Showing 84001 words to 87000 words out of 261165 words
Chapter 29 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete
mikukeson maidanine a gidannan kai da Shahudah? shin bazaka nutsu kai ka fahimci uzirinmuba, Na shiga uku ni Aysha, wane irin mugun asiri wannan yarinyar ta haɗaku da shine kaida yaronan Jawaad da kuke ɗaukar kowa ɗan iska akan lamarinta?”. Cikin zafin murya Qaseem yace, “Nifa kin bala'in cikani da surutu hajiya, Please ki barni nai aikin gabana Mtsooww!!”. Ya ƙare maganar dajan wani wawan tsaki yana ɗauke kansa ya cigaba da loda kayansa a motar. Mutuwar tsaye kawai Momy tai tana kallonsa, Aamilah ta kwashe da dariya tana kallonsu, “Faɗan Uwa da ɗa abin birgewa, kucigaba da gashi guys”. Baki Shahudah ta taɓe tana mai juya manyan idanunta alamar zubama Qaseem harara, tace, “Ɗan jaraba duk bakai kaja manaba, wani iyayi da ƙwala kai a farantinne ya kaika nacema banzar yarinyarnan ƙazamiya mara gata, idan da baka maƙale matanba ta gidan uwarwa aurena da naka zasu haɗu ballema har bb ya aikata haka, asararre kawai mai baƙar zuciyar tsiy.....”
Jikake tasss!! Qaseem da babu wanda ya lura da isowarsa gaban Shahudah ya sauke mata wani wawan mari, ƙasa ta zube tana garsheƙ
ar kuka daja masa ALLAH ya isa, to daman zuciyar ƴan mazan a kusa take, neman wanda zai amayarwa yakeyi, gashi ya samu cikin sauƙi, dan haka ya shigar tamkar an aikosa. Duk ihun da Aamilah keyi da Momy bai sauraresuba, sai ma tsarabar mari Aamilah ta samu itama, Momy kuwa ya hankaɗeta. Qaseem yanada Masifaffiyar zuciya irin wadda idan ta yunƙuro ɗinan sam bayajin bari, dan tamjar zugasama yake, sannan shifa cinnakane baisan na gidaba. Wanna. mugun zuciyan da ALLAH ya basu shida Jawaad itace ta hanasu zama ƙarƙashin inuwa ɗaya, dan kowa yanaji da kalar tasa, kawai shi Qaseem yafi Jawaad saurin fushine, dan Jawaad na dannewa yay kawaici har saika kaisa ƙarshe, amma ga Qaseem sam ba haka bane, sha yanzu magani yanzu, ga kuma ɗanbanzan riƙo saikace dangin kutare🤦🏻.
Iya gwargwadon iko babu algus Shahudah ta daku harma da Aamilah daya koma haɗawa daga ƙarshe, dama yanajin haushinsu akan abu biyu, dukan Bilkisu da jimata ciwo, saikuma gudunmawar da suka bada akan ai masa aure da Azeema. Daƙyar da suɗin goshi baba mai gadi da kuku suka amshi Shahudah da Aamilah a hannunsa, dan yay musu kaca-kaca abinka da farar fata, Shahudah harda fasa mata baki akai jini sai ɗiga yake. Yace, “ƙananun marasa kunya, daga yau idan harku kun cika tsagerune dan ALLAH kusake shiga cikin al'amurana”. Kuka kawai suke daga su har Momy, babu wanda ya iya tanka masa har kuku da baba mai gadi suka gama loda masa kayansa a motar, sashensu ya koma ya ɗakko sauran tarkacensa ya shige mota ya fice batare da ya sakebi takantaba.
Kai tsaye gidansa ya zarce, dama harya ajiye mai gadi tun jiya, kodaga waje kasan gidan ya haɗu, ya mugun ƙawatuwa da shukoki masu ƙamshi da daɗi, ga ƙamshin sabon fentima na tashi. Dakansa yayta shiga da kayan, da yake ALLAH yayisa mutum mai hanzari da zafin nama sai gashi ya gama sakasu ciki tas.
