Showing 249001 words to 252000 words out of 261165 words
Chapter 84 - Kwai Cikin Kaya Part 2 Hausa Novel Complete
duk ƙwalisarnan yanzu babu ita, babu Dad babu dukiyar da ake taƙama da ita.
A ɓangaren rose kam ta buga ta buga taga babu ci, mai shiga tsakanin soyayyar Jawaad da Bilkisu sai dai ALLAH. Babu kalar ƙulle-ƙulle da munafurcin da bataima bily ba a station ɗin sai dai babu tasiri, daga ƙarshema da Jawaad ya ganota sai yasa akai mata transfer waje mai nisa a tsakaninsu. Wannan abu ya sakata jin takaici harda kukanta kuwa, ballema randa taji anƙarama su bily girma da ƙyaututtuka susucewa tayi duk da itama harda ita, a ganinta bily batakai ta kamotaba, amma ya ta iya da abinda yafi ƙarfin wuta inji kishiyar ƙonanniya. tana kewar jawaad ainun. dan koba komai idan tana ganinsa kusa da ita tana ɗanjin sassauci.
__________________
ZAFAFA 2021
_______________
Masoya naku taurarinfa sun sake dawowa da sabon salo a 2021.
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO
TEAM#ZAFAFABIYAR🔥
★★★★
A gidan Iyayen gayya kuwa ai ba'a cewa komai, cikin Bilkisu da har yanzu gata nanneda ya fito sosai, dan yana cikin wata na bakwai. Tattali sosai take samu a wajan Jawaad da duk ahalinsuma baki ɗaya, inda aka maido mata Nabeelah gidan tana tayata zama, gefe kuma tana shan soyayyarta da masoyinta Anuwar.
Faruwar wannan al'amari ya sake maida bily miskilar gaske, dan ko Jawaad ɗin idan bata gadamaba saita yini batai masa maganar data zarta gomaba. Ta ƙara ƙwazo akan aikinta fiye da zaton mai hasashe, musamman ma da bayan lafawar abubuwa suka samu ƙarin girma itada duk jami'an da sukaje wannan aiki a waccan rana. Saboda cikinta dai bata fita operation, sai dai tayi ayyukan cikin gida kawai daga office. A gefe kuma tana sake samun ƙwazo da horo a wajen mijinta, wanda a kullum cikin sake nuna mata ƙauna da soyayya mai tsanani yake. Sam baison yaga tashin hankalinta ko damuwarta balle fushinta. Shidai fatansa ALLAH ya sauketa lafiya ta haifo masa little Beejay kamar yanda yake faɗa a kullum.
Cikin Bilkisu nada watanni taƙwas Jawaad ya sakata ɗaukar hutun dole, acewarsa saita haihu ƴarsa tayi ƙwari sanan. Aranar da hakan ta faru harda kukanta, amma sai yaƙi kulatama yay kamar bai jitaba, sai Anuwar dake mata dariya shi da Nabeelah suka koma lallashinta da lallaɓata.
Tana shiga watan haihuwa Ummah babba tace zata maidata can gidanta, dan bazai yuwu a barta ta zauna nan babu babba tare da ita ba. Babu kunya Jawaad ya murje idanu yace shifa bai yardaba, idan dan babbane ya amince asamo wata tsohuwar ta zauna da ita, amma shi bai yarda matarsa tai nesa da shiba gaskiya.
Ranar Bily ta tasashi gaba ta dinga kwasar dariyar mugunta, dan kawai ta rama abinda yay mata na sakata ɗaukar hutu a office saita shiya kaya kusan akwai huɗu na tafiya gidan Ummah babba, aiko ya murje ido ya balbaleta da masifa kamar zai cinyeta ɗanya jagab🤣.
Aifa ganin yanda ya harzuƙa dole Ummah babba ta janye ƙudirinta, aka samo wata dattijuwa zata zauna dasu, ga kuma Nabeelah da Anuwar tare dasu. Ummah ƙarama da babba kusan kullum saisunje ganinta. Hakama maman Amina, dan cikin na shiga wata tara sai ya ƙara girma kamar wadda zata haifa ƴan biyu.
★★★★★★
A wannan ɗan tsakanin akasha bikin su Amaturrahman suma, inda Bilkisu ko sau ɗaya bata samu leƙawaba saboda cikinta, Jay yace idan ta haihu taje taima Ummu ALLAH ya sanya alkairi.
