sameer, sauran kuma naɗan yanayi dasu sai dai basa tsananin kama, ukun zamu iya sa'anni dasu, biyun kuwa bazasu wuce shekara goma sha uku ba. Cike da girmamawa naga ma'aikatan na gaishesu, sai dai yanda suke amsawa babu wulaƙanci sai suka birgeni, gashi sai murmushi suke mana, nima sai na maida musu murmushin kamar yanda sukeyi, cikin manyan ɗaya ta miƙomin hannu mukai musabaha tana faɗin, “Kitsonki yayi ƙyau”. “Nagode” nace mata a taƙaice. Sauranma duk muka gaisa, suka kuma gaisa da sauran da muke zaune.
Ɗaya a Ƙaramar tace, “Aunty Amaturrahman nidai irin kitson auntyn nan nakeso” tai maganar tana nunani. Wadda aka kira da Amaturrahman ɗin ta amsa mata da cewar, “Okey Safah sai a miki ai, burina dai ayi kitson kamar yanda Ummu tace”. Ɗayar tai ƴar dariya idonta akan waya, tace, “Mudai dan ALLAH karki cikamana kunnuwa da ihunkin nan Safah, Marwah dai nasan bamai jinta, inba hakaba ALLAH muka koma saina bama kowa labari a masarauta har Momma”. Ɓata fuska yarinyar tayi, tace, “Ai bazanyiba, salon kisa su Jalaludden Su ringa rainani ko Aunty Meenal? Ni wlhy wajen Uncle Sauban zan koma india can babu ruwan mutum da wani kitso ko nabi Aunty Amatullah Niger”. Dariya sukai mata, banda wadda suka kira Marwah shugabar miskilanci da jin kai, daka ganta kaga Sarki Sameer Saifudden sak kamar yay kaki ya ajiye, ni dai ina saurarensu ne sama-sama. Bayan an gama minne na miƙe nai musu sallama na fita, ashe wajen ɗaukko Atm ɗin boss dana saka a jakka gudun basai naje wajen biya naita dube-dube ba na yarda ɗan abinda ID cards ɗina suke ciki da wasu passport ɗina dake a tare.
Ina cikin biyan kuɗin wayata tai ring, na kalla kamar bazan ɗagaba saboda sabuwar Number ce sai kuma na ɗauka na saka a kunne batare da nayi magana ba, daga canma shiru akayi, hakanne ya sani cewa, “Asslamu alaikum wanene?”. “Kin gama?” muryar wanda banyi zato ko tsammaniba ta daki kunnena a bazata. Da sauri na cire wayar a kunnena na sake kallon Number, gabana sai faɗuwa yakeyi, dan nasan nidai baida Number ta, jin an yanke wayar na amshi atm ɗin da ake miƙomin na fice da sauri domin tabbatarwa.
Jinai wani abu ya tsirgamin daga saman kai har yatsan ƙafa saboda ganin motarsa fake a inda ya tsaya ɗazun, a fili nace, “Mikenan? Zaunawa yay jirana?’. Azababben horn ɗin daya danna ne ya sani nufar motar tamkar mai tsoron hakan. Nasan duk abinda zan zaunayi bayan shiga motar laifi zai zama kuma, hakan yasa na buɗe na shiga. Baiko kalleniba ya tada motar muka fice. Sai da muka ɗauki hanya nai dauriyar cewa, “Dan ALLAH kayi haƙuri sir, wlhy nazata tafiya kayi ne, shiyyasa da suka ce na zauna sumin kitso na yarda”. harara ya ballamin ya ɗauke kansa ya maida ga titi. Ban sake cewa komaiba, nacigaba da kallon titi, kamar yanda shima yake gudu kamar shi kaɗaine a titin. Wayarsa ce ta shiga ruri, batare da ya kalli waye ba ya ɗaga da hannunsa na haggu yasa a Hans free, daga can akai sallama, ya amsa cikin ladabi tamkar bashiba, “Ya mukai da kai ranar juma'a akan zuwa meeting ɗin nan Jawaad?”. yay saurin dafe kansa da faɗin, “Oh ALLAH, kayi haƙuri Uncle, naɗan fita wani wajene amma insha ALLAH gani nan zuwa”. “To ALLAH yasa” daga can aka faɗa ana yanke wayar. Huci ya furzar yana ɗan bugar sitiyarin, Na ɗan saci kallonsa na ɗauke kaina, sai kawai naga ya canja hanya saɓanin inda muke. Nidai ban iya cewa komaiba, domin ko wainar dake cikin tanda a yau ta fini samun freedom ɗin kanta. Sai da naga ya shigo layin gidansune na iya kallonsa tamkar zanyi kuka. “Sir wlhy nifa akwai inda zanje”. bai kulaniba, yay fakin a waje batare da mun shiga cikin gidanba, sai da ya kashe motar sannan ya juyo ya kalleni.