★★★★★
Bayan barin Qaseem gidan babu jimawa Dad ya dawo, iske Momy yay zaune ta zabga tagumi, Shahudah na kwance barcin wahala yay gaba da ita ta ɗora kanta a cinyar momyn. sai Salman da Aamilah dake lido a d/table. duk sannu sukai masa, ya amsa yana zama kusa da momy tare da kamo hannunta cikin nashi. “Humairah mike faruwane?”. Muryarta na rawa tace, “Qaseem ne ya tafi?”. “Ya tafi? Ina ya tafi to?”. “Muma bamu saniba, ya kwashe duk kayansa na gidannan”. Cikin taune leɓe Dad yace, “Bari dai zamuyi magana, yanzu tare nake dasu Alhaji Nasir suna falon baƙi, mun kira yaronan ne da aka ɗaura aurensa da mamana zaizo”. Zumbur Momy ta miƙe jikinta har rawa yake ta ture kan Shahudah batare data tuna tana jikinta tana barciba, tace, “Ya yarda ɗin zaizo Dadynsu?”. Fuskarsa ɗauke da murmushi yace, “Eh ya amince, drivern Alhaji Nasir ma yaje ɗakkosa”.
________________________________
Bayan Jawaad ya dawo daga sallar magriba shiryawa yay ya amsa kiran da Alhaji babba yay masa, kansa ciwo yake masa, amma bashi da ikon bijirema kiran kakan nasa, ballema yaji muryarsa wani iri kamar yana tare da damuwa, tun da ranama ya fahimci hakan, ya haƙurane kawai ya barsa da yace masa babu komai..
Fitowa yay yanata baza ƙamshi, sai dai fuskarnan a cinkushe babu walwala. ya tsaya suka gaisa da mai-gadi har yake tambayarsa gimba bai shigo bane?. mai-gadi yace, “Aiko bai isoba Oga, ni harma na fara tunanin ko lafiya? Dan tunda ya tafi bamuyi wayaba kuma kaga har lokacin daya saba dawowa ya shige amma shiru”. Jimm Jawaad yay alamar tunani, dan shima dai tunda gimba ya tafi basuyi wayarba kam, to wannan hargitsicinne ya ɗauke masa hankali gaba ɗaya har bai ɗauki hakan komaiba. Ya ɗan sauke numfashi yana kallon mai-gadin. baba bara dai naje na dawo, idan har lokacin bai shigeba saina nemesa naji mike faruwa?”. Mai gadi yace, “To to ba laifi oga, ALLAH ya maidoka lafiya”. “Amin” Jawaad ya faɗa yana ficewa, sai dai acan ƙasan zuciyar tasa maganar gimba taƙi gushewa.
A ƙofar gida ya iske Alhaji babba zai shiga massallaci, dan haka yay fakin anan waje ya fito suka shiga tare, bayan sun fito Alhaji baba yay sallama da mutane maƙwaftansa da ragowar ƴan anguwa masu salla anan kamar yanda ya saba, kafin ya kama
hannun Jawaad dake masa shagwaɓan shifa fura zaisha, Alhaji babba ya bada a siyo masa. Alhaji babba dake murmushi ya tsaya yana dungure masa kai, “Kai miyasa idan rikicinka ya motsa babu wanda ka raina saini? Kaje kaima su Mariya mana”. Fuska Jawaad ya yatsine saboda ciwon da kansa ke masa yace, “Nidai ka daina sawa gaban mamana na faɗuwa a darenan, kabama Tanimu ya sayo mani inba hakaba bazan sake zuwa kwana gidanka ba”. Dariya Alhaji babba yay da jan hannunsa suka cigaba da tafiya, yace, “Yoni ALLAH na tuba aina yayeka da zuwa kwanarmin gida, matarka ta jajiba nima na huta da rigimarka hakanan”. Jawaad yace, “Basai na ɗakkota muke kwana anan ɗin tareba”. “Bana gayya, ku zauna gidanku nima aure zanyo”. Ciki dauriya Jawaad ya ƙyalƙyale da dariya, koba komai yarage nauyin da zuciyarsa tayi da tattaunawa da kakan nasa, shi kansa Alhaji baba sai yaji damuwarsa ta sassauta.