Bayan anyi biki an shashshare Umm-Anum da itama ta halarta da Aunty Mahfuzah sukazo nan dansu gaisa da Alhaji babba. Randa suka cika kwana uku gidan Alhaji babban sai sukazo nan gidan Jay duba bily, danshi kullum yana zuwa can ya gaidasu, itako saita waya tunda bata fita sam.
Ta taresu da tsantsar farin ciki, inda sukuma suketajin tausayinta da mata fatan sauka lafiya. Su Anuwar ne dai ke amsawa, itako kanta na a ƙasa dan kunya.
Anuwar ya kumbura fuska yana kallon Umm-Anum daketa mammatsa ma bily hannunta daya kumbura. “Umm-Anum gaskiya nimafa amin aure, so kuke sai little tazo duniya taga Abbanta tuzuru”.
Dariya duk suka sanya ƴan falon, banda Jay dake zaune gefen Umm-Anum yana latsa waya, yadai ɗan ɗago ya kalli Anuwar ɗin ya zuba masa harara ya ɗauke kansa. Sai da suka gama dariyarsu sannan ya sake kallonsa fuska babu wasa. “Kai baka da kunya ko......?” “A'a yayanmu nifa wlhy gaskiya na faɗa, yanzu dan ALLAH little zataji daɗine idan aka haifota ta iskeni babu aure, ita dai ai nasan tanason iske kawunta a dattijonsa ko”. Kai kawai Jay ya girgiza ya sake ɗauke kansa, dan indai shaƙiyancine akazo wajen Anuwar kowa ya shafama kansa lafiya, duk masifarsa kuresa yake shima har yagaza cewa komai.
Umm-Anum da itama ke dariya yanzun tace, “To ni miye nawa, aiga mai maka auren nan a gabanka” tai maganar tana nuna Jay. Tasowa yay ya tsuguna a gaban Jay ɗin yana wani marairaice fuska. “Yayanmu dan ALLAH ka aurar dani kar a haifi little ina a ƙasa” yay maganar cikin harshen nasara da haɗawa da ƴar hausar daya fara kowa wajen Nabeelah”. Kunnensa Jay ya kama ya murɗa da ƙarfi, aiko a take yahau roƙo daban haƙuri. su Bily kuma namasa dariya.
Cak ta tsaya daga dariyar tata jin bayanta ya riƙe, ta shiga yamutsa fuska tanason fiskewa amma hakan ya gagara, kamar wasa saiga ƙaramar magana ta zama babba, dan kuwa kafin wani dogon lokaci naƙuda ta tashi gadan-gadan, dama a gaba ɗaya kwanakinan naƙudar tsaye takeyi.
Cike da rikicewa Jay ya sugunmeta daga ita har cikin sai mota, Anuwar ya jasu sai asibiti.
BAYAN AWA BIYAR.
Bayan gumurzu da wahalar da bily tasha a ɗakin haihuwa ta sunkuto ɗiyarta mai kama da ubanta sak, dan yarinyafa tun bata gama hucewaba kamanin Jawaad ɓaro-ɓaro a fuskarta, sai dai kalar fatarta tazo daɗan duhu saɓanin yanda ake haihuwar jarirai farare tas.
Ai murna wajen wannan ahali ba'a magana, a take Jay ya tauna dabino ya zuba mata a baki tare da miƙama Anuwar yay mata huɗiba da suna BILKEESU MAI GADON ZINARI, Alƙawarin ALLAH ya cika, Jawaad Abdul-aziz yousif ya zama Ɗan BILKEESU, mijin BILKEESU, baban BILKEESU, saura kakan BILKEESU🙄😜🤣lol.
A ranar aka sallami mai jego da jinjirarta dan suna cikin ƙoshin lafiya, bakin Jay ya kasa rufuwa, ya murje idanu sai kulawa yakebama matarsa da ƴarsa a gaban kowa.
Washe gari ƴan barka suka fara ɓarkowa ta ko ina, ciki kuwa harda Shahudah dataita kuka dan damuwa, yayinda takejin zafi da tsanar bily har cikin ranta. (Shiriyar wanifa sai ALLAH yaso, bashi yuwuwa lokacin damu mukaso😫).
Yah Qaseem ma ya kawo ƴar Aminatunsa, hakama matan su Jabeer dasu Ummie da abokan aikinsu harma da ƙawayen makaranta. Bily kam tayi goshi, kaga ƴar gatan dangi. Baba ƙaura ma daya koma daji abinsa tuni sai gashi yazo, dan yace yafi son zaman can, alkairan da manyan ƙasa sukai masa dasu Jawaad duk tattarawa yay ya bada gidan marayu, acewarsa sun fishi buƙata, sai dai ya riƙe waya suna gaisawa da abokan arziki irinsu jay, tananma ya sanar masa da haihuwar anayinta.