A bazata kawai naji yace, “Inga kitson”. “Uhyim!” na faɗa ina ɗago kai da sauri da waro masa idanu cikin tsagwaron firgicin jin abinda yace. Banga alamun shi ya fuskanci abinda yay ɗin kamar yanada ban al'ajabiba, dan ya wani sake haɗe fuska fiye da da.
“Karki cinyeni da idanunkin nan malama, ɗaukesu a kaina, zan ganine idan sun iya sai nake kai matata can”.
Fuska na kumbura cikin suɓutar baki nace, “Aunty Shahudahr da batason kitso ɗince zataje?”. Saukar yatsun hannunsa kawai naji kan laɓɓana ya ɗallamin da ƙarfi, azabar zafin danajine ya sakani saurin dafe bakin idanuna na cika da ƙwalla na kalleshi, ya dallamin uwar harar tamkar zai haɗiyeni da idanun, saurin maida kaina nayi gefe hawayen da suka cikan ido suka sami damar silalomin, dan da gaske naji zafi. kafin nagama fita daga zafinne, naji hannunsa saman kaina ya zame gyalen dana yana da hular, ya saukesu saman kafaɗata, yana faɗin, “Magulmaciya waye ya tambayeki to?”. Maybe idan nace muku kaɗan ya rage zuciyata ta fito ta baki a wannan lokacin bazaku yardaba, jikina kansa tsuma yake, lokaci ɗaya dukkan ilahirin gashin jikina ya miƙe domin jin ya ja jelar gashina dake ɗaure da ribbon yana faɗin “Ashe ba ƙwaiƙwaido bace?” yay maganar a can ƙasan maƙoshi yana ɗauka hular yana ƙoƙarin maidamin a kai, na rintse idanuna ina fisgar numfashi da ƙyar tamkar mai Asthma, ya ɗauka gyalenma ya naɗamin kamar yanda ya gansa sannan ya kalleni fuska a matuƙar ɗaure, yace, “Kalleni nan”. Daƙyar na iya juriyar ɗagowa na zuba idanuna cikin nashi, yanda ya kafeni da idanu sai na kasa jurewa nai ƙasa da kaina saboda wasu abubuwa danaga suna fitowa a idanunsa waɗanda ban taɓa ganiba, ga idon ya kaɗa da jaa kaɗan tamkar wanda yake cikin fushi. Cikin ɗacin murya da saukemin wata harara mai firgitarwa da ban mamaki yace, “Hankalinki ya kwanta waɗanda kika fitama tallan jikin sun gani harsun tanka, Saina sauyama wannan fuskar taki kamanni idan na sake ganin kin fita ba hijjab”. Yana gama faɗa ya buɗe motar ya fice abinsa batare da ya sake kallona ba.
Tamkar sokuwa haka na bisa da kallo, shiko ko waiwayena baiyiba har ya isa jikin ƙaton gate ɗin ya tura ƙaramar ƙofar ya shiga. Baya nai luuu na faɗa jikin kujerar na jingina bayana, ina sauke wata nannauyar ajiyar zuciya da lumshe idanu, nace, ‘Na shiga uku ni balkisu’. naja kusan mintuna uku a haka kafin na samu numfashina ya dai-daita. Gaba ɗaya man kaina ya gama tsiyayewa, nama rasa yanda zan fassara abun nasa, nakai hannu na shafa laɓɓana da har yanzu sukemin zafi, sai kuma na buɗe ido na kalli mirror, har laɓɓana sunyi ja, a fili nace, ‘Mugu, aiko Yah Qassem dake dani bai kafan wannan dokarba saishi daga mijin Auntyna’. Sai kuma nai saurin dafe bakin na kalli inda ya tashi sai kace ancemin gashi ya dawo. Da sauri na sake rintse idanu da dafe kai, a fili na sake faɗin, ‘Ya rabbi ka kawomin ɗauki, Mutumin nan zai kasheni’. Sai kuma na harari ƙofar gate ɗin na buɗe motar da sauri na fice abina,
★★
Jawaad kam Haka kawai ya tsinci kansa dayin murmushi lokacin daya buɗe gate ɗin ya shiga gida, sai kuma ya taɓe baki tare da jan ƙaramin tsaki ya nufi sashen mama Atika yana ƙwafa mai nuna takaicin wani abu da har yanzu yake cimasa rai. yasan dai taron meeting ɗin bai wuce can ɓangaren mama Atika ba saboda shegen fitinar tsohuwar. Da sallama ya shiga, suka amsa kusan su duka alamar shi ake jira, wani iri yaji a ransa saboda ganin harda kakansa dasu Umma, yadai samu waje ya zauna sannan ya gaidasu.