Bayan sun zauna Alhaji baba ya zubama Jawaad fura mai ƙyau da daɗin gaske da bai rabo da ita ya dubesa, cike da jin daɗi yake shan furan sanyinta na ratsa masa zuciya da ƙirji. “Muhammad kasan miyasa na kiraka kuwa?”. Kallonsa Jay yayi ya girgiza kansa batare da yace komaiba. Alhaji baba ya ɗan sauke numfashi, murya a sanyaye yace, “Akan matarkane” Saida Jawaad ya haɗiye furan daya sha kafin yace, “Matata kuma?”...............✍
Ƙyan alƙawari cikawa, sai dai wanda na ɗauka ni ya gagara cikar dalilin birkicewar wattpad, harna fara canja page ɗinma sai ALLAH ya taimakeni ya dai-dai ta🤦🏻, page ɗinnan kaɗai gareni babu nagobe saboda matsalar wattpad ɗinan ta ɗauki hankalina banyi typing ba, ƴan telegram sunce a turo muku kawai, amma da wuya kujini gobe idan ALLAH ya kaimu zan samu nayi typing ɗin jibi idan munada rabon kaiwa. Gaisuwa ga kowa da fatan alkairi😍😍😘😘.
ZAAFAFAN LITTATAFAI GUDA GOMA da sukazo muku cikin ƙyawawan tsari a baya har yanzu suna nanfa a kasuwa.
SAFIYYA HUGUMA tazo muku da;
ƊAURIN ƁOYE
ALƘAWARIN ALLAH.
HAFSAT RANO tazo muku da;
SAUYIN ƘADDARA
ƊAURIN GORO
MAMU GEE tazo muku da;
BURI ƊAYA
ƘAUNAR MU.
MISS XOXO tazo muku da;
KAIMIN HALACCI
IGIYAR ZATO.
BILYN ABDULL tazo muku da;
WUTSIYAR RAƘUMI...
GUDU DA WAIWAYE....
abin birgewa books ɗinan duk sun wanzune akan farashi mai rahusa, guda goma duka 1k ne, guda biya 500, guda huɗu 450, guda uku 400, guda biyu 300, ɗaya 200 gamai buƙata zai iya tun tuɓar wannan numban domin samunsu a documents dan an kammalasu.
Katin waya mtn za'a turaahi tanan. 09032345899
sai kunma masu tura kuɗi ta bank zaku tura tanan 0225878823
Hafsat Kabir Umar GTB.
Saiku tura shaidar biyanku ta wannan number 0803 081 1300
Sai kunzo😍😍😍😘.
ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻
[12/15/2020, 2:54 PM] HASNA✍🏻: Billy Abdul, [12/15/20, 12:50 PM]
Page 28
................Alhaji babba ya gyaɗama Jawaad kai alamar eh ita. Cike da mamaki Jay ya ajiye kofin hannunsa yana tsatstsare kakan nasa da idanunsa cike da sonjin ƙarin bayani.
Murmushi Alhaji Babba yay masa tare da kamo hanunsa, “Daina tsareni da waɗanan idanun naka ba wani abu bameba, kawai inason sanin dangin mahaifinta ne”. Sassanyar ajiyar zuciya Jawaad ya ɗan sauke, kafin shima ya riƙe hanun Alhaji Babba da ƙyau a cikin nashi, “Baba nima inason saninsu, sonake kawai wannan ƙurar ta lafa itama ta sakejin sauƙine”. Alhaji babba yace, “Kayi tunani mai ƙyau, inason kayi ƙoƙari ka bincika, sannan yaya maganarka da mutanen gidanku? Da kuma maganar shi wanda kasa ya auri yarinyarnan ta wajen Ali?”.