Su Umm-Anum basu komaba har saida akai suna, inda kowa dai yasan sunan jinjira BILKEESU. Su Firdausi duk sunzo sun taka rawar gani, hakama abokansa su Abbati na ƙauyensu, inda ɗunbin jama'a sukai masa alkairi da dama wanda shi wasuma bai sansuba.
Amaryar jego tasha gayu harta gaji, koni dai ta gama burgeni aradu🤗, balle kuma ubangayya Jay. Ansha hotuna inda naita hango fans cikin ƴan taron suna🤗. (Kunyima Jay halacci gaskiya😘😘😍🤣, dan yau Ƴan Team Beejay da team Qaseem da team Shahudah duk sun dunƙule waje ɗaya😋☺😉💃🏻.
★★★★★
Ansha hidimar suna kowa ya gaji, wasuma har sunyi barci. Da ƙyar na iya miƙewa na shiga bayi dan na samu na watsa ruwan da Anum ta haɗamin. ita kuma na barta tare da Little Bee. Ban wani jimaba, da dai na samu jikin ya saki na fito.
Tsaye nai a ƙofar bayin ina kallon wanda banyi zaton ganiba, shima juyowa yay yana kallona fuskarsa ɗauke da murmushin nan nasa mai tsada dasai ya gadama yake yinsa. “Umm-Bee ƙaraso mana”. Murmushi nayi na cigaba da takawa a hankali zuwa garesu, hannuna dake da damshin ruwa ya kama ya zaunar dani gefensa. Na ɗan sauke ajiyar zuciya ina kwantar da kaina gefen kafaɗarsa. “Sweet Love bakayi barciba daman?”. Fuskata ya shafa yana sake rungumoni jikinsa sosai. “Nakasa barcin Miemaa”. Idanuna na ɗaga da sauri ina kallonsa, “Miyasa hakan Dear?”. “Saboda MIN QALB (Littafin Mamu gee na zafafa 2021) ɗina mana”. Na ɗan lumshe idanu na sake buɗewa a kansa, cikin sake sanyaya murya nace, “Minene shi?”. Nunani yay tare da ƴarsa yana murmushi. Nai ƴar dariya da komawa jikinsa na kwanta ina shafa kan baby bee daketa barcinta hankali kwance, dan tasha wankane wajen inna tsohuwa yanzu babu jimawa.
“Wai kinsan miya faru?”. Kaina na girgiza masa ina cigaba da shafa mata kai. “Ummuna tafa dage tare zaku tafi, nifa gaskiya gaskiya.......” kallonsa na sakeyi da sauri cikin ɗan zaro ido, sai ya fasa faɗa ya ɓata fuska kuma. Ƙyalƙyalewa nai da dariya da sumbatar kumatunsa ina faɗin, “Boss na Miemaa”. Ya ranƙwashi kaina yana hararata, “Oh hakama zakice ko? To nama fasa babu inda zaki, gara ki zauna nanda wata biyun ki sake ɗaukar wani cikin”. Idanu na zaro ina buga ƙirji, “Dan ALLAH rufamin asiri sweet Luv daina min wannan fatar kaji”. Dariya sosai ya sanya, ya kwantar da Little Bee tare da jawoni jikinsa muka faɗa saman gadon yay min runfa da jikinsa. Kallon juna muke cike da shauƙi babu mai ko ƙiftawa, sai da naji bakinsa cikin nawa na dawo hayyacina da sauke nannauyar ajiyar zuciya, son tureaa nake amma yaƙi bada damar hakan, na rinƙa dukan bayansa amma bai barniba saida yayi san ransa sannan ya sakeni ya miƙe yana dariya damin gwalo. “Dama abinda ya kawoka kenan ai” na faɗa iana ɓata fuska kamar zanyi kuka. Gwalo yaymin dai-dai zai fita yace, “Eh naji ɗin”.
Fariya sosai nayi ina girgiza kai, na jawo ɗiyata na rungume ina sumbatarta dajin kamar na haɗiyeta na huta dan ɗunbin son da nake mata.
BAYAN WASU SHEKARU.