★★★★★★★
A LADIES MIRROR kuwa lokacin da abinda ID cards ɗin Bily suke ciki ya faɗi akan idon Safah ne, amma sai taƙi magana, sai da ta tabbatar bily ta daɗe da barin wajen sannan ta ɗauka tana faɗin, “Lah Aunty Meenal diba kiga auntyn nan da nace amin irin kitsontace ta yarda”. Duk kallonta sukayi, Amaturrahman ta dalla mata harara da faɗin, “Shine dan iskanci bakiyi maganaba sai yanzun?”. Baki ta tura gaba tana langaɓe kai gefe, “To ai mantawa nayi ko”. Amatullah tai dariya da cewa, “Kai Safah lamarinki sai ke wlhy, saiki bada a ajiye mata dan nasan zata dawo nema”. Da sauri tace, “A'a aunty Ama mu kai mata dai”. Marwah da tun ɗazun bata kula kowaba tanata game a ipad ɗinta ta harari Safah. Ramawa Safah tai, cikin tsiwarta data gada wajen Munaya tace, “Miye kike wani hararana ke kuma malama?”. Lips Marwah ta cije like Sarki Sameer, ta ɗauke kanta batare data tanka mataba.
Duk yanda sukaso Safah ta bada a ajiyema bily saboda idan ta dawo nema ma'aikatan wajen su bata fir taƙi, daga ƙarshe Amaturrahman tayi kiran Ummu ta sanar mata, Sarauniya Munaya dake kishingiɗe a kilisarta ana tausa mata ƙafa ta girgiza kai kawai da lumshe ido, babu abinda Safah ta bari na halayyarta, ta tabbatar kuma akwai dalilin da yasata yin hakan, a hankali tace, “Kubarta tazo dashi, sai a nema yarinyar”. Amaturrahman tace, “Ummu yanzu nan biye mata zakiyi?” yanke wayar Munaya tayi batare da ta bama Amaturrahman amsaba. Dole badan sun soba akabi abinda Safah keso sukatafi dashi bayan an kammala musu kitso su duka kamar yanda Ummu ta korosu suyi badan sunso hakanba..............✍
Maison zuwa gagara badau ya shirya muje gaida Sarki Sameer Saifudden da gimbiya Munaya😉😉lol.
ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏🏻.[11/30/2020, 12:56 PM] HASNA✍🏻: Bilyn Abdull 📚:
Page 16
...............Napep na samu na tare nai tafiyata gidan Inna zainabu. Can nai zamana mukasha hira da Lawusa da a yanzu muke ɗasawa har bayan sallar isha'i sannan na nufo gida.
★★★★★
Bayan an buɗe taro da addu'a Uncle Nasir ya fara jawabi kamar haka. “Kamar yanda kowa ya sani mun fara tattaunawa akan maganar zaman Jawaad babu aure a kwanakin baya, har takai mukai masa tayin cikin yaran gidannan ko akwai wadda ya keso, sai dai ya nuna a lokacin zaiyi tunani, tun daga wancan lokacin ban sakeji daga gareshiba, to magana ta gaskiya mun gaji da ganinsa yana yawo a gari haka ana zaginmu, shi kansa bama girmansa bane, ƙannen-ƙannen bayansa ma gasunan duk da iyalansu har da ƴaƴa, yakamata Jawaad kaima kanka faɗa, dan lokaci bawai zai zauna jiranka baneba, kai kaɗai Abdul-aziz ya haifa, zamuso ganin ƴaƴanka a duniya kamar yanda mukasan da yanada rai zai ɗokantu da haka shima. A wannan karon ba shawara muke bakaba, umarnine, shiyyasama mukazo da Alhaji Baba domin ya zama shaida, tare da iyayenka, dolene a wannan karon kayi aure, ka zaɓi mace ɗaya a cikin ƴaƴan gidannan koma fiye da ɗayar mukuma zamu aura maka”.