Murmushi Jawaad ya ɗanyi ya ɗauki furarsa zai cigaba da sha, ganin zai basar da zance Alhaji babba yace, “Nasanfa ka jini”. Ƴar dariya Jay yayi yakai kofin bakinsa, “ALLAH ka iya rigima kaima tsohon nan, karka damu ina sane da komai”. “Nasan kana sane da komai Muhammad, sai dai hankalina ya tashi matuƙa jin ba mutumin kirki bane habibun, kajifa wani suna da Nasiru ya kirashi dashi ranar”.
Jay yay murmushi kawai batare da yace komaiba.
Sun cigaba da hirarsu har zuwa ƙarfe tara ya fita, yaso zuwa asibiti, amma ganin dare yayi sai ya haƙura ya nufi gida abinsa. A gate ya tsaya ya tambayi mai-gadi ko gimban ya dawo?. mai-gadi ya tabbatar masa da bai dawoba, ya kira wayarsa kuma gashi tana ring amma ba'a ɗagaba.
Sosai abin ya ɗaurema Jawaad kai, daga baya kuma ya ajiye tunaninsa akan inhar da safe bai dawoba zaisa abi bayansa garin nasu aga ko lafiya?. Da wannan tunanin yay shirin barci ya kwanta.
_________________________________
Su Dady sun karɓi baƙuncin surikinsu habib, duk yanda Dad yaso su Momy su zauna basai sunzo falon baƙiba hakan ya gagara, dole ya barsu sukabi bayansa, ba ƙaramin tashin hankali Shahudah ta shigaba da ganin wanda ake kira wai matsayin mijinta, daka gansa kaga cikakken tantiri marajin magana, cike da isa ya zauna a kujerar da aka nuna masa sai wani cika yake da batsewa.
Ya kafe Aamilah da Shahudah da kallo yana wani lasar laɓɓa tamkar tsohon maye, ko kunyar su Dad bayaji, dama daya shigo babu wanda ya gaida, bama su ishesa kallon arziƙiba.
“Wace cikar tawa anan?” yay maganar cike da gadara. Babu wanda ya tanka masa a cikinsu, sai Shahudah da Aamilah da suka zuba masa wata shegiyar harara. Ya bushe da dariyarsa mara daɗin ji yana faɗin, “Dama ace ana auren yaya da ƙanwa wlhy da duk haɗawa zanyi hhhhh! Dana kwashi gara aradu...” cike da tsiwa Aamilah da tafi Shahudah jin hausa tace, “Uwarkane garan shege mai suffan aljanu.....” wata wuta data gitta ta idanunta mai stars ce ta hanata kaiwa ƙarshe, lokaci ɗaya jinta da ganinta ya ɗauke baki ɗaya ta zube a jikin Dad daya tarota. Babu wanda yaga sanda Ɗan-fir'auna ya ƙarasa gaban Aamilah sai ƙarar maruka sukaji kawai.
A fusace Dad yace, “Kai ƙaramin ɗan tsagera, wanene ubanka da har zaka mararmin yarinya a gabana?”. Kallon dad ɗan fir'auna yay ya watsar, kafin cike da gadara yace, “Sanin ubana a gareka dattijo ai tamkar yankewar numfashinka ne, dama kun kiranine domin kuci zarafina komi? kunga dalla malamai ku bani matata na wuce na fasa zaman....” da sauri Uncle Uwaisu ya taresa cikin lallashi yana bashi haƙuri, amma fir ƴaki sauraren kowa, Aamilah dai ta farfaɗo da ƙyar bayan an zuba mata ruwa, Shahudah na rakuɓe lungun kujera sai tsiyayar da hawaye takeyi jiki na rawa, harga ALLAH tsoronsa takeji, a ranta kuwa ayyanawa take ashe Bilkisu baturiyace, dan ɗan-fir'auna ALLAH ya bashi baƙi, wanda daga gani kasan shaye-shaye ya sake taka rawar gani wajen ƙara masa shi. Da ƙyar suka samu ɗan-fir'auna ya zauna bayan an saka Shahudah da Aamilah sunbar falon, Salman kam yay laƙe kamar baya falon (hege yaga maza🤣😜).