Yarane kusan uku keta wasan basket ball a madaidaicin filin wasa dake a cikin wani ƙaton gida mai ɓangarori kusan huɗu. ina tsaye a wajen kusan mintuna huɗu saiga mata da miji sun fito daga ɗayan ɓangare na gidan, ba kowa bane face Anuwar da Nabeelah, suma suna sanye ga j.c. ihu yaran suka fara, biyu na kiran Abbah! Abbah! Abbah. Biyu na kiran Mamma! Mamma! Mamma!! Cikin ɗaga hannu irin na jinjina da ɗokin isowar abokin wasa. Anuwar yaja ƴan team ɗinsa, Little Bee, da ƙaninta na biyu Abdul-aziz suna kiransa (Awwab). Nabeelah kuma taja nata ƴan team, ƙanwar Little bee mai bimata Maryam suna kiranta (Khairiyya) sai yaron su Anuwar ɗin mai sunan Jawaad, suna kiransa (Khalifa). Wasansu suka fara cike da nishaɗi, basufi mintuna talatin da farawarba sukaji horn. Maigadi dake kallonsu daga gate yay saurin zuwa ya buɗe. Farar mota tas ta shigo gidan wadda Bily ke mazaunin driver cikin kayan aiki, Jay na gefenta shima sanye da suit yanata faman danne-danne a laptop.
Da gudu yaran suka nufi motar suna faɗin, Abie! Miemaa! oyoyo. Bily dake murmushi ta kalli Jay shima ya kalleta, kafin su maida idanunsu ga yaran nasu dake tunkarosu. Awwab da Khairiyya suka nufi sashen da bily take suka buɗe mata, Little Bee da Khalifa kuma Jay suka buɗemawa. A tare suka fito fuskarsu ɗauke da murmushi. Jay ya ɗaga khalifa tare da sumbatar kumatumsa, shima yaron ya sumbaci Jay ɗin yana dariya da faɗin, “Abie i love you”. “I love you too second Jawaad” ya faɗa yana lakace masa hanci, kafin ya duƙa ya sumbaci Little bee ƴar kimanin shekaru goma itama. “Little BeeJay ɗina”. Fuskarta washe da murmushi sak irin na Bily tace, “Sweet Abie na i love you” tai maganar da sumbatar hannunsa itama. Ta matsa jikinsa ya rungumeta ta gefen hannun damarsa, na haggun kuma yana ɗauke da khalifa.
Acanma dai Awwab da khairiyya suna maƙale da Bily, saida suka gama ɗokin ganinta sannan suka dawo wajen Abie, ya sumbacesu suma a kumatu kamar yanda yayma su Khalifa. Kafin su Anuwar su ƙaraso suna musu barka da dawowa.
Cikin tsokana bily tace, “Iyayen da basa girma da shiriritar ƴaƴansu”. Dariya Anuwar da Nabeelah sukayi, Jay dake murmushi shima yace, “Karki ja mana yanda muka dawo a gajiyanen yanzu su tara mana ciwon kai suda ƴaƴansu, zomu gudu muje mu hutama ranmu princess”. Cikin dariya Anuwar yace, “Idanma kun gudu binku zamuyi, dan yau a falonka aka haɗa dinner. Idanu Jay ya zaro sosai. sai kuma ya ɓata fuska yana kallon Bily cike da langaɓe kai. “Miemaa kinajifa, nidai ALLAH ban yardaba hutawa zanyi”. Kafin bily ta bada amsa yaran suka shiga ihu da tsalle suna faɗin suma basu yardaba a falon Abie zasuyi dinner yau”.
Ƙwafa Jay yay yana kallon Nabeelah, “Auta kece kika haɗamin wannan aikin ko, maganar gaskiya ayi hutu na tarkataku ku tafi Saudia wajen Ummuna muma muɗan huce gajiya da matata a gidanga. A waje dambe da ɓarayi a gida dambe da iyayen yara da yaransu”.
Sosai Nabeelah da Anuwar ke dariya, Nabeelah tace, “ALLAH babu ruwana, Abban Little ne”. “Kai ko?”. Jay ya faɗa yana kama kunnensa. “ALLAH da zafi Yayanmu” Anuwar ya faɗa cikin marairaicewa yana riƙe hannun Jay. Yaran suma duk sai suka marairaice suna faɗin, “Sorry Abie Abbanmu yanajin zafi sosai”.
Dariya Bily takeyi. Jay dake murmushi ma ya saki kunnen Anuwar ya kama hannun matarsa suka shige dan anfara kiran sallar magrba. Kayansu yaran suka kwasa daga mota tare da tsarabar da aka yo musu sukabi bayansu. Anuwar da Nabeelah ma suka nufi ɓangarensu dansu watsa ruwa tu fito.✍😭🙏🏻
ALHAMDULILLAHI ALA KULLI HALIN.