Jawaad da kansa ke ƙasa yay guntun murmushi domin son ɓoye ɓacin ransa, batare da ya ɗagoba yace, “Uncle ku gafarceni, bazan jaku da nisaba, duk cikin yaran gidannan bazan iya auren kowaba, dan kallon ƙannena nake musu tamkar ciki ɗaya...” da sauri Uncle Uwaisu yace, “Ai tamkar kace, bawai hakan bane, tunda babu ta inda ALLAH ya haramta maka, Jawaad bamason shirme, garama ka zaɓa komu mu zaɓa maka, kokuma ka ɗauki zaɓi na biyu, wato ka maida matarka ɗakinta kuje kuyi haƙuru da juna tunda yarinyarnan ta horu kuma tana sonka”. Yanzu kam kasa daurewa yay saida ya ɗago kansa ya kalli Uncle Uwaisu, kamar zaiyi magana sai kuma yay shiru saboda gargaɗi da Alhaji Baba yay masa da ido, kansa ya maida ƙasa yana sauke ajiyar zuciya.
Uncle Sulaiman yace, “Son!” ɗago kai Jawaad yay ya kalli Uncle ɗin nasa da yake matuƙar so saboda ƙyawun halinsa, yace, “Na'am Uncle”. “Ko Kanada wadda kake sone?”. Ƙasa Jay ya maida kansa yana motsa laɓɓansa, sai dai babu maijin mi yake cewa, Uncle Taheer ya katsesa da faɗin, “Kai muke saurare Jawaad”. Batare daya ɗagoba ya girgiza musu kai alamar a'a. Shiru falon ya ɗauka kowa ya zuba masa idonu, shi kuma yaƙi kallonsu. Mama Zuhurah da bata da yawan magana tace, “To Jawaad ya kakeso ayi kenan? Yanzu kai kafijin daɗin kullum aita zaman meeting akanka akan maganar kaƙi aure, ka rufa mana asiri ka fidda kanka damu iyayenka daga zargi da zunɗen al'umma kaji, ƴar uwarka na sonka, tayi nadamar kuskuren datai a baya, kayi haƙuri a maida aurenku kaji”.
Ɗagowa yay zaiyi magana fitowar Shahudah ta katse masa hanzari, gabansa taje ta durƙusa tamkar yanda Mama Atika da Mom suka kitsa mata, ta fashe da kuka tare da kama ƙafafunsa, cikin gurɓatacciyar hausarta da harshen turancin da tafi ƙwarewa ya cinye tace, “Bb dan ALLAH ka gafarceni, wlhy nayi nadamar abinda na aikata, nakumayi alƙawrin bazan sakeba, na yarda zan haihu maka yara komai yawan da kake buƙata yanzun, idan ka barni mutuwa zanyi wlhy, dan ALLAH ka ceci rayuwata Bb...” hannunta ya ture daga saman ƙafarsa yana hararta, “Kima daina ɓata lokacinki, indai haihuwace bana buƙata daga gareki Hudah, karki damu kije kicigaba da cin moriyar ƙuruciyarki kinji, indai nine kima saka a ranki baki taɓa sanin mai kama daniba dan mun rabu kenan”. Fashewa tai da matsanancin kuka yanzunkam fiye da da, dan har ƙasan ranta kalamansa sun masifar sosa mata zuciya, ta dafe kanta dake juya mata, babu zato sai kawai ganinta ƙasa sukai ta yanke jiki ta faɗi. Gaba ɗaya ƴan falon da suka zuba musu ido suka miƙe, shi kansa Jawaad ɗin kallonta yake, dan ya zata salon iskancinta ne, sai daga baya da aketa jijjigata babu alamar rai tattare da itane ya fuskanci babu wasa a lamarinta, gaba ɗaya falon ya rikice, dan iya ƙoƙari anyi Shahudah taƙi farfaɗowa, Mom sai kuka take da sambatu.
Dole aka kwashi Shahudah zuwa asibiti da gaggawa kuwa, dan wasunsu harsu fidda ran da gaske ta mutu.
★★★★★★★
Tun a gate baba maigadi yake sanarmi
n ai babu kowa a gidan duk suna asibiti aunty