Duk yanda su Uncle Nasir sukaso lallaɓa ɗan-fir'auna akan ya saki Shahudah yace shifa sam baisan wannan zanceba, dan yanzuma da shirin ɗaukar matarsa yazo yana buƙatar abinsa, tunda yana zamansa aka kawo masa tallansu. Har ƙasa Momy ta duƙa tana kuka da roƙonsa amm
Billy Abdul, [12/15/20, 12:50 PM]
a sai dariyar wulaƙanci da cusa haushi yake musu.
“Kungafa kubar ɓata lokacinku akan roƙonama, tayaya kuke tunanin zanyi sake da wannan babbar kaddarar ne haka, yo ko shugaban ƙasa ai nafishi hura hanci yanzu akan wannan cikar tawa, ku manta kawai a saimin royal bed zan kama hayar gida aje aimin jere gobe, babu damuwa idanma kunkai sati danshi shiri wuyane dashi, ko a hotel mayi amarcin satin guda kafin ku kammala surukai..” ya ƙare maganar da miƙewa yay salute nasu zai fice. Da sauri Dad yace, “Nawa kake buƙata a biyaka ka sakarmin yarinya?”.
Tsayawa ɗan-fir'auna yayi, ya juyo yanama Dad wani matsiyacin kallo maiban tsoro, sai kuma ya bushe da dariya tare da dawowa da baya. Yace, “Zan iya amsar kuɗi na saketa pale, tunda yanzu na auri ƴarka ka zama pale ɗina nima, ammafa kasani saina ɗanɗana kona sati ɗayane dan yawuna ya biya, a shiryata da safe nazo na amshi kayata, nanda sati biyu saiku cakemin naira miliyan hansin na baku ƴarku, idan haka bai mukuba kuma banida matsala, iyakaci inta mata ciki duk bayan wata tara ta ringa juyen jajayen ƴan dugwi-dugwi irinta, koba komai na samu surukai masu kuɗi nima nan gaba tunda naga jar fatar ake yayi yanzun” ya wani ɗage musu gira cike da barikanci yay ficewarsa.
Babu wanda bai jiƙe da zufaba a falon, tun fitar ɗan-fir'auna babu wanda ya iya magana sai kuka Momy dake tashi. Salman ya miƙe cikin raɗa-raɗa yace, “Wlhy kuyi ƙoƙari ku biyashi, dan wannan dagani zai iya take mutum ya yanka tamkar ya yanka kazar gidan gona, ku rufa mana asiri dad dan kuwa su momy sun kwaso mana bala'i, wlhy barin ƙasarnan zanyi idan an gama watandarku na dawo zaman gaisuwa”. Ya ƙare maganar da ɗai-ɗai yana kallon ƙofa, da gani kasan a tsorace yake (Kana bani yaji Salman🤣, lusarin banza😠).
WASHE GARI.
Dad na zaune a harabar gidansa abin duniya ya taru ya masa yawa, tunda ya dawo sallar asuba bai iya shiga cikiba, a daren jiya da ƙyar suka samu Shahudah tai barci, dukta gama fita hayyacinta.