Na godema UBANGIJIN al'arshi daya bani ikon kammala wannan littafi daya jani dogon zango, kuskure. dana tafka a cikinsa ALLAH ka yafeni, abinda nayi dai-dai ALLAH ya haɗamu a ladan daku masoya da mukai tafiyar tare.
Nagode, nagode, nagode irin trillions trillions trillions ɗinan da haɗin kai da ɗunbin soyayyar da kuka nunamin akan wannan littafi. Alkairin ALLAH da rahamarsa su tabbata a gareku a duk inda kuke.
Duk wanda na ɓatama rai a yayin rubuta wannan Littafin ya gafarceni dan ALLAH, nima kuma na yafema duk wanda ya ɓatamin😭🙏🏻😍😍😍😘😘.
inajin kewarku tun yanzu, sai dai kuma nasan insha ALLAH zamu haɗu a ZAFAFA 2021🤗.
Masoya na Telegram, Wattpad, Facebook, WhatsApp dama duk wata manhaja da wannan littafi ya leƙa ina muku fatan alkairi da sake miƙa godiya a gareku.
Zakuga ba'a sake kawo maganar Jazuga da gidan ƴan lesbians ba. Haka rayuwa take, wani yakan shigo rayuwarkane bisa ZAREN ƘADDARA bawai sai kaga wani abu daga gareaaba daga baya, mutane da yawa sukan shigo rayuwarmu su taka rawa, walau alkairi ko sharri, daga baya kuma saisu ɓace mana ɓat komu mu ɓace musu. Alka gafarta mana😭🙏🏻.
Sai mun haɗu a ZAFAFA BIYAR 2021, karku bari a baku labari, dan aumafa sunzo da ɗunbin sabon salo mai birgewa ta musamman, bazance muku komaiba akai sai mun fara sakin ɗanɗanon free pages😋 zaku tabbatar da hakan. Masoya ku garzaya kar a baku labari, dan idan babuku muma babu mu ai😪🚶🏻.
Taku Bilyn Abdull ce🤗.
Insha ALLAH bayan sallah sannan an gama zafafa zamu sake dasa free book mai daɗi😉💃🏻😍😍😍
Ina fatan yanzu kowa ya fahimci ƙaddarar jini a cikin jini da zai zama jini🤗.
Shahudah, Bilkisu, sun haɗu akan son abu guda, Jawaad, wanda kuma ya kasance jininsune su duka. Ga kuma
Ya rabbi ka gafartama iyayenmu damu baki ɗaya🙏🏻😭
[2/17, 9:22 AM] HASNA: __________________
ZAFAFA 2021
_______________
Masoya naku taurarinfa sun sake dawowa da sabon salo a 2021.
Hafsat miss xoxo🥰
KIBIYAR AJALI......!
(Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗
Mamu gee🥰
MIN ƘALB!!😋🤗
Hafsat rano🥰
ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗
Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗
Bilyn Abdull🥰
SARAN ƁOYE🤗😋
Duka akan farashi mai rahusar gaske.
Kamar haka👇🏻💃🏻
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇
ACCOUNT NO 0812652655
ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO
BANK NAME: ACCESS BANK.
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇
0903 234 5899
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇
09033181070
Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne
SABUWAR SHEKARA
SABON SALO
TEAM#ZAFAFABIYAR🔥
Page 62
....................Wani irin tsuma jikin Jay ya keyi irin wanda kowama bai taɓa ganiba, idanunsa sunyi masifar rinewa abun tsoro, duk wata gaɓa ta jikinsa ta sake buɗewa, ƙwanjinsa ya kumbura hakama jijiyoyin kansa dana dukkan sassan jikin nasa. Da sauri Alhaji babba daya fahimci komai zai iya faruwa a wajen dan yasan wanene jikansa da zafin zuciyarsa. yay azamar riƙo Jay ya rungume a jikinsa, duk da neman ƙwacewa da ya keyi bai sakesaba. sai ma taimaka ma Alhaji babba da Uncle Sulaiman yay suka danne Jawaad ɗin yanda bazai iya tashiba duk yanda yaso hakan. Kuka kawai ya fashe dashi dan zuciyarsa tai masifar kaiwa maƙura, Alhaji babba ma kuka ya keyi. ya kalli su Dad yana faɗin, “Amma Ali ka cuceni, yanzu kunsan da wannan zaluncin da kuka aikata amma harka iya zuwa neman auren Rahmah a wajena?”.
Cike da tashin hankali da tsoron Jawaad dake