Baƙon da aka turo daga masarautane ya samu isowa, ya ƙwanƙwasa gate mai gadi ya leƙa, sai da suka gaisa sannan yace, “Magatakarda ne daga masarautar gagara badau, an aikoni domin isar da saƙo ga Alhaji Ali ko yana nan?”. Mai-gadi yace, “Ƙwarai yana nan, sannu da zuwa bara a sanar masa”.
Sai da baba mai-gadi yay sallama sau kusan uku sannan Dad ya jisa, bai amsaba sai zuba masa idanu da yayi. Baba mai-gadi yace, “Alhaji baƙone wai daga masarauta”. “Masarauta kuma? Ni miya haɗani da masarauta malam Amiru?”. “To Alhaji wlhy ban saniba, yadaice daga can yake”. Da hannu kawai Dad yay nuni alamar baƙon ya shigo. Baba mai-gadi ya koma domin shigo dashi.
Sai da baƙo ya zauna a kujerar robar da baba maigadi shima ya ajiye masa sannan suka gaisa da Dad, cikin nutsuwa magatakarda ya korama Dad bayani akan gimbiya ta bada umarnin Bilkisu zata koma masarauta da zama har sai ranar tarewarta gidan mijinta. rasa abinda ma zaice Dad yayi, sai tsurama magatakarda ido yay kamar zai haɗiyeshi dasu. Har magatakarda yaymasa sallama ya tafi bai dawo hayyacinsa ba, sai faman juya takardar hannunsa da magatakarda ya kawo yakeyi, shi yanzu abin tambayarsa anan Bilkisu ce takai ƙararsa masarauta kokuwa Jawaad? Kai yasan halin Jawaad da shegen taurin kai, bazai taɓa kai magana masarauta ba dan tsaurin idonsa bazai barsa ganin ya gaza ba. To amma bai zaton Bilkisu nada irin wannan wayon, kuma itada takema kwance a asibiti. Gaba ɗaya ransa ya kuma jagulewa, cike da sassarfa ya tashi ya shige ciki.
★★★★★★
Jawaad kam koda ya gama shirinsa na office ya fito sai ya iske Gimba bai dawo ba, mamaki ya kuma cikashi, dan jiya bayan ya dawo ya kira Number gimba har sau biyu kafin ya kwanta amma ba'a ɗagaba, yanzu kam yafara tunanin babu lafiya, akwai wani saurayi a gidan da aikinsa kawai kula da flowers ɗin gidanne, garinsu kusada garinsu gimba yake, hakan yasa Jawaad ya kirashi yanama tsaka da aikinsa na bayin fulawar. Durƙusawa yay yana gaida Jawaad, Jawaad ya amsa da masa nuni ya tashi. “Banace ka dainamin irin wannan gaisuwarba Balarabe, kadaina min wannan durƙuson kamar
Billy Abdul, [12/15/20, 12:50 PM]
wani mai neman gafara kaji”. fuskar balarabe ɗauke da murmushi yace, “Alhaji nagode sosai, amma nariga na sabane, koba aiki nake ƙarƙashin kuba aika girmeni nesa”. Girgiza kai kawai Jawaad yayi, ya ciro kuɗi a aljihunsa ya miƙa masa 3k, “Balarabe ajiye aikinnan naka zakai dan ALLAH kaje garinsu Gimba ka ganomin ko lafiya yake? aikasan garin ko?”. Da sauri balarabe yace, “Eh Alhaji, ai daga garinsu zuwa namu da ƙafama muke zuwa, kuma har gidansa na sani tunda naje sunan yaronsa da aka haifa masa na ƙarshenan mai sunanka”. “Okey Alhmdllh, kayi ƙoƙari kaje yanda zaka dawo da wuri, bani number ka na kira kaga tawa, daka isa kasan halin da yake ciki ka kirani na sani kafin ka juyo”. Cike da girmamawa balarabe yake sauraren number da Jay yake faɗo masa yana sakawa a wayarsa nokia, bayan ta cika ya kira shima jay yaga tashi.
Mota Jawaad ya shiga, yau da kansa